Friday 27 October 2017

MIJINA SIRRINA.. 71-END

[10/2, 7:47 PM] Bint Khalil: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
    _(Labarin k'auna)_


    *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*
  _Home of expert & perfect writers_


         *71*

aishaummi.blogspot.com


   *S*ake murtuke fuska tayi tana kallonshi ta cikin dan hasken da yayi saura acikin dakin,

"Baby akan wannan maganar fa ina iya batawa dake garama tun wuri ki bari.."

"Kaga ni ka kyaleni bacci nake ji.."

"Dama zan kyaleki kiyi bacci amma sai nagama yimiki kashedi da gargadi akan wancan mutumin..."

Kwace jikinta tayi ta koma ta kwanta gamida juya masa baya,

Duk da adan cikin fushi yake hakan bai hanashi rungumeta ta baya ba bayan ya kwanta,

Da asuba ta rigashi tashi bata tasheshi ba sai bayan ta iyo alwala domin ka'idane tare suke yin salla, tashinshi taje tayi,tashi yayi yana kallonta yana dan harararta alamun bai huce ba daga fushin da yayi adaren jiya,

Yi tayi kamar bata ga hararar da yake aika mata ba, sauka daga kan gadon yayi ya nufi toilet yana fitowa yaganta akwance taja bargo ta lulluba,

Bargon yaje ya yaye yana kallonta,

"Sallar fa?..."

Dan juyi tayi sannan ta waiwayo ta kalleshi,

"Kayi sallarka kai daya ni banayi.."

Wata hararar yasake jifanta da ita baice komai ba yatafi kan dadduma yatada kabbarar salla,

Bayan ya idar ne yayi addu'o'i kamar yadda yasaba sannan yatashi yakoma kan gadon,

"Gaskiya ni kin gama dani gaba daya, wai dama kin san yau zaki tashi da wannan abun shine zaki sakani agaba jiya da masifa ki hanani samun farin ciki, abu kadan ki wani hade rai kina ciccin magani dan kawai anfadi gaskiya akan wannan...."

"Yau kuma da abinda katashi kenan?? Lallai" tafada tana sake gyara kwanciyarta,

"Ehhh da abinda natashi kenan"

Shiru tayi masa ta lumshe idonta kamar mai yin bacci, tana jinshi sai faman juyi yake har gari yayi haske tun tana jin motainshi har bacci ya dauketa,

Ganin tayi bacci yasashi komawa falo ya kunna labarai yana gani anan shima baccin ya daukeshi bashi ya farka ba sai misalin karfe 8 nasafe,

Motsinta yajiyo acikin kitchen alamun tana hada abun karyawa, tashi yayi yabita zuwa cikin kitchen din ahankali ya sadada yaje ya rufe mata idanuwanta,

"Malam meye haka?"

Murmushi yayi ya matsa kusa da ita tareda kallon fuskarta, tasha kwalliya sosai sai kamshi take zubawa, tana sanye da atamfa maroon mai zanen hang bag ajiki,

"Kinyi kyau amaryata..."

Baki ta turo batare datace komai ba,

"Baby wai maganar jiyanne har yau bata wuceba, kinga fa sabuwar wayar da na siyo miki can har yanzu baki dauka ba idan bakya so ki fada min sai inkaiwa budurwata..."

Jin abinda yafada daga karshe yasata hada girar sama data kasa sannan tabashi amsa,

"Ka kai mata nima mijina zai siyo min idan nakoma gidanshi..."

Bai san lokacin da yakaiwa bakinta damka ba,

"Kinada wani miji ne bayan ni, har alahira nine mijinki bama a duniya ba..."

Ture hannunshi tayi tana kallonsa,

"Sakar min bakina,karka sake matse min baki tom.."

"Koma dai me zakice ki fada amma keda kabiru jagwal sai kallo"

Yafada yana kokarin barin cikin kitchen din, har yakai bakin kofa yasake waiwayawa,

"Kallon ma ko ahanya kuka hadu ya kalleki Allah ya isa tsakanina dashi.."

Karasa ficewa yayi daga cikin kitchen din ita kuma taci gaba da aikinta acikin zuciyarta tana cewa,

"Kaji dashi dai sarkin kishi kawai.."

K'arfe 9 daidai tagama kammala hada breakfast din dan haka ta kinkimo ta nufi kan dining,

Zaune ta sameshi akan dining din yana hada mata sabuwar wayar da yasiyo mata, daga ganin wayar mai tsada ce domin tahango tambarin kamfanin HTC ajiki,

Kalar wayar golden ne yar shafal shafal kalar ta mata amma kuma katuwa ce ba canba,

Zama tayi akujerar dake kusa dashi tana kallonshi sakamakon kamshinshi da yacika kofofin hancinta, ba karamin kyau yayi ba awannan lokaci domin pink din riga yasa ta polo da bakin trouser, sumar nan tashi tasha gyara sai kyalli take, ya daura agogon silver ahannunshi na hagu,

"Baby ga wayar zan jona miki ita a charge.."

Bai jira amsarta ba yatashi zuwa socket yajona ajiki ya dawo wurinta lokacin har tasoma kurbar tea din data hada,

Daukarta yayi cancak daga kujerar datake ya maye wurin tareda dorata asaman cinyarshi,

"Wannan fushin dai da kiketa yi dani sai kin dainashi ayau..."

"Fushi ai kai kasiya.."

"Nawa na siya? Fada min inji"

Yace da ita yana zame dan kwalin dake daure akanta,

"Ya zaka cire min dankwali na? Kasan kuwa dadewar da nayi agaban mirror kafin indaura shi?"

"Zanyi miki wanda yafi wannan.."

"Tayaya?"

"Zaki gani ai.."

Gashinta yafara sinsina,

"Serious baby yakamata ki daina fushin nan dani haka karkisa inshiga wani hali.."

Tureshi tasoma yi saboda jin yana niyyar hada bakinshi da nata,

"Ni kabari kar kasa tea dina yahuce.."

Baiyi magana ba wayarshi tafara ringing, karkacewa yayi ya cirota daga aljihunshi yana kallon screen din wayar, ganin sunan zee yasashi kallonta yana murmushi, bai dauki wayar ba ya ajiyeta akan table din dake gabansu,

"Ni ina nawa tea din? Ko tare kika hada mana.."

"A'a.." Tabashi amsa,

Wayar tashice tasake daukar kara,

"Kinga ke kin sameni sai faman wahalar dani kike amma ga wata can agefe tana son samuna domin tabani kulawa.."

Baki ta zumbura cikeda takaici ta kalli wayar tashi nan taga sunan zee baro baro,

"Ko zaki daga kuyi magana?"

Ko kallonshi batayi ba ta juyar da kanta, shi bai son yayi laifi awurin gimbiyar tasa shiyasa ma yaki daga wayar daga karshema kashewa yayi gaba daya ya ajiyeta,

Tea dinta ya dauka ya kurba, ya kula tunda yayi mata maganar zee ta sake tunzura, dan haka har suka kammala bata sake cedashi ko uffan ba,

Tana jikinshi ya dauketa zuwa falo,

Kallonshi tayi saboda jin yafara yimata ajiyar zuciya akunne,

"Lafiya..?"

"Itace ta kawo haka.." Yabata amsa, hannunshi ta buge daga kan kirjinta,

"Meye haka? Baby dan Allah kibari"

"Ni bana so.."

"Ni ai inaso.."

Harararshi tayi shima ya rama amma tashi awasance yayi,

"Bari idan andan jima zamuje kiga motar taki kinji, uhmmm baby.."

"Banjiba.."

Gwalo yayi mata,

"Duk abinki dai nine nan..."

"Bakai bane..",

"Wallahi nine kuma bari ma kiji, idan kika kara ambatar sunan wannan..."

Murtuke fuska tayi ta katseshi,

"Amma dai kasan ko babu maganar su fadeela yaya kabeer dan uwana ne najini dan haka babu mai rabani dashi..."

"Allah ya isa idan kika kara yimin maganarshi..."

Hawaye yaga tafara yi,

"Amma ai kaine kafara ko, shine sai yanzu nikuma zaka hanani.."

Rungumeta yayi yafara lashe hawayen nata dake silalowa bisa kuncinta,

"Yi hakuri baby, nine ko? Yi shiru, mubar maganar kinji..."

Rarrashinta yaci gaba dayi bai barta tasake yin magana ba har tsawon wani lokaci,

Zamewa tayi daga jikinshi ta tashi,

"Bari naje nagyara maka bedroom dinka nagyara ko ina shi kadai ne kawai ban gyara ba.."

Gyara kwanciyarshi yayi yazuba mata fararen idanuwanshi mayalwata masu dauke da bakin yalwataccen gashi,

"To sai kin dawo..."

Mikewa tayi ta nufi dakinshi mintuna kadan sai gata tafito tana kallonshi,

"Haba didi,Kaine kuma mai aikin gidan yanzu?"

Murmushi yayi ya kalleta,

"Meya faru?"

"To naje zan gyara naga already har ka gyara..."

"To kuma menene baby? Rage miki aikin nayi fa.."

Juya mishi baya tayi,

"Nidai kadaina yimin irin wannan, duk wani aiki idan kaga banyi ba kafin nafarga kayishi, ai sai inzama marar tausayi, bayan kafita ka nemomin abinda zanci kuma sannan harda su aikin gida"

Tashi yayi yakarasa inda take ya rungumeta ta baya,

"Baby wallahi ni ban dauki hakan amatsayin wani abu ba, ahar kullum ina fada miki na daukeki ne a matsayin abokiyar rayuwa bawai baiwa ba, wallahi idanma akwai abinda yafi haka zan iya yimiki saboda bazan iya kwatanta miki matsayinki agareni ba, wani irin sonki ne Allah ya jarrabeni dashi..."

Jin alamun saukar kwallarshi akan kafadarta yasata juyawa tana kallonshi kumatunshi ta fara shafawa,

"Didi na, nima ina sonka, ba son maso wani kakeyi ba, kadauka aranka cewar ban taba son wani da namijiba sai kai, bana ganin ko wanne da namiji sai kai kadai..."

Murmushinshi mai tsada taga yayi mata kafin yadagata sama yafara juyawa da ita, gaba dayansu shida ita dariya sukeyi, yau yana cikeda farin cikin da bai taba yin irinsa ba,

Sauketa yayi yana rikeda kugunta,

"To saura ni, nima adagani.."

Yafada cikin shagwaba, hannayenta tasa wai zata dagashin amma maimakon haka sai ji tayi sun fadi akan center carpet din dake shimfide afalon,

Dariya suka fara yi babu kakkautawa,

"Wai dama babyn tawa bata da karfi?"

"A'a inada shi"

"Gashi kuwa kin kasa daga mijinki.."

Hannunta yaja suka mike tsaye,

"Dauko gyalenki muje yawo amotarki.."

Fuskarta dauke da farin ciki ta shiga bedroom dinta ta ciro mayafi da takalmi kalar kayanta tafito bayan ta fesa turare,

Afalo ta sameshi yana kunna wayarshi wadda yakashe dazu,

"Baby anya kuwa fitar nan zata yiyu?" Yafada idonshi akan screen din wayarshi,

"Meya faru?"

"Wani kamshi naji Wanda yatayar min da..."

"Dan Allah kayi hakuri muje mudawo.." Tafada tana kamo hannunshi,

"Gaskiya dakyar, kar muje mutafi nutsuwata ta tafi atsakiyar titi kinga ke kuma ba driving kika iyaba"

Kallonshi tayi bayan tadago fuskarshi,

"Wai dagaske kake ne?"

"Au da dawasa kika dauka? Bari dai kawai nayi ganganci nadaukeki mutafi idan kuma ansamu matsala shikenan asan yanda za ayi"

"Bama wata matsala da za asamu.."

Jan hannunshi tayi suka fita hannayensu sarke cikin juna, saida suka fara zuwa suka gaida hajiya sannan suka wuce wurin motar tata, kusan suman tsaye tayi saboda ganin haduwar motar, ko da wasa bata taba kawowa zata mallaki irin wannan motar ba,

Motar yar karama ce ta mata kalarta blue sai sheki take, budewa yayi ya shiga itama ta shiga ta zauna kasancewar glasses din masu duhu ne yasashi janyota zuwa saman cinyarshi bayan ya kwantar da kujerar tashi,

"Infara koya miki daga yanzu?"

"Didi tsoro nakeji..."

"Babu wahala fa baby, bari kiga, taka muje ahankali.."

Tafiya suka fara yana rike da sitiyarin itama ta rike suna juyashi ahankali, ahaka suka fice daga farfajiyar gidan, saida yaga sun kusa zuwa babban titi sannan yamayar da ita kujerarta yaci gaba da driving din shi kadai,

Wuraren shakatawa kala kala suka ziyarta daga karshe yakaita gidan anty siyama, ba karamin murna anty siyama tayiba da ganinsu nan tahau tsokanar amadi,

"Anty amadi kadai zama jela duk inda nadiya take kana bibiyarta abaya.."

"Anty siyama ni ai nafi jela ma, ki kirani da kowanne suna zan amsa"

Dariya sukayi dukkaninsu, har yamma suna gidan sai daf da magrib suka tafi, ba gida yanufa dasu ba, lovers garden yakaisu,bude ido kawai nadiya tayi tana ganin yanda masoya ke guje guje wasu kuma yan tsalle tsalle,

Kallonshi tayi bata san lokacin datayi kissing dinshi a baki ba,

"Baby wannan babban tukwici haka ai sai kisa na sume.."

Dariya tayi, "wannan somun tabi ne sauran bayani sai munje gida.."

"Kice duk ranar da nashiga hannunki sunana sorry"

Dariya tayi tajashi suka fita zuwa filin wurin, babu laifi suma sun dan wataya sosai, karfe 7 suka koma gida.

   Tunda suka koma kuma yadameta da mitar fashin sallar da takeyi, juyawa tayi ta kalleshi,

"Dadina dakai rashin hakuri didi, kwana uku nefa amma duk kabi ka damu kanka.."

Shiru taji yayi mata baiyi magana ba, janshi tayi tasashi ajikinta tafara shafa sumar kanshi,dagewa tayi wurin bashi kulawa tunda tarigada tasan halin kayanta,da yan dabaru tasamu har yasamu nutsuwa yayi bacci dama haka yakamata mata su kasance bawai kawai dan kina period ba ki kauracewa miji wata ma sai ki samu mijin yana gabas ita tana yamma wannan babban kuskure ne.

A daddafe dai yasamu yahakura har kwana ukun tayi, kamar wani marar lafiya yazame mata har saida yasamu abinda yake kulafuci sannan yaware yakoma kamar da,

Lokaci zuwa lokaci yana daukarta sufita su zagaya gari amma har yanzu bata gama koyon motarba kasancewar kullum suna hanyar zuwa wudil gashi anfitar musu da time table na exam,

Yanzu bai fiya zama a part dinsu ba yafi zama a part din hajiya saboda yabata damar yin karatu sai dai abunda yake damunsa yanda yanzu duk tazama wata lazy, shi kanshi yanzu bata iya hidimta masa kamar da abu kadan sai tace masa tagaji, ana cikin haka kuma sai tafara yawan amai daga taci abinci sai amai babu abinda take jin dadinshi sai lemon zaki shikam koda yaushe cikin shansa take,

Amadi ko kadan bai san abinda yake damunta ba amma dai yaga canji atareda ita musamman ma ajikinta wanda yake sashi kasa hakuri ita kuma yanzu idan da abinda ta tsana to abinda yake shaukin ne, kusan koda wanne lokaci sai yasha aikin rarrashi kafin yasamu karbuwa,

Rigarshi yake sakawa yana kallonta tana kwance akan gadonshi,

"Dan Allah didi kayi sauri karka dade.."

"To antyn lemon zaki yanzun nan zan dawo.."

Fita yayi ganin motar anty siyama yasashi shiga part din hajiya, gaisawa sukayi kawai yajuya zai fita,

"Anty amadi ina zuwa ne?"

"Anty ina zuwa lemon zaki zanje in siyowa mutuniyar, yanzu bata iya cin komai da zarar taci sai amai narasa gane meke damunta..."

Dariya anty siyama tayi tace,

"Allah yabata lafiya"

"Amin anty"

Ya amsa mata tareda yin gaba hankalinshi akwance domin shi bai fahimci abinda anty siyama ke nufi ba....

*_Ummi Shatu_*
[10/6, 6:07 PM] Bint Khalil: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
     _(Labarin k'auna)_



    *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITER ASSO.*
   _Home of expert & perfect writers_

  _Wannan shafin sadaukarwa ne agareku masoyana, nagode Allah yabar zumunci._

        *72*

aishaummi.blogspot.com

     *A*hanzarce yake tuki bayan yadawo daga siyo mata lemon zakin kamar yadda tace, sauri yake yakoma gidan da wuri domin yakai mata,

Packing yayi yashiga cikin part din nasu amma sam baiji motsinta ba, cikin bedroom dinta yashiga nan dinma bata nan, dayan bedroom din yaleka ananma bai ganta ba dan haka yayi gaggawar nufar dakinshi koda yaje can dinma wayam,

"To ina baby ta shiga?" Yatambayi kansa, tunani yayi ko tana bathroom dan haka ahanzarce yaje ya dudduba, gaba daya kaf bata nan hakan yasashi zuwa part din hajiya ko tana can amma abin mamaki hajiya sai cemasa tayi ai yau kwata kwata ma nadiya bata shiga part dinta ba,ganin anty siyama tatafi yasashi juyawa batare da ya zauna ba,

Part dinsu yasake komawa yana shiga idanuwansa sukayi arba da wata farar takarda akan dan madaidaicin Stoll din dake gefen kujerun falon,

Da saurinsa ya karasa yadauki tskardar ya warwareta yafara karantawa,

  _Zuwa ga didi na abin alfahari na, nasan kanata nemana amma baka ganni ba to kayi hakuri kuma kayafe min duk da nasan kai dama mai hakurin ne sannan nasan kabawa rayuwata gudun mawa ta bangarori daban daban, ni nadiya ina mai bakin cikin sanar maka da cewar natafi inda bazaka sake ganina ba, na zabi inbarka saboda wasu dalilai..._

Kasa karasa karantawa yayi yazauna sharafff akan kujera idanuwanshi jajur, tunani yake aransa shin wanne laifi yayi mata da har zata yanke masa wannan mummunan hukuncin, baiyi zatoba kawai yaji kwalla na neman cika masa ido, goge kwallar yayi yasake duban wasikar tata,

_Kayi min afuwa didi na nasan hankalinka yatashi idan kadawo daga siyo min Orange din kasameni a corridor zanyi maka wani albishir, duk abinda nafada da farko ba gaskiya bane am joking..._

Cillar da takardar yayi ya nufi corridor da gudu gudu, kwance ya hangota kan doguwar kujera tana sanye cikin bakar doguwar riga ta materia taci kwalliya abinta sai kamshi ne mai dadi yake fita daga jikinta,

"Baby..." Yakira sunanta yana girgizata, bude idanuwanta tayi tana murmushi,

"Meyasa zaki yimin irin wannan wasan, kin san kuwa yanda hankalina yatashi?"

"Didi kenan nima ai haka kayi min, ramawa nayi.."

Zama yayi agefenta yakamo hannunta yarike,

"Shikenan anyi 1-1 yawuce, ki fada min albishir din da kikace zaki yimin.."

Dan yatsina fuska tayi ta muskuta,

"Ina lemon zakin yake..?"

"Yana falo.."

"To dauko min sai infada maka amma fa ka yanko min shi"

Tashi yayi mintuna kadan sai gashi yadawo rikeda filet wanda ya yanko mata lemon akai,

Tashi tayi ta dauki lemon takai bakinta tana kallon amadi wanda shima yabada attention yana kallonta,

"Kasan me? Kakusa zama dady..."

Kallonta yayi cikin rashin fahimta,

"Baby ban ganeba"

"Ina nufin nakusa inhaifa maka baby.."

Rungumeta taji yayi sosai cikin farin ciki kwalla fal acikin sexy eyes dinshi,

"Baby dagaske kike, kin gama yimin komai baby.."

Sakinta yayi yakai hannunshi yadora akan mararta yana shafawa,

"Allah yaraya min kai baby na, Allah ya fito dakai lfy.."

"Abin nema yasamu ko? Ansamu nayi.."

"Sosai kuwa domin nima nakusa nahaifi dan kaina adaina yimin gori.."

Murmushi tayi tana tsotsar lemon dake hannunta,

"Allah sarki.."

"Yes fadi ki kara, may be ma gaskiya sai dai kihakura da exam dinnan har sai kin haihu"

Kallonsa tayi afirgice,

"So kake insake maimaici? Wallahi bazai yiyu ba, kabarni kawai inyi abina ingama ni zan iya"

"Baby bana son yarona ya wahala ne"

Sakin baki tayi tana kallonshi tun daga ranar ya hanata aikin komai babu abinda takeyi abu kadan sai yace shi baya son babynshi ya wahala, ko girki yanzu tadaina yi hajiya ce ke basu sai dai kawai ita tadafa dan abinda take kwadayi,rigarta kuwa kullum cikin dageta yake yana kallon cikinta kamar wani mudubi,

Daurewa tayi sosai tayi karatun jarabawar da zatayi amma duk dare amadi cikin yimata mita yake idan yaga taki yin bacci tana karatu, ahakan dai ta samu ta kammala exam din anan kuma hutu yasamu domin babu abinda takeyi ahalin yanzu, amadi kuwa yadauki son duniya yadorashi akan wannan cikin wanda sai yanzu ne ma zai shiga wata na hudu,

Koda yaushe cikin yiwa cikin hira yake, yayi ta magana shi kadai kamar wani zautacce idan tayi magana kuma yace shida babynshi yake hira, idan zai fita aiki da safe sai yayiwa cikin sallama haka idan yadawo ma sai yace masa yadawo,

Nadiya dai kallonshi kawai take tana jin wani sabon sonshi yana ratsata saboda ko acikinta nafari bata samu irin wannan kulawar awurin kabeer ba amma shi amadi saima ya tambayeta abinda zataci, me zata sha, me take sha'awa, kullum idan zai fita tambayarshi kenan,

"Baby me zan taho miki dashi? Yau mekike sha'awar ci..?"

Ko tace babu abinda take sha'awa baya yarda sai yataho mata da kayan makulashe, ko shakka babu tasan tayi sa'ar miji mai kaunarta wanda ya share mata hawayen da suka jima suna gudana akan kumatunta, duk sanda zai tafi wudil kuwa dakyar take rarrashinsa yatafi domin baya son yayi nesa da ita,

Cikin weekend ya dauketa suka tafi rano saboda tunda tatare bataje ba, tsaraba sosai amadi yayiwa su mama su amira da twins,

Kowa agidan saida yayi murnar ganin nadiya saboda tayi bul bul takara kyau fatarta inbanda sulbi babu abinda takeyi,

Wuni cur sukayi saida yamma suka tafi wanda harda su fadeel saboda anyi hutun makaranta, nadiya jin hankalinta tayi ya kwanta saboda yanzu bata da matsalar komai,

Tana kwance acikin bedroom dinta tajiyo hayaniyar su amadi a kitchen shida su fadeel, tashi tayi tafita wurinsu daga ita sai rigar bacci iya gwiwa ash colour cikinta yadan bayyana kadan,

Kallonta amadi yayi ya hadiyi yawu,

"Baby gaskiya yau fa zanyi tawaye, gaskiya yau ina bidar wani abu.."

"Kaga ni zubo min kwan inje inci yunwa nake ji, yanda kake da ci haka babynka yake kamar gara.."

Murmushi yayi yadauki filet yana saka mata kwan da yake soyawa, rungumeta taji su fadeel sunyi suna cewa,

"Good morning momy"

"Morning fadeel, morning fadeela na.."

Karba tayi tafita falo tazauna tahada tea tafara karyawa, ita kanta mamakin yanda akayi amadi ya iya girki take saboda idan yayi maka abinci sai ka rantse itace tayi bashi ba,

Har tagama basu fitoba, tashi tayi takoma bedroom dinta ta dauki towel tashiga wanka, dama kamar jira amadi yake wuf taji yafado cikin toilet din,

"Baby kawo intayaki wankan..."

"A'a barshi basai ka tayani ba"

"Uhm uhm nidai sai natayaki.."

Babu yanda ta iya dole tabarshi yafara tayata din wanda daga karshe ya bige da abinda yafi muradi wanda dama tasan abinda yakeso kenan shine ya bullo ta haka,shiryata yayi shima ya shirya cikin kananan kaya,

Tana gani suka fita suka barta agidan shida twins yace banda ita ayawon saboda baison babynshi ya takura, jin zaman kadaici yadameta yasata shiga part din hajiya, acan suka dawo suka isketa nan ya goyeta ganin hajiya bata cikin falon ya tarkatosu suka koma part dinsu yakawo mata tsarabar kwakwa da dabino, zuba masa ido tayi tana kallonsa suna boxing shida fadeel,

"Meye ne kiketa kallona..?"

"Ina son haifar baby mai kamada kaine shiyasa"

Murmushi yayi mata,

"Ko baki kalleni ba dama na tabbatar dan da zaki haifo min mai kamada nine sak dan jinina yafi naki karfi"

Dabinon ta dauka tana ci tana kallonshi,

"Inji waye...?"

"Inji ni saboda jinin last born yafi na first born karfi"

Dariya tayi taja pillow din kujera ta kwanta taci gaba da kallon boxing din da suke yi.

"To yanzu dai fada min dalilinka na siyo min wannan kwakwar da dabino"

"Kinfi dan dako sanin tasha,Saboda tunda nabaki babyn nan kika zama wata lazy..."

Pillow tadauka ta jefeshi nan yakare dukan da hannunshi yana dariya.

***

  Al'amarin kabeer yanzu yadan samu wani aiki na wucin gadi awani companyn sarrafa auduga, amma har yanzu yana jin radadin abinda asabe mc tayi masa musamman ma rabashin datayi da abar sonshi nadiya,

Haka dai ya daure ya rungumi kaddara domin babu yanda ya iya yasan nadiya tayi masa nisan da bazai taba cimmata ba,agaba abbanshi da mama suka sashi kan dole sai yanemo aure saboda zamanshi ahaka bazai yiyuba tunda Allah yasa yasamu abinyi,

Acikin unguwarsu yasamu wata yarinya murja kawar Aisha kanwarshi suka daidaita har aka yanke ranar aure, shi dai yasan samun madadin nadiya arayuwa abune mai wahalar gaske shiyasa duk lokacin da yatuna da asabe sai yaja mata Allah ya isa.

***

Awurin nadiya su fadeela suka gama hutunsu sannan amadi yamayar dasu rano, sati daya da tafiyarsu fadeel yayi mata albishir da cewa alkawarin da yayi mata da jimawa wanda yace sai ta kammala karatu zai bata shine nanda sati biyu zasu tafi kasar Paris domin bude ido, shiru nadiya tayi dan tsananin murna tama rasa me zatayi sai kawai tafashe da kuka ta rungumeshi tana yimasa addu'ar samun babban rabo acikin rayuwarsa ta duniya da lahira,

"Nidai abu daya zaki bani tukwici" yarada mata a kunnenta,

Acikin yan kwanakin suka shirya yakaita rano da sumaila tayi sallama suka bar kasar, gaba daya amadi yasata tamanta da kowa bata iya tuna kowa sai shi sai yanzu ta gasgata maganarshi da yayi mata tun kafin aurensu lokacin tana tsaka da bashi tension cewar zai sota zai kula da ita kuma itama zata soshi tabbas kuwa hakance take faruwa domin yanzu babu wani wanda take kauna sama dashi in aka dauke mahaifanta,

Sun rabarbashi soyayya kamar babu gobe sun ziyarci wurare daban daban dan shakatawa, kasancewar cikinta yakai kimanin wata takwas yasa suka jibgo kayan babies acan,

Satinsu bakwai suka dawo nigeria, koda suka dawo dinma wata kulawar yashiga bata ta musamman har Allah ya sauketa lafiya lokacin yana wudil bai dawoba sai a standard hospital ya tarad dasu yana zuwa yasamu ta haifi yaranta maza guda biyu Ku kanku masu karatu nasan basai nafada muku irin kyawun yaranba domin kyawun amadi ne yahadu da nadiya yabada wani kyawu nadaban,

Amadi rasa inda zai cusa kanshi yayi dan tsananin murna nan yashiga kaffa kaffa da yaranshi da matarshi har aka sallamesu suka koma gida,koda wanne lokaci zaka sameshi rikeda yaran yana kissing dinsu,

Amira da husna sune suka zo domin zama awurin mai jego saiko umman sumaila wanda kunsan ita kuma dalilin zuwanta shine sabinta tsoho yakoma sabo, nan tafara bawa yartata kulawa ta musamman domin haskakata azuciyar amadi,

Abdullah da abdurrahman shine sunan da aka radawa yaran ranar suna,raguna biyu da babban Sa amadi ya yanka musu, sunan yatara dunbin mutane masu yawa domin hatta anty Dija da anty hamida yayun amadi sunzo haka Yaya yaseen shima yazo da iyalansa wannan dalilin ne yasa masaukin hajiya yacika dam dan haka tace wasu suje part din nadiya su sauka acan domin itama yan uwanta sun zazzo tunzuro baki amadi yayi kamar wani karamin yaro domin yasan takurashi za ayi shida nadiyanshi sam bazai sake ba da ita,

Ansha shagalin suna sosai sannan taro yawatse kowa yakama gabanshi sai iya umman sumaila kadai da Amira, cigaba da gyarata umman sumaila tayi har suka cika kwana 40 ranar ta hada nata yanata itada amira suka tafi bayan amadi ya hada musu sha tara ta arziki. Amadi zaucewa ne kawai bayiba saboda irin yanda nadiyan shi ta sauya,kwana yayi yana yi mata sunbatu ita kuma ta wuni tana zolayarshi da tsokanarshi, bashida bakin ramawa sai dai murmushi, ko ina tayi yana biyeda ita, sati daya yadauka agida bai fita ko inaba sai renon twins dinsu da yake tayata sai kuma fitinar da yasakota agaba da ita, itama din sam baya isarta saboda tana mutukar sonshi ahalin yanzu, wata soyaya mai wuyar fadi suke yiwa junansu.

Soyayya mai tsayawa arai amadi yashiga bata itada yaransu lokaci kankani yaran suka zama kamar basu ba saboda girma, shiryawa sukayi sukaje rano suka wuni, har gidansu kabeer nadiya taje tana rikeda abdallah shi kuma amadi yana rike da abdulrahman akan kafadarshi yasha dark blue din danyen boyel da hula ita kuma nadiya tana sanye da wani swiss les pink colour kai idan kagansu sai kaji sun burgeka, agidan kabeer ya samesu yaje gaida mamanshi ganin nadiya da iyalanta yasake tayar masa da hankali amma yasan babu yanda zaiyi tunda ta rigada ta subuce masa har abada, shi kuwa amadi ganin kabeer yasashi murtuke fuska yafara ciccin magani yana yiwa abdurrahman wasa, dakyar ya yarda suka gaisa da kabeer,cewa nadiya yayi tatashi su tafi domin yaga kamar kallonta kabeer yake yi. Har acikin mota sai faman fushi yake ta yimata duk tagane dalilinshi nayin fushin dan haka tasoma lallashinshi,

"Ayya didina kayi hakuri kadaina fushi wallahi ko bayan ranka bazan iya rayuwa da kowanne namiji ba saboda kai kadai nake so.."

Sai lokacin yaji yasamu nutsuwa, "idan kina son nahakura nidai sai kin bani abinda nafi so"

"Zan baka.." Murmushi yayi yashiga saka mata albarka.

Sosai amadi ya mayar da nadiya yar gata kuma sarauniya acikin dukkan mata, mota ya koya mata saboda baya son idan zataje wani wuri ace sai driver ne zai kaita, cikin kankanin lokaci ta kware tana iya kai kanta duk inda zataje,

Tunanin maganar da amadi yafada mata takeyi tana murmushi cewar wai next year iyanzu tasake haifa masa wasu yan biyun, dafata taji anyi tana juyawa taganshi tsaye, girarshi ya daga mata,

"Ya akayi.."

"Maganarka nake nazari da kace wai zan sake haihuwa wata shekarar.."

"Insha Allah"

"A'a gaskiya, zee tazo sai ta dora daga inda natsaya.."

Kai yagirgiza ya rungume ta,

"Ai Allah ma cewa yayi fa inkiftum fa wahidatan au mamalakat aimanikum.."

"To me kake nufi kenan? Ashe kai ba adali bane.."

"Sosai kuwa, duk matar da tashigo bayanki to bazan iya yin adalci ba domin zanyita fifitaki kinga maganin kar ayi kar asoma" yafada yana bata wani cool kiss agefen wuyanta.

Kamar kuwa yafada da bakin mala'iku shekara na zagayowa ta haifi yan biyunta mace da namiji, ranar suna aka radawa yara abdulrahim da amatullah domin dama amadi yace mata bismillahir rahamanur rahim yake son hadawa shiyasa yasawa yaran abdullah, abdurrahman da abdulrahim,

Amadi hade kan iyalanshi yayi yana basu kyakkyawar kulawa ta musamman da tafiya tai tafiya ma sai ya debo su fadeel yahada su da nashi sam baya nuna banbanci komai tare yake yi musu, shi kansa kabeer yadauki hakuri yabar musu yaran sai dai idan anyi Hutu duk term ana kaisu gidanshi hutu saboda su saba da yan uwansu,domin matarshi har ta haifi yara biyu yanzu macen sunan nadiya yasa namijin kuma Mohd.

Sam amadi baya gajiya da nadiyanshi haka kuma bai taba nuna mata cewar wai ba a budurwa ya aureta ba, koda yaushe cikin nacin son kasancewa da ita yake wannan dalilin be yasa umman sumaila sake zage dantse wurin gyara yartata domin mata saida gyara,amadi kam kullum cikin sonshi yanmata suke amma ko kusa basa gabanshi nadiyanshi ita kadai ta isheshi rayuwa.

Familyn amadi abin burgewa ne ga kowa koda yaushe cikin farin ciki suke suna ziyarta wurin bude ido, cikin yawace yawacensu sukaga asabe mc tana bara abakin titi da sanda wacce take dogarawa domin yanzu kafa daya gareta saboda ayawon barikinta taje ta dauko cuta mai karya garkuwar jiki yanzu bata da komai kawaye duk sun gujeta, mazan da take hulda dasu sun daina yayinta, dama haka duniya take yau gareka gobe ga waninka.

   ALHAMDULILLAH

Anan nakawo karshen labarin mijina sirrina, labarin yafaru agaske ba kirkirarren labari bane dafatan Allah ya amfanar damu darrusan dake cikinsa ya yafe mana kurakuran da nayi nidaku baki daya.

Littafin mijina sirrina sadaukarwa ne gareki Nasiba I uba (the writer of kannen mijina)

Tukwicine agareki Feedohm (the writer of bakonmu hasken mu)

Godiya ta musamman ga yan kungiyar haske writers Allah yasake hade kawunanmu amin.

Masu karatu sai mun hadu acikin labari nagaba idan Allah ya amince, duk wata masoyiyar ummi shatu, ko wacce taji tana kaunarta,ko son ganinta ko kuma take son jin muryarta, to ummi shatu tana mutukar kaunarta itama, gaisuwa mai yawa agareku masoyana hakika da bazarku nake rawa, ina sonku har cikin zuciyata aduk inda Luke fatana Allah yabarmu tare.

*_Ummi Shatu_*

Friday 29 September 2017

MIJINA SIRRINA... 57-70

[9/5, 8:58 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
       _(Labarin k'auna)_


       _*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*


         *57*

aishaummi.blogspot.com

       *S*ai da ta hade rai ta daure fuska sannan ta kalleshi tana kokarin fincike hijabinta daga hannunshi,

"Kai baby...... Dan Allah kiyi hakuri please...."

"Amma ai ba haka mukayi dakai ba ko?", ta tambayeshi cikin bacin rai,

Kai ya daga mata cikin kalar tausayi,

"Ba haka mukayi ba baby amma ai abu daya dama kikace nayi miki alkawari akai kuma na amince nayi....wallahi bazan karya alkawarin da nayi miki ba, kuma ma baby inbanda rikici irin naki ai ba wani abu zanyi mikiba tunda fa a off kike..." Yakarasa maganar cikin rad'a,

Jin abinda yafada yasata rabuwa dashi bayan ta dauke kanta sai faman b'abb'ata fuska take, k'asa k'asa yake kallonta yana murmushi saboda sai yau yagane bata da wayo bare dabara,

Cikin doki da farin ciki ya zare hijabin tareda fara nuna mata wata soyayya mai mutukar sanyi, duk da tana nuna mishi cewar bata sonshi kuma bata son abinda yake mata hakan bai hanata samun kanta cikin dunbin farin ciki da nishadi ba,

Ya kwashe lokuta masu yawa yana gwada mata so daga yaji tafara yimasa masifa zai fara rarrashinta,

"Baby kiyi hakuri iya fa nayau ne kadai kinga gobe tafiya zanyi, dan Allah kiyi min wannan alfarmar..... Kinji baby"

Da haka yasamu yasha kanta ya lallabata har yasamu ta kyaleshi yasamu farin ciki mai tarin yawa, har karfe 2 nadare yana manne da ita ganin abun ba na karau bane yasata yin magana,

"Gaskiya nifa bacci nake ji...."

Sai da ya rungumeta tsam tsam ajikinshi sannan yayi mata magana ahankali cikin yanayin rada,

"To baby ai ma kinyi min halacci, kinyi kokari, yi baccinki babu mai tashinki har sai gari ya waye, nagode baby, Allah yayi miki albarka, Allah yabarni dake har karshen rayuwata, Allah yayi miki albarka baby...."

Yatsun hannunta na dama yakama yana murzawa ahankali sai faman godiya yake yimata wanda har sai da taji kanta ya daure da wannan godiyar da yadage yanata yi mata banda saka mata albarka da yaketa faman yi kamar wadda tabashi wani abu, nan ta tuno first night dinsu da yaya kabeer,sam baiyi mata irin wannan karramawar ba amma shi amadi da ba a budurwa ya aureta ba kuma ba komai ne ya shiga tsakaninsu ba yadage yanata faman lallabata tareda saka mata albarka, jin irin godiya da rarrashin da mijinta keta faman yi mata yasa tayi fatali da tunanin kabeer tama manta dashi gaba daya, babu bata lokaci bacci mai mutukar dadi ya dauketa.

Amadi kam sam bai yi barci ba yakasa yanata faman juyayin tafiyar da zaiyi yabarta, zaije ya kadaice shi kadai batare da itaba, zaiyi nesa da ita a daidai lokacin da yafara shakuwa tareda jin dadin zama da ita, har aka kira sallar asuba idonshi biyu bai runtsa ba, ahankali ya tashi daga jikinta ya shiga toilet.

  Yana idar da salla ya tashi bayan yayi addu'o'inshi kamar yadda ya saba, kan gadon yakoma ya zauna ya jawo laptop dinshi yaci gaba da ayyukan jiya wadanda ya fatalar bai karasa ba, har karfe 6 tayi gari yayi haske nadiya bata farka ba, sai misalin karfe 7 sannan tayi juyi ta bude idanuwanta,

Jikinta ta kalla sannan ta juya ta kalli amadi wanda ke zaune yanata aikinshi,fuska ta daure tafara dabarar yanda zata tashi, hijabinta ta daura ta mike fuskarta a daure,

Waiwayawa yayi ya kalleta nan yaga irin yanda ta daure fuska, murmushi yayi ahankali ya furta,

"Duk ciccin maganinki dai sai da naga yanda matata take kafin natafi...."

Toilet ta shiga sai da ta dade sannan ta fito tana sanye da kayanta na jiya wanda tazo dasu,

Can daya gefen gadon taje ta zauna, "ina kwana...?"

"Yes my baby, ai ba ahaka zamu gaisa ba, bari nazo na debi gaisuwa, just 1 minute....." Yafada idanuwanshi na kan laptop dinshi, ajiye laptop din yayi ya tashi ya nufi wurinta, tana ganin haka ta dauke kanta tareda sake bata rai,

Agabanta ya tsugunna ya kamo hannuwanta masu mutukar taushi,

"Baby ya kika tashi?, ina fata kin tashi lafiya....?"

"Lafiya lau..." Tabashi amsa batare data kalleshi ba,

"To ki kalleni mana baby..." Yace da ita yana murmushi,

"Tunda mun gaisa ni ka tafi"

Murmushi yasake yi saboda jin abinda ta fada maimakon ya tashi sai ji tayi ya kwantar da kanshi akan cinyarta,

"Idan natafi ina zanje inda yafi nan? Haba baby ya zaki rinka korata alhalin kuma kin san banida wurin zuwa...."

Shiru tayi masa bata amsa masa ba, yadade kanshi bisa cinyarta kafin ya dago yana kallonta,

"Baby masu duniya...."

Nan dinma dai shirun tayi,

"Kina jin yunwa ko? Bari nasa akawo mana breakfast.."

Ita dai batace komai ba shi kadai yake maganarshi,tashi yayi yana rikeda hannunta yana kallonta,

"Zoki rakani to..."

"Kaje ka dawo"

"To shikenan ina zuwa"

Sakin hannunta yayi yafita nan tabishi da kallo, "maza babu ta ido.." Tafada ahankali,

Bai wani jimaba ya dawo, zama yayi agefen gadon yana kallonta,

"Dan matso nan dan Allah..."

Yi tayi kamar bataji ba, "baby... " yasake kiran sunanta,

"Na'am.."

"Cewa fa nayi ki matso kusa dani..."

Shiru tayi batayi ko motsi ba,

"Shikenan ni bari nazo tunda ke kin ki zuwa..."

Matsawa yayi wurinta,

"Bari na daukeki nakaiki tunda kin ki zuwa..."

"Dan Allah kabari bana so...."

Kokarin daukarta yafara yi nan suka shiga kokawa dama abinda yake so kenan tahaka yasamu damar rabata da hijabin da ta saka yabarta da sexy dress din dake jikinta,

Duk da bata so sai da ya dauketa yakaita side din da yake zaune dazu, ajiyeta yaje yi nan yaci tuntube tayi saurin rikeshi suka fada kan gadon tare,

Kura mata ido yayi yana dariya,

"Baby karfa mu karya musu bed, ko zaki iya biyansu idan wannan ya karye? Uhm.....?"

Fuskarta ta dauke ta soma tuttureshi wai yatashi, gyara kwanciyarshi yayi ajikinta, nan taci gaba da faman tureshi, laptop din shi ya mika hannu ya dauko, kokarin zameshi tafara yi zata tashi,

"Wallahi idan har kika tashi ban yafeba kuma sai Allah ya tambayeki garama ki zauna..."

Hakura tayi ta zuba masa ido tana ganin isa da mulki irin ta maza inbanda tsabar nuna isa ajikinta fa ya kwanta rub da ciki kuma yake danna laptop dinshi yana yin aikinshi,

Dole haka ta hakura har ya kammala aikin da yake yi lokacin har karfe 8:30 tayi, breakfast aka kawo musu wanda yayi musu order, nan ya fita ya karbo yadawo dakin inda take,

Sauko da ita yayi daga kan gadon ya zauna itama ta zauna yafara ciyar da ita, soyayyen dankali da kwai sai farfesun hanta, sam bai damu da kanshi ba ta ita yakeyi har sai da yaga ta koshi sannan yace itama sai ta ciyar dashi, tana cika tana batsewa fuska a daure haka tabashi yaci ya koshi,

"Nifa ina son komawa makaranta da wuri...." Tafada tana hararar wani wuri,

"Karki damu yanzun nan zamu tafi baby..."

Tattara kayanashi yayi suka fita, duk ta damu da irin kallon da mutanen wurin suke yi musu ita dashi musamman ma ita ko sun dauka budurwarshi ce ba mata ba oho hakanne yasake bakanta ranta, koda suka shiga mota yafara driving yanata janta da hira amma taki kulashi abunku da marar fushi ko da wasa bai damu ba, lokacin da suka shiga makarantar hannunta ya kamo yafara yi mata magana cikin sigar lallashi,

"Baby dan Allah ki shirya mu koma kano tare dake saboda ina son hajiya ta sanki before natafi...."

Shiru tayi kamar bazata amsa ba amma jin ya ambaci hajiya yasata amincewa,

"Shikenan zan shirya..."

"Yawwa baby nagode Allah yayi miki albarka"

Bude kofar motar tayi ta fita shikuma yakarasa administrative block.

Karfe 2 na rana ta fito cikin shirinta,wata jar atamfa ce ajikinta mai zanen akwati da ratsin yellow ajiki, dan tsabar jan fada saida ta caba kwalliya a fuskarta sannan kuma ta yafa mayafi a kafada gashi dinkin fited ne riga da skirt,kai idan kaganta zaka rantse cewar budurwa ce,

Tunda ta taho yake kallonta ta cikin mirror har ta karaso, lokacin da ta shiga cikin motar kuwa wani fitinannen kamshi yaji ya doki hancinshi,

Kallonta ya juya yana yi kawai baice komai ba, yadade yana kallonta baiyi magana ba,

"Ya lafiya...?" Ta fada batare da ta kalleshi ba,

"Amma dai baby ai kin san nahanaki saka mayafi ko?"

"Ohhhh kenan kwata kwata bazan saka ba kake nufi?"

Key yayiwa motar batare da yayi magana ba, har saida suka yi nisa da makarantar sannan ya kalleta,

"Kita sakawa idan kinada ra'ayi ni ban hanaki ba, duk abinda kike so kiyi kanki tsaye..."

Kallonshi tayi saboda tana son ta tabbatar da gaskiyar abinda yafada ko gatse yayi mata, kallonta yayi tareda yimata murmushi nan tayi saurin kawar da kanta, hannunta ya kamo ya rike cikin nashi,

Lokaci lokaci yana yimata hira amma ba sosai take amsawa ba da haka har suka shiga cikin kano,

"Wowwwww ga wata hadaddiyar....."

Yafada sai kuma yayi shiru, kallonshi tayi shima ya kalleta,

"Bafa wani abu zance ba cewa nayi ga wata hadaddiyar riga can wadda nasan idan kin saka zata yimiki kyau... Kin ganta can"

Juyawa tayi gamida tabe baki.

  Lokacin da suka karasa gidansu amadi nadiya ba karamar karramawa ta samu awurin hajiya ba kamar hajiya ba zata ajiyeta a kasa ba dan farin ciki, ita kanta hajiya saida ta yaba da zabin amadi lokacin da taga nadiyan, nan dadi ya rufeta saboda ganin surikar tata,

Gabatar musu da abinci hajiya tayi bisa table nan amadi ya dakinshi yafito bayan yasha wanka yana sanye cikin wata t shirt lemon green agaban rigar an rubuta _big guy_ da bakin three quarter sai kamshin turaren _axe_ ne ke fita daga jikinsa,

Table din yakarasa yana kallon nadiya tareda jan kujerar dake kusa da ita, hajiya kam sai murmushin farin ciki take ganin wai yau autanta ne yayi aure gashi tareda matarsa,

Dambun shinkafa da sos ya zuba musu cikin flate yasaka spoon guda biyu yatura gabanta, ita dai nadiya akunyace taci wannan abincin saboda ga hajiya na zaune awurin gashi kuma sai kokarin wai sai yabata abaki yakeyi, lokacin da suka kammala cin abincin mikewa yayi yana kallonta,

"zo muje ki tayani shirya kayana baby"

Bata yi musu ba saboda hajiya dake zaune, hannunta ya kama zuwa bedroom dinshi wanda ke kusa da na hajiya......


  _Fatan alkhairi ga Anty Baraka & Meenarh parrot sannunku na yaba mutuka da kokarinku wajen kwaikwayon salon rubutun ummi shatu...._


*_Ummi Shatu_*
[9/7, 9:07 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


   *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO* _(Home of expert & perfect writers)_

    _Fatan alkhairi ga anty Jidda musa this page is yours..._

*Masoya masu karanta mijina sirrina dan Allah kuyi min uzuri na rashin ganin post akan lokaci ina cikin hidima ne amma insha Allah komai zai zama normal, gaisuwa agareku mai tarin yawa...*

       *58*

aishaummi.blogspot.com

     *Y*ana rike da hannunta har cikin dakinshi wanda ke dauke da kayan ababen more rayuwa kala kala,

Akan tamfatsetsen gadonshi ya zaunarta ya tsugunna agabanta gamida kama hannuwanta yana kallonta,

"Dan Allah baby idan natafi ki kula da kanki sosai kinji? Duk da dama nasan ke mai nutsuwa ce..."

Karo nafarko data iya kallonshi kallo na nutsuwa nan taga idanuwanshi sunyi ja, can lungun idonshi kuma ruwane kwance, ko ba afada ba tasan kuka yake kokarin yi mata, duk da bata damu dashi ba sannan ba sonshi takeyi ba saida taji jikinta yayi wani irin sanyi,

Shiru suka yi gaba dayansu daga shi har ita,

"Kayan nan sunyi miki kyau sosai baby, muga dinkin...." Yace da ita bayan ya koma jikinta ya zauna,mayafin ya janye yana kallonta tako ina,

Bata iya cemishi komai ba saboda irin sanyin da taji jikinta yayi illa sunkuyar da kanta kawai da tayi tana jin yanda yake kissing din wuyanta asanyaye,

Yau dai dayake yan zaman lafiyar nata suna kusa kasa hanashi tayi har sai da ya kyaleta dakanshi,

"Baby kinga jakar da zan zuba kayan can akusa da wardrobe..."

Mikewa tayi domin taje ta dauko nan yabita ya rungumeta ta baya, ahaka sukaje ta dauko jakar suka dawo gaban gadon,

"Kayan suna cikin wardrobe..." Yasake fada har lokacin yana rungume da ita ta baya, tare sukaje tafara debo kayan tana cillawa saman gado, shine yake nuna mata wanda zata dauka har sai da yace sun isa tabarshi haka,

"Baby saura vest da short nicker..."

Ciro masa gajerun wanduna tayi da vest nan suka koma wurin kayan yana makale da ita, zama tayi shima ya zauna a bayanta ya zagayeta da hannuwanshi ya rungumeta tareda dora kanshi bisa kafadarta,

Jera masa kayan tafara yi acikin jaka shikuma yafara yi mata magana acikin kunnenta,

"Baby ki gama ki zana yanda kike son gidanki ya kasance saboda kafin nadawo za agama ginin ayi komai da komai ina dawowa tarewa kawai zamuyi aciki nida ke....., zan nuna miki filin da za ayi mana ginin yanzu idan kin gama shirya min kayana"

"Uhummm" shine kawai amsar data bashi ta cigaba da zuba masa kayan cikin jaka, abayanta taji ya kwanta ya dora kanshi ajikin wuyanta,shiru taji yayi kamar mai yin bacci, ita dai batayi magana ba aikinta kawai takeyi,

Daf da zata gama taji anbude kofar dakin anshigo da sauri ta kalli kofa saboda duk azatonta hajiya ce nan taga yayarshi ce anty siyama, kokarin zameshi daga jikinta tafara amma yaki saima sake kankameta da yayi kamar zai mayar da ita cikin cikinshi,

"Sorry nashigo muku kai tsaye...." Anty siyama tafada tana murmushi,

"Babu komai anty ai ba wani abu bane..." Inji amadi,

"Ahhh dan dai ban san ku biyu neba nayi tunanin kai kadai ne.. Ashe kaida amarya ne" ta karasa maganar tana kallon nadiya,

"Sannu da zuwa.." Nadiyan tafada akunyace,

"Yawwa sannu amarya, yagida?"

"Lafiya lau"

"Anty amadi amma dai ba yau zaku tafi ba..."

Dariyar sunan yaso bawa nadiya wai anty ita bata taba jin ancewa namiji anty ba sai shi,

"Haba anty yau bazaki ce yaya amadin ba sai anty kinga gashi nan kinsa matata tana yimin dariya....."

Dariya anty siyama tayi, "to ai bakina yasaba ne, tun kana yaro lokacin..."

"Kai anty dan Allah basai kin tona min asiri ba..."

Juyawa anty siyama tayi tana dariya,

"Kiji antyn nan zata fasa min kwai agabanki..." Yafada yana sake kwantar da kanshi akan wuyanta, batayi magana ba har ta gama shirya kayan ta rufe jakar,

Tashi yayi yakama hannunta zuwa gaban window dinshi wanda ke kallon baya, ya dage labulen nan ta hango fili kato mai girman gaske,

"Kinga filin da zan gina miki gidanki can, hajiya tace bazan yi nisa da ita ba dole tare zamu zauna..."

Kai ta daga batayi magana ba,

"To zo muje ki zana gidan..."

Abakin gado ya zaunarta yabude drewar din jikin gadonshi ya dauko plane sheet da pencil ya bata, abayanta ya zauna ya rungumeta,

"To zana ingani, nafi son ki zana da kanki saboda kar ayi miki wanda bashi kike so ba..."

Zanawa tafara duk da bata san yanda ake yiba, falo ta fara fitarwa sannan sai bedrooms guda uku, biyu suna opposite da juna daya kuma takaishi can gefe da nisa shi kadai kwal,

"Baby wannan bedrooms din guda biyu nasu waye?"

"Nawane daya, guda dayan kuma na baki.."

"Shikuma wancan wanda kika kai gefe fa?"

"Naka ne.."

Murmushi yayi, "wato ni aka kai gefe kenan..."

Mika mishi takardar tayi wai tagama,

"Baby baki zana bathroom ba, baki fitar da kitchen ba bare store..."

Ita shaf ta manta sai lokacin ta tuna,

"Nuna min a inda kike so asaka miki kitchen din..."

Nuna mishi tayi ya zana, haka yayita tambayarta idan ta nuna sai ya zana mata har zanen gida ya kammala.

Da dabara ta samu tafita daga dakin ta koma falo wurinsu hajiya da anty siyama saboda tasan idan zamansu yayi yawa a daki itada amadi su hajiya zasu zargi wani abu,

Tana zaune awurinsu hajiya har amadin yafito daga dakinshi idonshi fes akanta,

"Anty siyama kinzo da driver ne ki ara min shi ya mayar min da baby school..?"

Kunya maganarshi tasaka nadiya jin agaban hajiya da yayarshi yana kiranta da baby,

"Ehhh yana nan yaya amadi, yaushe zata tafi?"

Anty siyama tabashi amsa,

"Sai zuwa anjima..."

"To shikenan"

Zama yayi akusa da nadiya ita duk sai take jin nauyinsu hajiya tana ganin kamar zasu ga rashin kunyarta amma shi sai sake matsawa yake kusa da ita.

Har misalin karfe 6 na yamma tana gidan saboda shi amadi tashin tsakar dare zasuyi, ganin 6 ta dan gota yasa nadiya tace mishi zata tafi, albarka sosai hajiya ta shiga sanya mata tareda yimata godiya kamar wacce takai musu wani abu, sallama sukayi da anty siyama wacce keta faman janta da hira kamar ba yayar miji ba,

Hannunta yakama bayan sun fito daga falon hajiya,

"Baby ki kular min da kanki dan Allah, ki kular min da kanki,nasan zanyi missing dinki mutuka but ako ina nake akuma duk inda na tsinci kaina kina nan acikin zuciyata, soyayyarki daga Allah ne bani na sakawa zuciyata ba, namanta ban fada miki ba shekaran jiyafa naje rano nayiwa su mama sallama,baby zan tafi nabarki a lokacin da nake da tsananin bukatarki amma babu komai insha Allah kamar yaune zaki ganni nadawo gareki, zan kiraki anjimabkafin mu tashi..."

"To shikenan Allah ya kiyaye hanya" tafada batare data iya kallonshi ba, kiss ya manna mata akan lips dinta sannan ya rakata wurin motar anty siyama inda drivernta malam mudi yake tsaye yana jiran karasowar nadiya, amadi da kanshi ya bude mata kofar motar ta shiga ta zauna ya mayar ya rufe, gefe yakoma ya tsura mata ido ta cikin glass din motar daga karshe yafara daga mata hannu yana yimata sai wata rana......


_*Ummi Shatu*_
[9/8, 9:28 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_


       *59*

aishaummi.blogspot.com

    *T*saye yayi ya harde hannuwanshi a kirjinshi yana kallonta, dagowa tayi itama ta kalleshi nan ta hangoshi ta cikin glass din motar yana yimata murmushin shi mai tsananin tsada,

Saurin kawar da kanta tayi bata sake kallonshi ba har suka fita daga gidan,

Shima bai bar wurin da yake tsayeba har saida yaga fitarsu nadiya sannan ya juya ya koma ciki wurinsu hajiya,

"Kai yaron nan gaskiya kanada matsala yanzu saida ka dauko yarinyar nan kaji dadi.." Anty siyama tace dashi tana daddanna wayar dake hannunta,

"Anty kenan to wani abune? Ni jiyama awurinta na kwana"

Yabata amsa yana kallonta yana dariya,

"To ya isheni haka marar kunya kawai"

Dariya yayi yatashi yabi hajiya cikin kitchen inda take soya masa dambun nama wanda zai tafi dashi.

   Bayan sallar magrib sosai su nadiya suka shiga wudil, har cikin makaranta drivern yakaita, fita tayi tashiga hostel, tana zuwa dakinta ko zama batayi ba amadi ya kirata,

"Dan naci..." Tafada ahankali kafin ta daga wayar,

"Baby kunje ko?" Taji yafada cikin muryarsa mai sanyi,

"Ehhh mun sauka harma drivern yatafi"

"To naji dadi tunda ya mayar min da matata lafiya..."

"Uhmmmmm" tafada,

"Kin san abinda anty siyama tace bayan kin tafi? Wai saida na daukoki nikuwa nace mata ai jiyama awurinki na kwana..."

"Kafada mata haka?"

"Ehhh mana ai ba karya nafada ba ko ba tare muka kwana ba?"

Shiru tayi masa saboda taji yafara neman sakin layin da suke,

"Uhmmmm? Baby ko bahaka bane?"

Nan dinma shiru tayi masa bata amsaba, kasancewar idan da sabo yasaba da halinta yasashi cigaba,

"Jiya najini acikin wata duniya ta daban, ban taba samun kaina acikin wannan yanayin ba, naji dumin jikin matata Sosa...."

"Kaima wallahi ka iya maganganun...." Sai kuma tayi shiru bata karasa ba saboda nauyin da kalmar tayi mata abakinta,

"Meyasa baki karasa ba? Wata nafadawa ba matata nafadawa ba? Idan banyi hira dake ba dawa zanyi? Uhmmmm"

"Uhmmmm" tafada,

"Uhmmmmm?" Yasake fada,

"Uhmmm" itama tasake bashi amsa,

"Uhmmm?"

"Nace uhmmmm"

"Haba baby kiyi magana mana.." Yafada yana dariya saboda tabashi dariya sosai,

"Umhum.." Tabashi amsa,

"To tunda bazaki yimin magana ba shikenan sai anjima, yunwa nakeji abinci zanje naci"

"Toh"

"To sai anjima, ki kular min da kanki, i love you..."

Ko jiranta baiyi ba ya katse wayarshi saboda yasan ba amsa mishi zatayi ba,

Tun 9 ya kirata yake yimata hira wacce kusan shi kadai yake yin kayarshi domin ita daga uhm sai um um, bashi yayi sallama da itaba sai karfe 2 nadare saboda lokacin zasu tafi airport domin 2:30 zasu tashi,

Lokacin da yaje airport dinma saida ya kirata yasake yi mata sallama daga karshe kuma taji yayi shiru kamar wanda yake jiran wani abu,

"Shikenan baby sai nadawo..." Yafada tareda goge kwallar idonshi, duk sai taji wani iri,

Ita dai tasan bata sonshi ko yaya amma kuma saita gagara bacci, daren ranar gaba daya kasa bacci tayi tun lokacin da yace mata yatafi sai yaje zai kirata.

Haka tatashi da safe duk jikinta sanyi kalau kamar marar laka ajiki, duk da bata damu dashi ba sai da taji hankalinta ya tattara yatafi kanshi gaba daya,

Haka haka dai ta wuni ranar har dare yayi shiru bai kirata ba, ta karfi da yaji tasamu ta yakice damuwar taci gaba da al'amuranta,

Tunda yayi kwana biyu da tafiya kuma sai tafara mantawa da tunaninshi saboda dama bawai wani shiga ranta yayi ba domin yanzu bazata yi gaggawar sakashi aranta ba har sai ta fahimci wanene shi,

Kwananshi 5 da tafiya tafito daga lecture sai taga number din waje na kiranta domin akwai plus ajiki,

Jikinta ne yabata cewar amadi ne,

"Hello..."

"Baby nah..." Taji yafada cikin muryarshi kamar mai jin bacci,

"Na'am.."

"Baby ya kike? Inata missing dinki sosai,ke kuwa bakya missing dina ko?"

"Hmmmm"

"Ban gane hmm ba, kinga daga zuwana har mura ta kamani"

"Allah ya sawwake"

"Amin baby, abar sona, ina sonki baby..."

Shiru tayi tana jinshi, ya dan jima yana fada mata kalamai na soyayya zalla amma har yayi yagama bata mayar mishi da martani ba daga karshe dai yayi mata sai anjima ya kashe wayar wai yayi fushi tunda bata taba cemishi tana sonshi ba,

Bata kirashi ba har dare, shi da baya zuciya shine ya sake kiranta,

"Har ka huce kenan?" Tace dashi lokacin da ta dauki wayar, murmushi mai sauti taji yayi,

"Da anfada miki nayi fushi dake ne? Ni ai bazan taba yin fushi dake ba arayuwata... Ni yanzu bacci ma zanyi shine naji baccin bazai yiyu ba har sai naji muryar matata, ki cemun you love me..."

"Uhmm"

"Uhmm ki fadi abinda nasaki mana..."

Shiru tayi batayi magana ba,

"Baby..."

"Na'am"

"Kiyita fada min kalaman so har sai nayi bacci, idan kuma bakiyi ba Allah zai saka min..."

"Ni gaskiya ban san me zance ba..."

"Tunda baki saniba to kiyita cewa kina sona, kinga nasanar dake abinda zaki fada.."

Shiru tayi shima yayi shirun yanata yimata dariya kasa kasa tayadda ba zata jiba,

"Baby kina son nabarki da Allah? Idan bakya so kiyi abinda nace kinga mu dare yayi sosai anan, oya start...."

"Me zance?"

"Kice kina sona, kuma kiyita fada har sai nace ya isa haka.."

Kamar zatayi kuka taji saboda ita gaskiya bata son fadin abinda yace,

"Nidai gaskiya ka sauya wani.."

"Wallahi wannan zaki fada kuma idan baki fada ba ban yafeba..."

"I love you..." Tafada tana bata fuska kamar yana ganinta,

"To ai fada zakiyi tayi har sai nace ya isa..."

Cigaba da fada tayi shikam har wani lumshe ido yakeyi saboda yanda Kalmar take yimasa dadi duk da yasan adole take fada bawai dan tana son nashiba.

Saida tafada fiyeda sau 20 sannan yace mata ya isa haka, shiru tayi fuskarta akumbure dan takaici da bacin rai,

"Nagode my baby, sai munyi magana gobe kinga yanzu bacci zanyi, nagode Allah yayi miki albarka, I love you..."

Katse wayar yayi yana dariya ita kuma ta katse tata cikeda takaici, tun daga wannan ranar kullum haka yake mata shiyasa wata rana har bata son bude wayarta kuma idan yakira yaji arufe idan yasake kira sai yace mata idan takara kashe masa waya itada Allah, babu yanda ta iya dolenta haka ta hakura ya zatayi da nacin amadi.

Akwana atashi ahaka wannan semester din takare akayi musu hutu ta koma gida yanzu semester daya ya rage mata, time din watan amadi 3 a birnin London,

Kullum cikin kiranta yake sannan kuma ya tsareta lallai lallai sai tayi masa kalaman soyayya ko kuma tace masa i love you, amma wani lokacin bama ya kulata da ya kirata zaice ta hadashi da twins susha hirarsu,

Ganin har yanzu bata kamu da son amadi ba abin yabawa Amira mamaki, gaba daya takasa gane nadiya wacce irin mace ce mai tsaurin rai da taurin kai tunda ai kodan kyautatawarsa agareta itada yaranta ya kamata ace tafara sonshi Sannan bai rageta da komai ba duk karshen wata kudi yana shiga account dinta saboda yace mata yanzu nauyinta akanshi yake,

Wurin nadiyan ta nufa a inda take zaune tana gyara fuskarta su fadeela kuma sun tisata agaba suna son suyi mata kuka wai sai sun bita ita kuma tace babu inda zataje dasu,

"Anty wai sai ina da yamman nan?" Amira ta tambayeta tana kamo hannayen twins,

"Amira gyaran gashin nan zanje saboda wallahi kaina yacika da yawa.."

Karar da wayar nadiya tafara yine yahana Amira yin magana, dauka nadiya tayi saboda ganin amadi ne dama tana son kiranshi ta tambayeshi cewar zata fita,

"Hello baby" taji yafada lokacin data daga wayar,

"Na'am, dama yanzu zan kiraka"

"Sai kuma gashi na kiraki, meya faru?"

"Ina son zan fitane"

"Ina zakije?"

"Gyaran gashi zanje"

"To, waye naji yana kuka?"

"Su fadeel ne wai sai sun bini nikuma bazanje dasu ba.."

"Akai suke kuka kenan?"

"Ehhh"

"To kema bazaki jeba nahana, idan kuma kina son zuwa ki tafi dasu.."

"Ni bazanje dasu ba"

"To shikenan kema ban yarda kijeba dama ai gashin nawane so abar min kayana ahaka basai an gyara ba"

"Bazanje ba kace fa?"

"Ehhh" yabata amsa,

"Hmmm" tafada tareda katse wayar wadda ko ba afada masaba yasan fushi tayi, kallon su fadeel tayi ta hararesu,

"Sai na zaneku idan baku daina yimin kuka ba, shima harda wani cewa bazanje ba to kar Allah yasa yabarni naje din sai me.."

Tafada cikin bacin rai tareda cire dan kwalin dake kanta ta wulla kan gado ta sulale awurin tayi kwanciyarta.

Ba afi mintuna biyar da faruwar hakaba sai gashi ya sake kiranta, kin dagawa tayi shikuma bai hakura yadaina kiraba har saida taji karar ta isheta sannan ta dauka,

"Baby fushi kikayi ko? Kiyi hakuri to, kije nabarki,sai kin dawo..."

Shiru tayi masa tana cije lip dinta nakasa,

"Baby kije nace, kiyi hakuri tunda ranki ya baci, karki yi fushi dani kinji... Uhmmm baby, kinji?"

"Naji"

"To adawo lafiya, ki kular min da kanki"

Kit ya katse wayar, zama Amira tayi akusa da ita,

"Anty nadiya nikam Yaya Ahmad yana bani tausayi, wai har yau kinki sonshi bare ki nuna masa kulawa"

"Lallai Amira bakida hankali, anfada miki ni sakarya ce da har zan sake garajen fara sonshi? Idan ku kun manta da butulcin Yaya kabeer agareni ni ban manta ba,ni yanzu babu filin so acikin zuciyata"

"Karki ce haka anty, ni ina ganin kibawa Yaya Ahmad dama domin ki gane irin son da yake miki, idan kina son fahimtar shi waye akwai hanyoyi da yawa da zaki iya gudanar da hakan"

Lipstick ta dauka tana gogawa lips dinta, "kamar wacce kenan?"

"Kina iya gwadashi ta hanyoyi da dama, ma'ana ki rinka kiranshi ko yi mishi text da wata number ta daban wacce bazai taba tunanin cewa kece ba kinga ta haka zaki fahimci inda yasa gaba"

"To Amira kin kawo shawara kam, bari amir ya shigo zan bashi kudi ya siyo min sabon sim.."

"Yawwa anty ko kefa"

Karasa shiryawa tayi ta mike tayiwa su fadeel wayo ta zare jikinta ta fita bayan ta yiwa mama sallama..

Jama'a wai ina labarin kabeer ne da asabe mc? Mu hadu a page nagaba domin jin inda suka makale.


*_Ummi Shatu_*🏻
[9/10, 8:07 AM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


   *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO.*  _(Home of expert & perfect writers)_

     *60*

aishaummi.blogspot.com

     *K*amar yadda amira tabawa nadiya shawara haka ta dauki shawarar acikin kwana biyu tabawa amir kudi ya siyo mata sabon sim special number,

Dayake wayarta 2 sim ne sai kawai tasashi acikin wayar,kiran amadi tafara yi Amira na zaune akusa da ita amma abin mamaki koda wayar ta shiga sai yaki dauka, kira taci gaba dayi nanma bai daga ba har saida ta kira sau hudu ana biyar dinne taji ya dauka,

Sai da ta lankwashe muryarta ta yadda bazai ganeba sannan tayi magana,

"Hello Ahmad..."

Shiru ya danyi kafin yayi magana,

"Wacece?"

"Amma ai kabari dai ma gaisa ko? Kamata yayi mufara gaisawa kafin nasanar dakai ko ni wacece.."

Kitttt taji ya kashe wayar, dariya Amira tafara yi harda rike ciki saboda jin yadda nadiya ta wani kashe murya dan kar ya ganota,

Sake kira tayi nan ya dauka,

"Haba Ahmad ya zaka kashe wayar bayan bamu gama ba? Dan Allah kayi hakuri wallahi ban son bacin ranka, sunana jalila ni daliba ce a makarantar wudil.."

"To meya faru kika kirani? Sannan waye yabaki number ta?"

"Hmm yaya Ahmad kenan ai duk wannan mai saukine tunda kasan bahaushe yace mai son kayanka yafika dabara, dalilin kiranka kuwa shine agaskiya ka dade kana burgeni gashi ina mutukar sonka.."

Sake kashe wayarshi yayi bai karasa jin bayananta ba, kallon Amira tayi tana dariya,

"Ji yasake kashewa,bari nabarshi haka sai zuwa gobe sai insake kiranshi inji"

Dariya Amira tayi "Allah sarki yaya Ahmad daga jin maganar so sai kuma akashe waya"

"Ke kyaleshi wai shi nan Jan aji, zan kureshi ne ai.."

"Anya kuwa? Anty banga alama ba"

"Kya gani ai..."

Rufe sim din tayi tabar wanda take amfani dashi kawai a bude, shi kam Amadi ko takan maganar ma bai kara bi ba bare ya binciki ko wacece saboda da farko ya tsammaci zee ce kanwar mijin anty siyama amma kuma daga baya sai yagane cewar ba ita din bace nan yayi watsi da maganar domin bama yason yasan ko wacece.

Bayan sallar isha tana tsaka da shirin bacci sai gashi ya kira,

"Baby" yakira sunanta cikin so domin akoda yaushe jin sonta yake yana sake ratsashi,

"Na'am.."

"Bakiyi bacci ba?"

"Yanzu zanyi shiryawa nake.."

"Shiri kuma? Baby wanne irin shiri bayan bana nan? Ki tattara duk shirye shiryenki ki ajiye har sai nadawo"

"Hakane"

"Ko baki yarda ba?"

Bata bashi amsa ba takarasa saman gado tayi kwanciyarta abinta,

"Baby ina yimiki magana shine kika rabu dani ko?"

"To me kakeso ince?"

"Ohhh aiki kike nema kenan ko? To bari inbaki kiyi, kiyita kissing dina har sai nace ki daina ya isheni.."

"Nidai gaskiya wallahi a'a.."

Murmushi yayi, " a'a fa kikace, kifara tun kafin kiyi laifi awurin Allah"

"Wallahi nidai indai haka zaka rinka yimin zan daina daukar wayarka.."

"Idan kin daina daukar wayata ma wani laifinne dai kikayi gara ma ki dauka.."

"Indauka kayita sakani aiki.."

"Menene aikin aciki? Ai ban fara saki aikiba sai nadawo tukunna, yanzu dai fara ina jinki"

Wani haushi ne ya turnuketa saboda jin yana yimata dariya wadda tun yana boyewa har yafito fili,

"Ahmad" takira sunanshi,

"Na'am baby love"

"Meyasa kake yimin hakane?"

"Saboda ke matatace nikuma mijinki ne sirrinki..."

"Shine dalili?"

"Ehh shine, fara ina jinki"

Kamar mai shirin yin kuka haka tafara kissing dinshi ahankali ta cikin wayar, tafi minti biyar tanayi amma baice ya isa ba sai da ta kusan mintuna goma sannan ya dakatar da ita,

"Baby barshi haka dan wallahi za a iya samun matsala idan kikaci gaba dayi gashi kuma bakya kusa"

Shiru tayi masa saboda yanzu taga yagama zama marar kunya bata san meyasa ba kwanan nan wasu maganganu yake zarowa yafada mata kuma idan yafada ko a kwalar rigarshi babu ruwanshi da jin kunya,

"Washhh, baby wallahi yau akwai matsala..."

"Nikuma meye nawa aciki?" Tace dashi tana turo baki kamar yana ganinta,

"Meye naki aciki? Kekuwa kikeda ruwa da tsaki aciki tunda mijinki yana bukatarki yanzu gashi bakya kusa dashi"

Shiru tayi masa tana sauraron yanda yake yi mata wani ajiyar zuciya akunne,

"Nifa kaga ka cika min kunne gaskiya idan ka gama wannan ajiyar zuciyar taka ka kirani.."

Shiru taji yayi wanda tasan kasa maganar yayi badan hakaba da tuni ya bata amsa,

"Ina magana kayi min shiru..."

Har lokacin dai bai iya yimata magana ba yayi shiru abinshi sai ajiyar zuciyar da yake ta faman ajiyewa daga bisani kuma yafara wani tari babu kakkautawa sai da yajima yana yi sannan tarin ya tsaya sai kuma shakuwa, shak'uwa yake yi sosai,

"Maganinka ai, gobe ma dan Allah ka kara.." Tafada ahankali, ashe yaji abinda ta fada,

"Baby..." Taji yakira sunanta amma kuma sai yayi shiru saboda shakuwar da yaketa yi,

"Ya?" Tafada tana dariyar mugunta,

"Da biyu kikayi min wannan abun ko?"

"Bawani da biyu, bakaine kasani ba? Harfa rokonka nayi akan karnayi amma kaki kace sai nayi maka"

"Hmmmm" yace yana murmushi,

"Kaje kasha ruwa ko zaka daina wannan shakuwar.."

"Babu ruwanki dani malama.." Yace da ita wanda har lokacin shakuwar taki barinshi, jin abin bamai karewa bane yasashi tashi yaje ya dauko ruwa yadawo ya kwanta,

"Kaima ance maka kasha ruwa kaki"

"Gashi ai zan sha"

Saida ya shanye robar ruwa guda daya amma shakuwar bata barshi ba, nan kuma nadiya tasan abin nashi ba karami bane,

"Wai baka sha ruwan ba?"

"Wallahi nasha, roba dayafa na shanye baby"

"Ohh to zata daina"

Shiru yayi mata yaci gaba da shakuwarsa zuwa can sai yaji ta tsaya yadaina yi kwata kwata,

"Tunda kadaina shakuwar to saida safe ni bacci nakeji"

"To baby saida safe, i love you"

"Uhhhum"

Katse wayar tayi ta turata karkashin pillow, dariya ce ta subuce mata lokacin da ta tuno amadi,

"Yaro yasha tafi karfin cikinsa, maganinka ai" tafada tana dariya, nan bacci ya dauketa tayi abinta cikin kwanciyar hankali shikuwa bawan Allah yana can yakasa bacci sai juyi yake yi saboda kewar matarshi data dabaibayeshi.

Washe gari da safe nadiya ta sake kiranshi da sabon sim din da ta siyo nan yaki dauka tayita kira amma bai dauka ba daga karshe sai ta tura masa da massage cewar ita masoyiyarshi ce kuma sonshi take, ko takan text din baibi ba bare ya turo mata da reply,

Hakura tayi ta rufe sim din tunda taga alamun kamar bazai kulaba ai kuwa bai kula dinba shi duk da bai san wacece ba bata burgeshi ba domin mace daya ce kacal ke burgeshi a duniya itace nadiya kuma ya rigada ya mallaketa,

Kiranta yayi awaya lokacin tana kitchen tana soya miya, fadeela ce takawo mata wayar tana yimata surutu,

Karba tayi ta kara akunnenta,

"Baby yakike?"

"Lfy lau"

"Yau banji kiba, kina lafiya?"

"Lafiya lau"

"Ya twins dina?"

"Lafiya"

"Me kikeyi yanzu?"

"Aiki nake"

"Nikuma kin ganni nadawo gida duk agajiye da ace kina kusa da kinyi min tausa ko?"

"Uhmm" tafada tana juya miyar da takeyi,

"To yanzu me zaki bani duk da bakya kusa?"

Shiru tayi batayi magana ba,

"Baby"

"Na'am"

"Kice you love me"

"Dan Allah kayi hakuri basai nafada ba"

"Why? Gaskiya bazan hakura ba har sai kin fada sannan kiyi kissing dina.."

"Ka manta jiya ko?" Ta fada afili amma acikin zuciyarta cewa take "babu abinda zanyi maka bare ka cika min kunne da wannan shakuwar taka da ajiyar zuciya"

"Baby yi mana ina jinki.." Taji yafada a marairaice,

Daga murya tayi tace "na'am mama, to gani nan"

Jin haka yasashi rabuwa da ita saboda a tunaninshi mama ce ke kiranta,sallama yayi mata ya kashe wayar anan ta ajiye wayar taci gaba da aikinta. Tun daga wannan lokacin duk sanda ya kirata aikin da yake sakata kenan amma sai taki sai taji yana neman barinta da Allah sannan sai tayi amma kuma da zarar tafara zataji ya dameta da ajiyar zuciya ko shakuwa shiyasa ma bata son ta rinka biyeshi tana yimishi abinda yasata din,

Daren yau kam akalla sai da ya shafe awanni biyu yana wannan shakuwar,duk rashin tausayinta akanshi yau sai da taji yabata tausayi wanda bata san dalili ba,

"Sannu Ahmad.."

"Yawwa baby"

"Kasake shan ruwa"

"To baby"

Tana jinshi yana shan ruwa amma koda ya shanye sai yaci gaba da shakuwar, dakyar yasamu ya daina,

"Baby da zaki yarda da na turo miki kudin jirgi kin biyoni"

"Ka manta alkawarin da kayine? Idan na biyoka me zanyi maka?"

Ajiyar zuciya ya saki mai karfi,

"Kuma fa hakane, sorry mantawa nayi"

Jin yadaina shakuwar yasashi yi mata sai da safe ya katse wayar.

Akwana atashi har amadi ya kwashe watanni 8 a kasar london wanda yanzu har yafara lissafin dawowa,ita kam nadiya basu koma makaranta ba saboda yajin aiki da aketa gudanarwa,duk abin baiyi mata dadiba domin bata son ta tare bata gama makaranta ba,

Shiryawa tayi ta tafi sumaila gidan umman sumaila bayan ta sanarwa da amadi dama shi ba hanata fita yakeba daga tace zataje wuri kaza zaice adawo lafiya babu ruwanshi da yimata kulle,

Lokacin da taje gidan umman sumaila, umman murna tayi sosai da ganinta saboda dama tanada niyyar zuwa ranon itama domin kayan gyaran da tasa aka tanada musamman saboda nadiyan,tunda takai kanta kuwa nan umman ta shiga tula mata abubuwa, wasuma bata taba saninsu ba bare ganinsu,

Shikuma dan nacin nata akoda yaushe yana tareda ita a waya, ko abinci yake ci sai ya kirata kome yake yi sai ya kirata,

Sabon sim din da ta saka domin kiranshi kuwa harma ta daina kiran saboda baya dagawa ita abin har daure mata kai yayi.

Gyara na musamman umman sumaila ke yimata baji ba gani, ita duk ma tagaji da dure duren da ake yimata  gashi umma ta hanata tafiya, ita da taje da niyyar sati uku saida ta shafe fiyeda sati shida har saida akace an janye yajin aiki sannan umman ta kyaleta ta tafi amma tace zata rinka yi mata aike kuma lallai lallai duk abinda aka kai mata tayi amfani dashi,

Tana komawa gida tafara shirin tafiya makaranta saboda Allah Allah take yi tagama makarantar kafin amadi yadawo amma tasan hakan ba mai yiyuwa bane tunda shi yanzu saura watanni biyu kacal yadawo.

Sai da ta tanadi komai na bukata sannan ta tafi wudil can dinma dai da kayayyakin umman sumaila ta tafi wadanda yanzu har ta saba dasu,

Kan karatunta ta mayar da hankali sosai, koda wanne lokaci amadi yana kiranta, wata rana ai fada wata rana ayi dadi kun san halin mutuniyar taku da taurin kai, amadin ne kadai ya iya da ita saboda shi mai hakuri ne sannan bashida riko domin ko fadan akayi ba ayin minti biyar zai sake kiranta nan zai shiga lallashinta yana bata hakuri koda kuwa shi dinne da gaskiya, yawancin fadan ma shine mai gaskiyar amma sai yayi hakuri ya dauki laifin ita yabata gaskiyar yayita rarrashinta yana bata hakuri har sai ta hakura, ita kanta ta san yana tsananin sonta kawai dai zuciyarta ce har yanzu bata sauko ba daga fushin baya.

Yau da gobe babu wahala awurin Allah domin amadi har ya kammala abinda yaje yi yafara shirye shiryen dawowa, wani boutique yashiga ya rinka jibgowa nadiya sexy dress, duk kayan da ya siyo mata babu wanda zata iya sakawa ta fita koda tsakar gida sai dai adaki domin kayane na garari,

Koda wasa bai fada mata dawowarshi ba shiru yayi mata, kullum yana yi mata waya kamar yadda ya saba amma ranar da zai dawo sau daya ya kirata daga nan sai bata kara jinshi ba.....


*_Ummi Shatu_*
[9/11, 9:22 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...*🌹
      _(Labarin k'auna)_


   _*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_

   _Kuna ina? A'isha chuchun gaye, A'isha Dansabo, A'isha Gambo, A'isha (Maman khadija),A'isha (mom minal) wannan shafin nakune takwarorin Ummi Shatu.._

       *61*

aishaummi.blogspot.com

   *K*asancewar shigowar yamma yayi sai bai samu zarafin kiranta da wuri ba,

Yana ajiye jakarshi ya nufi part din da aka gina musu shida nadiya domin baya son asamu kuskure daga yanda ta zana,

Part din ba karamin kyau yayiba amma babu abinda aka zuba na furnitures, yanda nadiya ta zana haka akayi shi babu abinda aka sauya,

"Wowwww.." Yafada bayan ya zira hannuwanshi acikin wandon jeans dinshi,sai da yabi ya dudduba ko ina sannan yafito yakoma part din hajiya,

"Autana ina kaje ne inata nemanka, kazo kayi wanka kaci abinci mana"

Hajiya dake tsaye cikin falon ta fada,

"Hajiya part din baby naje nagano, bana sone ayi mata ba yanda ta zanaba asamu problem, amma naga komai yayi daidai.."

"Ohhh autana da rawar kai kake, tunda ka dawo ai sai akawo maka ita ku tare kowa ya huta"

"Yawwa hajiya dan Allah kisa baki nanda 2 weeks ta tare.."

"To shikenan autana, yanzu dai shiga dakinka kayi wanka kafito kaci abinci, nayi maka mutumin naka wato tuwo"

"Woohhhhh" yafada harda dan tsallenshi sannan yawuce dakinshi.

  Nadiya kuwa koda taji amadi shiru bata kawo cewar yadawo ba kuma bata kirashi ba, har dare yayi shiru bata jishi ba,

Bayan ta kwanta ne misalin karfe 9 sai ga kiranshi koda ta duba ba number din waje bane dan haka taji mamaki ya kamata,

"To shi wannan ya haka?" Ta tambayi kanta tareda kara wayar acikin kunnenta,

"Baby.."

"Uhmm"

"Shine ko ki nemeni ko bayan kuma kinji ni shiru"

"To ai nasan lafiya kake tunda najika shiru"

"Hakane, to nadawo dazu, yaushe zaki zo yimin sannu da zuwa?"

"Kadawo?"

"Wallahi nadawo baby"

"Sannu da dawowa"

"Yawwa yaushe zaki zo kiyi min sannu da zuwa? Ko nine zanzo?"

Shiru tayi tana tunani,

"Sannu da zuwa kuma? Bayan wanda nayi maka yanzu"

"Haba baby yanzu ai ba sannu da zuwa kika yimin ba, idanuwana fa suna bukatar ganin fuskar matata ko kin manta yau rabona dake 11 months da yan kwanaki akai? Allah ina son ganinki.."

"To yanzu ya kakeso ayi?"

"So nake kizo gobe, zan turo driver ya daukeki, wallahi son ganinki nakeyi"

"Allah ya kaimu goben idan banida uzuri da yawa to"

"Insha Allah ma bakida shi baby"

Dakyar dai yasamu ya dan lallasheta ya shawo kanta harta amince cewar zataje din nan yayi mata sallama ya katse wayar saboda bacci yakeji.

Washe gari kuwa koda ya kirata saida ta gama jan ajinta sannan tace yaturo drivern, shidai ta inda take so tanan yake binta, lallabata yakeyi saboda baya son taki amincewa da zuwan,

Wurin 12 daidai na rana suka karasa gidan, iya hajiya ta tarar a babban falonta ita da mai aikinta, hajiyan tana sanye da glass a idonta suna shirya bit,

A kunyace nadiya ta shiga cikin falon,cikeda murna gamida soyayya hajiya ta tarbeta,kai idan ba sani kayiba bazaka taba cewa hajiya surikarta ce ba saboda irin tarbar arzikin da tayi mata,

Lokaci kankani aka cikata da kayan marmari gamida kayan jika makoshi, jin bataji motsinshi ba yasa ta fara kiranshi awayarta amma kuma wayarshi akashe,

Ta jima zaune afalon itada su hajiya lokaci lokaci hajiya tana dan yimata hira har tsawon mintuna 20,

"Autan yana dakinshi yanata faman bacci tashi ki shiga" hajiya tace da ita tana murmushi,

"Wai dama komawa yayi?" Mai aiki ta tambayi hajiya tana dariya,

"Kema kuwa ai kin san halin auta da shegen baccin safe sai yakai azahar yana baccin nan, aida ya fito sake komawa yayi.."

Ita dai nadiya tana zaune bata tashiba har saida hajiya tasake ce mata ta shiga sannan ta tashi akunyace ta nufi dakin nasa,

Ahankali ta bude ta shiga,nan wani kamshi mai dadi ya doki hancinta wanda ya gauraye da sanyin air condition din dake sanyaya dakin,dakin ya tsaru mutuka kamar dakin mace,

Kwance ta hangoshi akan gadonshi daga shi sai gajeren wando da round neck t shirt sai sharar bacci yake yi abinshi batare da damuwar komai ba,

Karasawa tayi zuwa bakin gadon ta zauna, tashinsa tafara yi,

"Ahmad.... Ahmad" ta kira sunanshi ahankali,

Ko motsi baiyi ba bare yasan tanayi, hannu takai jikinshi tafara dan dukanshi,

"Ahmad..."

Idonshi ya bude wadanda suka yi ja saboda tsabar bacci,

"Uhm uhmmm baby..." Yafada yana kokarin tashi zaune, bata ankara ba kawai sai ji tayi ya rungumeta,

Binta da kallo yakeyi sosai domin ba kadanba ta canja mishi, kamar yadda itama take ganin ya sauya sosai, dama shi farine sosai to farinshi na yanzu yafi nada sannan ya danyi yar kiba amma ba mai yawa ba,

Shi kam ganin nadiyan shi yayi ta cika sosai tako ina, wata atamfa ce kalar purple ajikinta,dinkin ya zauna daram ajikinta, riga da skirt, sannan tayi simple daurin dan kwali tana sanye da wani gyale shima purple colour,

Jikinta take kokarin janyewa bayan ta bata fuska,

Riketa yayi kam yana murmushi nan yafara kokarin lalubar bakinta amma taki tanata faman kawar da kanta, murmushi yayi,

"Baby nadawo zamu fara ko? Za afara yimin rowar da aka saba..."

Ganin taki yarda yasashi fara kissing din wuyanta, tureshi tafara yi har tasamu nasarar tureshi din ta matsa gefe,

Kallonta yayi fuskarshi dauke da murmushi baiyi fushi ba yasake matsawa kusa da ita nan ta matsa shima yasake matsawa,

"Dama dalilin da yasa kasa a daukoni kenan?"

"A'a baby ba dalilin kenan ba but kin san dai nayi missing dinki da yawa shiyasa..."

"To nidai gaskiya a'a.." Tafada tana zumbura bakinta,

"Baby pls karkiyi min haka.."

Dauke kanta tayi, ya bude bakinshi kenan da niyyar yimata magana yafasa saboda tarin da ya sarkeshi nan yafara yinshi babu kakkautawa,

Juyawa tayi ta kalleshi,

"Sannu"

Kai ya daga mata kafin yafara shakuwar da yasaba,

"Indauko maka ruwa?"

Hannunta ya kamo yajata jikinshi, yanzu kam maganar daru takare tunda taga halin da yake ciki, shiru tayi tai luf ajikinsa amma har lokacin wata irin shakuwa yake yi k'wat,

Bakinta ya luluba da nashi cikin doki abin mamaki ko minti daya ba ayiba taji yadaina shakuwar,

"Nikam yau nashiga uku kuma" tafada acikin zuciyarta,shikam amadi tunda har yasamu dama bai tsaya awuri daya ba.

Sai da yaji nutsuwarshi ta dawo mishi sannan ya kwantar da ita ajikinshi,

Hannunta Yakama acikin nashi,yafara yi mata rada akunnenta,

"Baby ga maganin shakuwar awurinki amma da zakice wai zaki dauko min ruwa..."

Murmushi ya sake yi yana kallon fuskarta, idanuwanta arufe fuskar nan gata nan dai babu yabo babu fallasa,shi gaba daya yarasa nadiya wacce irin macece wadda bata da saurin manta abu koda yake yasan sai ahankali zata manta da wulakancin kabeer har takarbi soyayyarshi domin dauriya da hakurin da tayi ba kowacce mace ce zata iyaba,

Kissing din wuyanta yayi sannan yafara jan dan kwalin kanta nan tarike hannunshi,

"Karka cire min dan kwali.."

"Saboda me?"

"Kawai"

Murmushi yayi, "baby rigima, badai kawai ba,ina son ganin kalar kitson dake kan matata ne"

"Ni babu kitso akaina"

"To zan gani haka"

Juyi tayi zata matsa daga jikinshi yayi saurin rikota ya mayar da ita,

"Baby dadina dake rikici kuma rikicin ma narashin gaskiya, inbanda haka nida mallakina amma ahanani?"

Saida ta zunbura masa baki sannan ta bude da niyyar yimasa magana, ruf ya rufe bakinta da nashi, neman kwacewa tafara yi amma kuma takasa dolenta ta hakura domin yau tasan ita takawo kanta gareshi,

Idonshi dake lumshe ya bude ya kalleta, mayar da kanshi yayi saman kirjinta ya kwantar yana sauke mata ajiyar zuciyar da yasaba yi mata awaya,

"Ka matsa zan tashi" tace dashi tana dan harararshi,

Baiyi mata magana ba illa kankameta da yasake yi,

"Nace ka matsa zan tashi.."

Nan dinma shirun yayi mata sai wata ajiyar zuciya da yake ajiyewa ahankali,

"Ai da nasan haka ne da bazan zo ba, daga zuwa na shikenan kuma kawai...." Hannunshi yakai ya rufe mata baki,ture hannun nashi tayi,

Baice da ita komai ba saida yagama sauke ajiyar zuciyarshi sannan yajuya kanshi akan kirjinta yana murmushi,

"Allah yabaki hakuri ya huci zuciyarki baby, karfa ki manta raboda dake shekara guda kenan kuma yanzu zuciya taga abinda take so take kauna sannan take bege bazata yi wani feelings ba?, wallahi wannan sakonnin badaga gareni bane daga zuciyata ne, ita keso itake muradi.."

Hannunshi yakai saman kirjinta nan ta buge hannun,yasake mayarwa ta sake bugewa yasake mayarwa ta kuma bugewa,

"Idan kika sake buge min hannu ban yafe miki ba har lahira.."

Ta inda yake cin galaba kenan idan ya hadata da Allah, tana ji tana gani dole ta rabu dashi tunda yace bai yafeba idan tasake buge masa hannu,

"Allah nan gaba ko kace inzo bazan zo ba" tafada kamar zata saka kuka,

Kiyi hakuri.." Shine abinda ya iya cemata, shiru tayi masa ta dauke kanta,

Har lokacin sallar azahar yayi suna nan tare ita dai nadiya duk yagama takurata, dan tureshi tayi,

"Dan Allah kabari ni fita nake son yi"

"Ina zakije inda yafi nan?"

"Wurin hajiya zanje.."

"A'a, ita hajiya babu ruwanta da dadewarki anan tunda tasan wurin mijinki kika zo sannan yadade bai ganki ba..."

"Nidai dan Allah kabarni intafi"

"To zan barki amma sai kinyi kissing dina sau 30"

"Gaskiya a'a" tace dashi tana zunburar baki,

"To narage miki kiyi guda 20"

"A'a"

"Allah sai kinyi, fara tun kafin mala'iku su fara tsine...."

Tashi tayi tana harararshi fuskarta babu fara'a, nan tafara abinda yace ta shiga kissing din bakinshi mai dauke da jajayen lips,

"Ai nayi sai anjima kaga tafiyata"

Daukar mayafinta tayi da dan kwalinta ahannu saida taje bakin kofa sannan ta tsaya tafara daura dan kwalin,

"Bari nataso..." Taji yafada ba shiri ta bude kofar da sauri zata fita, dariya taji yayi, toilet ya nufa yana cewa,

"To da wasa nake yimiki.."

Duk da haka dai bata koma cikin dakin ba falo tawuce wurinsu hajiya, hajiyan na kokarin tashi nadiyan tafito bedroom dinta ta shiga mintuna kadan ta leko tace nadiya ta shiga tayi salla.

Amadi kam cikeda farin ciki yayi wanka ya fito yayi salla sannan yasa kayanshi ash colour din t shirt da yellow din rubutu ajiki manya anrubuta _FUN TIME_ sai yellow colour din trouser, hatta belt din da ya daura yellow colour ce, turarenshi na axe yafesa sannan ya fita, fitarshi tayi daidai da fitowar su hajiya itada nadiya,

Kan table suka wuce direct amadi sai kallonta yake yana yi mata murmushi amma ita taki koda kallonshi ne, hajiya diban abincin ta tayi a flate tabasu wuri ta nufi falo taje tayi zamanta tana kallon labarai a CNN,

Matsawa yayi kusa da ita ya dauki flate ya zuba musu jalop din couscous wanda yasha hadin kayan lambu yayi kyau sosai,

"Kaga ka kori hajiya daga nan" tafada tana kallonshi, dan lips dinshi ya lasa,

"Baby bani fa nakoreta ba, kawai dai tabamu wuri ne..."

Bata sake magana ba tayi shiru, abincin yafara diba yana bata shima yana ci amma yasha daru da rigimarta kafin ta yarda taci abincin, diba yake a spoon ya bata idan ta diba taci sai yaci wanda ta rage acikin spoon din,

Suna tsaka da cin abincin anty siyama tayi sallama zee kanwar mijinta na biyeda ita cikin wata shiga ta alfarma.....

_Get well soon luvly sister @Khairat Dandawaki_

_Fatan alkhairi agareki stylish bitch_

_Gaisuwa mai yawa ga duk masoyan anty amadi... Musamman kawata maryama qaumi_

*_Ummi Shatu_*
[9/12, 9:50 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


   *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO.*  _(Home of expert & perfect writers)_


        *62*

aishaummi.blogspot.com

    *T*un daga nesa zee ta kafe amadi da ido tana kallonshi domin ba karamin kyau yayiba, yayi mutukar tafiya da hankalinta gamida tunaninta gaba daya cikin lokaci kankani,

Dan kallon nadiya tayi nan ta fahimci itace matar shi dan haka tayi saurin dauke idonta daga gareta ta mayarshi kan amadi,

"Anty amadi duri aketa yine haka?" Anty siyama tafada fuskarta dauke da fara'a tana faman karkada key din motarta dake hannunta,dago da kanshi yayi shima fuskarshi dauke da fara'a ya kallesu, saida gabanshi ya dan harba sakamakon ganin zee da yayi domin bai so ganinta ba kwata kwata a wannan lokacin saboda yasan zaiyi wahala idan batayi abinda zai b'ata mishi shirinshi ba,

Kallonta yayi sosai tayi kyau cikin wani dark blue din material dinkin doguwar riga, fuskar nan sai sheki takeyi saboda kwalliyar da tasha, kanta daure da wani hamshakin gwaggwaro, tamkar wacce zataje dinner ko kuma zaben sarauniyar kyau, dan mayafinta kuwa akafadarta guda daya kawai ta ajiyeshi batare da ta koda yafashi ba,

Saida yasakawa nadiya abinci abakinta sannan yayiwa anty siyama magana,

"Kai anty dan Allah, wai ya akayi kika daina fadin yayan ne.."

"Saboda kai ba yayana bane..."

"Sannu da zuwa anty siyama" nadiya tafada wadda maganarta ce ta katse hirar anty siyama da amadi,

"Yawwa amaryar mu, har anzo tarbar angon ne?"

Sunkuyar da kai nadiya tayi tana murmushi abinta cikin kunya,

"To ba dole ba, aini dan gatane.."

Dariya anty siyama tayi tajuya tawuce falo wurin hajiya, ita kuwa zee tana tsaye rikeda waya a kunnenta tana magana ahankali sai wani kashewa amadi ido takeyi,

Koda wasa bai nuna ya santa bama bare nadiya ta kawo wani abu acikin ranta, ci gaba da bata abincin yayi har suka cinye wanda ya zuba musu,

Cikeda yanga da jan aji zee tabar wurin itama ta nufi falo batare da tayiwa amadi magana ba,

Kallon nadiya yayi, "baby akara abincin ko kin koshi?"

"Nakoshi"

Murmushi yayi ya tsiyayo juice acikin glass cup yakai saitin bakinta nan ta sha sannan ya tsiyayi ruwa yabata,

"Baby anya yau ma baki sa nayi over feeding ba, kinga nakasa motsi..."

Hannunta ya kamo ya mike tsaye nan itama ta tashi suka nufi falo, suna zuwa daf da falon ta fincike hannunta daga cikin nashi, juyawa yayi ya kalleta,

"Haba baby..." Yaceda ita tareda langabe kanshi gefe guda,

"To ahaka da kakeso muje wurinsu hajiyan.. " tafada tana harararshi,

"Ehhh mana" yaceda ita da nufin tsokanarta,

"Wallahi a'a"

Janta zuwa jikinsa yayi nan tasa iya karfinta ta tureshi,

"Kai kika ture ni? Kamota nan..."

Da sauri tayi wuf ta fada falon tabarshi atsaye awurin yana yimata dariya, duk abin nan dake faruwa akan idon zee yafaru nan taji zuciyarta tayi baki saboda tagama kwallafa ranta akan amadi sannan tana mutuwar sonshi shiyasa lokacin da anty siyama tace mata yayi aure haukane kawai batayi ba,

Kusa da anty siyama nadiya taje ta zauna tana gaidata nan suka gaisa kowannensu fuskarshi asake,

Cikin falon yakarasa hannunshi rikeda robar ruwa yana sha, akusa da nadiya ya zauna,

"Autan hajiya ansauka lafiya ?"

"Lafiya lau anty.."

"Ai dama nace bari muzo sannu da zuwa tunda wuri kafin mu shiga bakin list"

Dariya ya danyi ya kalli zee wacce tawani kafeshi da ido ko kifatawa bata yi,

"Ashe dai kema kin san idan baki zo dawuri ba hajiya zatayi fushi dake.."

Dariya hajiya tayi "auta abin harda su fushi kuma"

"To hajiya ai duk wanda baizo ba ya cancanci fushinki.."

"To wannan kuma da hamida kake itada anty Dija yaro tunda nikam nazo"

Murmushi yayi ya kalli nadiya, "baby ga ruwa"

"Girgiza masa kai tayi, nifa tafiya ma zanyi.."

"Ko zaki tafi sai munje kinga part dinki tukunna, taso muje kiga"

Ayanda suke maganar babu wanda yajisu balle yasan abinda suke cewa, mikewa yayi itama tatashi, kallonsu anty siyama tayi,

"Matar auta sai ina?"

"Anty ginin gidanta zan kaita tagani"

Murmushi anty siyama tayi, "dakyau autan hajiya"

Bai jira komai ba yajata suka fice daga falon, kallon zee anty siyama tayi,

"Zee muma zo muje mugani, nifa kullum ina gidan nan amma ban taba zuwa Nagani ba"

"Ai kuwa dai kuma kuje ku gani kar ayi babu ku" inji hajiya,

Mikewa sukayi suma suka fita suka marawa su amadi baya,

Su amadi na fita daga cikin falon ya dubi mutuniyar tashi,

"Baby yanzu fa idan akace kije can acikin 5 minutes bazaki iyaba..."

"Ehhh saboda ga giwa ko"

Kafadarta ya sakalo hannuwanshi akai ya karata da gefen jikinshi,

"To tunda kina tantama mu gwada mana, wallahi tsaf zan rigaki zuwa.."

"Ni babu wani gudu da zanyi yanzu"

"Allah sai kinyi, tsere zamuyi so get ready..."

"Gaskiya ni kana wahalar dani"

"Yi hakuri muyi, idan kuma kinki kin san sauran kawai zan barki da Allah ne"

Sakinta yayi ya sunkuya,

"Get ready, 1...,2...,3..."

Gudu yasa yayi gaba yabarta, badan tasoba ita dinma tabi bayanshi aguje, saida ya karasa ya tsaya sannan ita kuma ta isa tana haki,

Sunkuyawa tayi ta dafa gwiwowinta saboda har ta dan gaji a wannan gudun da tayi,

Dago da ita yayi yadauketa abayanshi yayi ciki da ita,

"Baby ke raguwa ce, daga yin dan wannan gudun shine zaki fara yimin haki kamar wacce ta shekara tana gudu..."

Lumshe idonta tayi har lokacin tana gadon bayanshi agoye,

"Dama ai nafada maka wahalar dani kawai kake son yi.."

"Ba wahalawar bane baby, kidai shirya domin agidan nan kullum nida ke sai munyi wasan tsere.."

"Gaskiya bazan iya ba kuma zai iya saka min ciwon kirji.."

"To naji, amma daga bedroom zuwa falo fa?"

"Shima bazan iyaba"

Murmushi yayi yasake rungumeta,

"To acikin daki fa akan bed..."

Shiru tayi saboda ta gano Inda maganar tashi tasaka gaba,

Kitchen yafara kaita har lokacin bai sauketa ba tana bayanshi,

"Nayi miki magana kinyi shiru ko?"

Nan dinma shirun tayi masa amma kuma ta bude idonta tana kallon irin dukiyar da aka zuba acikin kitchen din, komai na amfani da wuta gashi nan burjik abun ba acewa komai, suna kokarin fita daga cikin kitchen din su anty siyama suka shigo, saurin sauka tayi daga bayanshi cikeda kunya, ita anty siyama ma sam bata luraba amma zee ita taga lokacin da nadiya ta sauka daga bayanshi,

Nan suka rankaya gaba dayansu suka fara zagaya dakunan da dukkan sauran wuraren dake cikin part din,

Wani pipe amadi ya hango tawaje nan yabi ta dan corridor din dake tsakanin falon da dakin shakatawa yafita,

Dama zee alla alla take ta kebe dashi dan haka ta faki ido tabishi, yadawo kenan zai shigo sai gata adaidai corridor din tana rikeda kofa tana kallonshi, ja yayi ya tsaya yana dubanta,

"Zee ya akayi kuma?"

"Amadi bakayi min adalci ba, ka cutar da zuciyata ka wahalar da ita bayan kuma kasan irin dunbin son da take yimaka..."

"Zee kiyi hakuri kinga yanzu ina tare da wife dina bana son ta zargi wani abu.."

Sakin kofar tayi ta taka ahankali ta karasa gareshi idanuwanta suna zubar da kwalla,

Tana zuwa batayi wata wata ba ta fada jikinshi ta rungumeshi, shikuma ganin halin da take ciki sai bai hanata ba yakyaleta dan ko zata samu sassauci acikin zuciyarta domin shima yasan so yasan zafinsa kuma yasan dafinsa musamman ma idan kai keson mutum shi baya sonka,

Hannuwanta ta sakala ajikin wuyanshi hawaye na malala akan kuncinta,

"Wallahi Ahmad kaine namijin da nake so arayuwata, ina jin sonka har cikin jijiyoyin jikina..."

"Zee kiyi hakuri, shi aure mukaddari ne.."

"Nidai ina son ka aureni, nayarda zan zauna da matarka..."

Daidai lokacin nadiya ta nufo wurin domin ta hango wasu shuke shuke abaya wadanda suka yi mutukar jan hankalinta,

Cikeda tausayawa amadi ke kallon zee musamman ma da yaga tana kuka, dagoda idonta tayi ta kalleshi, batayi wata wataba ta manna bakinta kan nashi,

Nadiya da tafito dan zagayawa baya nan idanuwanta suka gane mata amadinta rungume da zee bakinshi kan nata......


*_Ummi Shatu_*🏻
[9/14, 8:59 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
     _(Labarin K'auna)_


    _*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*  _Home of expert & perfect writers_


     _Gaisuwa ta musamman ga aminiyar kwarai cwt KAUSAR LUV.._

_Fatan alkhairi ga STAR GIRL.._

          *63*

aishaummi.blogspot.com

    *C*ikin kissa da jan hankali zee tafara kissing din bakinshi,

Tsaye nadiya tayi tana kallonsu gabanta yana faman dukan uku uku, jikinta har wani rawa yake yana tsuma, bazata iya tantance yanayin da take cikiba saboda rudun da ta shiga,

Kamar ance ya kalli wurin da nadiya take nan ya hangota tsaye babu shiri yayi azamar ture zee daga jikinsa hankalinsa atashe,

Tun kafin ya ture zee daga jikinsa nadiya ta juya tabar wurin cikin tashin hankali,

Baibi takan zee ba ya nufi wurin da nadiya ta nufa har yana cin tuntube, shi kansa yasan yayi kuskure da har yabar zee ta rungumeshi tayi kissing dinshi yanzu yasan gaba daya plan dinshi yagama rushewa sannan nadiya dakyar idan zata amince dashi har ta soshi tunda ada ma ya aka kare,

"Baby... Baby..." Yakira sunan nadiya wanda har yana hadawa da dan gudu akan saurin da yake yi,

Ko sauraronsa batayi ba ta nufi part din hajiya, sauri ya kara akan wanda yake yi da,

"Baby dan Allah ki tsaya kiji, dan Allah.."

Ko kulashi batayi ba illa tafiyarta da taci gaba dayi,

"Baby..." Yafada yana biye da ita cikin sauri wanda har yana buge kafarshi da wani katon dutse amma baiko tsaya ba duk da irin zafin radadin da yaji yana shiga cikin kafar tashi,

Jan kafar tashi ya rinka yi tana yimasa zugi da haka har ya cimmata, gyalenta ya riko nan ta tsaya cak batare da ta jiyo ba,

"Baby dan Allah ki tsaya inyi miki bayani.."

"Bayanin me? Bayan abinda idona ya gane min harda sauran bayanin da zakayi min? Ai shi bayani ana yinshi ne a inda ba aga zahiri ba amma yanzu ni babu bayanin da nake bukata daga bakinka tunda idanuwana sun gane min komai..."

"Ohhhh my God! Haba baby karki bari shaidan yayi tasiri acikin zuciyarki.."

Juyawa tayi ta kalleshi idanuwanta sunyi mutukar ja kamar wacce ta jima tana kuka,

"Idan ni ban bari shaidan yayi tasiri agareni ba kai ai kadade da barinshi yayi tasirin agareka tunda har ka iya rungumar matar da bataka ba kuma baka tsaya a iya nanba har saida ta kaika ga shan bakinta, shiyasa nabaku wuri ai kuje ku karasa abinda kukayi niyya..."

Gabanshi ne yayi mutukar faduwa nan take zuciyarshi ta harba saboda jin abinda tafada badai zarginshi da neman mata nadiya takeyi ba? Tambayar tazo cikin kwakwalwarshi batare da ya shirya ba,

"Baby dan Allah karki yimin zargin zina ko neman mata wallahi tallahi haka bai taba faruwa daniba, wallahi ban taba rungumar kowacce maceba sai ke itama wannan din wallahi yaune hakan tafaru dan Allah ki tsaya ki saurareni..."

"Yayi kyau kuma ni dama bance kana aikata zina ba, sakar min mayafi zan tafi.."

Sake rike mayafin nata yayi sosai ya matsa kusa da ita nan taja baya da sauri kamar wacce taga wani abun tsoro,

"Baby, baby karki yimin haka dan Allah, dan Allah ki saurareni kiji abinda zan fada miki, wallahi kece mace tafarko da nafara romancing kuma wallahi bayan ke ban taba gwada yi da wata maceba, wallahi yau ma bada nufin naji dadi ko wani abu makamancin haka nayi ba.."

Tana niyyar bashi amsa kenan ta hango su anty siyama da zee suna tahowa dan haka tayi shiru ta dauke kanta,

"A'a anan kuke tsaye..." Anty siyama tace dasu daidai lokacin da sukazo daf dasu,

"Ehhh anty" amadi yafada yana kallon fuskar nadiya,

"Wallahi wuri yayi kyau Allah yasanya alkhairi yasa wurin zamanta ne har abada..."

"Amin anty" ya amsa mata still dai idonshi nakan nadiya,yana rike da mayafinta tamau,

"Amaryar mu yaushe zaki tare to?"

Murmushin dole nadiya ta kakalo tayi amma batace komai ba,

"Anty sai nanda 3 weeks" inji amadi,

"Ato Allah yakaimu"

Wucesu sukayi zasu shige nan zee ta kalli nadiya, itama nadiyan kallonta tayi idanuwanta jajur, wani dan malalacin murmushi zee ta jefeta dashi sannan ta dauke kanta,

Saida taga shigewarsu anty siyama cikin part din hajiya sannan ta dubeshi,

"Nifa kaga duk tawa mai sauki ce, nidama ba wai sonka nake ba bare abinda nagani ya dameni, sannan dama ni banyi trusting dinka ba bare nace kayi disappointing dina,kula yanmata dai dama halinka ne shiyasa yau Allah ya toni asirinka..."

"Ohhh God" yafada tareda dafa goshinsa,

"Sakar min mayafi zan tafi.."

"Baby yanzu ni zaki yiwa haka?"

"Akan me bazanyi maka haka ba? Ni bakaga abinda kayi minba? Tafiya zanyi yanzu inbaka wuri gata can kaje ka dauketa kutafi inda kuka saba zuwa..."

"Baby wai meyasa kike yimin kallon dan iskane? Meyasa kike yimin kallon mazinaci?"

"Saboda halinka ne..."

"Halina?"

"Ehhh tunda gashi naga alamu da idona, da ai nunawa kayi baka santa ba saida kabari kuka kebe sannan...."

"To ya isa haka, naji ni mazinaci ne kuma halina ne nasaba...." Yafada tareda sakar mata mayafinta, tafiya tafara yi yana biye da ita abaya har suka shiga falon hajiya,

Dukkaninsu suna zazzaune suna faman shan dariyar wani film da akasa a African magic mai suna Jennifer's diary,

Wurin hajiya nadiya taje tace zata tafi nan hajiya ta kalleta cikeda mamaki domin ta zaci kwana zatayi,

"Dama ba kwana zakiyi ba?"

"Ehh hajiya saboda inada lectures gobe da sassafe.."

"To ai shikenan, Allah ya taimaka yabada sa'a" hajiya tafada bayan ta mike zuwa cikin bedroom dinta, wata leda ta dauko cikeda kaya ta bata, dakyar ta karba duk da tayi kokarin boye damuwar dake kan fuskarta,

Sallama tayiwa anty siyama ta fita ko kallon inda zee take batayi ba,

Bin bayanta amadi yayi suka fita har zuwa compound din gidan nan ya kwallawa driver kira yataso da gudu yazo,

"Wudil zaka kaita.."

"To ranka ya dade.."

Daga ita harshi babu wanda yasake yiwa wani magana har ta shiga mota driver yaja suka nufi gate din fita, juyawa yayi ya koma falon hajiya yana jan kafarshi wadda yaji ciwo, shi kansa bai san meya samu kafar ba amma jinta yake tana yimasa wani zugi gashi kamar kumbura take yi,

Cikeda jin haushi sosai yake kallon zee, ko magana baiyi ba yanufi dakinshi yaje ya fada kan gado ya kwanta yana jin kamar ya zubar da kwalla ko zai samu saukin kuncin dake cikin zuciyarshi.

  Tun acikin mota nadiya keson zubar da hawaye amma ta gagara saboda bata son drivern su amadi ya fuskanci akwai matsala, gaba daya jinta take kamar acikin mafarki,sai tambayar zuciyarta take wai dagaske amadi tagani yana rungume da wata budurwa?

Tsaki taja ta dauki wayarta tafara kiran mama, mama na dagawa suka gaisa nan tace ahada ta dasu fadeel mama tace basu dawo daga islamiyya ba sun tafi,

Amira tace ahadata da ita suna gaisawa tacewa Amira zata tura mata text massage yanzu saboda ahanya take,

Abinda yafaru ta kwashe gaba daya ta fadawa amira ta cikin text din, nan amiran ta dawo mata da reply tana bata hakuri sannan tace zasuyi waya idan ta sauka.

Amadi Amira ta kira bayan sun gaisa sai yaji tayi shiru,

"Amira lafiya kuwa?"

"Lafiya lau yaya Ahmad nakiraka ne ingaisheka dama ina fata kowa lafiya?

"Amira ba lafiya ba wallahi, nadiya ta burkice min kin san halinta sam taki ta karbi uzurina.."

"Yaya Ahmad mai yafaru?"

Babu abinda ya boye mata nan yafada mata dukkan abubuwan da suka faru babu tantama ko kadan amira ta yarda da bayaninsa domin tasan yana mutukar son nadiya dan haka zaiyi wahala yaci amanarta,

Hakuri amira tabashi sannan sukayi sallama, babu jimawa nadiya ta kirata ta inda take shiga bata nan take fita ba harda cewa bazata zauna da amadi ba sai ya saketa,

"Haba anty karfa ki manta yaya Ahmad yana sonki kuma lokacin da abun yafaru tare kuke, idan da ace yayi niyyar aikata hakan ai ina ganin da bazai yi ananba tunda yasan zaki iya ganinshi, wallahi ya rantse min da Allah akan shi ba halinsa bane kuma bada wata manufa yayiba... Dan Allah kiyi hakuri ki saurareshi"

"Haba amira taya zan saurareshi bayan da idona nagansu.."

"Duk da haka dai ki danni zuciyarki kitsaya kiji abinda zaice"

"Shikenan amira nagode"

Katse wayar tayi tafada kogin tunani ta kusa yarda kadan da kalaman amira amma kuma tasan halin maza na iya maida baki yakoma fari,

Tana zaune tarasa abinyi taji shigowar massage,

_Baby am so sorry, pls kidaina fushi dani dan Allah..._

Tsaki tayi ta mayar masa da reply,

_Malam kadaina rokona kar ka hadani da Allah, dama kawai halinka ne kariga da ka saba bin yanmata._

Reply ya dawo mata dashi,

_Wallahi ba halina bane, dan Allah ki yarda dani kinji baby_

Kyaleshi tayi taki mayar mishi da reply nan yafara kiranta amma taki dauka saida yayi mata 15 miss called amma taki dauka,

Jawo kafarshi yayi ya fito falo lokacin harsu anty siyama sun tafi sallama yayiwa hajiya wai zaije wudil yadawo ita kanta hajiya saida abin yabata mamaki saboda taga dazu nadiya tatafi,

Jan kafarshi yayi wacce ke sanye da silifas domin bazai iya saka wani takalmin gayuba,

"A'a auta ya naga kana jan kafa, zo mugani me yasamu kafar?"

"Hajiya bugewa nayi amma idan naje zanje aduba min ita"

"To Allah ya kiyaye"

Fita yayi ahaka ya shiga motarshi yayi mata key, dakyar yake iya taka motar saboda zafin da kafar keyi, lokacin da ya isa wudil makarantarsu nadiya kuwa tuni har kafar ta kumbura tayi suntum wanda shi kanshi saida abin yabashi tsoro,

Text ya tura mata,

"Ina cikin makarantarku ina jiranki, idan kuma baki fitoba Allah ya isa...."

Haushine ya kamata lokacin da taga text din nashi domin badan yayi mata Allah ya isaba idan taki fita to da babu abinda zaisa taje wurinshi, cikeda takaici ta dauki gyalenta ta fita fuska adaure cikeda fushi wanda ita kanta bata san dalilinshi ba....

_Fatan alkhairi ga yan groups din,Duniyar makaranta 1&2,Duniyar littattafan hausa, Zauren karatu,da sauran wadanda ban ambata ba, Ummi Shatu ta gaisheku kyauta._


*_Ummi Shatu_*🏻
[9/16, 7:53 AM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
     _(Labarin k'auna)_


    *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.* _Home of expert & perfect writers_


  _Godiya mai yawa ga 'yan kungiyar haske writers association wannan shafin sadaukarwa ne agareku..._

        *64*

aishaummi.blogspot.com

    *Z*uciyarta ahargitse ta fita wurin amadi, fuskar nan tata babu walwala ko kadan bare alamun fara'a,

Zaune ta hangoshi acikin motarshi ya bude kofar sannan ya ziro kafafuwanshi waje,

Fuska adaure ta karasa jikin motar ta tsaya batare data kalleshi ba,

"Baby...." Yakira sunanta,

Wani kallo ta juya tayi masa sannan ta dauke idonta batare data amsaba,

"Dan Allah baby ki daure kiyi min uziri ki saurareni sannan ki yarda da duk abinda zan fada miki, da ace zee budurwata ce kamar yadda kike zargi da wallahi kin fahimta tunda jimawa, ni ba sonta nakeba itace dai ke sona ki tambayi anty siyama kiji, wallahi kawai tausayinta ne ya hanani taka mata burki daga rungumar da tayi min har kika zo kika samemu..."

Sake dauke kanta tayi bayan ta gyara tsayuwarta,

"Shine kawai abinda kazo ka fada min?"

"Shine.."

"To naji.."

"Dan Allah kiyarda dani shine kawai fatana.."

Wani malamine yazo wucewa a cikin motarshi wanda suke department daya da amadi, ganin amadi yasa malam munnir tsayawa tareda yiwa amadi hon,

Mikewa amadi yayi ya nufi wurin malam munnir yana dingisawa wanda kusan ma ko daga kafar bayayi illa janta da yakeyi sai lokacin nadiya ta kula da dingishi yakeyi,

Hannu yabawa malam munnir suka gaisa malam munnir yace,

"Yaushe agari?"

"Wallahi jiya jiyan nan.."

"Ok sannu da zuwa, yaushe zaka fara shiga aji?"

Dariya amadi yayi "sai nanda wani month din.."

"To Allah ya nuna mana agaida amarya.."

"Zataji"

Sake musabaha sukayi malam munnir yaja motarsa yayi gaba shikuma amadi ya nufi wurin nadiya,

K'afarshi ta zubawa ido tana kallo wacce ta kumbura suntum tana kokarin tsinka silifas din dake kafarshi,

Zama yayi ya dan kalleta,

"Kinga saboda kina fushi dani kafata tana yimin ciwo amma haka najanyota nataho wurin.."

"Ai dai banice na jimaka ciwon ba"

"Wallahi Allah kece sanadi, lokacin da nayita kiranki kika ki tsayawa lokacin ne naji wannan ciwon, ina jin targade nayi.."

"Allah sawwake.." Tafada kanta na kallon wani wuri,

"To zaki rakani agyara min?"

Shiru tayi batayi magana ba wannan ya tabbatar masa da cewar watakila idan yayi sa'a ta rakashi din, ATM dinshi ya dauka saiko wayarshi yafito daga cikin motar ya kulleta,

"Muje to..."

Kamar ba zataje ba sai kuma yaga tafara tafiya,

"Baby dan Allah ki tsaya ki rikeni.."

Tsayawa tayi batareda jiyo ba har yakarasa kusa da ita yana zuwa ya dafa kafadarta,

"Muje baby.."

Ahaka suka fara tafiya yana dafe da kafadarta duk inda suka wuce mutane sai sun kallesu musamman ma daliban makarantar wadanda ke farfajiyar cikin makarantar a wannan lokacin,

"Washhhh kafata..."

Taji yafada cikin raki, tausaya masa tayi ta rikeshi sosai ta hanyar zagayeshi da hannunta guda daya dayan hannun kuma ta rike hannunshi dake kan kafadarta, shi kansa yasan ciwon dake kafarshi ne yasata saukowa daga dogon fushin da tayi da wuri badan Allah ya rufa masa asiri yaji wannan targaden ba dako kallo bai isheta ba,

Da haka suka fita har gate suka tsaya suna jiran adaidaita sahu, suna nan tsaye suka samu ta taimaka masa ya shiga sannan itama ta shiga ta zauna,

Hannunta ya kamo ya rike cikin nasa,

"Hajiya ina zakuje?" Inji mai adaidaita sahu,

Bude baki tayi da niyyar bashi amsa amma sai amadi yayi saurin rufe mata baki da hannunshi,

"Ni yakamata ka tambaya ba itaba saboda ita matar aure ce.."

"Yi hakuri mai gida ai naga kamar kai din bakada lafiya ne shiyasa.."

"Ai ciwon ba abakina yake ba, cikin gari zaka kaimu gidan gyaran targade"

"To yallabai.."

Saida suka gama magana da dan adaidaita sahun sannan ya dauke hannunshi daga kan bakin Nadiya,

Da ido take kallonshi kawai har Allah yakaisu gidan mai gyaran targaden.

Sauka sukayi yasoma labuba aljihunsa,

"Baby kinga ashe ma banida ko kwandala ajikina sai dai amma ga ATM card dina.."

"To yanzu yakake so ayi?"

"Muje can may be akwai ATM machine"

Sake rikeshi tayi ya dingisa suka tafi duk da cewar mai adaidaita sahun yace zai kaisu amma fur amadi yaki amincewa saboda ganinshi rike jikin nadiya abun na mutukar burgeshi,

Yana rike ajikinta har suka je wurin da suka samu ATM machine nan ta taimaka masa ya haura yar barandar dake wurin,

20,000 taga ya cira yasaka a aljihunshi sannan ta sauko dashi suka tafi, duk inda suka wuce idon jama'ane ke rakasu wanda har shi kanshi amadin yafara kosawa da wannan kallon,

Dan adaidaita sahu yabawa kudinshi sannan yasamu wuri ya zauna ita kuma ta shiga gidan, mintuna kadan tafito,

"Zo mu shiga" tace dashi batare da ta kalleshiba,

"Mace ne ke gyaran ko namiji?" Ya tambayeta yana dan murmushi,

"Namiji ne.." Tabashi amsa, hannunshi ya mika mata alamun ta tayar dashi tsaye nan ta kama ta jashi ya mike tsaye, rikeshi tayi suka shiga cikin gidan gyaran targaden,

Mai gyaran na zaune akan tabarma da jerin wasu kwalabai agabanshi wadanda ke dauke da magungunan gargajiya aciki,

Zama sukayi mai gyaran yafara duba kafar amadi wacce tazama wata himmm kamar anhura tattali

"Yaushe kaji wannan ciwon?" Mai gyaran ya tambayeshi,

"Dazun nanne na buge da dutsi"

"Wannan ba targade bane tsagewar 'kashi ne amma yanzu za agyara da yardar Allah"

Ba karamin wahala amadi yasha ba amma abin mamaki ko gezau baiyi ba babu raki babu komai har aka gama gyaran,

"Wannan yayan naki namijin gaske ne ba nawasa ba kodai soja ne?" Mai gyaran yafada cikin raha saboda ko manya yazo yiwa gyara ihu suke bare yara,murmushi kawai tayi batace komai ba shi kuma gogan sai aikin binta da na mujiya yake kamar yaune yafara ganinta,

Magani yabasu a kwalba yace ta shafa masa akafar idan sun koma gida bayan ta gasa masa kafar da ruwan zafi,

Dubu daya ya ajiyewa mai gyaran suka mike itada shi, yana rike ajikinta suka fita,

"Baby yauma fa inajin guest lodge dinnan zamu koma mu kwana acan saboda wallahi bazan iya komawa Kano da kaina ba"

Batace masa komaiba sakuci gaba da tafiya har suka samu dan adaidaita nan suka shiga yakaisu minal guest lodge,

Wannan karon ma shine yaje ya biya kudin daki yadawo da key din a hannunshi suka nufi dakin da aka basu,

"To yanzu da ka kawo mu nan a ina zamu samu ruwan zafin da za agasa maka kafar?"

"Za akawo mana, nafadawa wani ma'aikaci a reception din cewar ina son ruwan zafi"

Goshinta ta dafa saboda tasan ma'aikatan abinda zasuyi tsammani daban,

"Baby menene naga kin dafa goshi? Ko afasa kar akawo?"

"A'a akawo"

Kwanciya yayi akan gado ruf da ciki ya dage kafar tashi mai ciwon yana jijjigata,

"Baby zoki daddanna min kafar tawa please"

"Kabari akawo ruwan zafin sai ingasa maka ita.."

"Tom.." Yabata amsa yana faman jujjuya kanshi saboda zafin da kafar keyi masa.

Zaman jiran ruwan zafin sukaci gaba dayi har aka kawo musu cikin wani dan karamin bucket din roba, itace tafita ta karbo ta dawo,

K'asa ya sauka ya zauna itama ta zauna tareda zame dan kwalin kanta domin babu tsumma awurin, ruwan inbanda tururi babu abinda yakeyi nan ta tsoma dan kwalinta aciki ta nado ruwan tafara matsewa take yafara kokkonata saboda zafinshi yarfe hannu tafara kafin ta dora akan kafar amadi.....


*_Ummi Shatu_*
[9/17, 2:46 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
    _(Labarin K'auna)_



    _*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO.*

  _Wannan shafin nakune yan group din baby Isah together with sidiya and friends group especially mama 4h...._

          *65*

aishaummi.blogspot.com


 
    *J*in saukar ruwan zafin akafarshi yasashi sakin wata yar kara kadan wacce kanaji kasan ta shagwaba ce,

Hannunta ya rike cikin raki yace,

"Baby da zafi..."

"Komai zafinshi ai hakuri zakayi"

Bata sake sauraronshi ba ta kara jiko dan kwalin tadora akan kafarshi wata kara yakuma yi harda bata fuska tamkar zaiyi mata kuka,

"Baby bakijin tausayina ashe? Allah zanyi miki kuka.."

Jin yanda yayi maganar ashagwabance tamkar karamin yaro yasata yin murmushin da bata shirya ba,

Kafarshi ya janye saboda ganin tana sake tsoma dan kwalin nata acikin ruwan,

"Dan Allah ka tsaya.."

"To bakece ba kinki rarrashina.."

"To yi hakuri ka tsaya ingasa maka, kaga Allah ruwan yafara hucewa"

Mika mata kafar yayi yana yimata karar shagwaba,

"Ni banma taba ganin ragon namiji ba irinka, daga gashin kafa harda su neman yin kuka.." Tafada amaze kamar ba itace tafada ba,

Kallonta yayi tareda rike hannunta,

"Nidai ba rago bane, ke dince bakya tausaya min kawai"

Hannunshi ta ture taci gaba da gaggasa masa kafar tashi har ruwan yayi sanyi, mikewa yayi yana dingisa kafarshi yakoma kan gado ya kwanta,

Binshi kan gadon tayi ta zauna ta dauko maganin da zata shafa masa akafarshi tafara shafa masa ahankali bayan ta dora kafar tashi akan cinyoyinta,

Daga kanshi yayi ya kalleta domin wani abune yake ratsashi idan tana murza masa maganin akafarshi,

"Baby...."

"Uhmmmmm"

Mayar da kanshi yayi ya kwantar,

"Zaki fara yimin wannan uhmmm din naki kamar wata bebiya ko?"

Shiru tayi masa taci gaba da shafa kafarshi tana lailayawa musamman ma tafin kafarshi,

"Baby baki gama bane?"

"Ya akayi?"

"Nan zaki zo dan Allah.."

Kafada ta makale, "hum ummmmm"

"Please baby, badan niba dan Allah nace.."

Kin tashi tayi taci gaba da abinda take tana kallon kafar tashi, shikam komai nashi mai kyaune ita kanta ta shaida da hakan domin kafar tashi kamar bata taka kasa dan kyau da laushi, kusan ma laushin ne yahanata daina shafar kafar tashi, sabanin wasu mazan da zakaga kafarsu duk kaushi da faso wanda har acikin matan ma ana samun haka,

Lumshe idonshi yayi saboda yanzu kuma tafiyar tsutsa take yimasa atafin kafar tashi,

"Baby..."

"Uhmm"

"Kina son nafara wannan shakuwar marar magani?"

Saida tayi murmushi saboda jin abinda yace sannan tace,

"Uhmmm"

"Kikace uhmm ko?"

"Uhmmm" tabashi amsa,

"To shikenan.."

Wayarta ce ta shiga tsuwwa nan ta dauka sakamakon ganin sunan umman sumaila ajiki,

Dauka tayi suka gaisa nan umman take fada mata da ta aiko da sako lallai lallai tatafi gida wannan satin sannan kuma ta tabbata tayi amfani da duk abinda ta aiko mata daga karshe umman takare maganar da cewa,

"Kina shan wanda kika tafi dashi dai ko ba jibge min su kikaje kikayi ba dan nasan halinki"

"Wallahi umma ina sha"

"To shikenan Allah yabada sa'ar karatu"

Sallama sukayi ta kashe wayar tana dan kunkuni,

"Ita umman nan wallahi ta cika cikawa mutum ciki da abubuwan da zasu dameshi..."

Batayi auneba tajita luuuuu ya jata zuwa jikinshi, kallonshi tayi idanuwanshi a lumshe,

"Zo ki fada min abinda umman kebaki wanda har zai dameki"

Bude idanuwanta tayi sosai akan fuskarshi shikuma idanuwanshi arufe,

"Uhmmmm baby, fada min..."

"Babu koma...."

"A'a, da komai... Fada min mana"

"Nace maka babu komai"

"Ni ban yarda ba"

Kallonshi kawai taci gaba dayi tana mamakin kanta domin bata san lokacin da tafara sakin jiki dashi hakaba,

"Bazaki fada minba ni infada miki?"

Ido ta kwalalo tana kallonshi,badai yagano ba? Ta tambayi zuciyarta,

"Uhmmm baby? Ni kin bani dama infada miki?"

Shirun dai tasake yi hakan yashi bude idonshi akan fuskarta nan ita kuma tayi gaggawar lumshe nata idon,

"Baby babu magana?...."

Jin yafara sauke mata ajiyar zuciya yasata saurin bude idonta,

"Menene kuma?"

Ta tambayeshi, gashin kanta yashafa sannan yasake matseta jikinshi wanda tana iya jiyo bugun zuciyarshi,

"Wai menen...."

Hanata karasawa yayi ta hanyar kai bakinshi kan nata, zabura tayi kamar ya tsikara mata allura ta tashi fuskarta adaure,

"Menene haka? Ni karka sake sa bakinka akan nawa"

Murmushi yayi yasake janta jikinsa da hannunshi guda daya,

"Haba baby, wannan wanne irin horo ne? Ni ban taba jin macen dake yiwa mijinta rowa irin wannan ba kamarki, ke komai naki hanani kike.."

"Ai ban taba hanaka wannan ba sai yau"

"To meyasa zaki hanani? Ai horon zaiyi min tsanani da yawa"

"Ni ba horo nakeyi maka ba, laifinka ne tunda da idona naganka kana kissing din wata..."

"Dan Allah baby kiyi hakuri..." Shine abinda yake ta maimata mata, shiru tayi tana sauraron ban hakurinsa,

Yabata hakuri yafi sau dari amma batace komai ba domin yagama kashe mata jiki da salon da yake yi mata, ita kanta bata ma san ya akayiba itadai kawai taji bakinta cikin nashi nan ta manta ma da batun wai taganshi yana kissing din zee dazu.

Tunda suke da amadi bata taba sakin jiki dashi irin yau ba, yaune kadai ta taba biye mishi aduk zamansu dashi, ko da wasa kuma yau bataji haushinshi ba bare tayi fushi dashi,

Duk abubuwan nan dake faruwa shikuma amadi bai taba gwada karya alkawarin da ya daukar mata ba,

Bayan sallar magrib ta kalleshi yana jikinta idanuwanshi a lumshe, sai yau ta sake tabbatarwa da amadi yarone karami,

So take ta tashi saboda anyi salla tun tuni amma kuma takasa tashi domin tama rasa awanne yanayi take, yanayin da take jinta ciki harda kunya ta kawo mata gudun mawa,

Idonshi taga ya bude yafara mika,

"Kayi mika da kyau.." Tafada acikin ranta,

"Baby..."

"Uhmmm"

"Dan Allah baby kiyi hakuri kinji, kiyi hakuri akan abinda yafaru dazu wallahi bazan sake ba.."

Ita tausayi ma yake bata yanzu saboda tunda yaga tayi fushi yakasa samun sukuni Kalmar hakuri taki fita daga bakinsa ko yanzun ma da suke duniyar so kalmar hakurin taji yanata furtawa,

"Kinji baby? Kiyi hakuri dan Allah"

"Nahakura"

Jin abinda tace yasashi sake rungumeta sai kuma ya sassauta rikon da yayi mata,

"Baby duk kinbi kin faffama min kafata wallahi..."

"Yaushe..?" Tafada bayan ta bude idonta arazane,

"Lokacin da..." Sai kuma yayi shiru,

"Meyasa da tun lokacin  baka fada ba sai yanzu?"

"Ai lokacin banji zafinba sai yanzu take yimin zafi..."

Tashi tayi ta dago kafar tashi tana gani, sam ta ma manta da cewar babu riga ajikinta,

"Su baby budurwa, wallahi kamar baki shayar dasu fadeel b..."

Saurin jan rigarshi tayi ta rufe kirjinta tana harararshi,

Wata kunyarshi ce take saukar mata asannu asannu, kawai sai tagagara kallon ko wurinda yake kwance,

"Katashi bafa muyi salla ba.."

Tashi yayi ya dingisa ya shige toilet,tana ganin haka tajawo rigarta tasa ta shirya kafin ya fito,mintuna kadan sai gashi ya fito,

"Baby zo muje muyi tare.."

Kai ta girgiza masa alamun a'a, har inda take yaje yaja hannunta,

"Dan Allah kiyarda yau daya dai mu yi tare.."

Duk da bata so saida yajata zuwa cikin toilet din.....


*_Ummi Shatu_*
[9/19, 2:49 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
    _(Labarin k'auna)_


     _*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.* _Home of expert & perfect writers_

 

   _Fatan alkhairi agareki Hawy, this page is for you dear...._

      *66*

aishaummi.blogspot.com

    *I*danuwanta alumshe har suka shiga cikin toilet din,

D'aga idonshi yayi ya kalleta fuskarshi dauke da murnushin farin ciki gamida jin dadi,

"Baby bude idonki ki gani..."

Sake runtse idonta tayi a maimakon ta bude, juyin duniya yayi da ita amma takasa bude idonta, yagane tsaf kunyarshi wai takeji dan haka yasaketa ya fara kokarin tara musu ruwan da zasuyi wankan dashi,

Cikeda kunya ta zame jikinta tafita daga cikin toilet din tana murmushi amadi kawai sai juyowa yayi yaga bata nan, bai matsa sai yasake dawo da ita ba saboda yasan ko yanzu yasamu dama dayawa wacce ada bai samuba,

Wankanshi yayi ya gama sannan ya fita yana shafa sumar kanshi hannunshi daya rike da jeans da t shirt dinshi,

Acikin dakin ya sameta tana zaune agefen gado,

Saida yaje kusa da ita ya lakuce mata hanci sannan yayi magana,

"Raguwa mai tsoron yin wanka da mijinta kawai..."

Kafarta ta dora akan kafarshi mai ciwo,

"Kana sake kirana da raguwa zan fama ciwon nan yanzu..."

Murmushi yayi,

"Ki fama mana ai ke zaman jinya zai kama.."

Dauke kafarta tayi ta mike nan yaja hannunta,

"Inzo inyi rakiya..?"

Makale kafada tayi tazare hannunta ta shiga toilet, jiranta ya zauna yi harta fito sannan ya saka kayanshi sukayi sallar tare,

Kwanciya yayi yadora kansa bisa cinyarta,

"Baby...."

"Uhmmm"

"Dan Allah kiyi min wani taimako"

"Ina jinka"

"So nake kitare nanda 3 weeks.."

Saida ta danyi shiru na wasu yan sakanni sannan tayi magana,

"Bazaka bari ingama makaranta ba tukunna?"

Hannunta yakama acikin nasa yadan daga kanshi yana kallonta,

"Baby zamu rinka tahowa tare, inada bukatarki ne kusa dani, rashinki atareda ni gaskiya tsautsayi ne..."

Shirun ta sakeyi sannan tace,

"Shikenan amma dai kabari indanyi shawara.."

"To shikenan nabari.."

Janta yayi ya kwantar da ita ajikinsa yafara lalubarta, hannunshi ta rike,

"Ya akayi kuma?"

Murmushi yayi,

"Yi hakuri baby na"

Kawar da kanta tayi tana lumshe idonta,

Saida lokacin sallar isha yayi sannan suka tashi sukayi suna idarwa yace tatashi sufita yadan take kafarshi,

Rufe dakin sukayi yakama hannunta suka fita wajen guest house din domin ganin gari, ahankali suke tafiya yana rike da ita yana yimata kalamai masu sanyaya zuciya na irin son da yake yimata,

K'arfe 9 da wani abu suka koma guest house din bayan ya siyo musu balangu da soyayyen kifi, suna shiga kuma yayi musu order din abinci,

Tare suka zauna suka ci yana bata abaki, langabe kai yayi ya kalleta,

"Baby nifa?"

"Me fa?" Ta tambayeshi,

"Abincin? Dan Allah kibani"

Diba tayi tafara bashi shima yana bata da haka har suka kammala.

Washe gari da misalin karfe 9 nasafe suka bar hotel din suka nufi cikin makarantarsu nadiya,

"Baby tafiya zanyi yanzu sai yaushe?"

Mayafinta ta gyara tana kallon wani wuri,

"Nima gida nake son tafiya ranar friday umma tace lallai lallai inje"

"To kibari zanzo inkaiki"

"Kaida kake ciwon kafa, kabarshi kawai zan shiga mota intafi"

Girgiza kai yayi, "ban yarda ba, zanzo inkaiki"

"To shikenan, Allah yakiyaye hanya"

"Amin baby, shikenan intafi babu special sallama?"

Shiru tayi kamar bata jishi ba saboda tasan abinda yake nufi,

"Kagaida hajiya"

"Zataji" yafada yana murmushi saboda shi yarasa dalilinta najin kunyarsa,

Shiga cikin motarshi yayi yai mata key tana tsaye tana kallonshi har saida taga yafara tafiya sannan tabar wurin tawuce zuwa hostel.

Tun yana hanya yake kiranta baima bari yakarasa cikin kanon ba,

"Baby Allah yayi miki albarka, Allah yabaki aljanna, nagode sosai da abinda kika yimin..."

"Amin, ka karasa gidane?"

"Nakusa dai.. Yanzun nan zan shiga kano"

"Ok Allah yakiyaye hanya"

"Amin baby i love you"

Katse wayar tayi tana murmushi, koda amadi yaje gida hajiya tsokanarsa tai tayi tana cewa daga rakiya kuma sai ya kwana acan, dariya yayi yawuce dakinsa saboda shidai yasan Allah ne kawai yayi masa nasibi nadiya ta sauko.

Ranar yakirata awaya yafi sau a kirga, bini bini sai ya kirata da haka har dare yayi, bai sake haduwa da itaba sai ranar juma'a ranar da zai kaita rano,

Har cikin makarantar ya shiga yayi packing yana jiranta, fitowa tayi cikin doguwar riga ta Arabian gown orange colour da dan mayafinta, ba karamin kyau rigar tayi mataba, kafarta sanye cikin flat shoe shima Orange colour,

Kallonta yayi bayan ta shiga ta zauna acikin gaban motar,

"Baby bakya jin magana ko? Dubi shigar jikinki, wai meyasa kike yimin wasarere da halin ko inkula da kayana?"

"Dan Allah yanzu meye laifin wannan shigar?" Tafada tana kallonshi, ba karamin kyau yayiba cikin Skye blue din wani yadi mai kamar tissue marar kauri wanda yabata damar ganin farar singiletin da yasaka,

Dinkin half jamfane mai dogon hannu, kansa yasa hula amma yaturata baya, kamar wani balarabe haka ya fito,

Bakinta ya kalla wanda yasha jan janbaki rangadadau, pink lips dinshi ya dan lasa,

"Ohhh wato ke baki ma san laifin kayan ba ko??"

"Gaskiya ni banga laifinsu ba"

Tace dashi tana tura baki,

"Zo kiga wani abu.."

"Ina zanzo?"

"Dan matsawo nan zakiyi.."

"Gaskiya a'a..."

"Kina ki wallahi Allah ya isa zanyi miki"

Matsawa tayi tana tuttura baki nan ya cafke bakin nata da nashi, 24 hours din data shafa gaba daya saida yayi dama dama dashi agefen bakinshi da nata.

Sakinta yayi yana sauke ajiyar zuciya ahankali, kasa kallonshi tayi amma ta dan hade rai kadan wanda yaushe rabon da yaga tayi,

"Baby muje ko..."

Yafada cikin jan magana, shiru tayi masa dan haka sai kawai yayiwa motar key yabata wuta, saida suka bar cikin makarantar sannan ya kula da jan bakin da ya bata masa fuska mirror yasake kallo nan yaga fuskarshi tayi baja baja,

Packing yayi agefen titi ya kalleta,

"Baby goge min to jan bakin da kika shafa min"

Ita kanta tasan dan neman magana yafadi hakan shiyasa bata kulashi maganar tayi tsaho ba, tissue ta yago tafara goge mishi duk wurin da jan bakin ya taba,

"Kafar taka tawarke..?" Ta tambayeshi tana mai goge masa fuskarshi,

"Ehh baby tagama warkewa saura kadan, kin gani.."

Nuna mata yayi tagani sannan yadaura belt yahau titi bayan ta kammala goge mishi jan bakin, ita dinma belt ta daura ta jingina mintuna kalilan barci ya dauketa, kallonta amadi yayi yai murmushi,

"Rigimammiya daga fara tafiya kuma sai barci.."

Wa'azin sheikh jafar Mahmud Adam ya kunna yana saurara mai taken tambayoyi da amsoshi, har sukaje cikin rano nadiya bata farka ba har saida suka shiga layinsu sukaje kofar gidansu yayi packing sannan ya matsa kusa da ita yafara hure mata ido da bakinshi,

Dan motsi tayi amma bata bude idonta ba, saitin kunnenta yakoma yafara hurawa, sake juya kanta tayi har lokacin dai bata tashi ba,

Idonta yasake busawa da iskar bakinshi nan ta dan bude idonta kadan ganinshi yasata bude idanuwan gaba daya tana kallonshi, murmushi yayi mata,

"Baby yar kauye shine harda su yin bacci acikin mota.."

Daure fuska tayi, "waye yar kauyen?"

"Wai da.." Yafada yana murmushi,

"Hmmm" tafada tana dauke kanta,

"Dadina dake iya daure fuska.."

Bata tanka ba tafara kokarin bude kofar, komawa sit dinshi yayi yacire belt din daya daura yabude kofar ya fita lokacin nadiya har ta shige cikin gida,

Bayanta yabi ya isketa atsakar gida tana daga su fadeel shida fadeela wadanda dawowarsu kenan daga makaranta domin ko cire musu uniform dinma ba ayiba, ai suna ganin amadi suka bar nadiya suka tafi wurinshi,

Yasamu kyakkyawar tarba mai kyau awurin su mama, shi kam dama yasan yayi sa'ar surukai kuma duk yan uwan nadiya kowa na sonshi shiyasa shima yake son bin duk wata hanya dayake ganin zai kyautata musu suji dadi,

Wata katuwar jaka yakawo musu cike da kaya wai tsarabarsu ce, kowa na gidan akwai tsarabarsa aciki amma duk tsarabar twins tafi yawa domin bayan kayan sawa harda kayan wasa kala kala yasiyo musu, shi dai Allah ne yadora masa son nadiya da yaranta domin yana jin son yaran har cikin jininsa tamkar shine ya haifesu,

Nadiya kuwa babu ita acikin tsarabar da yakawo ko kyalle babu nata acikin kayan sai su amira da husna da sauran mutanen gidan, yana tare da twins har lokacin sallar juma'a yayi nan ya daukesu suka tafi masallaci tare basu suka dawo gidan ba sai wurin 3 lokacin har abba yadawo shima,

Nadiya ce tayi masa jagora zuwa falon abba, tana gaba yana binta abaya yana shakar kamshin turarenta na beautiful woman sannan adon da tayi awannan lokaci ba karamin daukar hankalinsa yayiba domin wata doguwar rigace ta atamfa coffee colour ajikinta, rigar tayi mata das sannan ta bayyanar da kyawunta afili dan haka kasa hakuri yayi harsai da ya cimmata ya rungumeta ta baya,

Cikin mutuntawa da girmamawa ya gaida Abba, bayan sun gaisa abban yayi masa maganar tarewar nadiya nanda sati biyu tunda yadawo,

Satar kallonta yayi yaga kanta akasa bata ko dagoba ajiyar zuciya yasaki saboda Allah yarufa masa asiri agabanta abba yayi maganar da abayan idonta ne cewa zatayi shine yafadawa Abba haka, saida ya danyi jim sannan yacewa abban adai barshi asati uku ba sati biyu ba saboda yana jira akawo masa furnitures din da yayi order daga kasar Italy wadanda zasu zo nanda sati biyu sannan baya son asiyawa nadiya ko cokalin cin abinci domin yagama siya mata komai wanda duk zata bukata na amfanin gida,

Duk da Abba yaji haka saida yace a'a shima zai sake siya mata wasu nan amadi yace a'a idan ansiya ma asara zai zama domin yagama siyan komai, albarka Abba yasa mishi tareda yi masa godiya anan suka bar maganar tarewar nadiya nanda sati uku.

Tare suka taso suka fito da ita sai ciccin magani take fuska babu nishadi, shidai bai ce komai ba domin lallabata yake yasan babu wuya tahau sama, danma kar yayi mata laifi sai yayiwa mama sallama yace zai tafi, mayafi ta dauka ta rakashi waje sai kumbure kumbure take,

"Baby ke taki tsarabar tana gida na ajiye miki sai kinzo zan baki kinji"

"Uhmmm naji, nagode, Allah ya kiyaye hanya, agaida hajiya"

"Zataji baby.."

Dahaka suka rabu yashiga motarshi yatafi cikeda murnar nan da sati uku yana tareda ita, gida ta koma tana kukkumbura baki.

***

   A bangaren kabeer da asabe mc kuwa abin sai wanda yagani, duk wanda yaga yanda kabeer yakoma sai ya tausaya masa domin tun lokacin da ya tsallaka bakin asirin da asabe ta ajiye masa shikenan yazama kamar bawanta, komai shine yake yimata, maganarta kuwa bai isa ya musanta ba, daga tace masa abu jiki yana rawa zaije yayi mata, gaba daya dukiyarsa ta koma hannunta, takardunsa nagidaje da filaye duk ta karbe daga gareshi, aiki kuwa tuni yadade da sallama shi wannan dalilinne yasa kamfanin da yake aiki suka bashi takardar sallama saboda wasa da aikinsa da yakeyi,

Hankalinsa gaba daya yabar jikinsa sai abinda asabe tace, ita kuwa yanzune ma take shanawa ita da kawayenta saboda ansamu dukiyar banza, amma duk da haka tana sonshi shiyasa take dan raga masa awani abun, shidai yazama shine matar itace mijin sai abinda tace, rabonsa da iyayensa da kannensa kuwa har ya manta domin asirin da asabe tayi masa harda wanda zai rabashi da danginsa,

Suma iyayen nashi sunyi watsi da harkarsa babu Wanda yake nemansa, A'isha da Fati ne kawai suke son zuwa su gano halin da yake ciki dan haka awata ranar litinin da safe fati ta shirya taje gidan A'isha suka wuce gidan kabeer din.

*_Ummi Shatu_*🏻
[9/21, 3:03 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
    _(Labarin k'auna)_

 
    *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO.*
  _Home of expert & perfect writers_

    _Gaisuwa ta musamman ga iyalan Alh Ali Bukar Dalori Borno state,na sadaukar da wannan shafin agareku tareda Rashidat Abdullah Kardam..._

      *67*

aishaummi.blogspot.com


   *L*okacin dasu fati suka shiga gidan kabeer sai da hankalinsu yatashi domin gaba daya gidan yagama sauyawa sannan hatta motocinsa duk babu asabe mc ta salwantar dasu, mota guda dayace kawai tayi saura wadda itace take hawa,

Asabe najin sallamarsu amma tayi burus dasu taki koda amsawa ne domin acewarta tasan munafurcine ya kawosu,

Basu yi fushi ba suka tura kai zuwa cikin falon, tana zaune akan 3 sitter ta dora daya akan daya tana chaten tamkar bata jisu ba,

Kallon juna A'isha da fati sukayi,

"Asabe ashe kina ciki..." Fati tafada cikin rashin girmamawa domin yanzu aduniya su asabe ce matsalarsu,

"Ehhhh gashi kuwa kingani" asabe tabata amsa tana turo dan kwalinta gaban goshi,

Kabeer ne yafito daga kitchen yana yiwa asabe girkin faten wake da alayyahu wanda tasashi,

Kallonsa suka tsaya yi cikeda tausayawa domin duk yazama wani sakarai sannan babu alamun hutu ko jin dadi atare dashi yanzu sabanin da wanda kabeer ada cikakken dan gayune mai aji mai jida kyau da kudi,

"Yaya kabeer... Haka kadawo? Haka kazama? Yanzu yaya kabeer ka kyautawa rayuwarka kenan? Ka manta da iyayenka da yan uwanka da danginka da kowa naka kazo ka tare akarkashin mace, haba yaya kabeer Kaduba kaga yanda kadawo fa kamar ba kaiba, yaya kabeer baka kyautawa kanka ba iyayenka sun dade suna fushi dakai, fushinsu ne yake bibiyarka..." Fati tafada tana zubar da hawayen tausayinshi,

Karasawa wurinsu yayi shima yana jin kamar zaisa kukan,

"Fati, A'isha dan Allah ku tayani da addu'a nikaina ban san abinda yake damuna ba, ban san yanda akayi nadawo haka ba... "

Wata tsawa asabe mc ta daka masa sai kace uwarsa,

"Kai, wuce kaje ka karasa min girkin da nasaka..."

Jiki narawa kabeer ya juya kamar zai kifa yana waiwayen su A'isha yashige kitchen,

Wata kwalla mai zafi A'isha ta fara fitarwa ta kalli mc,

"Insha Allah sai kinga karshenki, yanda kika mayar dashi bawa sai Allah yasaka masa.."

Mikewa asabe tayi cikin fada,

"Kai ku fice kubar min gida, sannan karku kuskura kusake zuwa gidan nan, banzaye mararsa kunya, idan kunje gida ku fadawa tsohuwa sako injini danta ni ta haifawa dan haka tsakaninta dashi sai ido.."

"Karya kike jahila,kinyi kadan ahaifa miki yaya kabeer.." A'isha tabata amsa, kan A'isha asaben tayi tana huci,

Duk da haka bakin A'isha bai mutuba, dakyar fati ta janyeta suka bar cikin falon dukkaninsu suna zubar da kwalla, nan asabe ta mayar da kofarta tasaka key ta kulle,

Ta cikin window din kitchen kabeer ke lekensu amma bashida bakin yin magana domin asabe tadade da gamawa dashi.

***

  Tunda amadi yatafi nadiya taketa kumbure kumbure marar dalili domin ita tafi son sai tagama karatu sannan zata tare amma tunda Abba yayi maganar tasan dolenta sai tatare din koda kuwa bata so barema bata da halin da zata musanta maganar Abba,

Duk mama nakula da ita da kumbure kumburen da take ta faman yi, shi kansa amadi din fushin ya dan fara shafarsa domin ko ya kirata awaya baya samun kanta yanzu shiyasa duk yabi yadamu,yana murnar zata tare yana kuma fargabar fushin da takeyi,

"Wai ke meke damunki ne? Yarinya kamar mai iska, daga wannan sai wannan.."

Mama tace da ita cikin fada tana zaune akofar kitchen ita kuma nadiya tana wurin wanke wanke tanayi,

"Babu komai mama"

"Badai babu komai ba, tunda kika dawo shekaran jiya kalau amma daga ji anyi miki maganar tarewa shikenan kika bi kika damu kanki, keda haka zaki zauna da aure akanki kina gida? Ai bazai yiyuba nadiya, ita mace duk gatanta da asalinta da nasabarta to gidan mijinta shine gatanta in fada miki"

Shiru tayi taci gaba da sauraron fadan da mama take tayi mata har tagama wanke wanken mama bata daina fada ba, daki takoma ta kwanta.

  Yarage saura sati biyu tarewarta amadi yaturo mata da 50,000 yace gashi nan ta yi duk wani abu wanda zatayi na shirye shiryen tarewa,

Kayan cosmetics da turaruka ta siyo masu dadin kamshi, sai turaren wuta da humra kala kala,

Duk da bata son yin gyaran jiki saida umman sumaila ta tilastata dole tafara zuwa gidan wata mata yar sudan aka fara yimata gyaran jiki safe da yamma,

Umman sumaila kuwa tunda tazo dama da guzurinta tazo shiyasa sam nadiya bataso zuwanta ba domin hadaddun kayan gyara tazo dashi kuma agaba take tisata sai ta shanye,

Haka lokaci yayita karatowa, shi kuma amadi yana can yana gyara mata gidanta inda zata zauna, komai sai yakirata yaji wanda takeso saboda kar asa mata wanda baiyi mata ba, hatta labule da carpet da komai na kwalliyar falo da bedrooms saida ya tambayeta kalolin da takeso nan tace purple colour take so.

Cigaba da gyarata umman sumaila tayi tako ina, ita dai mama yar kallo tazama kallonsu takeyi saida taga gyara yaki karewa sannan tayiwa umma magana,

"Dan Allah ahakura haka nan karku rikita musu yaro..."

"Ba maganar hakuri anan, gyara ban ma gamaba saura yana baya.."

Tashi mama tayi tana cewa, "duk dai gyara tsoho bazaiyi kamar ya saboba"

"Waya fada miki? Ko za asamu banbanci to kalilan ne"

Ita dai mama bata sake magana ba tafita tana dariya,

Nan umman sumaila ta dora daga inda ta tsaya,

Saura kwana biyu tariyar aka yiwa nadiya gyaran gashi da kunshi, zanen kunshi mai kyau na ja da baki yar sudan tayi mata,

Ranar alhamis da daddare Abba da mama harda umman sumaila suka zaunarta suka yimata fada da nasiha akan tabi mijinta tayi masa biyayya kuma tarikeshi hannu bibbiyu domin masoyinta ne na hakika,

Cikin sanyin jiki tatashi tafita bayan su Abba sun sallameta, kwanciya taje tayi amma saita gagara bacci saboda fargaba,ko alokacin aurenta nafarko batayi fargaba kamar wannan ba ko dan yanzu ta san yanda auren yake ne,

Har asuba tayi idonta biyu saida tayi sallar asuba sannan bacci ya dauketa,

Gaba daya kayanta amira tagama shirya mata su tun kafin ta tashi daga bacci, gaba daya ranar kashe wayarta tayi domin jikinta yayi mata sanyi, haka tawuni bata um bare um um,

K'arfe takwas na dare anty siyama sukazo daukar amarya ita da wasu kawayen hajiya guda biyu,

Motoci guda uku sukazo dashi domin amadi yana mutukar kimanta nadiya shiyasa ako ina yake nuna ita din mai daraja ce agareshi,

Fito da nadiya umman sumaila tayi itada maman su kabeer domin sune zasu rakata nan tayiwa mama sallama aka fita da ita, fadeel da fadeela dama tuni sunyi bacci tun bayan sallar magrib.

8:40 suka shiga cikin Kano suka wuce gidansu amadi kai tsaye, part din hajiya aka fara kaita hajiyan na zaune tasha kwalliya cikin wani leshi mai tsada ja takafa dauri ko ina najikinta gwalagwalai ne ke daukar ido,

Cikin faran faran hajiya ta karbi bakinta nan su umma suka damka mata amanar nadiya tace ta karba Allah yataya su riko dama kuma ita nadiya yarta ce halak malak, ita da amadi duk dayane awurinta,

Fita akayi da nadiya zuwa part dinta wanda abin sai wanda yagani saboda mutukar tsaruwar da yayi, sai santin gidan su umma keyi domin ya tsaru karshe,

Dakin dake hannun dama suka kaita domin shine nata, komai nacikin dakin purple colour ne, abakin gado suka zaunarta suka fita domin ganin tsarin gidan,

Saida suka gama ganin ko ina sannan sukazo suka yimata sallama suka tafi, itama anty siyama tafiya tayi bata zauna ba,

Kallon dakin nadiya ta daga kanta tanayi, komai ya burgeta yanda aka ajiyeshi akan tsari,

Bude kofar dakin taji anyi an shigo, amadine sanye cikin wata shadda kalar ruwan kasa kanshi babu hula yayi mutukar kyau fuskarshi kumshe da murmushi sai zuba kamshi yake,

Kallonta yake yi tun daga nesa har yakaraso kusa da ita,akan bedside drewar dake kusa da ita ya zauna yana kallonta,

"Baby..." Yakira sunanta tareda kamo hannayenta wadanda suka sha kunshi yarike acikin nashi yana bin zanen yana shafawa,

Kallonta yayi,wani blue din material ne ajikinta dinkin riga da skirt, takalmin kafarta shima blue sai babban mayafi data rufe jikinta dashi, dago habarta yayi ya kalli cikin idanuwanta,

"Nazata ai kuka kike yi..."

Shiru tayi bata yi magana ba,

"Baby Ina yimiki sannu da zuwa cikin gidana gidan dake kunshe da dunbin farin ciki da soyayya, da kauna tareda kulawa ta musamman, ina mai yimiki albishir da samun tsantsar soyayya ta gaskiya da samun farin ciki marar yankewa domin ni amatsayin abokiyar rayuwa na daukeki, sannan kuma na daukeki a matsayin abokiyar zamantakewa, abokiyar shawara, abokiyar gudanar da komai tare, ban daukeki a matsayin mata kawai ba, a'a har matsayin juya akalar rayuwata duk yana hannunki, dan Allah baby ki rikeni amana nikuma nayi miki alkawari insha Allah zaki sameni mutum nagari mai cika alkawarinki akoda yaushe..."

Dan tsagaitawa yayi yabar kan drewar din dayake zaune ya matsa kusa da ita,

"Daren yau darene wanda yake cike da tarin albarkatu masu yawa, domin daren juma'a ne haka kuma darene wanda nadiya ta kasance cikin dakin mijinta amadi, yanzu me yarage?"

Yi tayi kamar bataji tambayar tashi ba hakan datayi yasashi murmushi tareda yaye mayafin dake rufe ajikinta, karkatar da kanshi yayi zuwa gefe guda,

"Baby am asking you, yanzu me yarage agaremu? Me yakamata muyi?"

"Ban fahimceka ba?" Tayi magana muryarta can kasa,

"Cewa nayi yanzu meya kamata muyi?"

Shiru tasake yimasa ta dauke idonta daga kanshi,

"No idea...?" Ya tambayeta yana murza yan yatsunta,

Jin tayi shiru yasashi mikewa,

"To yanzu tashi zakiyi muyi salla sannan ina mai tabbatar miki da cewa ban manta da alkawarinmu ba so fell free...."

Tashi tayi yana rikeda hannunta suka fara tafiya,

"Ko indaukeki?"

Ya tambayeta bayan yayi kasa da muryarshi,

Bata kai ga yin magana ba kawai taji yayi sama da ita ya dagata, har cikin toilet din yakaita sannan ya ajiyeta,ba karamin kyau cikin toilet din yayi mata ba bayan haduwar da yayi gashi katon gaske,

Fanfo ya kunna ya daura alwala sannan ya jawota gaban sink din,

Hannuwanta ya kama yafara yimata alwalar, saida ya kammala wanke mata kafafu sannan ya kashe fanfon yasake daukarta zuwa cikin bedroom din,

Wata babbar dardumar salla sabuwa yadauko ya shimfida musu yajuya yana kallonta,

"Yi hakuri ki daure kizo muyi sallar sai kici abinci ki kwanta ki huta.."

Mayafinta ta dauka ta nade jikinta dashi taje bayanshi ta tsaya yajasu salla,

Salla sukayi raka'a biyu bayan sun idar yadafa kanta yafara karanto addu'o'i wadanda bata taba zaton ya iyasu ba, yajima yana yimusu addu'a sannan ya shafa yana kallonta, fuskarshi kadai zaka kalla kagane irin dunbin farin cikin da yake ciki,

Tashi yayi yafita babu jimawa sai gashi yashigo da wani babban farantin silver, agabanta ya ajiye farantin, robar sanyayyen laban ce babba sai glass cup guda biyu sannan sai wani filet dauke da gasasshiyar kaza mai romo wacce tasha kayan hadi sai kamshine yake tashi da turiri daga jikinta,

"Baby ga abinci kici..."

"Naci abinci..."

"A'a baby ko kinci zaki kara..."

"Nace maka nakosh..."

Shiru tayi sakamakon jin yasa mata naman acikin bakinta, dolenta tahadiye maganar tafara taunar tsokar naman,

"Ban son magana kawai dai kici kaza malama.."

Harararshi ta danyi ta dauke kai nan yafara rarrashinta sai kace cikinsa zata bawa, ahankali yake saka mata naman tana ci har saida ya tabbatar taci fin rabi sannan ya tsiyayo laban cikin cup ya bata, jinta take ta koshi dam dan haka kadan tasha ta dauke kanta,

Murmushi yayi ya dauke kayan yafita jim kadan sai gashi yadawo,

"Baby saura wanka daga nan sai ki kwanta kiyi bacci ko..?

Cikin toilet ya leka ya ciro mata babban towel guda daya, janta yayi jikinsa ya rungumeta sannan yafara yin kasa da zip din rigarta, rikeshi tayi,

"Kabarshi zanyi da kaina.."

"Ayya baby ban son ki wahala nefa shiyasa..."

Ji tayi ya daura mata towel din sannan yasaki rigar tafadi, saurin rike towel din tayi nan taji yayi sama da ita yanufi toilet,

"Ajiye anan zan shiga inyi, basai ka kaini ciki ba..."

Ajiyeta yayi yana yimata dariya,

"Babyn nan tawa akwai tsoro da yawa..."

Shigewa cikin toilet tayi bata mayar masa da martani ba, komai wanda zata bukata gashi nan an ajiye bisa kan wata yar kanta ta silver wacce ke daure ajikin bango kama tun daga kan sabulan wanka,gel, shampoo, maclean, brush da duk wani abu na bukata lokacin wanka,

Ruwan zafi ta tara ta surka da na sanyi tayi wanka da sabulu mai dadin kamshi sannan tayi brush ta fita,

Amadi baya cikin dakin amma ga sleeping gown nan ya ajiye mata akan gado, saida ta shafa dan cream marar maiko sannan ta shafe jikinta da body fantasy sannan ta dauko rigar,

Iya haduwa rigar ta hado amma kuma rigar bata da kauri bare duhu, pink ce pink dinma mai haske, dan siririn hannu gareta sai wani ado da aka yimata daga kirji bayan an danyi tattara kadan,

Kafada ta daga ta dauki fararen inner wears din da ke ajiye tareda rigar tasaka sannan ta zira rigar ta dauki towel din takai bisa kofar toilet ta rataye ta dawo ta kwanta,

Lumshe idanuwanta tayi tana jin wani irin sanyi yana ratsata,

Bata fi minti goma da kwanciya ba taji shigowar amadi, sanye yake da kayan bacci na maza maroon colour riga arm less da wando iya cinya, kan gadon ya hau ya matsa kusa da ita yafara mammatsa mata jikinta,

"Baby inyi miki tausa ko...?"

Bata iya amsa mishi ba illa sake lumshe idanuwanta da tayi bacci yasoma fisgarta sama sama.....

_Fadi kalma daya tak akan amadi, nidai nace gwani at fannin so....kufa?_



_*Ummi Shatu*_
[9/24, 7:39 AM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
     _(Labarin k'auna)_


    _*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*


® *HASKE WRITERS ASSO.*


          *68*

aishaummi.blogspot.com


      *Z*aman dirshan amadi yayi yana aikin yiwa nadiya tausa har saida yaji alamun bacci yayi gaba da ita sannan ya danyi magana ahankali cikin muryarsa mai mutukar sanyi,

"Baby.... Baby kinyi bacci ne?"

Jin bata amsaba ya tabbatar masa da cewar tayi bacci, tashi yayi yaje ya kashe light yadawo bayanta ya kwanta tareda kanannadeta acikin jikinshi,

Yajima baiyi bacci ba saboda tsantsar farin cikin da yake ciki,

Misalin karfe 2 nadare bacci yasamu nasarar daukarshi asuba nayi kuma ya farka,

Jikinsa ya zare yaje ya shiga toilet ya dauro alwala bayan yayi brush sannan yafito, kusa da nadiya yaje ya fara shafa fuskarta ahankali, jin sanyin ruwa akan kumatunta yasata sake tukunkune jikinta wuri guda tafara jan bargo zata sake lulluba,

Bargon ya rike da hannunshi,

"Baby...." Yakira sunanta ahankali,

Sake lumshe ido tayi ta yunkura zatayi juyi, riketa yayi,

"Baby tashi muyi salla sai ki koma baccin..."

Idonta ta bude ahankali tana kallonsa,

"Sallah...? Sallar yaushe?"

Murmushi ya danyi,

"Sallar asuba"

"Har lokaci yayi?" Ta tambayeshi tana mayar da idanuwanta rufe,

"Lokaci yayi..."

"Ba yanzu zanyi ba.."

Yaye bargon yayi ya kinkimeta ya saba akan kafadarshi yayi cikin bathroom din da ita,

"Wai kai baka gajiya da daukar mutum ne?"

"Ya za ayi ingaji da daukar ki? Ai bakida nauyi"

Bata yimasa magana ba har ya ajiyeta acikin bathroom din sannan yafita, brush tayi ta daura alwala ta fita tana lullumshe ido saboda bacci,

Hijabi taga ya ciro mata da zani,karba tayi ta daura zanin tasa hijab din, saida suka fara gabatar da sallar nafila raka'a biyu sannan suka yi sallar asuba,

Bata jima azaune ba ta shafa addu'a takoma kan gado ta kwanta batare data cire hijabin dake jikinta da zanin data daura ba.

Shi kam amadi zama yayi yafara karanta littafi mai tsarki,sai da ya karanta rabin suratul bakara sannan ya rufe alqur'anin ya mike daga kan abin sallar,lokacin har gari yayi haske sosai domin karfe 6 nasafe,

Wurin nadiya yaje nan yaganta tayi rub da ciki agefen gadon, ahankali ya dagata ya juyata yacire mata hijab din yazare mata zanin dake jikinta ya kwantar da ita,

Ac ya kunna mata ya fita, baccinta ita dai take sosai bata ma san abinda ke faruwa ba, ba ita tatashi ba sai misalin karfe 9 nasafe,

Zaune tatashi tana kallon gefenta ko amadi na nan amma bata ganshi ba, jikinta ta kalla taga babu hijabin da ta kwanta dashi sannan babu zanin data daura nan ta tabbatar da cewar amadi ne ya cire mata su,

Sauka tayi daga kan gadon ta nufi toilet, wanka tayi tafito tana daure da towel, gaban mirror taje ta zauna tafara shafe jikinta da lotion mai kamshi,

Kwalliya ta danyiwa fuskarta, body spray ta dauka tafara feshe jikinta dashi,

Jin alamun bude kofa yasata dan juyawa, amadi tagani tsaye yana kallonta yana sanye da t shirt yellow anyi rubutu da pink din kala anrubuta have a nice day, sai bakin jeans da yasa fuskar nan tashi annurin kyau ne kawai ke fita daga cikinta,

"Good morning baby?.."

Yace da ita yana murmushi, ahankali yafara takawa zuwa gareta yana yimata murmushi,

Ta bayanta yaje ya tsaya yana kallonta ta cikin mirror, ita dinma kallonshi ta danyi,

"Ina kwana?"

"Lafiya lau baby na, how was your night...?"

Bata amsaba dan haka yayi hugging dinta ta baya yafara kissing din wuyanta,

"Dan matsa zanje na saka kaya.."

Matsawar yayi kamar yadda tace nan tawuce zuwa wurin drewar din kayanta, tana budewa taga wasu hadaddun english wears ajere kamar boutique, kayan tabi tana dagawa amma kaf babu na hausawa,

Juyawa tayi ta kalleshi yana tsaye ya harde hannuwanshi akan kirjinshi yana kallonta,

Batayi magana ba ta ciro wata dark blue din doguwar riga mai hannu daya sannan anyi tsaga tun daga wurin cinya har zuwa kasa ta gefe daya,

Inner wears ta ciro ta juya ta kalleshi,

"Ka fita zan sa kaya"

Murmushi yayi yajuya yafita, inner wears din ta saka sannan ta saka rigar,

Gaban mirror taje tafara gyara gashin kanta da cumb, sake dawowa cikin dakin amadi yayi,

"Wowwww....baby you look..."

Ji tayi ya rungumeta yana kissing dinta cikin so da kauna,

Wata yar siriryar sarka da dan kunne tasa,

"Zo muje kiyi breakfast.."

Hannunta yakama sai faman binta da kallo yake yi har suka fita falo suka wuce kan dining,

"Hajiya ce tayi mana dazu naje na karbo.."

"Allah sarki ai da bata wahalar da kanta ba ni sai inyi.."

"Karki damu baby kin cancanci haka"

Kulolin dake ajiye akan table din ya fara budewa, wainar shinkafa ce fara tas da ita sai miyar agushi wacce taji naman rago, gefe daya kuma kayan tea ne da ruwan zafi acikin tea flask,

Wainar ya zuba musu yafara bata tana ci,

Cikeda kulawa ya ciyar da ita takoshi sannan shima yaci,

"Wai ina kayana ne? Ina son zuwa ingaida hajiya.."

"Zakije ba yanzu ba sai da yamma.."

Batayi maganaba tayi shiru, ji tayi ya kinkimeta yayi daya bedroom din da ita wanda yake can gefe daya,

Suman zaune takusa yi saboda tsabar haduwar da dakin yayi, komai naciki pink and ash colour ne, daga gani shine dakin amadin,

Akan gado ya kwanta da ita yabita ya kwanta asamanta,

"Kallo zamuyi ko labari?"

Rufe idanuwanta tayi bata amsa ba, remote yajawo ya kunna tv yakamo tashar zee world, cakulkuli yafara yi mata tun tana daurewa saida tayi dariya,

"Dan Allah bari.."

"To kibude idonki muyi kallo.."

"Zan bude.."

"To bude"

Budewa tayi sannan yadaina yimata cakulkuli din, pillow yaja yatasa kanshi dashi sannan yasata ajikinshi ya rungumeta,

Ita dai kawai kallon take amma bawai dan tana so ba, har azahar tayi suna tare suna kallon, sakinta yayi taje tayi alwala, tana cikin daura alwalar yashiga toilet din,

Shima alwalar yayi suka fito atare,salla suka yi sannan suka koma falo, wainar da sukaci da safe ita suka kara ci,

Janta yayi suka zagaya gidan taga yanda aka kawatashi da ababen more rayuwa na zamani, ko ina yayi ba karya, hatta dan corridor dinnan wanda tagansu yana kissing din zee aciki an kawatashi da wasu kyawawan flowers sannan anzuba kujeru da dan table atsakiya domin hutawa,

Bayan sun gama zagaya ko ina yajata suka koma cikin falo,

"Zo inyi miki doki.."

Makale kafada tayi alamun bata so,

"Ko bakya so sai nayi miki saboda jikina yayi min nauyi.."

Sunkuyawa yayi ta haye bayanshi yafara zagaya falon da ita.

Saida yaji yagaji sosai sannan ya zame ya kwanta tareda birkitota kanshi, ajikinshi ya rungumeta sosai yafara lumshe ido alamun bacci ga mamakinta kuwa mintuna kadan taji ya fara ajiye ajiyar zuciya ahankali yana fitar da numfashi cikin nutsuwa alamun bacci,

Zama taci gaba dayi ajikinsa har na tsawon wani lokaci kafin ta janye jikinta takoma dakinta, wanka ta sake yi tasha kwalliya, tunowa tayi da tunda tazo bata leka dakin dake opposite da nataba dan haka batare da bata lokaci ba ta nufi dakin,

Komai nacikin dakin sak irin natane sai ko kala da ta banbanta domin shi wannan milk and coffee colour ne kayan ciki,

Akwatunan kayanta tagani ajiye agefe guda nan farin ciki yakama ta,bude akwatin taje tayi ta dauko wata atamfa Holland dark green mai zanen buta ajiki ta saka,

Sarka da dan kunne da bangles tasa ta koma falo wurin amadi yana nan ayanda tatafi tabarshi yanata shakar baccinshi,

Kan doguwar kujera tahau ta mike tana bin falon da kallo, komai na gidan amadi yafi na gidan kabeer kyau da haduwa sannan shi kansa kabeer din amadi yafishi kyau da gogewa irinta gayu, ta tabbata Allah ne yayi mata zabi har yabata amadi domin ya maye gurbin kabeer bawai iyawarta ko dabarar ta ba,

Ita dinma baccin ne yadan fara daukarta sama sama sai kuma taji motsin mutum ajikinta, bude idonta tayi ahankali nan taga amadi yana aika mata da tsadadden murmushi mai sanyaya zuciya da kashe jiki,

"Baby kinyi kyau...." Bai kai ga barinta tayi magana ba yakai lips dinshi kan nata,

"Shine kika tashi baki tasheni ba ko.."

"Ai naga bacci kake"

Mikewa yayi ajikinta, yana shakar kamshin da jikinta yake fitarwa, ganin lokacin salla yakusa yasashi tashi yaje yayi wanka yasake kaya yafito,

Sallar la'asar suka yi sannan suka tafi part din hajiya domin gaidata,

Ba karamin murna hajiya tayiba lokacin data gansu, har kasa nadiya ta tsugunna ta gaisheta shi kuma amadi sai wata shagwaba yake zubawa hajiya kamar wani yaron goye,

Basu suka bar part din hajiya ba sai bayan sallar isha, yau ma kamar jiya shine ya timaka mata tayi komai sannan ta kwanta sai lokacin shikuma yaje ya shiryo yadawo dakinta, rungumeta yayi yana shafar kanta,

"Baby yau dai bazaki yi bacci da wuriba dan haka kiyi min tatsoniya.."

"Ni ban iyaba.." Tabashi amsa,

"Ni na iya bari inyi miki.."

Tatsoniya yashiga yi mata wanda tun tana amsawa har dai yaji tayi shiru alamun tayi bacci, addu'a yayi musu ya lullubesu, gaba daya kasa baccin yayi sai tunane tunane kala kala dake addabar zuciyarsa.

  Haka suka kasance har na tsawon kwana biyar, kullum hajiya ke aiko musu da abinci har nadiya tafara girki da kanta sannan idan tayi sai ta zubawa hajiya nata daban a kula akai mata,

Iya soyayya amadi yana nuna mata, komai tare suke yi dashi baya barinta tayi ita kadai.

Fitowarta daga wanka bayan tagama aiki ta zauna tayi kwalliya, towel dinta ta sauke domin saka kaya,

Burum amadi yashigo kamar wanda aka koro,

"Ahmad menene haka.." Tafada batare data jiyo ba,

"Baby abu nake nema yi hakuri..."

Riga ta saka sannan ta juya tana kallonsa yana bincike acikin drewar din gadonta,

"Wai me kake nema?"

"Wani sim pack da nashigo dashi nan jiya"

Murmushi tayi tajuya takarasa shiryawa sannan ta dauko sim pack din ta nuno masa,

"Ka ganshi nan amma tunda kashigo min daki batare da excuse ba bazan baka ba..."

Tsalle yadaka sai gashi agabanta, daga shi sai short nicker babu ko riga,

"Yi hakuri baby bazan sake ba.."

Yace da ita tareda langabe kanshi,juyawa tayi zata matsa daga wurin yayi gaggawar rikota,

Hannuwanta ta boye abaya bayan ta matse sim pack din atafin hannunta, janta yayi zuwa jikinshi yana kallon fuskarta,

Gam tarike sim pack din tahanashi turata baya yayi tafada kan gado yabita nan yafara kokarin kwatar sim pack din,

Sun dade suna burgima akan gadon kafin ya rufe bakinta da nashi, difff sukayi daga shi har ita sai ko numfashinsu dake cin karo da juna wurin fita,

Sun debe lokaci mai tsawo cikin wannan yanayi, amadi ne yafara sassauta rikon da yayi mata, tashi yayi jikinsa a mace ya fita daga dakin, sim pack din da bai dauka ba kenan yakoma dakinshi ya kwanta rub da ciki akan gado, ajiyar zuciya yake ta faman saki ahankali yana jin wata irin matsananciyar bukatar nadiya a wannan lokacin,

Saida yadanji nutsuwa sannan yatashi yashiga wanka,

Itama acikin yanayin mutuwar jiki yatafi yabarta, ahankali take sauke numfashi har numfashin nata ya daidaita, kasa fita tayi dan haka taci gaba da zamanta acikin daki har amadi ya shigo,

Blue din t shirt ce ajikinsa sai farin jeans, batare da ya karasa wurinda takeba yayi mata magana yana murmushi,

"Baby abinci...." Yafada cikin shagwaba, tashi tayi ta sauko daga kan gadon tazo zata wuce ta gefenshi, sim pack din dazu ta mika masa batare data yi magana ba, karba yayi yana murmushi,

Koda sukaje dining dinma domin cin abinci nan dinma wani sabon yanayin ne yarinka ziyartar su,

Akoda yaushe hakace take faruwa tsakaninsu, satinsu uku da tarewa yan gidansu nadiya suka zo harda mama ganin gida, wuni suka danyi mata sannan suka tafi,da kuka suka rabu itada twins dinta kamar wata yarinya haka ta zauna tana kuka, rarrashinta amadi yafara yi,

"Yi hakuri baby, tunda babu twins ai gani..."

Jin batayi shiru ba yasashi manna bakinsa kan nata, shiru tayi batare data shiryawa hakan ba,nan yashiga rarrashinta a aikace bada bakiba,

Daren ranar dakyar amadi yasamu bacci, tunani yafara yi aranshi kodai yadaina zuwa dakinta ne saboda kullum awahale yake barci sannan koda rana ne idan suna tare hakanne ke faruwa shikuma baya son karya alkawarin da ya daukar mata,dan baya baya yafara da ita, ko zuwa kusa da ita yadan rage to amma kuma shakuwar da ta dade da shiga tsakaninsu ita ke hanashi nisantarshi domin ko yawo bai iyaba kullum daga wurin aiki sai part din hajiya sai ko gida, koda yaushe suna kusa da juna sannan komai tare suke yi, ko makaranta sukaje basa iya rabuwa, daga yaji baiji motsinta ba zai lalubota awaya ko ita ta kirashi, haka daya baya iya cin abinci batare da daya ba wannan sabonsu ne,

Irin zaman da suka cigaba da yi kenan, kullum tare suke tafiya wudil su dawo tare, aikin gidan tare suke yi, girki, shara, wanke wanke,cin abinci komai tare suke gudanarwa,wannan dalilin ne yasa suka shaku mutuka.

Kasancewar yau weekend ne duk suna gida shida ita, farcenta yagyara mata ya kankare mata shi, itama tagyara masa nashi,

Part din hajiya yatafi ita kuma ta shiga kitchen ta sauke girkin da ya kammala na rana,

Daga ita sai wata yar farar yaloluwar riga iya cinya,dakinta takoma ta kwanta akan gado tafara tsifar kitson dake kanta, tun tanayi har tagaji ta kwanta sai bacci,

Ahaka amadi yashigo ya sameta, gefen kanta yaje yazauna ya dora kanta akan cinyarshi yafara yi mata tsifar, har yagama bata tashi ba yana kokarin zameta yatashi ne yaga ta bude ido,

"Baby kin tashi? Nayi miki tsifa saura abu daya.."

"Me?" Ta tambayeshi,

"Wanke gashi.."

Baj jira amsarta ba ya ciccibeta sai bathroom, ajiyeta yayi ya debo man wanke gashi kala kala yasoma wanke mata,

Rigarta ya sabule,

"Saura wanka.."

Rigar tarike, "nidai a'a"

"Wallahi sai nayi miki wanka yau.."

Jin abinda yace yasata kyaleshi ruwa ya sakar musu akansu, ganin yafara zare rigarshi yasata saurin lumshe idonta,

Sai da yayi musu wanka tas shida ita amma yakasa daina saba mata soso da sabulu, sunfi awa daya dakyar ya iya daura mata towel ya ciccibeta zuwa cikin dakinta, idanuwanshi sun gama sauya kala jikinsa duk babu kuzari amace,

Akan gado ya shimfidar da ita, ita dinma tana jinta cikin wani irin wahalallen yanayi domin dure duren umman sumaila yau kam sunce sai anfitar dasu, har wani hajijiya takeji da hajijiya tana daukarta banda murdawar da mararta tafara yi kamar wacce zatayi period,

Jin ya ajiyeta yana kokarin tafiya yasata bude lumsassun idanuwanta wadanda ke jike jalaf da ruwa sunyi wata kala tadaban,

Hannunshi ta riko......

_Sakon fatan alkhairi gareki mamu Allah yaraba lafiya..._




*_Ummi Shatu_*
[9/27, 7:50 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
   _(Labarin k'auna)_


    _*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*
  _Home of expert & perfect writers_

   _Fatan alkhairi ga masoyana masu karanta labaraina aduk inda suke, wannan shafin kyauta ne agareku,duk wata masoyiyar Ummi Shatu wannan shafi natane... Ina alfahari daku_


          *69*

aishaummi.blogspot.com


      *J*uyowa yayi yana kallonta, ganin irin kallon da yake yi mata yasata saurin lumshe idanuwanta,

Dawowa yayi zuwa gaban gadon ya tsugunna yana rike da hannunta jikinsa yana digar da ruwa,

"Baby ya akayi..?" Ya fada acan kasan makoshinsa,

Ita maganar ma gaba daya bata jin zata iya dan haka tayi shiru sai sake matse hannunshi da tayi cikin nata,

"Baby..."

Yasake kiran sunanta domin yana son gasgata abinda zuciyarshi ke raya mishi,

Mikewa yayi nan taja hannunshi, ajikinta ya samu masauki ya daga kanshi yana kallonta, bakinta takai bisa nashi,

Dakyar ya iya raba bakinsa da nata,

"Baby kin amince? Bazaki zargeni da laifin karya miki alkawari ba..?"

Kai ta daga masa, cikeda farin ciki hadida doki yafara warware towel din dake nade ajikinta.

***

  Abangaren kabeer kuwa al'amura sun fara sauki domin tunda su fati da A'isha sukaje suka ga halin da yake ciki suka koma suka sanarwa da mama da abbansu daga mama har abban babu wanda ya kula maganar domin sunce sun dade da cireshi daga sahun yayan da suka haifa,

Kuka A'isha da fati suka shiga yi suna rokon su abban amma basu sauraresu ba daga karshe saida maganar taje kunnen abban su nadiya da umman sumaila, taruwa sukayi gaba dayansu suka tattauna tareda bawa juna hakuri tunda dai kabeer dansu ne babu yanda zasuyi sannan hannunka baya rubewa kace zaka yanke ka yar, dan haka yazama wajibi su tsaya su taimaki rayuwarsa su rabashi da asabe ko zai samu damar fita daga halin hau'ula'in da yake ciki tunda dai Allah ya rufa asiri ta sanadiyarsa zumunci bai rabu ba,

Dakyar aka samu Abba da mama suka sauko suka yarda da abinda yan uwa suka fada, nan aka dukufa ka'in da na'in wurin rokon Allah tareda yin sadaka akai akai domin Allah ya raba kabeer da masifar da yake ciki,

Cikin ikon Allah hankalinsa yafara dawowa jikinsa tun da ya kyalla ido yaga asabe agidansa hankalinsa yatashi domin bai san ya akayi ma har ya aureta ba, jinsa yake kamar wani sabon mutum wanda ya shafe shekaru aru aru cikin halin lalurar tabin hankali, jinsa yake kamar dogon barci yayi mai tsawo sai yau ya farka,

Tamkar zautacce ya zama sai faman kiran nadiya yake, nan hankalin asabe yayi kololuwar tashi domin bata tsammaci aikin boka na kududu zai karye da wuri ba,

Cikin dare kabeer yaketa aikin zuba mata masifa yana zaginta yana cewa sai tabar masa gidansa, ina nadiya? Wannan tambaya yayi mata ita tafi sau dari cikin wannan dare,

Daren ranar basu runtsa ba saboda tashin hankali, zagi kuwa asabe ta shashi agun kabeer yafi akirga sai kiranta da karuwa yake,

Lokacin da asuba tayi yafita salla lokacin ne tasamu damar kiran kawarta teemah ta zayyane mata abinda yake faruwa nan teemah tabata shawara, sosai taji dadin shawarar teemah kuma tayi na'am da ita,

Shi kuwa kabeer yadade yana addu'a a masallaci domin yaushe rabonsa ma da zuwa masallacin? Shi kansa bazai iya tuna lokacin ba domin tunda asabe ta shigo cikin rayuwarsa komai nasa ya lalace,

Yana fita daga masallaci yaje ya figi mota sai gaidansu, ganinsa sassafe yasa mama cikin tashin hankali domin tayi zaton ba kalau ba,

Kuka yasata agaba yafara yi yana neman gafararta tareda rokon cewar ta yafe masa,

Mama cewa tayi ta yafe masa duniya da lahira, cikin wannan hali abba yashigo ya riskesu shi dinma gafararsa kabeer ya nema yana kuka hawaye bibbiyu akan kumatunsa,

Dukkaninsu iyayen nasa sun yafe mishi amma Abba yabashi shawarar cewar ya tsaya yadage da addu'a sannan indai yana son ya zauna lafiya to ya zama dole yarabu da asabe, shiru yayi yana goge hawayen fuskarshi domin dama ko abba bai fada ba yanada wannan tunanin na sakin asabe,

Har karfe 10 tayi yana gidansu tareda iyayen nasa suna dorashi akan hanya mai bullewa, 10:30 ya tashi ya tafi da niyyar zai dawo gidan anjima,

Koda yakoma Gida tun daga get ya hade rai domin yau so yake ya nunawa asabe cewar tayi babban kuskure amma kuma koda yashiga cikin gidan sai me??

Komai an hargitsa shi baya bisa ka'ida, fuskarshi ahade yashiga falonta nan dinma anyi kaca kaca dashi, haka bedroom dinta ma amma kuma ita bata nan, nan yashiga dubata amma babu ko alamarta, ganin babu wasu muhimman kayanta ya tabbatar masa da cewar bata gidan, gaba daya ta tattare kayanta da nasa masu amfani ta gudu.

Zama yayi cikeda takaici gamida dana sani mai tsanani tareda bacin rai dake faman ziyartar zuciyarsa, in banda tafarfasa babu abinda zuciyarsa keyi, sannu ahankali wasu hawayen nadama suka fara bin kumatunsa,

Yadade zaune yana kukan takaici kafin ya iya tashi, yama rasa abinda zaiyi domin idan yace zaibi asabe mc to bai san ta inda zai fara nemanta ba domin ko yaje jos zaiyi wuya yaganta,

Sake rufe gidan yayi yafita ya nufi masallaci domin har azahar ta kusa, daga can gidansu yasake komawa nan ya zauna tareda su mama, mama sai nasiha take yimasa tana yimasa fada akan rayuwa domin ko yanzu yaga darasi irin na kaidin mata.

Sai dare yabaro gidan yakoma nasa, kasa bacci yayi sai aikin tunani, can karfe 2 nadare yaji alamun dirgowar mutane cikin gidan, ta window yaleka nan ya hango mutane guda hudu da bakaken kaya hatta fuskarsu rufe take da bakin abu, mai gadin gidan yaga suna kokarin daurewa dan haka yayi gaggawar neman wurin buya.

Cikeda da sand'a hannuwansu rikeda bindigogi suka shiga dakin nasa amma neman duniya sunyi basu ganshi ba, ko ina na gidan saida suka caje tsaf amma babu kabeer,

"Ya oga yakamata fa mu ware tunda bamu ga wannan gayen ba, kar asuba tayi mana anan.."

D'aya daga cikin yan fashin ya fada,

"Haka za ayi zaki bari nakira waccar mata..." Ogan yafada yana latsa wayarshi, mintuna kadan yakara wayar a kunne,

"Ya kun kasheshi..?"

Asabe mc ta tambayeshi ta cikin wayar,

"Ai bamu ganshi ba, da ace mun ganshi da tuni mun dade da hallakashi.."

Dan shiru yayi yana saurarenta kafin yace,

"Shikenan bari mu faso.."

Juyawa yayi ga yaranshi, "ya kuzo mubar gidan nan kun san tafiyar mu mai nisa ce.."

Basu kara bi takan mai gadin ba suka kama katanga suka tsallaka bayan yan mintuna kuma yaji sun sake dawowa sun dauki motarsa kwaya daya wacce tayi saura, duk abinda yake faruwa akunnen kabeer ne domin yana makale cikin rizabuwa yana jinsu, dama rizabuwar babu ruwa yanzu aciki ita yabude yashiga ciki ya buya,

Duk da yaji tafiyarsu amma bai iya fitowa ba har saida asuba tayi, duk yabi yahada zufa,

Mai gadi yaje ya kunce wanda duk yajigata.

  Gari yana wayewa kabeer ya sallameshi sannan shima ya hada duk kayanshi wadanda sukayi saura wanda yasan zai bukata ya kulle gidan yanufi gidansu,

Al'ajabi sosai su mama suka shiga domin abin al'ajabine wai asabe mc tasa ana farautar rayuwar kabeer, tun daga wannan rana yakoma gidan da zama, gashi babu aikin yi nan yashiga fafutukar neman wani,

Duk da yanajin kunyar abban nadiya da mamanta haka ya daure ya cije yaje gidan ganin yaransa, yaji dadin yanda aka karbeshi babu wanda ya nuna masa koda afuska, tun daga ranar yasamu wurin zuwa, kusan kullum sai yaje gidan yaga yaransa.

***

   Soyayya mai sanyi amadi ya shiga nunawa nadiya, ita kanta tasan tayi sa'ar miji domin komai nashi cikin nutsuwa yake aiwatar dashi sai dai abinku da sabin shiga dole sai ya nuna rawar kai,

Ita dariya ma yake bata amma bata samu zarafin yin dariyar ba har saida nutsuwarta ta dawo gareta,

Hannunshi takama tana dariya kasa kasa, idonshi ya bude ya kalleta yana sauke ajiyar zuciya ahankali,

"Baby dariya..." Yafada ahankali cikin sanyin murya yana kallonta,

Girgiza masa kai tayi tana kunshe dariyarta, jikinta ya matsa ya rungumeta yana gyara mata gashin kanta wanda yake ajike jalaf ya zubo ya rufe mata fuska,

"Baby Allah yayi miki albarka, Allah yasa ki haifa min twins..."

Kallonshi tayi ta mayar idanuwanta ta lumshe,

"Saboda baka san wahalar dawainiyar yan biyu ba ko shiyasa kake yimin fatan..."

"Meye wahalar aciki?" Ya katseta,

"Rainonsu.." Tabashi amsa,

"Zan tayaki.."

Yatsanshi yadora akan lips dinta ya hanata magana, wani sanyayyen kiss ya manna mata akumatu sannan yafara nuna mata soyayyar da yake mata akaro na biyu, sam bata yi yunkurin dakatar dashi ba domin shi bai taba aure ba yaune rana mai daraja agareshi,

Jinsa yayi acikin wata duniya ta daban wacce bazai iya fassara yadda takeba,

"Baby indai hakane amma kin dade kina cutar damu, meyasa baki bari mun samu wannan farin cikinba tun farkon auren mu... Kar Allah ya maimaita min rayuwar da, baby da batayi ba, yanzu ne nasan ni dan gatane cikakke..."

Rungumeta yayi yana jin sonta yana sake ratsashi,

"Amadidi tashi..." Yaji tafada,
"ba amadidi ake cewa ba, amadi zaki ce" yabata amsa idanuwansa arufe,

"To didi..."

"Meye kuma wani didi sai kace yaro..?

"Dafa? Koda yake yau ka dan fara girma ashe.."

Ya fuskanci tsokanarshi take yi shiyasa ya rabu da ita yana murmushi shi kadai,

"Kaida wa?"

"Muje inyi miki wanka.."

"A'a nagode..."

Ko saurarenta baiyi ba ya dauketa zuwa toilet,duk da itace ta nema da kanta saida taji ya isheta saboda wankan ma bai yiyuba, yau ta barowa kanta aiki,

Sai da aka dade iya dadewa sannan wankan yasamu suka fito yana goye da ita abayanshi.

Towel yadauka yafara goge mata jikinta dashi yana aika mata da murmushinsa mai sanyi,

"Baby.... Ince wani abu?"

"A'a karka ce"

"Saboda me?" Ya tambayeta yana yi mata murmushi, cumb ya dauka yasoma taje mata gashinta,

"Saboda nasan abinda zaka ce.."

"Taya akayi kika sani?"

"Nidai nasani dan haka basai kafada ba..."

Dariya ya danyi yalashi jan lips dinsa,

"Allah baby yau kin sa nazama kamar maye..."

"Shine"

Tabashi amsa bayan ta kwace cumb din, bai hakura ba yakoma bayanta ya zauna tareda rungumeta,

Rabuwa dashi tayi taci gaba da taje gashinta tana gyarashi,

Daure gashin tayi da blue din ribom ta mike taje ta dauko wata doguwar riga mai santsi yar kanti mai karamin hannu tasa,

Amadi ta kalla wanda ke zaune ya langabe kai yasa yatsanshi daya abaki, murmushi tayi,

"Wallahi yan auta dama sai ahankali, kalleka fa yanda kayi kamar wani dan karamin yaro..."

"Su kuma yan fari fa? Fada min su yasuke" yabata amsa bayan ya mike,

"Ai kasan dai yan fari sunfi yan auta ako ina..."

"Sharafffff malama.." Yace da ita tareda ficewa daga dakin, dakinshi yaje ya shirya mintuna kadan sai gashi ya shigo, tana gaban mirror tana saka dan kunne bayan tayiwa fuskarta kwalliya,

Ta cikin mirror din ya nuna mata rubutun dake gaban rigarsa, rubutun ta kalla _Yes I did it_ shine abinda aka rubuta, murmushi tayi masa wanda ya ratsa zuciyarsa har yakasa hakuri saida yakai ga bata tukwici ta hanyar shanye gaba daya jan bakin da ta shafawa lips dinta,

Duka ta dan kai mishi akirji ta harareshi,

"Biyani jan baki na..."

Saida yasake tsotson bakin nata sannan yashafa mata wani yana yi mata gwalo,sake shagwabewa tayi nan ya dauketa cak yayi falo da ita,

Sallar azahar suka yi tare sannan suka ci abinci, matseta yayi tsam ajikinshi yau gaba daya ya hanata ko fita nan da can, ko part din hajiya yahanata lekawa, duk inda tayi yana biye da ita kamar wani jela har dare yayi,

Yau ko yar hirar ma da suka saba yi bai barsu sunyi ba saboda fitinarshi, ita nadiya duk yagama isarta,

Da safe da zazzabi yatashi, dariya nadiya tayi,

"Maganinka, anfada maka haka akeyi? Kabi komai asannu kaki"

Kallonta yayi yatashi zaune,

"Dariya kike yimin ko baby? Dariya ko? Nagode.."

Tashi yafara kokarin yi nan tahanashi tashige cikin jikinsa tana murmushi,

"Yi hakuri didi na, wasa fa nake yimaka, anjima zakaji zazzabin yatafi ai, sannu"

Daga mata kai yayi, haka yawuni bai fita ko compound din gidan ba har yamma sai lokacin yaji jikinsa yayi masa daidai sannan zazzabin ya sauka, wanka yayi yasa kananan kaya na hutawa,

Kan doguwar kujera yahau ya kwanta ya tasa kanshi da cinyar nadiya, yar hira yake yimata kadan kadan yana lalubarta,

Dabara tayi masa tace yatashi suje su gaida hajiya, tashi yayi suka fita zuwa part din hajiyan, suna zuwa sukaga anty siyama sunzo itada yaranta guda biyu da zee din amadi,

"Lahhh anty dan waken zagaye akayi mana yau?... "

Amadi yafada yana rungume yaran ta,

"Dama na jira ku fito ne, kun san ba ashiga gidan amare kai tsaye... Ko ba hakaba anty amadi??"

Murmushi yayi ya kalli nadiya nan tayi saurin wucewa tabarshi,

Saida suka gaggaisa sannan suka dunguma suka koma part din su amadi, nadiya ko kallon zee batayi ba bare su gaisa,

Abaya amadi ya tsaya, yana ganin Anty siyama tawuce yajawo nadiya, ita dinma dayake tana son bawa zee haushi bata ki ba harda su bashi kiss akumatu,

Su anty siyama sun dan jima sannan suka tafi nadiya sai cewa take abar mata yaran suyi kwana biyu amma fur amadi yaki yace a'a angonci yake yi, anty siyama kam jan yaranta tayi tace itama bazata barsu ba dama.

Babin rayuwa mai dadi suka bude domin itama nadiyan yanzu tafara sonshi wanda ita kanta bazata ce ga lokacin data faraba,

Komai tare suke gudanarwa shiyasa suka shaku da juna sosai,saida sukayi sati uku agida suna gudanar da soyayya sannan suka fara fita.

Yau juma'a da misalin karfe 9 nasafe nadiya na kitchen tana shirya musu breakfast,

Amadi ne yashigo yana mika daga shi sai gajeren wando da riga armless milk colour amma duk da haka ba karamin kyau yayiba kamar badaga bacci yatashi ba,

Rungumeta yayi ta baya tareda kashe gas din datake girki,

"Didi meye haka?" Tafada tana harararshi awasance,

"Zo muje kiji, magana zamuyi.."

Bata musuba tabishi zuwa cikin bedroom dinshi, zaunarta yayi agefen gado shima yazauna yana facing dinta,

Yadauki mintuna masu tsawo yana kallonta batare da yayi magana ba,

"Didi menene? Kafada min mana"

Idanuwanshi ya lumshe nan kyawunsa yasake bayyana,

"Baby kina sona?"

Kallonshi tayi cikin rashin fahimta,

"Meya faru?"

"Kawai kibani amsa.."

Kai ta daga mishi,

"Ehhh ina sonka"

Ajiyar zuciya yasaki,

"Baby kiyi hakuri da abinda zan sanar dake ahalin yanzu, idan kabeer yadawo yace yana son ki koma gareshi zaki amince?"

Hankalinta ne yasoma tashi ta kalleshi,

"Haba didi, inkoma wurin kabeer inyi me bayan inada kai ahalin yanzu, meya kawo wannan maganar?"

"Baby zaki koma ga kabeer nanda dan lokaci takaitacce, yau ranace wadda zan fito infada miki gaskiyar koni waye... Yau zan bayyanar miki da wani labari wanda ke baki saniba..."

Hannuwanta da suka fara rawa ya rike yana kallonta, gaba daya jikinta rawa yake kamar mazari alla alla take taji abinda zai fada mata domin hankalinta yatashi mutuka,

"Didi ka sanar dani, me yake shirin faruwa ne?"

Kallonta yayi ya sunkuyar da kai,

"Nadiya nasan ada bakya sona kuma bakya kaunata, to ni dinma ban aureki dan kisoni ba domin inada wacce take sona kuma zan aurota mu zauna nan bada jimawa ba, ni dama na aureki ne kawai domin inyi taimako guda daya.. "

Idanuwa ta zaro tana kallonshi, tuni goshinta ya jike da gumi duk da sanyin ac din dake kadawa, wannan shine bazata, bakinta yana rawa tace,

"Didi taimakon me? Dalilin wanne taimako ka aureni?"

Nikaina Ummi Shatu tambayar da take makale akan fatar bakina kenan,haka kuma masu karatu nasan kuna bukatar wannan amsa....


*_Ummi Shatu_*
[9/28, 8:49 PM] Ummi ~ Liman: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
     _(Labarin k'auna)_


         _*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO.*
_Home of expert & perfect writers_


    _Ina mika sakon gaisuwa da babbar murya ga masoyan anty amadi musamman wadanda basa son rabuwarshi da nadiya, anty amadidi yagaisheku kyauta, haka duk wata wacce page 69 ya girgizata ko ya taba zuciyarta to ummi Shatu tabata page 70 kyauta tukwici agareta,sannan masoya kuyi hakuri kuma kuyi min uzuri domin littafin mijina sirrina labarine wanda yafaru agaske bawai kirkirar labarin nayi narubuta ba dan haka banida damar canjashi dole yanda yafaru haka zan rubuta saiko yan abubuwan da baza arasa ba, masu yimin text da masu kirana da wadanda suka nemi contact dina basu samuba duk nagode da kokarinku sannan ina gaisheku aduk inda kuke..._

  *Ke din ta dabance maryam qaumi, hakika banda kamarki kawata, Allah yabarmu tare,*

        *70*

aishaummi.blogspot.com


     *G*aba daya jikin nadiya karkarwa yake yana rawa, so kawai take taji labarin da Amadi yace zai sanar da ita wanda ita bata saniba,

"Didi karka yimin haka, amadi idan ka yaudareni kayi wasa da zuciyata har nafara sonka bayan ada ba sonka nake yiba wallahi sai Allah yayi min sakayya..." Tafada idanuwanta sunyi jajur kamar gauta amma bata bar hawaye ya disa daga idanuwanta ba,

"Kiyi hakuri nadiya, nima ba ason raina zan barki ba sai dan babu yanda zanyi,

Abune wanda yazama dole sai nasanar dake, dan Allah ki nutsu ki saurareni sannan ki yarda da kaddarar data riski rayuwarmu adaidai lokacin da muka shaku da juna, muka aminta da juna, zuciyoyinmu sukai tarayya awuri guda..."

Shiru yayi na dan lokuta yana kallonta wanda shi dinma idanuwanshi sun kada sunyi jajur kamar gauta,

Jin yayi shiru yakasa magana yasata kallonshi da jajayen idanuwanta, idanuwanshi akasa suke yakasa koda kallonta,

Yau nadiya jinta take kamar acikin mafarki take, gaba daya nutsuwarta bata tare da ita,

"Ka fada min abinda zaka fada min ina sauraronka.." Tace dashi bakinta yana rawa da jikinta gaba daya,

"Nadiya  kabeer ne yasani in aureki,

Mun hadu dashi ne akasar misra lokacin hajiya bata da lafiya an kwantar da ita, shikuma ban san uzurin da yakaishi ba, anan mukayi sabo dashi har takaimu ga kulla alkawarin taimakawa juna,

Nadiya ba auren kisan wuta nayi dake ba..."

Katseshi tayi cikin karaji,

"Karya kake macuci azzalumi, idan ba auren kisan wuta kayiba me kayi..?"

Kwalarshi taje taci tana girgizashi,

"Ina tambayarka idan ba auren kisan wuta ba me kayi? Kafada min abinda kayi.."

"Nadiya wallahi nafi karfin nayi auren kisan wuta, kin san dai munada kudi bare kice ko dan kudi nayi, inada ilmi bare kice dan neman wani abu nayi ko dan jahilci, inada duk wani abu wanda dan adam yake nema acikin rayuwa..."

Kukan data fashe dashi shine yakatse maganar da yake yi,

Kifa kanta tayi ajikin gado tana kuka,kafin ta dago ta rungumeshi tana fadin,

"Ni bana son kabeer yanzu kai nake so, meyasa zaka koya min sonka bayan kasan ba son gaskiya kake yimin ba...?"

"To ai kinki bari inyi miki bayani sai faman kuka kike..."

"Wanne bayani zaka yimin? Bayan kaci amanata.."

Zame hannuwanta yayi daga jikinshi ya mike zuwa wurin bedside drewar nan ya bude ya ciro wata zungureriyar takarda wadda dama da alama yajima da tanadarta,

Ajiye mata takardar yayi akan hannunta yafita daga dakin, dafe takardar tayi tana kuka batare data dauka ta karanta ba,

Kukanta taci gaba dayi bata ko motsa ba daga inda yatafi yabarta, tsabar kuka idanuwanta duk sun kumbure sunyi jajur, kanta kuwa kamar zai fashe da ciwo ga yunwa da take faman damunta domin bataci komai ba,

Haka tawuni a durkushe tana kuka, shikuwa amadi abisa dukkan alamu ma baya cikin gidan sai yamma yadawo da misalin karfe 3,

Dakin da yabarta aciki yaje ya bude yashiga, har lokacin tana sulale awurin taci kuka tagaji tana jan numfashi dakyar,

"Baby wai har yanzu baki bar..." Ganinta ayashe akasa yasashi kasa karasa maganar da yasoma,

Agaugauce yaje inda take yadagata zuwa jikinsa,

"Baby... Baby..."

Bude idonta tayi tana ganinsa tasake fashewa da kuka gamida kara rungumeshi,

"Dan Allah didi kace ka janye sakin da kayi min, wallahi ina sonka, bana son kowa yanzu sai kai,kaine MIJINA SIRRINA..."

Idanuwanshi ne suka cicciko da kwalla, kinkimarta yayi ya dora akan gado yakwanta ajikinta,

"Baby wai tun lokacin da natafi kike awurin nan baki tashi ba?? Meyasa zaki yimin haka?"

Jin jikinta yafara daukar zafi yasashi tashi arazane ya riketa,

"Baby zazzabi? Zazzabi zakiyi? Ko inyi miki wanka?"

Girgiza masa kai tayi alamun a'a, mintuna kadan jikinta ya gauraye da zafin zazzabi kamar garwashi,

Hankalinsa ba karamin tashi yayiba, Dr Salaha yayi azamar kira, yana gama kiranta yakoma jikinta ya kwanta yana jijjigata kamar jaririya,

Duk yarasa inda zai tsoma ransa yaji dadi ganin halin da take ciki,

Zuwan Dr salaha ne yasashi mikewa daga kan gadon yaje ya shigo da ita,

Duba nadiya tayi tabashi maganin da zai bata idan taci abinci sannan ta jona mata karin ruwa,

Sallama yayi da dr salaha ta tafi shikuma yakoma kusa da ita ya zauna yana shafar gashin kanta, har fuskarta ta dan fada saboda tsabar tashin hankali,

Ta dan jima tana bacci sannan ta farka, idanuwanta ta bude taga amadi akusa da ita yana rike da hannunta, jin tayi dan motsi yasashi tashi zaune yana kallonta,

"Baby kin tashi? Inkawo miki abinci kici kisha magani?"

Kai ta daga masa idonta dauke da kwalla, ruwan dake hannunta ya cire mata saboda yakare, sauka daga kan gadon yayi ya fita zuwa kitchen,

Bai wani bata lokaci ba sai gashi yashigo dauke da filet da cup,

Dankali da kwai da sos ya zubo mata sai dan ruwan tea acikin cup, zaune ya tadata yafara bata dankalin abaki tana ci, kallonsa kawai takeyi idonta cikeda kwalla,

Girgiza mata kai yayi yana rikeda hannunta guda daya,

"Baby meyasa baki nutsu kin karanta takardar da nabaki ba, da kin karanta da duk haka bata faruba saboda nasan zaki fahimci abinda nake nufi kuma zaki gane komai acikin sauki.. Dan Allah kiyi hakuri karki yi kuka, kidaina kwallar nan haka"

Goge mata kwallar yayi yaci gaba da bata dankalin tana ci, saida taci da yawa sannan yabata ruwan tea din tasha yabata magani tasha har lokacin jikinta akwai zafi amma dai taji saukin ciwon kan da yaketa azazzalarta kuma ciwon da jikinta yake yi mata shima ya dan ragu,

"Zanyi wanka kuma banyi salla ba.."

Tafada muryarta adashe, ahankali ya dagota ya riketa ajikinshi yazuge zip din rigar jikinta ya cire mata rigar, shi dama baijin kiwar daukarta akoda yaushe dan haka ya dauketa cak yayi toilet dinshi da ita,

Ruwa mai dan dumi yatara mata yasata aciki yayi mata wanka amma dakyar ya iya controlling kanshi,alwala yayi mata bayan yagama yimata wankan ya daura mata towel dinshi ya fita da ita, agefen gado ya zaunar da ita sai faman binshi da ido take yi, fita yayi zuwa dakinta ya dauko mata kayan da zata saka,

Wata jar doguwar riga mai mutukar kyau ya dauko mata, rigar bata da kauri dayawa sannan kuma irin mai mannewa ajikin mutum dinnan ce sannan anjera wasu duwatsu ajikinta,

Pant da bra ta karba tasa da kanta sannan yazira mata rigar yafesa mata turarenshi na axe, daga zaune tayi salla tana idarwa ya mika mata wannan takardar ta dazu, gabanta ne yasake faduwa ta daga ido tana kallonshi zuciyarta tana yimata wani irin suya wato dai amadi yadage sai ya rabuda ita ko?,

"Kiyi hakuri ki karba ki karanta baby..."

Jikinta yana rawa ta karba ta warware tafara karantawa, yana ganin haka yatashi yafita daga cikin dakin, cikin rawar jiki nadiya tafara karanta takardar kamar haka:

     _Farawa da dunbin gaisuwa agareki yake kyakkyawa kuma mace mai mutukar daraja awurina, hakika nayi farin ciki mai tarin yawa kasancewarki mata agareni, nasan abinda nayi miki ban kyauta ba kuma na sanya zuciyarki acikin wani hali amma ina neman afuwarki abisa laifin da nayi, kisani nayi hakane domin auna adadin irin soyayyar da kike yimin, actually ayau ina cikeda farin ciki mai yawan gaske saboda jin da bakinki kince kina sona yanzu, wannan kalmar da kika furta min bazan barta tatafi abanza ba shiyasa na tanada miki tukwici mai yawan gaske, dafarko ki duba cikin bedroom dinki zakiga tukwici nafarko, tukwici na biyu kuma idan nadawo zaki ganshi, tukwici na uku kuma sai kin kammala karatunki zan baki shi, kiyi hakuri duk abubuwan da nafada miki dangane da kabeer wallahi ba gaskiya bane am joking,kisani babu wata mace da nake iya gani sai ke kadai, i luv u...._

         Yours for Eva
         didi


Tukwikwiye takardar tayi ta mike tana jin wani irin karfi ajikinta, dakinta ta nufa tana zuwa tabude ta shiga, akwatina set biyu tagani guda 24 masu dan banzan kyau pink and purple kowanne anrubuta A & N ajiki da manyan harrufa,

Kobata budesu ba tasan kayan ciki bana wasa bane,

Juyawa tayi tafita ta nufi falo saboda daya tukwici din dama yace sai yadawo,

Key din mota tagani ya ajiye mata akan center table din dake tsakiyar falon tareda yar karamar farar takarda,

  _Baby kije waje kiga motarki..._

Shine abinda yarubuta ajikin yar takardar da ya ajiye mata zama tayi sharaff akan kujera batare data je taga motar ba,

Duk da cewar zuciyarta tayi sanyi amma har yanzu bugawa zuciyarta keyi bata daina ba ga ciwon kai, dafe goshinta tayi tana jiyo motsinshi a corridor,

Tana zaune acikin falo yashigo yasha jeans brown da blue din t shirt anrubuta awesome ajiki,

Zama yayi akusa da ita yana zuba kamshi fuskar nan sai annuri ne ke fita daga jikinta,

"Baby ga wayarki da na canja miki, kedin fa yar gatace..."

"Malam ni ka rike duk kayanka bana so, wancan dinma gara kaje ka kwashe abinka domin bana bukatarsu..."

Murmushi yayi yakai mata kiss ta tureshi batareda tabarshi yayi ba,

"Shiyasa akarshen takardar nabaki hakuri saboda kukan da nasaki,

Baby yanzu ke idan nace zan rabu dake sai kiyarda? Kisawa ranki cewar mutuwa ce kadai zata iya nasarar rabamu, idan har zan iya yaudararki ko naci amanarki ashe so karyane, da mutanen duniya sun daina yarda da kowa, da sun daina bawa kowa amana,

Abinda yasa kikaga na bullo miki ta wannan hanyar shine, ranar farko dana fara baiyanar miki da soyayyata agareki sai kika nuna min cewar bazaki taba sona ba har abada kuma da bakinki ma kin furta min hakan,

Har yanzu abun yana raina kuma yana damuna, zuciyata takasa tabbatar min da cewar kina sona ko kuma sabanin haka shiyasa nayi haka domin na samu tabbaci... Sorry baby"

"Kaga nifa yanzu duk wadannan kalaman naka bazasu yi tasiri ba agareni, sannan ina son kasani nima yanzu nadaina sonka..."

Katseta yayi ta hanyar dora yatsanshi akan lips dinta,

"Ai karma kiyi wannan maganar, nida ke ahalin yanzu duk muna son juna dan haka babu amfanin mu tsaya muna wahalar da zukatanmu,

Kuma ma inbanda abinki baby tayaya zan iya sakinki alhalin na dandani zumar dake tare dake? Kin san kuwa yanda nake kishinki? Wallahi ko kinyi min laifi babba zaiyi wuya in inya rabuwa dake saboda ban son kisake komawa kabeer, ina bakin cikin kasancewarshi mijinki nafarko, naso ace nine nafara aurenki, da nabaki jin dadi marar yankewa wanda zaisa bazaki kara kallon wani namiji ba domin zaki rinka kallonsu a matsayin mata yan uwanki,amma duk da haka ai nasan yanzun ma nayi kokari.."

Kicin kicin tayi da fuska ta hade rai kun san mutuniyar taku akwai iya tsare gida,

"Nidai nafada maka, nima yanzu bazan zauna dakai ba gidan tsohon mijina zan..."

Saurin rufe mata baki yayi da hannunshi yajata jikinshi ya matse,

"Me zaki koma kiyi agidan wannan bakauyen? Wani baki mummuna dashi, ni haushinsa nakeji yagama sanin sirrina.."

"Karka kara zagar min uban yayana.." Tafada bayan tasake daure fuska, jijjiga kai yayi yana murmushi,

"Nidai bazanyi fada dake akan wannan kucakin gayen ba saboda nasan ba iya kyau kadai nafishi dashi ba hatta bawa mace nutsuwa nafishi..."

Shiru tayi masa tafara kokarin kwacewa daga rikon da yayi mata,

"Kin san Allah haushin wannan kabeer din nakeji, Allah yasa sai yamutu sannan zan mutu saboda kar na rigashi mutuwa yasake maye gurbina yahanani kwanciyar kabari"

Bata sake kulashi ba illa fuska data hade ta bata rai, hijabin jikinta ta cire ta koma kan carpet ta kwanta,binta yayi kasan ya jingina da jikinta yayi ruf da ciki asamanta,

"Baby bai kamata alkhairi yazama mugunta ba, ya kamata ki karbi tukwicin da nabaki hannu bibbiyu.."

Jin tayi shiru bata tanka masa ba yasashi birkitota ya shige jikinta, koba komai dai taji dadi da ba gaskiya bane abubuwan da yafada mata da safe,

Shareshi taci gaba dayi sai shan kunu take tana ciccin magani har yagaji yatashi yatafi part din hajiya, sanin tana fushi dashi yasa yaki dawowa saida dare yayi,

Lokacin da yafita akwatunan da ya ajiye mata taje ta dan dudduba wadanda zata iya domin kayan sunyi yawa ita kanta tasan kayan nan sun lashe dukiya mai yawan gaske domin akwatun english wears daban, na shadda daban, na less daban, na atamfa daban, na hijabai daban, na gyale daban, na inner wears, komai dai da akwatinsa, sannan ga wasu kit guda biyu cikeda gwala gwalai,

Tea taje tahada ta dafa indomie da kwai ta ci tayi wanka ta kwanta, ko rigar bacci yau bata tsaya sakawa ba saboda jikinta babu karfi,

Jin alamun tafiya ya tabbatar mata da dan rigimar ne yadawo, dakin yashigo yana sanye da kayan bacci,

"Baby yau da towel za ayi baccin?" Yace da ita bayan ya sunkuya yana leka fuskarta,

Fuska ta daure ta kalleshi,

"Menene haka?"

"Baby kenan, wai maimaikon kiyi murna amma sai faman fushi kike yimin har yanzu kinki hucewa.."

"Akan me zan huce? Ai nafada maka nima yanzu bazama zanyi dakai ba gidan mijina zan koma.."

Jin kalmar yayi ta soki kirjinshi kamar kibiya,

"Kinga baby bana son irin wannan wasan, kibari ya isheki haka, kuma indai nine zan sallameki ki koma gidan wannan banzan to har abada kuwa bazaki koma ba.."

Ture hannunshi tayi daga shafa ta din da yakeyi,

"Nafada maka kadaina zagar min uban'yaya..."

Murmushi yayi ya rabu agefenta ya kwanta,

"Yakamata dai nima inyi zuciya na haifi yayan nan ko za adaina yimin gori.."

"Da wacce take sonka zaka haihu amma bada..."

Baki ya rufe mata,

"Insha Allah dake zan haihu kuma twins zamu haifa kodan inhuta gori.."

"Ai twins dinma ba kowanne rago ne yake iya bayar dasu ba.."

Fuskarshi yakai kan tata yafara shafarta yana dariya domin shi kome zaka fada masa baya fushi sai dai yayi dariya ko murmushi ita kanta tunda take dashi bata taba ganin fushinsa ba,

"Me kike nufi to? Kina son kice ni bazan iya bada twins ba? Wannan jemammen ma yabayar da twins bare ni, ni idan kika yi wasa ma nayi zuciya uku zan baki ko hudu alokaci daya.."

"Sai kayi kuma.."

Tashi yayi ya ciro mata rigar bacci pink colour yar karama marar nauyi mai siririn hannu yazo yasa mata yazare towel din da yake jikinta,

"Nima dai nakusa zama uban yayan..."

"Ko?"

Tace dashi cikin yatsina fuska,

"Ohhh tambaya ma kike? To kodai tabbaci kike nema.."

"Watakil.."

Janta da fada yaci gaba dayi yanata kushe kabeer ita kuma sai kare kabeer din take domin tana son ta cusa masa haushi, ai kuwa saida tayi nasarar cusa masa haushin sannan tayi shiru ta rabu dashi, sakinta yayi ya juya mata baya alamun yayi fushi,

Tana jinshi tayi luff kamar mai bacci, tashi zaune yayi saboda yagaji da kwanciyar,

"Mtswww Allah kasa badagaske take ba, wallahi ko zaku mutu daga ke har kabeer din bazan sakeki ba..."

Dariya ce ta taho mata tayi saurin toshe bakinta,

"Ohh saboda ni bamu haifi yaya ba shiyasa har ake yimin gori..., bari ki samu sauki nima ai ba iya yimiki cikinne zaifi karfina ba"

"Wai meye haka? Kafa dameni da surutu kuma bacci nake ji..."

Komawa yayi ya kwanta, yajuya yana kallonta,

"Baby..."

"Menene?"

"Ban saniba..."

"To shikenan" tafada tareda juyawa, juyo da ita yayi tana fuskantar shi fuskarshi dauke da kishi bayyananne.....





*_Ummi Shatu_*