Saturday 7 January 2017

RUWAN KASHE GOBARA.. 61-63

*RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_



     *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_



    *_61_*

     _Anty Maijidda kina ina? Wannan shafin nakine Anty nah! Tnx for ur Luv & care, i soo much luv u anty Jidda!._


~~~ Murmushi ya danyi ya saka hannunshi ya dago da fuskarta,

"Kalleni..!" Yafadi ahankali, kasa kallonshi tayi ta lumshe idanuwanta,

"Ki kalleni..." Ya sake fada yana kallon kyakkyawar fuskarta,

Dan yatsanshi yasa akan lips dinta yana zagayawa,

"Kinyi kyau sai dai matsalar baki saka jan baki ba why?"

"Babu komai.." Ta bashi amsa,

"Ki rinka saka jan baki zaki fi kyau"

"To" ta bashi amsa har lokacin ta kasa kallon fuskarshi,

Sake matsawa jikinta yayi nan hancinshi yasoma aika masa da fitinannen kamshin dake tashi daga jikinta,

"Wanne turare kike sakawa?" Ya tambayeta yana mai sake shakar kamshin jikinta,

Shiru tayi bata amsa masa ba saboda ta fuskanci ya fara kokarin wuce gona da iri,

Hannunta ya kamo ya makale cikin nashi,

"Ya kika barni inata magana ni daya ne?" Nan dinma shirun ya sake ji tayi, idonshi ya sauke akan lips dinta wadanda suka kasance jajaye duk kuwa da cewar bata saka jan baki ba,amma duk da haka sunyi mutukar jan hankalinshi,

Babu zato taji yayi hugging dinta yafara kissing din bakinta, sunsunkuyar da kanta ta fara yi,gaba daya ta rasa yadda zata yi saboda kissing dinta yake yi ta kowanne sashe dake kan fuskarta zuwa wuyanta,

"Ki rinka saka jan baki da jagira...,ina son irin wannan kwalliyar ciki harda saka wannan abun na saman ido da kumatu,da irin wannan zane zanen da kuke yi a kafa me baki da red...!" Taji yana rada mata acikin kunnenta,

"Kinji..!" Ya sake rada mata, kai ta daga alamun ehh amma ta kasa magana dalilin yagama saukar mata da kasala,

"Kunyata kike ji ne?"

Ya tambayeta bayan ya tarairayota gaba daya ya dorata ajikinshi,

"Uhm...!?" Ya sake tambayarta,

"Na kasa gane wacce irin kunya Allah ya halicceki da ita bayan kuma naji ana cewa idan mace tayi aure ta haihu to kunyarta na raguwa ba kamar lokacin da tana budurwa ba, hakane?"

Girgiza masa kai tayi alamun a'a,

"To yayane?" Ya tambayeta yana kallon idonta wanda sam taki dagasu ta kalleshi,

"Ai kunya bata karewa..." Tace dashi cikin yar karamar muryarta,

"Sai yaushe? Ya tambayeta yana sinsina wuyanta,

"Abban sadiq...." Tafada gamida rike hannunshi,

"Shhhhhh" yace da ita bayan ya dora dan yatsanshi akan lips dinta,

Dolenta tayi shiru ta rike maganar da tayi niyyar yi ta rabu dashi yaci gaba da juyata son ranshi.

   Bude idonta tayi ta kalleshi yana kwance ajikinta ya rungumeta tamkar wanda zai koma cikin cikinta,

"Abban sadiq zanje na hada breakfast.." Ta fadi cikeda jin kunyarshi,

"Yunwa kike jine??" Ya tambayeta,

Girgiza masa kai tayi alamun a'a,

"To ni kinga yunwa nake ji sosai..."

Lumshe idonta tayi domin ta gane abinda yake nufi amma ita kuma bazata bari hakan ta kasance agidan surukai ba,

"Kinji abinda nace?"

"Uhm naji" ta bashi amsa,

"To ya za ayi?" Ya sake tambayarta,

"Babu" ta bashi amsa,

"Haba? Rowa zaki yimin?"

"Abban sadiq rana fa tayi wallahi kalli agogo ka gani...!" Ta fada a shagwabance,

"To idan kina son na iya hakura kidaina yimin wannan shagwabar"

Shiru tayi masa bata sake magana ba, matsawa yayi daga jikinta yaje ya rungume sadiq wanda ke kwance agefe,

Tashi tayi da dan kwalinta a hannunta ta fita tana kokarin tufke gashin kanta wuri daya ta nufi kitchen fuskarta dauke da murmushi,

"Ohh abban sadiq kenan.. Rigima taki karewa?" Ta fada acikin zuciyarta tana murmushi,

"To ni yanzu ma me zan dafa ne?" ta tambayi kanta,

Doya ta fere ta soyata da kwai tayi yar sos mai dauke da kwai da hanta aciki,

Acikin flask ta zuzzuba ta dauka ta kai falo, hijabinta ta saka ta dauki na baffa ta nufi sashensa yana zaune da jaridar weekly trust a hannunshi yana karantawa idonshi sanye da farin medical glass,

Har kasa ta tsugunna ta gaishe da baffa ta tashi zata tafi,

"Ikhlas motar Lamido nagani ne awaje?"

Ta jiyo baffa yana tambayarta, ras gabanta ya fadi,

"Ehhh baffa motarshi ce tun safe ya kawota ya ajiye"

"To idan yazo gidan ki turo min shi"

"To baffa" tafada tareda juyawa tayi gaba gabanta sai faman faduwa yake domin bata son baffa ya gano lamido agidan ya kwana.

Dakinta ta shiga ta tsaya tana kallon lamido wanda ke kwance yana bacci yana rungume da sadiq,

Ba karamin kyau taga yayi mata ba domin har acikin barcin ma sai da beautiful points dinshi suka bayyana,

Agefenshi taje ta zauna tana kallonsa akaro nafarko domin bata taba samun damar karewa siffarshi kalloba,

Tun daga kan dan yatsan shi har zuwa gashin kanshi duk sun tafi da tunaninta, hannunshi kuwa gashine zara zara ajiki,

"Handsome.." Ta fadi ahankali gamida mika hannunta ta shafo gashin hannunshi ahankali ta yadda ba zaiji ba,

Fuskar sadiq ta kalla ta kalli fuskar lamido,

"Allah wasa wasa yaron nan yana kama da abbanshi"

Karar wayar lamido ce ta katse mata zancen zucin da takeyi, mika hannu tayi ta daukota daga kan bed side drewar dinta,

Ras gabanta ya fadi saboda ganin sunan wacce take kiransa,

"Xahar wacece kuma xahar?" Ta tambayi kanta,

A saitin kanshi ta tsaya nan ya bude idonshi daya ya kalleta,

"Menene? Idan ina bacci ba atsayawa akaina"

"Waya ake yi maka" ta fada tareda mika masa wayar,

Screen din wayar ya kalla ganin xahar ce me kiran yasashi yin dan guntun tsaki ya tura wayar karkashin pillow, nan wayar taci gaba da kara domin xahar bata fasa kiranshi ba, ita dai ikhlas tana tsaye tana kallonshi,

Zaune ya tashi ya jawo wayar ya kara ajikin kunnenshi,

"Hello xahar ya akayi ne? Bacci nake fa" yayi magana ahankali,

"Sorry abban sadiq" xahar ta fada daga daya bangaren hakan da ta fadane yasashi murmushi domin sai yaji kamar ikhlas ce tayi maganar saboda itace take kiranshi da wannan sunan,

"Babu damuwa meya faru?" Ya tambayeta yana murmushi,

"Kwana biyune ban ganka ba gashi idanuwana suna bukatar ganin beautiful face dinka" xahar ta bashi amsa cikin shagwaba,

"To zan shigo anjima" yafada yana mai satar kallon ikhlas wacce ke tsaye ta zubawa fuskarshi ido,

"To sai kazo ina nan ina jiranka" ya jiyo xahar tafada cikeda murna,

"Ok bye" yace da ita tareda kashe wayar,

Wani abune ya fara ratsa zuciyar ikhlas wanda bazata iya tantance ko menene ba amma tafi tunanin kishine,

"Kishi kuma? To ni me ya hadani da kishin abban sadiq..?" Ta tambayi kanta acikin zuciyarta,

"Saboda mijinki ne" wata zuciyar ta bata amsa,

"To amma akan me zanyi kishinsa bayan matanshi biyu nice ta uku kuma nasan sauran matan sonsu yake shiyasa ya aure su sabanin ni da ya aureni domin cikawa dan uwanshi burinshi" take taji wani bakin ciki da kunci ya rufeta ya lullube zuciyarta,

Hannunta taji lamido ya kama yana kokarin zaunar da ita akan jikinshi,

"Tunanin me kike yi?" Ya tambayeta yana mai kallon idanuwanta wadanda suke mutukar burgeshi domin kalarsu daban suke dana sauran mata,

Ajiye kwayar idonta tayi akasa tana son tambayarshi wacece wacce ta kirashi awaya kuma me zaije yi awurinta sannan menene matsayinta agareshi? Amma kuma sai taji ta kasa tambayar tashi domin nauyinshi take ji,

Karar wayarshi ne ta sake katse mata tunanin da take yi,

"Hello fadila" taji yafada yana shafar gashin girarta wanda yake kwance lif,

"My fadila ai ina son kiranki rigani kawai kikayi, ya hidimar biki?" Yafadi tamkar me yin rada,

Shiru ikhlas tayi tana jinshi amma aranta ji take kamar ta fashe da kuka amma wata zuciyar hanata take tana cewa "dama tunda kika auri mai mata har biyu ai kin san dole sai kinyi hakuri"

Ji tayi ya kwantar da kanta akan kirjinsa yana shafa fuskarta, shagala tayi ta ma manta da batun wayar da yake yi domin har ya kammala bata sani ba har sai da taji ya sunkuyo da fuskarshi saitin tata yana kallonta,

"Bacci kikayi?" Taji ya tambayeta ahankali,idanuwanta ta bude ta yi saurin kokarin tashi daga jikinsa, hannunta ya rike yana murmushi,

"Ina zaki je?"

"Nagama hada breakfast tun dazu fa"

Mikewa yayi yana rike da hannunta amma ita duk ta gama takura,

Tana baya yana gaba har sukaje falon ta tsugunna tafara zuba mishi abincin,

"Kar ki hada min tea bazan sha ba wannan ya isa" yace da ita yana kallonta,

"To" ta amsa mishi a takaice,

Daukar abincin tayi ta mika mishi ta koma nesa dashi ta zauna, tana kallonshi yafara ci har ya kammala ya mike,

"Bari naje gida nayi wanka"

"To, baffa yace yana nemanka"

"Ok bari naje"

Tana kallonshi ya wuce ya shiga dakinta ya dauko wayoyinshi ya fito ya wuce kallonshi tayi ta yi har ya fice daga falon,

Zama ta koma tayi aranta tana tunanin to Kodai lamido wani auren zai sake yi? Dakyar ta samu ta yakice wannan tunanin daga ranta.

Har yamma tayi shiru lamido bai dawo ba har akayi sallar magrib nan kuma hankalin ikhlas ya tattara ya koma kanshi domin shirun yayi yawa,

Wayarshi ta kira gabanta yanata faduwa,

"Hello" taji ya fada lokacin da ya dauki wayar,

"Abban sadiq mun jika shiru shikuma sadiq yanata nemanka.."

"Gani nan zuwa" yafada gamida tsinke wayar,

Tana zaune a falo tasha ado cikin pink din leshi dinkin fitet tana feeding din sadiq, ba karamin kyau tayi ba amma bata ga shigowarshi ba,

Rankwafawa yayi agabanta yana cewa,

"Saddiqu na abinci ake..." Tun kafin ya karasa ikhlas ta zabura ta janye sadiq ta saki rigarta,

"Me yake damunki ne?" Ya fada yana kallonta,

Shiru tayi tana kallonsa amma ta kasa magana, "ni narasa me kike boyewa bayan nafada miki cewar na dade da ganin abinda kiketa boye min"

Sunkuyar da kanta tayi, "karfa ki manta jiya..."

"Gashi" ta katseshi ta hanyar mika mishi sadiq,

Karbarshi yayi ya juya dashi zai fita fuskarshi dauke da murmushi domin lamarin ikhlas dariya yake sakashi ko bai shirya ba, mikewa ikhlas tayi tabi bayanshi tana rikeda mayafinta a hannu domin yin rakiya amma sai satar kallon lamido take domin yayi mutukar yi mata kyau saboda bakar riga ya saka da blue din wando abinka da farar fata nan yafito fes dashi,lumshe idonta tayi tana jin kamar taje ta rungumeshi "you look soo fine handsome" ta fadi hakan acikin ranta,amma afili sai tace dashi,

"Abban sadiq ina ka shigane baka zo kaci abinci ba alhalin kuma yanzu kai gwauro ne balle nace kaci awurin..."

Katseta yayi ta hanyar cewa,

"Nine gwauron? Me mata uku ai baza a kirashi da gwauro ba domin idan wasu basa nan to wata tana nan danma dai kin hanani angoncewa"

Murmushi tayi tana gyarawa sadiq kwanciyarshi akan cinyarta amma duk yasata taji kunya saboda maganar da ya fada dan haka tayi gaggawar kawar da zancen ta hanyar cewa,

"To meyasa baka zo kaci abincin ba?"

"Na koshine wallahi, tun abincin da kika bani da safe har yanzu jina nake a koshe may be da daddare ma ruwan lipton kawai zan sha"

Murmushi tayi tana kallon kyakkyawar fuskarshi wacce take kyalli tamkar mudubi.

Daukarsu yayi ya fita dasu cikin gari sune har wani hadadden store inda lamido ya fita ya siyo musu kayan makulashe ya hado da ice cream kwallo daya,

"Abban sadiq ya naga ice cream din guda daya? Kai bazaka sha bane?"

"Kece dai ba zaki shaba amma ni zan sha" yabata amsa tareda tashin motar ya fara driving,

"Saboda me kace haka?"

"Saboda bana son sanyi ya harbi sadiq saboda duk abinda kika ci shima ajiki zai samu"

"Tabb" ta fadi gamida budewa ice cream din tafara sha, packing yayi a gefen titi ya dauki sadiq ya mika shi kujerar baya ya kwantar ya dawo mazauninshi ya juya yana kallonta,

"Miko min abuna" ya ce da ita tareda mika mata hannunshi, ganin bata da niyyar bashi ya sashi matsawa jikinta ya matseta, kokawa suka fara yafara kokarin kwatar robar ice cream din amma ikhlas ta boye a bayanta, kujerar da take kai ya kwantar ya koma yaci gaba da kokarin kwacewa ice cream din,

A hannunta ta debo ta shafa masa a fuska tana dariya hakan ya sashi shima debowa ya fara shafe mata fuskarta dashi,

"Abban sadiq kabari wlh akwai sanyi.." Ta fada tana kare fuskarta tana dariya,

"Amma shine ni zaki Shafa min bayan kin san cewa akwai sanyin?"

Matsawa yayi jikinta sosai yasaka harshensa akan fuskarta yafara lashe mata ice cream din da ya shafa mata.



     _Gaisuwa mai tarin yawa agareki Sameerat (Dr meerath) naga sakonki nagode kwarai da gaske._





_*Ummi Shatu*_
[1/6, 8:31 PM] Itz Ummi Shatu🏻: *RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_


    *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_

      _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_

  _*62*_

      _Yabo da jinjina gareku Hawy nah & my AG tawa ni daya, tareda yan matan Lamido Faty B~B & my lovely namesake Ummi A'isha._


~~~Murmushi tayi ta rike hannunshi tafara kokarin dakatar dashi amma bai barta ba har sai da ya gama lashe ice cream din fuskarta gaba daya,

"Ki goge min abinda kika Shafa min a fuska.." Yafada yana rikeda ita,

Kafada ta make alamun tak'i, idanuwanshi ya rufe ya fara yar kara kadan,

"Washh idona... Samomin ruwa na wanke fuskata.."

Ai ikhlas najin haka ta rude bata san lokacin da ta makalkaleshi ba takai bakinta kan fuskarshi ba ta soma lashe masa ice cream din dake fuskarshi,

Lasar fuskarshi take babu kakkautawa har sai da ta gama lashe ice cream din tsaf,

"Abban sadiq ya fita ko akwai saura?" Ta tambayeshi tana girgiza shi,

Bude idonshi yayi yana kallonta ta cikin hasken street light din data haskesu, tsura mata ido yayi sai kuma ta ga ya kwashe da dariya yana kallonta,

Ta ganeshi sarai cewar wayo yayi mata dama can babu wani abunda ya shiga cikin idonshi,

Juyawa tayi ta soma kokarin sauka daga jikinshi tana cikeda kunya,

"Menene abin kunya kuma bayan kin riga da kin gama lasar min fuska.." Yafada tareda rikota,

"Ga ice cream din kasha" ta mika masa guntun na cikin robar wanda ya rage,

"Sha ki bani" ya mayar mata dashi yana yi mata wani irin shu'umin murmushi,

Girgiza kai tayi ta sake mika mishi, murmushi ya dan saki ya kalli kwayar idanuwanta, hakika yau ya yarda babu abinda yafi rayuwa da masoyi dadi domin shi ya tabbatar da hakan saboda wani irin shauki yau yake ji atare dashi sanadiyyar yana tare da abar sonshi prettynshi, karba robar yayi yana mai cigaba da kallon fuskarta ita kuma duk kunya ta gama cikata,

"Nasha na rage miki?"

"A'a ka shanye"

Hannunshi yasa ya shafi fuskarshi wanda duk dankon ice cream ya gama baibayeta,

"Fuskata danko..."

Kafin ya rufe bakinshi tuni ikhlas ta sake fakar idonshi ta debo ta zuba masa a fuska, nan ta shiga shafe masa fuskarshi dashi,

Kokawa suka shiga yi yana rirrike hannunta amma bata daina shafa masa ba,

"Yau dai ice cream dinnan ahaka zamu shanyeshi ko?"

Yace da ita gamida saka hannunshi ya debo ya yaba mata, "Abban Sadig wallahi zanyi mura.."

"Za muyi dai tunda haka kika zaba"

"Allah dagaske nake"

"To zo in lashe miki, kawo fuskarki..."

Sai da ya lashe ice cream din tsaf sannan ya dago da kanta yana cewa,

"Saura ni..., kinji"

Cike da kunyarshi tasa harshenta ta soma lasar fuskarshi har ta gama idonta arufe,

Sakinta yayi ya tashi ya koma kujerar zamanshi yana murmushin farin ciki,

"Mu koma gida ko? Amma pls rakani mu fara zuwa wani wuri"

Batayi magana ba ta mika hannunta sit din baya ta dauko sadiq wanda keta faman bacci,

Ita kanta ikhlas din yau wani nishadi takeji bata taba sanin haka lamido yake ba sai yau da yafara nuna mata irin salon soyayyarshi,

Titin gidanshi ya dauka dasu ya juyo yana kallonta,

"Banji kince komai ba"

"Game da mefa?" Ta bukata batare data kalleshi ba,

"Bakiga inda na dosa bane? Bakya tsoron tanan nakaiki dakinki",

Murmushi tayi ta dan saci kallonshi kadan,

"Ai nasan ba Zaka yimin haka ba"

Murmushi shi dinma yayi "waye ya fada miki? Tab ai ni banki ace na daukoki kenan ba daga nan sai gidana"

Daidai lokacin suka karasa kofar gidan nashi, awaje yayi packing ya bude motar zai fita,

"Ko zaki rakani?"

"A'a"

"Saboda me? Tsoro kikeyi? Shikenan bari naje na fito"

Kallo ta bishi dashi har ya shige cikin gidan, murmushi ta saki sam bata zaci haka lamido yake da iya soyayyaba sai tsakanin jiya zuwa yau da suka zauna awuri guda, ita da kallon murdadden namiji take yi masa marar sanin yanda soyayya take ashe abin ba haka bane, jinginar da kanta tayi ajikin kujerar motar tana murmushi,

Batare da taga tahowarsa ba kawai sai shigowarsa cikin motar taji, tashin motar yayi ya juya ya nufi gidan Baffa dasu.

  Lokacin da suka isa gidan a kafada ta dauki sadiq ta nufi cikin gida shikuma lamido ya wuce masallaci,

Yana fitowa daga salla ya shiga gidan nan ya isketa itama tana sallar ta kwantar da sadiq a gabanta,

Daukar sadiq yayi zuwa kan gado ya dorashi akan ruwan cikinshi ya fara yi masa wasa. Tana idar da sallar ta mike tana ninke abin sallar,

"Zuba min ruwa zanyi wanka, fuskata danko take yi har yanzu" lamido yace da ita yana kallonta,

"Tom" ta bashi amsa ta shige cikin toilet ta hada mishi ruwan ta fito, sadiq ta dauka ta fita dashi falo tabar lamido yana shirin shiga wanka,

Abinda suka shigo dashi na makulashe su ta bude ta fara ci, tana nan zaune lamido ya fito daga shi sai t shirt dark brown da boxer iya cinyarshi,

Akusa da ita ya zauna ya fara cin abinda take ci,

"Sadiq kai ka koshi ko?"

Murmushi tayi "uhm"

"Dama uhm zakice tunda kina barinshi da yunwa"

Murmushi tayi ta mike ta nufi cikin daki, wanka ta shiga tayi wanda tun tana cikin toilet din taji kukan sadiq ya yawaita danma a hannun lamido yake, hanzartawa tayi ta gama ta fito daure da zani daurin kirji da towel karami wanda ta rufe jikinta dashi,

"Ungo shi" lamido ya fada yana dan harararta saboda tabar sadiq yana kuka,

Karbarshi tayi ta zauna tafara shayar dashi bayan ta sakashi acikin towel din ta lullubeshi, tari ya fara yi alamun ya kware ai nan lamido yace bai san zance ba ya matsa kusa da ita ya yaye towel din yana fadin,

"Wallahi ba zaki cutar min da yaro inaji ina gani ba"

Dolenta babu yanda ta iya haka taci gaba da feeding din sadiq lamido yana tsaye yana kallonsu har sai da ya tabbatar da cewar ya koshi sannan ya karbeshi yaje ya haye gado ya kwanta ya rungumeshi,

Gaban mirror taje ta dan gyara fuskarta tasha turare kala kala ta je ta dauko kayan baccinta sai da ta waiwaya ta tabbatar da cewa lamido baya ganinta sannan ta saka kayan wanda suka kasance riga da wando milk colour masu laushi,

Bayanshi taje ta kwanta tana kallon sumar kanshi,

"Abban sadiq idan ka tashi yin kitso na iya" tafada ahankali, sadiq ya kwantar ya juya gareta ya rungumeta,

"Gobe zanje nayi aski ai, yau da naje wurin Baffa yace ya kamata na rage sumar nan"

Murmushi tayi "ai tashen samartaka kake yi shiyasa"

Murmushi yayi ya sake shigewa cikin jikinta "tunda kin iya kitson to yimin naji"

Hannuwanta ta nutsa cikin sumar tashi ta soma shafawa ahankali can taji ya rike hannunta,

"Bari da zafi fa"

"Kai abban sadiq ashe da kai mace ne da anga me kukan kitso" tafada tana murmushi, juyawa yayi da ita ya zame hular kanta,

"Tunda kema kanki a tsefe yake bari inyi miki kitson kiji idan babu zafi"

Idanuwanta ta rufe ta fara sauraron kalar sakon da yake son aika mata dashi.

  Sun dade basu runtsa ba har wurin karfe 2:30 nadare, karfe 6 ikhlas ta tashi tayi salla ta tashi lamido, tashi yayi yana hamma,

Toilet ya shiga sai da yayi wanka sannan ya fito da gajeren wando a jikinsa,

Kayansa ya saka yayi salla ya koma ya kwanta.

Ta bayanshi ta je ta kwanta take wani bacci yayi awon gaba da ita nan ta murgina ta rungume lamido acikin baccin batare da ta saniba, juyowa yayi ya sake rungumeta yana mai kallon kyakkyawar fuskarta, tunda ya kura mata ido bai iya daina kallonta ba har sai da ta farka,

Hamma tayi ta bude idonta nan suka hada ido da lamido yana yi mata wani kayataccen murmushi, kunya ce ta kamata saboda ganin yanda ta rungumeshi kamar tana tsoron kar wani ya kwace mata shi,

"Abban sadiq.., ina sadiq yake?" Ta tambayeshi tana zaro idanuwanta,

"Gashi can a bayana, me zaki yi mishi bayan kin zo kin rungume mijinki kin manta dashi, sai yanzu kika tuna dashi?"

Ya fad'i hakan yana kallon kwayar idonta,

Saukar da idonta k'asa tayi cikeda kunya nan tafara kokarin tashi lamido yayi saurin riketa,

"Ina zakije kuma?"

"Wanka zanyi" ta bashi amsa har lokacin idonta yana kasa,

"Wanne irin wanka?" Ya bukata yana lumshe mata idanuwanshi,

"Normal wanka" ta bashi amsa cikeda kunya domin ta gano inda tambayar tashi ta dosa,

"Ni kuwa kinga...." Hannunta takai kan bakinshi da sauri ta rufe masa baki,

"Please abban sadiq ya isa dan Allah.." Tace dashi bayan ta langabar da kanta cikeda kunya,

"Au kar na fada? Bakya son kiji damuwata? Shikenan tunda hakane" yace da ita cikin kalar tausayi,

"Nifa ba haka bane" ta fada a shagwabance,

"To yaya ne fada min...!" Ya fadi hakan yana matsa yan yatsunta,

"Please kabarni naje nayi wankan" ta sake fadi idonta yana kallon kasa,

"Nifa ba wani abu zance ba dama cewa zanyi ni kuwa tun ranar da na fara kwana a cikin dakin nan sai nayi wanka sannan nake yin salla.." Ya fada ahankali kamar me yin rada, kanta ta kawar daga barin da yake ta soma kokarin tashi ba tare da ta bashi amsa ba,

Sakinta yayi ya juya ya rungume sadiq.

  Zani ta dauka ta shiga toilet tayi wanka sai da ta leko ta tabbatar da cewa lamido bacci yake sannan ta lallaba ta fito ta shirya agurguje cikin jan material mai laushi, kwalliya ta dan yiwa fuskarta ciki harda saka jan janbaki, turaruka masu dadi ta fesa ta fita zuwa kitchen,

Ruwan zafi kawai ta dafa ta soya kwai ta dauka ta kai falo daidai lokacin lamido ya fito da sadiq a hannunshi,

Bata kalleshi ba ta dauki breakfast din baffa ta tafi ta kai masa ta dawo, karbar sadiq tayi domin yi mishi wanka amma duk motsin da zatayi idon lamido na kanta saboda tayi asalin yi mishi kyau.

  _Sakon gaisuwa gareku ummu Nura & maman inteesar, Allah ya raya muku yaranku._


*_Ummi Shatu_*
[1/6, 8:31 PM] Itz Ummi Shatu🏻: *RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_

 
   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*


     _Sadaukarwa ga k'awata KHADIJA SIDI_

   *_63_*


     _Sakon fatan alkhairi gareki Rukayyat Ahmad (mrs Mansur I yelwa) nagode miki dayawa._


~~~Yana zaune yana kallonta ta gama yiwa sadiq wanka ta shiryashi cikin jar riga da bakin wando ta fesa masa turare ta nufi wurin lamido dashi tana cewa,

"Zakaje ka gaida abba? In kaika wurin abbanka ko..?"

Mikawa lamido shi tayi wanda ke kwance akan doguwar kujera amma da alama ba kalau ba domin taga jikinshi yayi la'asar sannan duk girman idanuwanshi yanzu sun dawo kanana gashi sunyi wata kala,

Karbar sadiq yayi gamida riko hannunta, "yaushe zaki tare ne?"

Kallonshi tayi da mamaki "tarewa kuma? Basu innah sunce sai nan da watanni ukuba?"

Murmushi yayi wanda bai shirya yinshi ba, "gaskiya bazan iyaba, bazan jure ba, kifara shiryawa nanda sati biyu zaki tare"

Dagowa tayi ta kalleshi amma yanayin data ganshi aciki ya tabbatar mata cewar da gaske yake abinda yafa babu alamun wasa,

"Abban sadiq kabari mu kara koda wata dayane saboda kaga sadiq har yanzu.."

"Har yanzu me?" Sassauta muryarsa yayi yasake matse hannunta cikin nashi,

"Kina sone in mutu ko me?? Wallahi ina bukatarki akusa dani, i need you...! Yau dinnan zanje na samu baffa na fada masa, sassauci daya zan iya yi miki shine zan baki nan da sati uku kigama shirinki sai ki tare"

Yana gama fadin haka ya saki hannunta ya mike zaune yana rikeda sadiq a jikinshi,

Tsugunnawa tayi ta hada masa tea ta mika masa sannan ta ajiye masa sauran kayan agabanshi, tashi tayi ta shiga daki tana mamakin lamido saboda ita aganinta tunda yanada mata har guda biyu ai bazai wani damu da batun tarewarta ba,

Dakin tabi ta gyara ta fesa room freshener,tana kokarin fita lamido ya shigo,

"Hada min ruwa zanyi wanka" yace da ita ahankali,

"To" ta fada gamida juyawa ta shiga cikin bathroom din ta zuba mishi ruwan wankan ta fito,.

Falo ta fita ta zauna tahada tea tana sha, tana nan zaune ya fito rikeda waya a makale a kunnenshi yana magana,

"Nan da karfe nawa zaku karaso..? Ok sai kunzo"

Katse wayar yayi ya juyo yana kallon ikhlas wacce itama shi take kallo domin adon da yayi ba karamin kyau yayi mishi ba sannan ya fito dashi mutuka,

"Innah ce tace sun taho sun ma kusa karasowa"

"To Allah ya kawosu lafiya" ta fadi ahankali, juyawa yayi zai fita tayi saurin tsayar dashi,

"Abban sadiq dama akwai maganar da nake son muyi dakai.."

Dawowa yayi ya zauna yana saurarenta,

"Ina jinki"

"Uhm dama akwai wata islamiyya a unguwarmu ta da,marigayi ya karbo min foam din makarantar yace zan fara zuwa idan na gama cikewa to kuma sai ya rasu kafin nakai ga kammala cike foam din.."

"Wacce irice makarantar?" Ya tambayeta,

"Islamiyya ce ta matan aure kullum ake zuwa karfe 2 ataso karfe hudu saboda diploma ce ta Arabic"

"To zaki shiga amma ba yanzu ba sai bayan kin tare tukunna" mikewa yayi ya fita daga falon nan tabi bayanshi da kallo.

  Misalin karfe 12 narana innah ta karaso tun daga wannan lokacin kuma ikhlas bata ga lamido ba sai duk taji ta shiga damuwa, karfe 9 tagama shirin bacci ta kwanta amma ga mamakinta sai ta kasa baccin domin kewar mijinta itace ta fara addabarta, juyi tayi ta rungume sadiq tana shakar kamshin turaren da lamido ya bar mata akan pillownta,

Tashi tayi taje ta bude drewar din kayanta ta dauko kayan baccinshi wanda ya kwana dasu adaren jiya,

Rungume kayan tayi tana jin kamar zatayi kuka, lallai rashin masoyi abune mai nauyin gaske domin ita sai yau ta tabbatar da hakan,

Kayan ta saka akan fuskarta tana shakar kamshin da suke fitarwa, ahankali ta mika hannunta kan bedside drewar dinta ta dauko wayarta, sakon text massage take son tura masa amma kuma ta rasa wacce kalma zata yi amfani da ita wurin bayyanar masa da irin yanda tayi rashinsa a wannan daren,

Daurewa tayi ta rubuta _I miss you abban sadiq_ ta tura masa, yana kofar falon gidan yana kokarin shigowa yaga sakon nata, murmushi yayi yasaka kai ya shiga,

Ahankali ya kama kofar dakin nata ya bude ya shiga ya lalubi makunnar wutar dakin ya kunna,

Duk wannan hidimar bata san yanayi ba domin idonta arufe yake ta lullube fuskarta da kayan baccinshi,

"Allah sarki my pretty ashe kema zakiyi missing dina adaren yau kamar yadda nima na tabbatar da zanyi missing dinki" yafadi hakan acikin ranshi,

Ahankali ya karasa kan gadon ta bayanta ya zauna ya dafata ya mika fuskarshi saitin tata, hannunshi yasa ya fara zare kayan baccin nashi wanda ta rufe fuskarta dasu,

Tsorata tayi ta zabura zata mike, cikin sauri ya dakatar da ita,

"Ina zakije? Nine fa" taji muryarshi yana yi mata magana, take ta dawo cikin hayyacinta sai kuma kunya tafara shigarta domin yazo ya kamata tana lullube da kayanshi,

"Meyasa kike da zurfin ciki? Meyasa kike son cutar da kanki? Ni nasan kinada bukatata kamar yadda nake bukatarki dan haka ki yarda ki tare lokaci kusa.."

Shiru tayi ta kasa koda motsi, juyawa yayi da ita zuwa kan jikinshi, "bakice komai ba"

Nan dinma shirun tayi masa, "uhmmm" ya sake fada ahankali, sanin ba zata iya yi masa magana ba saboda tana jin kunya yasashi rabuwa da ita ya dagota zuwa jikinshi ya rungumeta, wani irin sanyi yaji yana ratsa zuciyarshi, bakinta taji ya fara laluba da nashi,

Sun dade cikin wani irin yanayi kafin lamido ya kwantar da ita ya rada mata a kunneta "natafi sai da safe"

Bata iya bashi amsaba har ya tashi ya fita daga cikin dakin bayan ya kashe mata hasken dakin, juyawa tayi ta sake rungume kayan baccinshi tana murmushi da tunaninshi ta samu tayi bacci marar dadi domin sam bata ji dadinshi ba.

  Washe gari lokacin da lamido yazo gidan wurin baffa yaje yace masa yana son ikhlas ta tare nanda sati uku, nan innah ta tada fada tace ba yanzu ba domin har yanzu sadiq bai gama yin kwariba dan haka ya bari sai nan da watanni uku kamar yadda akayi yarjejeniya dashi.Tashi yayi ya fita ranshi a bace ko cikin gidan bai shiga ba,

Tun daga ranar ya fara zarya agidan domin kusan kullum sai yaje gidan fiyeda sau hudu wani lokacin kuma har karfe 11 nadare yake kaiwa ganin abin yana neman yayi yawa yasa baffa kiran ikhlas yace tafara duk wani shiri wanda zatayi domin nanda sati uku zata tare agidanta,

Ba karamin murna lamido yayiba nan rawar kai ya karu kamar zaiyi me dan murna wanda har sai da su ihsan da fadila suka ji takaici, bash kuwa tsokanarshi ya shiga yi yana cewa shida yake da mata biyu kyawawa agida duk yanmata meye nashi na zumudi akan bazawara, duka lamido ya kaiwa bash yace,

"Bash baka san wacece ikhlas ba shiyasa, abin sirrine ba zaka ganeba"

Dariya bash yayi "wannan haka yake on top".

Gidan baffa sukaje bash yayi dropping dinshi ya wuce, cikin gidan ya shiga ya iske ikhlas a falo tana goye da sadiq yana bacci anan ta sanar masa cewar tana son zuwa Maiduguri kafin ta tare, da kyar ya yarda ya barta, dan haka ranar talata da safe ta shirya ta tafi amma ba ita ta isa gidaba sai daf da sallar magrib,

Tun da taje aka fara yi mata gyaran jiki irin na amare da sauran gyare gyare wadanda baza arasa ba, lokacin da taga abdalla sai da tayi mamaki domin ba karamin girma yayiba gashi kuma yana yi mata kama da wani Wanda ta kasa gane ko waye,

"Abdallah ka dada zama saurayi" tafadi tana dariya,

"Anty zaki tafi ki bar mana sadiq ko?" Abdallah yafadi yana murmushin da har sai da kumatunsa suka lotsa,ras ikhlas taji gabanta ya harba amma kuma ta gagara tuno wanda abdallah yake yi mata kama dashi,

"A'a abdallah bazan bar muku sadiq ba sai dai kai kazo mu tafi dakai"

Makale kafada yayi yace "ni bazanje ba awurin uncle Hussain zan zauna"

"Kaji ja'iri to dakai zasu tafi" ammi ta fadi tana dariya, sallamar yaya Hussain ce ta katse musu hirarsu,

Zama sukayi suka gaisa anan yake sanarwa da ikhlas cewa yabawa farida matarsa kudi wanda suka hada shida hassan gobe suje kasuwa itada farida su siyo duk abubuwan da take bukata domin tsofaffin kayanta kwasosu za ayi akawowa ammi itama tasaka adakinta, godiya sosai ikhlas tayi washe gari sukaje kasuwa itada farida nan suka fara jidar kaya masu tsada da kyau wanda ita dai ikhlas tsayawa kawai tayi tana kallon farida domin duk abinda ta nuna tana so daukoshi farida take ta biya kudin, bata san adadin yawan kudin da su Hussain suka bayar ba,

Sai yamma lis suka koma gida lokacin sun kammala siyayyar sun siyo dukkan abinda ya kamata, cigaba da gyaran jikin ikhlas akayi har ya rage saura kwana uku ta tafi yola wanda aranar da ta koma awashegarin ranar zata tare,

"Ina son kwalliya ciki harda irin wannan zanen da kuke yi a hannu da kafa.." Maganar lamido ce ta dawo cikin kunnuwanta hakan ta sata zuwa aka yaryada mata jan kunshi mai hadida baki wanda ya kama atafin hannunta da tafin kafarta radau,

Turaren wuta dana jiki da humra masu kamshin gaske aka harhada mata bayaga su kwalacca da sauran kayan kamshi,batun lamido kuwa tun ranar data bar yola yake faman kiranta awaya, kowanne lokaci cikin yi mata waya yake har ranar da zata dawo.

Tun asuba suka fita itada hajiya da matan yayunta ga kuma motar kayanta wanda yayunta suka sake mata, suna zuwa gidanta suka wuce dasu da motar kayanta bayan sun sauketa a gidan baffa, bata dade da sauka ba ta fita ta tafi saloon lokacin data dawo ta samu ni'iman elmustapha tazo gidan tana jiranta, yan kafi kuwa sai dare suka dawo bayan sun shirya mata dakinta da falonta tsaf, kitchen ne dai guda dayane ahade wanda nasune su duka ukun amma kowacce ta shirya kayanta agefe daya,sannan tunda sukaje gidan gaisuwa ce kadai ta hadasu dasu fadila da ihsan daga wannan kowacce shigewa dakinta tayi taki fitowa har suka gama jeren,

Adaren sukaje tsohon gidanta suka tattaro mata duk wani abu wanda zata bukata sauran kuma aka loda a mota domin tafiya dashi maiduguri,lokacin da suka je gidan saida ikhlas tayi kuka saboda tunowa da marigayi da tayi,

Sai wurin karfe 12 sannan suka samu damar yin shirin bacci,

"Kai mutuniyata kinga dakinki kuwa?? Komai ya hadu wallahi sannan ke din kanki ma kinyi kyau sosai, wallahi ina jin idan lamido ya ganki zaucewa zaiyi" farida tace da ikhlas tana dariya,

"Ai ni idanma akwai abinda yafi zaucewa zanso lamido yayi indai akaina ne" ikhlas ta fada acikin zuciyarta, amma afili cewa tayi,

"Dagaske? Bani labarin gidan dan Allah"

Kwanciya farida tayi tana cewa "kibari gobe idan kinje zaki gani ni yanzu ki kyaleni bacci zanyi domin nagaji"

Kwanciyar itama ikhlas tayi fuskarta dauke fa murmushi tana tunanin gobe iyanzu tasan tana tare da lamido a kusa da ita.

  _Gaisuwa mai tarin yawa agareki Fiddausi Zurmi,kwana biyu kin b'ace idan sakona ya riskeki ina gaisuwa._




*_Ummi A'isha_*

No comments:

Post a Comment