Monday 17 July 2017

MIJINA SIRRINA 1-20

[7/4, 5:13 AM] Humaira Khaleel: _©HASKE WRITERS ASSOCIATION (HWA)_

    *​MIJINA SIRRINA​.....!*🌹
        _(Labarin K'auna)_

  **Based on a true life story**


    _*NA​​*_

*_​​UMMI A'ISHA​​_*


   _​Dedicated to Alh .I. Uba family​_

   *_DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN K'AI,Rabbishrahli sadri, wa yassirli amri, yafqahu qauli.._*

_Shafin farko nakine pherty b~b.._


  *​1​*

~~~ "Oyoyo yaya kabeer...,oyoyo yaya kabeer.."

Wannan shine ihun da yaran dake zaune cikin tsakar gida suna wasa suketa faman yi daidai lokacin da suka ga shigowar matashin saurayin wanda ke sanye cikin farar shadda kansa babu hula sai yar kyakkyawar suma da ya dan ajiye,

Fuskarshi dauke da murmushi ya rungume yaran wadanda akalla zasu kai su kimanin guda hudu,

Daga inda take acikin kitchen ta sake lab'ewa saboda bata son ya ganta duk da sanin cewar dominta yazo gidan, sadadawa tayi ta buya a bayan fridge gamida leka kanta ta window ta yadda tasan bazai iya hangota ba,

Ganinshi tayi rike da hannun Amira da waleeda kannenta sannan ga amir da husna atsaye sai faman jajja masa riga suke suna tsalle,manyan chocolate samfarin coconut chocolate ya debo daga cikin aljihunsa ya mimmikawa yaran,

Sunkuyawa yayi wurin Amira saboda itace babba tafi su husna wayo,

"Amira ina mama?"

"Tana falon abba?"

"Yaya NADIYA fa?"

"Tana kitchen mama tasata aiki.."

Murmushi yayi ya mike saboda yasan aduk inda take taji shigowarsa shiyasa ta gudu ta buya,

Yana rikeda hannun su Amira ya bi hanyar da zata sadashi da falon Abba,

Sai da ya tsaya yayi sallama mama ta amsa ta bashi izini sannan yasaka kai ya shiga cikin falon,

Mama yasamu zaune kusa da abba suna yin hira gefe daya kuma kwanukan abincine da abban yaci kasancewar bai jima da dawowa daga wurin aiki ba,

Su walida da amira na biye dashi har cikin falon sai da suka rakashi ciki sannan suka ruga da gudu suka fita,wuri yasamu ya zauna kanshi a kasa saboda kunya da kuma girmamawa,

Ganinsa yasa abba sakin fara,a tareda mikewa daga kishingiden da yake ya gyara zamansa yana murmushi,

"Kabeeru yanzu kake tafe? Barka da zuwa.."

Cikin jin kunya da sose sosen keya kabeer ya daga ido ya kalli Abba,

"Ehh wallahi abba, shigowata kenan dama nazo ne in gaisheku saboda kwana biyu ban samu damar shigowa ba.."

Murmushi Abba yasake yi ya kalli kabeer din,

"Haba kabeer har yaushene rabonka da gidan, nazaci ai jiyane kawai baka zoba amma ai shekaran jiya ma kazo kodai ka manta ne?"

Maganar da abba ya fadice tasa mama tsoma bakinta tana dan murmushi amma fuskarta babu yabo babu fallasa,

"To ai Alhaji tunda yasaba zuwa kullum jiya kuma baizo ba ai dole yaji kamar yafi sati daya rabonsa damu"

Dariya abba yayi yakoma ya kishingida yana kallon kabeer wanda ya gyara zama yafara gaisar da mama,

Shiru falon ya danyi nawani lokaci saboda shi kabeer nauyin mama da abba yakeji yanzu sam baya iya sakewa yayi hira dasu yanzu kamar da,

Ganin yanata zaune shiru sai dai dan lokaci zuwa lokaci abba yana sakoshi cikin zancen da suke yi da mama yasashi mikewa,

"Abba bari naje waje.."

"To kabeer tafiya zakayi?" Abba yafada yana gyara zamanshi,

"A'a ba tafiya zanyi ba waje zanje"

Fita yayi daga cikin falon cikeda kunya, yana fita abba ya dubi mama yana fara,a,

"Nasan dama ba tafiya zaiyi ba wurin mutuniyar tasa zaije.."

Shiru mama tayi batace komai ba saboda ita kwata kwata bata son wannan maganar saboda wani dalili wanda ta barwa zuciyarta ita daya amma idan hali yayi zata bayyanar dashi ga abban shima yaji, ganin taki zancen yasa abba barin maganar ta hanyar shigo da wani zancen daban domin ya fahimci duk lokacin da zaiyi magana makamanciyar wannan wadda ta shafi kabeer da nadiya mama bata bada goyon baya.

Yana fitowa daga falon abba cikin kitchen yawuce, a bakin kofar kitchen din ya tsaya saboda ganinta da yayi tsaye tana mopping bayan ta kammala share cikin kitchen din,

Yarinyace yar budurwa wacce bazata wuce shekaru goma sha biyar aduniya ba, tanada hasken fata amma ba farace can ba, tana sanye da atamfa kalar koriya dinkin riga da zani, daga inda yake yana iya hango gashinta dake nannade cikin dan kwalin dake daure akanta,

"Sannu da aiki.." Yafadi yana murmushi har lokacin yana tsaye akofar kitchen din,

"Sannu da zuwa yaya kabeer" tafada ahankali sannan maganar ma tayi tane cike da kunya,

"Yawwa sannu sarki aiki.."

Tunowa da tayi cewar bata gaidashi ba yasata saurin dan rissinawa,

"Yaya kabeer ina wuni?"

"Bazan amsa ba har sai kin jiyo kin kalleni ido da ido.."

  Murmushi yasaki bayan ya furta mata hakan saboda yasan ba karamin aiki ya hadata dashi ba domin kunyarshi da takeji bazai taba barinta ta iya hada ido dashi ba...


_*Ummi Shatu*_
[7/4, 5:13 AM] Humaira Khaleel: _©HWA_


       *MIJINA SIRRINA.....!*🌹
         _(Labarin k'auna)_

**Based on a true life story**

   _*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_

   _Dedicated to Alh .I. Uba family_

  _Fatan alkhairi ga k'awata maryam qaumi, kina raina akoda yaushe yan matan shaddad.._

  _*2*_

aishaummi.blogspot.com

~~~Jin abinda ya fada ya sata sake sinne kanta kasa tana kallon tiles din dake malale a kitchen din,

"Bazaki gaida ni ba kenan in tafi ko?" Kabeer ya fada har lokacin fuskarshi tana dauke da murmushi,

"To ba na gaisheka ba kaki amsawa" nadiya tabashi amsa tana mai sake juya masa baya dan kar yaga fuskarta,

"Nadiya kenan wai wannan kunyar yaushe zaki dainata ne? Kullum idan nazo sai ki gudu ki buya alhalin nikuma saboda ke nake son zuwa gidan nan, duk ranar da ban gankiba idanuwana radadi da zugi suke yimin, kuma nazo sai ki hanawa idanuwa tozali da kyakkyawar fuskarki? Uhm nadiya? Dan jiyo mana.."

Badan taso ba ta dan jiyo dakyar tana kallon kasa,

"Kinga kyankyaso nan a bayanki.."

Tun kafin ya karasa maganar ta dako tsalle tabar wurin sai gata a bakin kofar kitchen din kusa dashi, dariya ya fara yimata domin dama yasan tana mutukar jin tsoron kyankyaso shiyasa lokuta da dama yake tsoratata dashi,

Ganin yanata dariya yasata gane cewar ba dagaske yake ba,

Fuska ta bata, "yaya kabeer ashe dama tsokanata kake?"

Dariya ya sakeyi ya daga mata gira,

"Wasane matar yaya kabeer.."

Hannuwa tasa ta rufe fuskarta cikeda kunya domin kowa adangi da haka yake kiranta tun tana yar jaririya har ta girma, kowa matar kabeer yake cemata,

"Yau ina ka bar hular taka ka taho haka?"

Sai da ya dan matsa kusa da ita sannan ahankali yace,

"Wai duk zumudin zuwa ganinki ne yasani manto wayata da hulata adaki har sai da nazo nnpc sannan na ankara.."

Dariya itama tafara yi masa, yayinda shikuma ya tsaya yana kallon yanda kumatunta ke lobawa, hakan ba karamin burgeshi yakeyi ba,

"Kici gaba da dariyar bana son ki daina"

Tsagaitawa tayi daga dariyar da takeyi,

"Yaya kabeer na kawo kayi min assignment din biology? Skeleton teacher dinmu yace mu zana nikuma ban iya drawing ba"

Makale kafada yayi,"nima ban iya drawing ba.."

"Please yaya KB"

Jin abinda tace yasashi kallonta tareda sakin wani tattausan murmushi,

"Dauko nayi miki"

"Yawwa yaya kabeer thanks.."

Rabawa tayi ta gefenshi ta wuce fuskarta dauke da murmushi, juyawa yayi ya bita da kallo, yanzu SS 2 take a secondary school alla alla yake ta kammala domin so yake ya zama mijinta sirrinta,

Yana nan a tsaye har ta fito hannunta rikeda pencil, cleaner da note book dinta sai kuma modern biology, tsayawa tayi ta bayanshi tana kallonshi domin a zahirin gaskiya yayi mutukar tsaruwa sam bashida makusa ko kadan.

Babu zato ya jiyo nan tayi gaggawar dauke idonta daga gareshi,

"Yaya KB gashi.." Tafada cikeda jin kunyarsa domin tasan yagane kallonsa ta tsaya yi,

Hannu ya mika ya karbi books din hannunta sannan ya sakar mata wani murmushi, ahankali ya furta,

"Ki ware idanuwanki ki kalleni son ranki kidaina kunya saboda nidin nakine...."

Fuskarta ta rufe da hannayenta ta juya ta nufi cikin kitchen tana cewa "kai yaya kabeer.."

Murmushi yayi kawai ya nemi wuri ya zauna kan wani dan dakali dake zagaye da wasu flowers wanda yake opposite da kitchen din,

Zana mata skeleton din yafara yi yayinda ita kuma ta kafeshi da ido tana daga cikin kitchen din bayan ta kammala mopping din da take yi,

Kallonshi ta tsaya take tayi ko kiftawa batayi,dago kanshi yayi da niyyar yi mata magana nan ya kamata tana aikin kallonshi,

Saurin kawar da kanta tayi ta juya zata koma cikin kitchen nan yayi gaggawar dakatar da ita,

"Nadiya zo nan.."

Tana rufe da fuskarta ta karasa gabanshi ta tsugunna,

"Meye kike satar kallona?? Ba nace miki idan kina son kallona kawai ki kalleni kanki tsaye batare da kunya ba..?"

"Nifa ba kai nake kalloba yaya kabeer" tafada muryarta na rawa dan jin kunyarsa,

"To naji, idan nazana miki skeleton din ai basai nayi miki labelling ba ko?"

Kai ta daga masa batare da tayi magana ba,

Murmushi yayi yaci gaba da zanen, "to bani labari inji.."

"Yaya kabeer nikuma wanne labari na iya bare in baka?"

"Ko na makarantarku ma idan kika bani ina so.."

"Ai makarantarmu babu wani labari acikinta"

"Kedai kawai bakya son ki fada min labarin makarantarku..."

Kafin ta bashi amsa mama ta zo daf dasu zata shiga kitchen domin dora tuwon dare, batare da mama tayi magana ba tasaka kai ta shige cikin kitchen,

Ganin mama yasa hirar tasu takare sai aikin murmushi da suke aikawa junansu,

Littattafanta ya mika mata ya tashi tsaye yana yimata wani murmushi wanda ita kadai ce ta fahimci sakon da yake son isar mata,

Kitchen yabi mama yayi mata sallama ya wuce batare da yayiwa nadiya magana ba amma kuma yana ta kokarin aika mata da sakon bankwana ta cikin idanuwansa sai dai ita ta kasa kallonshi, tana tsaye tana satar kallonsa har ya fice daga gidan,wucewa tayi ta nufi dakinsu itada su amira,

Akan gadonsu ta zube tana mai tuno yaya kabeer acikin zuciyarta duk da cewar har yanzu bai bude baki ya furta mata kalmar so ba amma tasan soyayya suke yi a boye ita dashi batare da sun bayyanawa junansu sirrin dake cikin zuciyoyinsu ba.


*_Ummi Shatu_*
[7/5, 3:35 PM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_

  *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*HASKE WRITERS ASSO.*



**True life story**

   *3*

aishaummi.blogspot.com

~~~Note book dinta ta bude tafara kallon zanen skeleton din da yaya kabeer yayi mata, gefe daya kuma kamshin turarenshi ne yake tashi daga cikin littafin,

Bin zanen kawai take yi da kallo tana murmushi wanda ita kanta bata san ko na menene ba amma kuma zuciyarta tafi aminta da cewar kawai na tsantsar farin cikine,

"I love you yaya kabeer.."

Tafadi ahankali tareda lumshe idonta,waleeda ce ta shigo cikin dakin da gudu,

"Yaya nadiya kizo inji abba.."

Ajiye littafin tayi ta dauki hijabinta ta fita saboda al'adar abbansu ce haka duk lokacin da ya dawo daga office ko kasuwa to tattara yaranshi yake yi a falonsa suyi hira masu wasa suyi wasansu yana zaune yana kallonsu masu karatu kuma suyi har lokacin sallar magrib yayi a lokacin ne kowa zai dauro alwala yajasu jam'i, haka sallar isha ma, wannan dalilin ne yasa su nadiya basa fita ko ina idan ba makarantar islamiyya ko boko ba sannan hakan ya haifar da shakuwa mai karfi a tsakaninsu dashi,

Ahankali ta tura kofar falon abbansu ta shiga, kishingide ta sameshi yana kallon labaran yamma a tashar AIT, can gefe daya kuma Amira ce da amir suke rubuce rubuce ajikin littafinsu na makaranta da alama home work suke yi, sai husna da walida daketa aikin mammatsa game wanda duk karar game din ta cika cikin falon,

"Sannu da hutawa abba.." Nadiya tafada tana kokarin zama kusa da abban nasu,

"Yawwa nadiya, kabirun har ya tafi ne?"

"Ehh abba ya tafi yanzu bai jima da tafiya ba.."

Shiru abban yayi ya maida hankalinsa ga kallon labaran da yake yi, ita kuma nadiya wurinsu Amira taje tasa ido tana ganin yanda suke yin home work din har mama ta shigo ta iskesu.

  K'arfe 9 nadare bayan su nadiya sun kammala cin abincin dare mama tace suje su kwanta domin har waleeda da husna sunyi bacci su amir ne kawai idonsu biyu,

D'aukar husna nadiya tayi zuwa dakinsu ta kwantar da ita akan katifarsu sannan ta sake zuwa ta dauki waleeda taje ta kwantar da ita su Amira suna biye da ita, gyarawa amir wurin kwanciyarsa tayi ya kwanta sannan itada Amira suka haye gadon dake cikin dakin suka kwanta,

Wayar mama dake ajiye a karkashin pillow dinta ta zaro ta yiwa yaya kabeer plashing, kusan kullum haka suke raba dare suna hira a wayar mama amma ita maman sam bata taba sani ba ita dai kawai tasan nadiya bata taba barin wayarta ta huta mutukar tana gida sai dai idan makaranta ta tafi to lokacin ne wayarta zata samu lafiya.

Ko minti biyu da yi masa plashing din bata yiba ya kirata,da murmushi akan fuskarta ta daga wayar,

"Yaya kabeer kaje gida lafiya?"

"Lafiya lau nadiya, yasu mama?"

"Suna nan lafiya"

"Ya kunya?"

Dariya tasa saboda jin abinda ya fada,

"Yaya kabeer kenan kaima ai ya kamata ka rinka jin kunyata.."

"Saboda me?.. "

"Saboda na cancanci hakan.."

Murmushi ya saki kafin ya bata amsa,

"See you, idan a wayane kibi ki isheni da surutu amma idan nazo sai kiyi shiru ki kasa magana kamar wanda zan kamaki"

Itama dariyar tayi, "to ba kaine ba"

"Nine me?"

"Kaine idan naganka sai naji nakasa yin maganar.."

Dariya ya sake yi, "nadiya kenan.."

"Meya faru yaya kabeeru?"

Murmushi yayi saboda jin ta kirashi da kabeeru,

"Kin ganki ko? Bakinki ya iya fadin kabeeru sake fada naji"

"Yaya KB.."

Dariya suka yi dukkaninsu musamman ma shi kabeer din wanda yake cike da nishadi cikin wannan dare,

"Yaushe zaka zo? Zaka zo gobe?"

"Yaushe kike son kara ganina? Duk lokacin da kike son sake ganina zanzo.."

"Koda kuwa yanzu ne?" Ta tambayeshi tana murmushi,

"Yes even now i shall come if you wish..."

"To ina jiranka idan har dagaske kake zaka zo din"

"Dagaske kike kina son ganina yanzun..?"

"Kaji yaya kabeer da dawasa nake? Dagaske nake mana"

K'arar bude kofa ta jiyo hakan yasata saurin dakatar dashi,

"Ina zaka zo da tsohon daren nan?"

"Sabon dare dai ba tsohon dareba,wurinki zanzo ki ganni"

"To yi zamanka na hakura da wasa nake yi.."

"Inama kiyi dagaske kigani idan zanzo ko bazan zoba"

"Yaya kabeer kenan ai nasan zaka zo"

Murmushi yayi, "to yaushe zan kawo miki budurwata ne ku gaisa?"

Jin abinda yafada yasata mikewa da sauri bayan zuciyarta ta harba, nan taji wani shiru ya ziyarci cikin kunnenta duhu ya mamaye ganinta yayinda bacin rai ya lullube zuciyarta gaba daya.

*_Ummi Shatu_[7/8, 6:42 AM] Humaira Khaleel: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


  *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*


  *_4_*

aishaummi.blogspot.com

~~~Hannu tasa ta danne zuciyarta gudun kada ta faso ta fito waje,

"Nadiya... Yanaji kinyi shiru ko bazaki gaisa da budurwar tawaba?"

Ajiyar zuciya ta ajiye ahankali, dakyar ta iya sassaita tunaninta tayi magana ahankali,

"Yaya kabeer me zai hana ingaisa da ita idan har ka kawo min ita?"

Dan murmushi yayi mai kayatarwa kamar yana gabanta tana kallonshi,

"Ina fata dai har zuciyarki kika fada ma'ana da zuciya daya.."

"Yaya kabeer kenan.."

"Nadiya kenan, nadiya yanmata"

Murmushin dole tayi kafin tayi magana,

"Yaya kabeer nafara jin bacci gashi kaga gobe zanje school"

"Nadiya nifa da wasa nake yimiki banida wata budurwa so karki dauka dagaske ne.."

Duk da cewar taji dadin maganarshi amma sai ta basar,

"Kaji yaya kabeer da wani zance, to idanma dagaske ne ni ba abin in tayaka murna bane??

Sanyayyen murmushi ya saki,

"Hakane to balle ma ba dagaske bane da wasane"

Itama murmushin jin dadi da farin ciki tayi,

"Shikenan tunda kaji tsoro ka sauya magana.."

Yar dariya yayi wadda har tana iya jiyo sautinta,

"Nayarda naji tsoron..."

Juyi nadiya tayi taja bargo ta dan rufe rabin jikinta,

"Yaya kabeer zan barka haka yanzu saboda kasan gobe zan je makaranta"

"To ya nadiya babu komai, Allah ya kaimu goben sai kin jini" yafada cikeda tsokana,

"Ok tom bye bye" tabashi amsa bayan ta lumshe idanuwanta, katse wayar tayi lokacin da taji yace "bye bye good night and have a nice sweet dream"

Addu'ar kwanciya bacci tayi ta shafe jikinta, da tunanin kabeer bacci yayi awon gaba da ita.

  Washe gari da misalin karfe biyu nadiya ta dawo daga makaranta dama ba makarantarsu daya dasu amir ba su akusa da gida suke ita kuma nadiya makarantarsu da dan tazara da unguwarsu, a gaggauce ta shiga gida tana shiga tasan cewar yaya kabeer yana gidan saboda taji kamshin turarensa sannan ta hango takalmanshi a kofar falon mama dan haka bata bari kowa yaji dawowarta ba ta wuce dakinsu ta ajiye school bag dinta ta fito ta shiga kitchen,

Abinci ta zuba ta zauna tana ci kamar ance kalli window tana kallon wurin tayi ido biyu dashi tsaye yana kallonta yana yi mata murmushi,

Sunkuyar da kanta tayi tadaina cin abincin, murmushi kabeer yayi ya saki karfen dake jikin window din,

"Kici abincinki dama kawai nazo ganinki ne, bari natafi inyaso sai nadawo da yamma lokacin kin gama laumar.."

Bai jira abinda zatace ba ya juya yawuce, murmushi tayi ta tashi ta leka sai da ta tabbatar da cewar yatafi baya gidan sannan ta koma ta dauki abincinta ta nufi dakin mama tana tafe tana cin abincin,

A falo tasamu mama tana shirya husna da alama wanka tayi mata,

"A'a kekuma yaushe kika shigo? Jibeki kina tafiya kina cin abinci, keda zaki yiwa wani fada amma kece meyi"

Zama nadiya tayi saboda mama kamar yayarta take sam batayi kamada mahaifiyarta ba kai idanma ba sani kayiba zaka zaci ya da kanwa ne domin kamar yadda abba yake jansu ajiki haka itama maman ke jansu ajikinta musamman ma nadiya domin kowanne abune yake damunta to ita take fadawa sannan idan shawarane ma da ita take yi,

"Hajiya mama kenan wallahi wata yunwa na debo kuma ina zuwa sai na iske yaya kabeer agidan shine nagudu kitchen na buya acan nazuba abincin nafara ci, yanzu kuma da ya tafi shine nadawo nan dan kisan nadawo.."

Tsayawa da shafa man da take yiwa husna mama tayi tana kallon nadiya,

"Nadiya wai menene tsakaninki da kabeer ne?"

Nadiya jin maganar tayi tazo mata a bazata dan haka tayi shiru tagagara bawa mama amsa wanda har sai da mama ta maimaita mata tambayar sannan tayi gaggawar zakulo amsa ta bawa Maman,

"Mama babu komai kawai zumunci muke yi tunda ni yar uwarsa ce shi dan uwanane"

"Nasani nadiya, amma bayaga wannan bana son wani abu ya hadaku muddin ba zumunci bane"

"Amma mama saboda..."

Katseta mama tayi bata barta ta karasa abinda take son tambaya ba,

"Ya isa haka bana son tambaya, ki maida hankalinki kawai kici abincin da yake gabanki"

Shiru nadiya tayi taja abincin taci gaba da ci tana ta sakar zuci saboda bata san dalilin mama na rashin son wani abu ya hadata da yaya kabeer ba amma
Koma dai menene sannu ahankali zata tambayi Maman....


*_Ummi Shatu_*
[7/8, 6:42 AM] Humaira Khaleel: ® *HASKE WRITERS ASSO*

     *MIJINA SIRRINA...!*🌹
          _(Labarin K'auna)_

  *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*


   *5*

aishaummi.blogspot.com

~~~Bata kara bi takan maganar ba suka cigaba da hirarsu ita da maman har ta kammala cin abincin da takeyi ta tashi tabar falon ta koma dakinta tana rikeda wayar mama, lafewa tayi akan gadonta suna yin waya da yaya kabeer, sun dauki lokaci mai tsawo kafin suyi sallama nadiya ta tashi ta shiga wanka ta fito ta shirya tasaka uniform din islamiyyarta domin karfe uku suke tafiya su dawo karfe shida na yamma,

Hannen kannenta ta kama suka yiwa mama sallama suka tafi, sai da misalin karfe shida da yan mintuna suka dawo, dawowarsu tayi daidai da zuwan yaya kabeer shi da wani abokinsa,

Nadiya bata bari sunga fuskarta ba tafara gaidasu,

"Baiwar Allah ya kiketa boye kaine kamar marar gaskiya,kodai bakida gaskiya?" Abokin yaya kabeer din yace da ita,

"Kabarta kawai musty domin yar kauye ce" yaya kabeer yafada cikin barkwanci da tsokana, ita dai nadiya shiru tayi musu tana jinsu sai dai ta lura wannan abokin na yaya kabeer wanda aka kira da musty sai faman binta da kallo yake, duk inda ta waiga sai taga yanata kare mata kallo,

Ganin haka yasa ta takura ta shige gida yayinda yaya kabeer ya mara mata baya,

A soron gidan suka tsaya kowannensu fuskarsa dauke da murmushin kauna,

"Yaya kabeer ina ka samo wannan abokin mai shegen kallon tsiya?"

Dariya maganarta ta bashi dan haka ya fara darawa yana kallonta,

"Wai musty? Abokinane unguwarmu daya sannan tare muka yi karatu dashi"

Dan karamin tsaki taja, "Allah na tsani mutum ya tisani agaba yayita kallona"

"To yanzu dai nayi laifi tunda har na kawo wanda yayi miki abinda bakya so, ayi min afuwa..."

Murmushi tayi, "ni ai ba laifi nace maka kayi minba amma dai wannan abokin naka gaskiya ya fiya kallo da yawa"

"To ai nabaki hakuri"

"Nahakura"

"To zan iya tafiya?" Yace da ita cikin tsokana,

"Zaka iya mana yaya kabeer..."

"To fara shiga gida nagani"

Wucewa tayi tana murmushi ta shige cikin gida sannan shima kabeer din ya juya yafita.

Fuskarta dauke da fara'a ta shiga cikin gidan, zaune ta tarar da mama da kannenta tana yimusu shari'a wanda kusan kullum aikin kenan amir da amira kamar zasuga hanjin cikin junansu,

"Ke kuma a ina kika tsaya su Amira suka rigaki shigowa?" Mama ta tambayeta idanuwanta akanta,

"Mama yaya kabeer ne ya tsayar ni wallahi.."

Shiru Maman tayi ta mayar da hankalinta gasu amir taci gaba da yimusu sulhu, yayinda ita kuma nadiya ta ajiye jakar islamiyyarta ta shiga kitchen domin ta jiyo tuwon da mama keyi ya fara kauri alamun ya kama,

Itace ta karasa girkin sannan ta fito daidai lokacin abbansu ya dawo nan kuma dukkaninsu suka dunguma zuwa falonsa kamar yadda suka saba.

   Tunda musty abokin kabeer yaga nadiya yaji ta kwanta masa arai domin yarinya ce mai hankali sannan kuma mai nutsuwa gata da kunya da ganin girman nagaba, gani daya da yayi mata yasashi kamuwa da sonta dan haka batare da ya shawarci abokinsa kabeer ba ya samu mahaifinsa yayi masa maganar nadiya domin shi dagaske yake sonta bada wasa ba sannan son aure yake yimata ba na yaudara ba shiyasa ma yake son mahaifinsa yaje ya tambayo masa aurenta,

Aranar da ya sanar da mahaifinsa aranar yaje ya samu baban nadiya daf da lokacin sallar magrib, kasancewar abba mutum ne mai karrama bako sai da ya karrama baban musty sosai ya fito musu da ruwa sukayi salla kamar dama sun san juna sannan baban musty yafadawa abba abinda ke tafe dashi,

Shiru abba yayi kafin ya cewa baban musty zai tambayi nadiyan ko tasan musty din inyaso duk yadda sukayi da ita zai kirashi a waya ya fada masa, anan suka yi exchanging din phone numbers dinsu abba ya shiga gida,

Lokacin da yashiga falonsa nadiyan ya samu ita da mama suna cin tuwo tare, su kuma yaran an zuba musu taliya suna ci,

Sai da abba ya bari sun gama cin abincin sannan yayi gyaran murya yace,

"Nadiya zo nan"

Kusa dashi ta koma ta zauna, "gani abba"

"Bakon da nayi dazu saboda ke yazo.."

Ras,ras gaban nadiya ya fadi saboda bata san abinda tayiba,

"Abba laifi yace nayi masa?"

Murmushi abba yayi,

"Ba laifi kikayi masa ba nadiya, yazo nemawa dansa aurenki ne, sunan yaron wai Mustapha abokin kabeeru ne yayanki"

Ba karamin faduwa gaban nadiya ya sake yiba, nan fuskar musty ta bayyana acikin zuciyarta lokacin da ya kafeta da ido yana yi mata wannan kallon kurullar....


*_Ummi Shatu_*
[7/11, 7:58 AM] Ummi A'isha *MIJINA SIRRINAH...!*🌹
      _(Labarin K'auna)_


   *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_


® *HASKE WRITERS ASSO.*



   *6*

aishaummi.blogspot.com

~~~Shiru nadiya tayi saboda bazata iya fadawa abba cewar yaya kabeer take so ba,

"Nadiya ya naji kinyi shiru ne?"

Muryar abba ta dawo da ita cikin hayyacinta,

"Abba babu komai.."

"To Mustapha dai ya turo mahaifinsa tunda babu wata matsala zan sanar dasu inyaso yafara zuwa har kusamu ku daidaita"

"To abba" ta fada kanta akasa, ita dai mama tana zaune tana jinsu amma har akayi aka gama batace ko uffan ba,

Mikewa nadiya tayi ta fita zuwa dakinta gaba daya tama rasa abinda yake yimata dadi acikin zuciyarta, gashi bata son fadawa yaya kabeer domin gudun sakashi cikin damuwa,please call me ta tura masa nan take ya kirata,

"Yaya kabeer yau ban ganka ba"

"Nidinma yau ban samu ganin fuskar gimbiya nadiya ba amma nasan dalili.."

"Wanne daliline?" Ta tambayeshi cikin dokin jin abinda zai fada,

"Yau naje unguwa ne sai dazunnan nadawo shiyasa ban shigoba, amma gobe sammako zan dako da sassafe inyi karin kumallo da kyakkyawar fuskarki"

Dariya abinda yafada ya bata dan haka tafara dariya,

"Kaji yaya kabeer da abin dariya sai kace wani abinci da zakace zakayi karin kumallo da fuskata"

"Ni ai kinfi abinci, da ace za a ajiye min ke inyita kallonki to da na tabbata bazanji yunwa ba.."

Wata dariyar ta sake yi har tana kokarin fadowa daga kan gadonta,

"Yaya kabeer zaka sa cikina ya fashe dan dariya gashi dama naci tuwo na koshi dayawa.."

"Wai wai, wai, overfeeding kikayi ai? Oya tashi ki fara exercise ina jiyoki daga nan"

Tashi tayi tana dan murmushi,

"Allah yaya KB jina nakeyi nagaji nidai ban son exercise dinnan.."

"To yi tsalle guda goma ina kirga miki, oya fara"

Tsalle tafara tanayi yana kirga mata har sai da tayi guda ishirin sannan ya barta takoma saman gado ta kwanta tana haki,

"Washh, yaya kabeer wlhi kabani wahala da yawa"

"Waye yasa kici abinci yayi miki over?"

"Kaine.."

"A'a ni karki yimin sharri.."

Murmushi tayi kafin tabashi amsa wayar tayi shutdown, komawa tayi ta kwanta tana cikeda farin ciki.

Kamar yadda kabeer yafada kuwa da safe sai gashi yazo lokacin ko school su nadiya basu tafiba, asalima lokacin suke shiryawa, kanta babu ko dan kwali tana cikin kitchen tana cin soyayyen dankalin da mama ke soyawa sai gashi ya shigo, ba karamin mamaki nadiya tayiba domin ta zaci wasa yake yimata da yace zaizo da sassafe ya ganta,

Dan tsananin kunya kasa gaisheshi tayi tana jinshi da mama suna gaisawa daga nan yawuce ciki falon abba,

Bata bari yaji fitarta zuwa makaranta ba ta zare jiki tagudu.

  Abangaren Mustapha kuwa ba karamin dadin labarin da mahaifinsa yazo mishi dashi yajiba musamman ma da yaji cewar ba ayiwa nadiya mijiba asalima ko tsayawa da samari bata fara yiba,wanka ya dauka ya shirya ya fito ya nufi gidansu nadiyan,

Tana falon abba tana yiwa su amir homework yaro yayi sallama yace wai nadiya taje inji Mustapha, kamar bazata yi motsiba har saida taji mama tayi magana sannan ta tashi tafita zuciyarta babu dadi,

Tsaye ta sameshi ya saka hannuwanshi acikin aljihu yana yimata murmushi sai dai ita ko kadan bai burgeta ba, sallama tayi masa ya amsa cikeda kulawa nan suka gaisa yafara koro mata jawabi,

"Nadiya wato tun ranar farko dana soma ganinki Allah ya jarrabi zuciyata da sonki da kaunarki saboda yabawa da nayi da hankalinki da nutsuwarki,ina fata zaki bani hadin kai har nakai ga cimma burina da muradina na mallakarki..."

Saida taji yayi shiru sannan tayi magana,

"Yaya Mustapha nagode da soyayyar ka agareni,hakika duk Wanda yace yana sonka to ya gama yimaka komai kuma bakada kamarshi,to amma nikuma inada wanda nakeso"

Cikeda mamaki ya kalleta saboda shidai mahaifinsa yace mahaifinta ya sanar dashi babu wanda yake zuwa wurinta,

"Kina da wanda kikeso? Waye?"

"Yaya kabeer ne abokinka"

Jin abinda tace yasashi yin shiru nawasu yan lokuta kafin daga bisani ya kalleta,

"Shikenan nadiya nagode da kika fada min gaskiya baki rufeni ba, kuma nayi farin ciki da jin cewa kabeer ne wanda kike so domin mutumne shi mai kyakkyawan hali da dabi'a mai kyau, Allah ya tabbatar da alkhairi"

Sallama yayi mata ya tafi nan itama ta juya ta shiga cikin gida tana dauke da farin cikin cewar tagama da babin Mustapha..


*_Ummi Shatu_*
[7/13, 7:02 AM] Ummi A'isha *MIJINA SIRRINA..!*🌹
     _(Labarin k'auna)_

  *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*

  *7*

aishaummi.blogspot.com

~~~Hankali kwance nadiya ta koma gida taci gaba da gudanar da harkokinta, soyayyarsu itada yaya kabeer kuwa kullum sake yin gaba take tana kara kulluwa, koda yaushe suna makale awaya suna hira, sannan kusan koda wanne lokaci yana gidan mutukar nadiyan tana nan.

   Tunda nadiya ta sanarwa da mustapha cewar tanada wanda take so yaji hankalinsa ya dan tashi amma idan yatuno da cewar kabeer ne wanda take so din sai yaji ranshi ya danyi fari saboda yasan kabeer zai riketa riko na gaskiya wannan dalilin ne ma yasashi sanarwa da mahaifinsa yanda suka yi da ita, shima mahaifin nasa baiyi k'asa a gwiwa ba ya kira abban nadiya ya fada masa abinda yafaru gudun kar aga musty din yadaina zuwa bayan kuma manya sun shiga, shiru abban nadiya yayi saboda shidai a iya saninshi nadiya bata da wani saurayi amma tunda yaji haka to ya zama dole ya tuntubeta da zarar ya koma gida.

  Kamar yadda al'adar gidan take yauma zaune suke dukkaninsu a falon abba suna kallon tashar mbc drama, rage karar volume din tv din Abba yayi yace,

"Yawwa nadiya kafin na manta zo ina son magana dake.."

Kusa da mama ta dan matsa tana kallon abba,

"Nadiya yaron nan mustapha da yazo wurinki yace kince masa kinada wanda kikeso hakane..?"

Kai ta dagawa abba, "hakane Abba"

"To waye?" Abba yasake tambayarta, kamar bazata yi magana ba dan kunya ta daure tace,

"Abba yaya kabeer ne"

Shiru abban ya danyi fuskarsa dauke da murmushi,

"To kira min kabeer din, dama yau ai naga baizo gidanba"

Tashi tayi ta fita tana cikeda murna, wayar mama ta dauka ta kirashi,

"Yan mata.."

"Yaya kabeer albishirinka?"

"Goro" yafada yana murmushi,

"To kazo abba yana kiranka"

"To ai baki fada min albishir din da kika yimin ba"

"Idan kazo zakaji"

"To gani nan zuwa"

Katse wayar tayi ta koma falon abba tana jin kamar ta daka tsalle dan tsananin murna,

Tana shiga falon abba ta dan saci kallon mama nan taga fuskar Maman babu walwala sosai amma dai batayi magana ba,

Nan kuma taji ranta ya dan sosu saboda tasan bacin ran mama yanada alaka da maganarsu itada kabeer tunda tun jimawa Maman ke yimata gargadin cewar karta bari soyayya ta shiga tsakaninta da kabeer,

Tana ta tunanin abinda zaije yazo aranta taji sallamar yaya kabeer nan tayi hanzarin jan hijabinta ta rufe fuskarta saboda kunya sai dai amma tun kafin ya karaso kamshin turarensa ya rigashi karasowa,

Cikin nutsuwa yayi sallama ya shiga bayan abba ya amsa masa, nan kuma su amir sukayi kansa suka cuccukumeshi domin yasaba basu sweet duk lokacin da yazo,

Yau dinma saida yabisu ya basu daya bayan daya sannan suka kyaleshi ya nemi wuri ya zauna, cikeda girmamawa ya gaisheda abba da mama,

"Kabeeru dalilin da yasa kaji nace kazo shine nadiya ce tazo min da wani zance cewar kai da ita kuna son junanku hakane?"

Sunkuyar da kai kabeer yayi cikeda kunya yace "hakane abba"

Dan fara'a abba ya fadada cikeda jin dadi yace,

"To kabeeru babu shakka naji dadin wannan labari domin hakan zai kara dankon zumunci da aminci a tsakaninmu domin nadiya yar uwarkace, sannan ni mahaifinka ne ako ina zan iya tsayawa in nema maka aure bare agidana,dan haka ni a matsayina na mahaifin nadiya nabaka ita a matsayin matar aure ko bana raye ban yadda nadiya ta auri kowanne namiji ba face kai har sai dai idan kaine ka sauya akalarka, dan haka abinda nake so dakai shine da zarar ka koma gida ka sanarda yaya cewa ga abinda mukayi dakai saboda sonake yi nadiya na gama makaranta ayi bikinku da ita batare da andauki dogon lokaci ba"

Ai kabeer najin abinda Abba yace yaji kamar an yimishi bushara da gidan aljanna, nan wani dadi ya rufeshi zuciyarsa ta samu wata nutsuwa mai kayatarwa tuni yafara yiwa abba godiya,

"Abba nagode madalla, Allah yasaka da alkhairi, Allah yabar zumunci abba.."

"Babu komai kabeer ai duk abinda nayi maka kaina nayiwa domin kai d'anane halak malak"

Saida kabeer ya sake jaddada wata godiyar sannan ya tashi ya fita, cikeda jin kunya nadiya tabi bayanshi, tana zuwa tsakar gida kuwa ta iskeshi lafe ajikin bango dama ita yake jira ya harde hannuwansa ajikin kirjinshi,

Kallonshi tayi yasha gaye cikin wata rantsattsiyar purple colour din shadda galila wacce tasha dinkin buba dan haka ba karamin kyau yayiba,

"Yanzu kaji albishir din da nayi maka dazu?" Tafada cikeda murmushin kunya,

"Naji wannan dalilinne ma yasani shirya baki tukwici, rufe idonki"

Rufe idonta tayi tana murmushi, "yaya kabeer Allah dai yasa nima chocolate din zaka bani irin wacce kabawa su amir..."

Bata iya karasawa ba saboda jin lebenshi akan nata, take jikinta yafara rawa tayi gaggawar bude idonta, nan ta juya zata gudu yayi saurin rikota,

"Ai abba yace yabani ke ko baya raye nine mijinki, tsananin farin cikine yasa kikaga nayi miki haka so karki fassara ni da wata manufa, ko ba komai dai kin san ni yayanki ne dan haka bazan taba cutar dakeba"

Har lokacin bata iya yin magana ba saboda tsantsar kunyar da ya haddasa mata,

"Yaya kabeer nidai.."

Hannunta ya rike ya matsa kusa da ita tareda leka fuskarta wadda ta kawar gefe guda,

"Kedai me?"

"Nidai kasani jin kunya"

Murmushi yayi ya mike tsaye yana kallonta zuciyarsa cikeda farin ciki...


*_Ummi Shatu_*
[7/13, 6:59 AM] Ummi A'isha: ® _HASKE WRITERS ASSO._

    *MIJINA SIRRINA...!*🌹
        _(Labarin k'auna)_

       
           _*NA*_

   *_UMMI A'ISHA_*


   *8*

aishaummi.blogspot.com

~~~ "Wai kina nufin haka zamuje gidan kina yimin wannan kunyar?"

Murmushi ta danyi "wai yaya kabeer ni duk ba wannan ba yaushe zaka zo muyi hira irin wacce muka dade ba muyiba?"

Daga kai yayi yana kallon sararin samaniya alamun tunani fuskarsa kuma kunshe da murmushi,

"Uhmmm, ina jin zanzo a weekend saboda ranar ne banida aiki da yawa sannan kema kina gida.."

"To Allah ya kaimu, yanzu dai bari nakoma ciki saboda kai naga kana cikin farin ciki.."

Dakatar da ita yayi ya hanata tafiya,

"Ina kuma zakije bayan akwai labarai da yawa da nake burin ji daga gareki"

"Labari kuma yaya kabeer? A wannan daren?"

"To da sai awanne daren?" Ya tambayeta yana murmushi,

"A'a yaya kabeer karfa ka sauya min maganata zuwa wata daban"

Murmushinsa ne yasake karuwa, "kaji min yarinya da wayo, wai ke waye ya koya miki wayone? Ni ban taba ganin first born mai wayo irin nakiba"

Dariya tayi ta rufe fuskarta, "har nakaika wayo? Kaima fa first born dinne amma kafini wayo ma"

"A'a ban fiki wayoba zadai muzo daya, musamman ma tunda zuciyoyinmu sun kasance guda daya, sannan nan bada dadewa ba zamu zama abu daya..."

Dariyace ta kwace mata nan tayi baya da sauri tana dariya,

"Nidai yaya kabeer natafi da wannan sai anjima.."

Shima dariyar yayi ya daga hannu alamun bye bye yana cewa,

"Ok bye yanmatan yaya kabeer"

Har taje daf da dakin mama dariyar take, a kofar daki taga mama tsaye fuskarta babu walwala sannan da alama ita take jira,

"Mama..."

"Zo nadiya" Maman ta fada idonta har ya danyi ja saboda bacin rai, jiki asanyaye nadiya tabi bayanta zuwa cikin bedroom dinta domin basu tsaya a falo ba,

Zama mama tayi agefen gado itama nadiyan ta zauna,

Kamo hannuwan nadiya mama tayi tana kallonta,

"Nadiya nasan ke yarinyace karama wacce bata gama sanin rayuwa ba, wadda hankali bai gama ratsata ba, wacce bata san rayuwar aure ba, wacce bata san irin gwagwarmayar da kowacce mace keyi agidan aurenta ba, bawai ina son rabaki da kabeer bane nadiya a'a sai dai ina son kisani shi auren zumunci yafi komai gyara zumunci idan har yayi dadi amma yafi komai b'ata zumunci mutukar baiyi dadiba shiyasa zakiga tun farko ban so soyayyarku da kabeer ba saboda kabeer dan dakinane akwai zumunci mai karfi tsakanina dashi haka iyayensa, bana son azo ayi abu ba aji dadinsa ba zumunci ya baci.."

Gaba daya jikin nadiya yagama yin sanyi saboda jin abubuwan da mama ta fada dan haka take taji jikinta ya fara yar rawa,

"Mama kiyi mana addu'a kawai akan Allah yasanya albarka acikin al'amarin amma ni sam bazan iya rabuwa da ya kabeer ba saboda nafara sonsa tun ban san wacece niba.."

Shiru mama tayi tana kallonta batare da tace komaiba, ita akwai abinda ta dade tana hangowa wanda ita nadiya ko kadan bazata iya hangoshi ba domin akwai kuruciya atattare da ita sosai saboda gaba daya yanzu bazata wuce shekaru 15 ba aduniya dan haka yanzune tafara saninma menene rayuwar,

"Shikenan nadiya tunda kin kasa fahimtata shikenan bazan hanaki abinda kikeso ba Allah ya sanya alkhairi da albarka acikin tarayyarki da kabeer"

Idanuwan nadiyane suka ciko da kwalla nan tayi saurin tashi ta fita saboda sai take jin kamar yanzu ne zata tafi tabar mamanta da yan uwanta,

Duk da cewar mama sunyi haka da nadiya bata iya hakura ba tashi tayi taje ta iske abba a falonsa yana zaune shida su amir da waleeda nan ta tashesu tace sutafi dakinsu suje su kwanta,bayan fitarsu ta samu wuri ta zauna kusa da abba,

"Abban nadiya wata magana nake son muyi dakai amma ta fahimta, dafarko ina son ka fahimceni ka gane cewar ni bawai bana son kabeer ne ko kuma yana da wani mummunan tabo awurina ba, kawai nidai bana son maganar aurensa da nadiya ne saboda auren zuminci bashida alfanu mutukar ba ayi daceba amma idan har aka dace yayi dadi to zumunci yana sake kulluwa,

Ban so lokaci daya farat daya ka amince ka bawa kabeer nadiya ba saboda gaskiya nidai auren zumunci baya daya daga cikin abinda nake son yiwa 'yayana.."

Abba bai tanka ba har saida yaji tayi shiru alamun ta gama sannan yafara magana da tausasashiyar murya,

"Haba hajiya bilkisu, ai kabeeru dan dakinki ne, kin sanshi kin san halinsa sannan kin san ko wanene shi tun yana yaro dan haka bakida kokwanta acikin halayyarsa, kuma insha Allah wannan auren akwai alkhairi acikinsa ba kadanba da yardar Allah sai kowa yayi alfahari dashi kedai kawai kiyi musu addu'a kuma ni ina ganin da ace mu dauki nadiya mu baiwa wani wanda bamu saniba, bamu san asalinsa ba bamu san halinsa ba bamu san ko waye shiba gara mu baiwa na gida wanda muka san tushensa muka san komai nasa.."

Jijjiga kai mama tayi alamar gamsuwa da bayanin da yayi mata sai yanzu ta danji ta samu nutsuwa akan zancen,

"Shikenan to Allah ya tabbatar da alkhairi"

"Yawwa hajiya bilkisu addu'ar da zamuyi kenan, kinga yanzu tana aji biyar next term zata shiga aji 6 nan da wata shekarar insha Allah zamu yi bikinta mu kaita gidan mijinta, amma kafin nan ina so nayi miki albishir da cewar keda ita yar taki na biya muku saudiyya zakuje ku sauke farali sannan ku iyo addu'a akan Allah ya basu zama lafiya da zuri'a dayyaba"

Murna ce ta kama mama saboda jin albishir din da abba yayi mata nan ta hau fara'a tana mai yimasa addu'ar Allah ya kara masa budi acikin harkokinsa...


*_Ummi Shatu_*
[7/14, 9:20 PM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
     _(Labarin k'auna)_


    *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*

     _Anty maijidda musa (maman twins) shafi na 9 zuwa shafi na 13 nakine ke kadai domin jin dadinki, ina mutukar ji dake anty Jidda..._

*9*

aishaummi.blogspot.com

~~~Nadiya na shiga d'aki ta kifa kanta jikin gado tafara rera kuka ahankali wanda ita kanta bata san dalili ba amma dai tafi zargin cewa na fargabar rabuwa dasu mama ne, shigowar su Amira da taji ne yasata yin shiru ta tashi ta shiga toilet, sai da ta gyara fuskarta sannan ta fito lokacin harsu waleeda sun kwanta,

Itama kwanciyar tayi ta dauki wayar mama dake wurinta tafara yin game, kiran yaya kabeer ne ya shigo nan ta d'aga jikinta a sanyaye,

"Yaya KB ya kaje gida?"

"Ni ai nayi fushi dake, wato ko ki kirani kiji yaya naje gida ko?"

"Ayya haba yaya KB ai kasan dai inada niyyar kiranka kawai dai Allah ne baiyi ba"

Jin yanda ta marerece murya ya sashi yin yar dariya mai dan sauti,

"Dadina dake ba a kada ke a magana mutukar a wayane amma idan a filine kuma kinfi kowa shiru"

"Ai kai dinne yaya kabeer kwarjini gareka, kwarjini kake yimin"

"Wanne irin kwarjini kuma?" Ya tambayeta ranshi cikeda farin ciki,

"Yaya kabeer in tambayeka mana"

"Allah yasa nasani yanmatan yaya kabeer"

Murmushi tayi ta sake makale wayar a kunnenta,

"Yaya kabeer kuma idan muka yi aure shikenan bazaka rinka kawoni gidan mama kullum ba ko?"

Dariya ya fara yi mata saboda jin yarinta afili,

"Haba nadiya kuma idan kikace kullum zan rinka kawoki ai sai su maman ma su gaji dake"

"To yaya kabeer kazo mu zauna agidan su Maman mana gaba daya basai munje gidanmu ba"

"Nadiya kenan, ke karamar yarinyace baki san menene aure ba, ko kin sani?"

"Nasani mana yaya kabeer"

"To fada min menene aure"

Shiru ta danyi tafara tunani kafin tayi magana,

"Yaya kabeer aure shine idan saurayi yaga budurwa yake sonta itama take sonshi sai ayi musu aure.."

"Daga nanfa?" Ya sake tambayarta,

"Sai akaita gidan da ya gina mata, iyayenta su siya mata kayan daki"

"Uhum daga nan kuma fa?"

Dan shiru ta sakeyi sannan taci gaba,

"Sai ya siyo kayan abinci ta rinka yi masa girki tana share gida tana yin wanke wanke"

"Shikenan?"

"Ehh" tabashi amsa tana murmushi, shima murmushin yayi,

"Shikenan kin gama?"

"Nagama mana"

Dariya yafara yi yana dad'awa har na tsawon wani lokaci domin sai yau yagama tabbatarwa da nadiya karamar yarinya ce wadda kuruciya ke dawainiya da ita,

"Ba ayi muku biology ne nadiya?"

"Ana koya mana.."

Shiru yayi saboda baya son yasata taji kunya shiyasa bai son fada mata kai tsaye,

"To tunda baki san menene aureba nabaki assignment ki zauna ki nutsu ki gano min menene aure"

"To yaya kabeer zan yi"

Murmushi ya dan yimata sannan yayi mata sallama,ajiye wayar tayi tanata tunanin maganganun da sukayi da yaya kabeer yanzu,

To ita yanzu tayaya zata samo wannan assignment din da yaya kabeer yace ya bata? Ta raya hakan acikin ranta, gyara kwanciyarta tayi taci gaba da tunani can sai ta tuno cewar yan ajinsu dayawa tana ganinsu suna karanta littattafan hausa sannan kuma tana yawan jinsu suna labarin aure ko labarin soyayya amma ita bata taba tsoma bakinta aciki ba amma itama daga gobe zata fara aro littattafai tana karantawa domin ganin abinda ke tattare aciki,

Sati biyu da kiran da abba yayiwa kabeer mahaifin kabeer suka zo domin su tattauna da abban nadiya.

***

Alhaji Bashar Usman da Alhaji Mu'az usman yan uwan junane ciki daya uwa daya uba daya suna da kanne mata guda uku wadanda yanzu haka kowaccensu tana can agidan mijinta tareda yaranta, Alh Bashar shine babba sai mai bi masa alh mu'az daga nan sai Hajiya Kubra sai haj sa'ade sai yar autarsu hajiya Maimuna,

Asalinsu yan jahar kano ne cikin wata karamar hukuma wacce ake kira da Rano, anan suka taso dukkaninsu sannan har yanzu anan kowannensu yake zaune tareda iyalinsa hajiya kubra ce kadai ke zaune a karamar hukumar sumaila, shi abbansu kabeer yana zaune a tsohuwar G. R. A, shi kuma abbansu nadiya yana zaune a unguwar Rano Quarters,

Alh bashar yana da 'yaya guda hudu biyu maza biyu mata, kabeer shine babba sai Fati wacce ke binsa daga nan sai Muhammad sai autarsu A'isha,

Tun lokacin da aka haifi nadiya yan uwa da dangi keta tsokanar kabeer suna cewa an haifa masa mata, haka itama nadiyan koda yaushe dangi da yan uwa cikin tsokanarta suke suna kiranta da matar kabeer, tun kabeer bai dauki abun da gaskeba har yazo ya fara yarda da abinda 'yan uwa ke fadi tsakaninsa da nadiya,

Ita kuwa nadiya lokacin ma bawani kwakkwaran sani ta yiwa yaya kabeer dinba amma kowa yazo gidan sai taji yana cewa "matar kabeeru" duk sanda aka tsokaneta da wannan sunan kuka take yi domin bata sanshi ba.....

*_Ummi Shatu_*🏻
[7/14, 9:19 PM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_



    *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*


  *10*

~~~~Lokacin da nadiya ta dan fara hankali a lokacin ne ta gane yaya kabeer sai ta tsinci kanta cikin jin kunyarsa, haka kawai take jin kunyarsa sam bata yarda suna haduwa dashi, shikuma gidansu nadiya wurin zuwansa ne koda yaushe kusan kullum sai yaje gidan tun bai fara jin son nadiya ba har yaji yafara sonta lokacin yana makarantar gaba da secondary wato jami'a, da sonta yayi karatunsa yagama yafito yazo ya kama aiki a wani kamfanin turawa dake nan cikin garin rano,

A boye suke gudanar da soyayyarsu ba tare da kowa ya furtawa dan uwansa ba amma su da kansu sun yarda cewa soyayya suke yi.

***

  Abban su kabeer da kanshi yaje yasamu abban nadiya domin kabeer ya sanar masa yanda suka yi da abbansu nadiya, gaba daya iyayen nasu abin ba karamin dadi yayi musuba musamman ma mahaifiyar kabeer domin tana mutukar kaunar nadiya tun lokacin da aka haifeta, kullum ita kenan aiken nadiya tazo tayi mata hutu amma ko sau daya nadiya bata taba zuwaba sai dai lokaci zuwa lokaci suna zuwa agaisa itada mama dasu Amira,

Tunda mahaifiyar kabeer taji maganar auren nan tarasa inda zata tsoma ranta dan dadi, nan da nan tace sai afara tanadi.

Batun soyayyar nadiya da kabeer kuwa abinsu gwanin sha'awa domin suna gudanar da soyayyarsu cikin burgewa da kulawa da juna,

Koda yaushe yana gidan wai zai koya mata karatu amma kuma ba karatun suke yiba soyayyarsu kawai suke yi, yanzu itama nadiyan ta tsunduma harkar karance karancen littattafan hausa dan haka tana karuwa da abubuwa da dama wadanda ada bata sansu ba.

  Term din da suke ciki yana karewa ta shiga SS 3 a lokacin suka tafi aikin hajji ita da mama, ba karamar tsaraba ta jibgowa yaya kabeer ba tayi masa siyayya ta burgewa mai yawan gaske musamman ma turaruka da jallabiyoyi kala kala,

Ranar da zasu dawo kabeer ne yaje airport domin daukosu, tun karfe 6 yake airport din amma jirginsu bai sauka ba sai misalin karfe 9 nadare,

Kallon nadiya kawai ya tsaya yi domin hakorin da tasako ba karamin kyau yayi mata ba, ganin mama nema ya hanashi magana,

Nan ya daukosu suka nufi gida, lokacin da sukaje mama fita tayi tana rike da jakarta nan itama nadiya ta yunkura zata fita kabeer yayi saurin riketa,

"Hajiya nadiya ina kuma zakije bamu gaisa ba?"

Murmushi tayi saboda jin ya kirata da hajiya,

"Inye muga hakorin Allah yayi miki kyau"

Hannu tasa ta rufe bakinta tana dariya, "haba yanmata na mugani mana"

Dakyar ta iya bude bakinta yagani, hannunta ya saki yana murmushi,

"Kinyi kyau sosai"

"Nagode yaya kabeer"

Tare dashi suka shiga cikin gidan yana rikeda kayansu da ya dauko musu daga nan yayiwa mama sallama ya tafi.

  Tunda su nadiya suka dawo kuma kabeer yaci gaba da zuwa gidan koda wanne lokaci,itama mama yanzu ta hakura tana son auren saboda ganin irin gata da soyayyar da Maman kabeer ke nunawa nadiyan sannan dama kabeer yarone mai biyayya

Nadiya taci gaba da zuwa makaranta sannan soyayyarsu da yaya kabeer na tafiya yanda ya kamata sai dai kuma yanzu nadiya ta dan fara d'ar d'ar da auren yaya kabeer saboda wani dalili,

Dalilin kuwa shine ayanda ta fuskanta yaya kabeer yanada yanmata masu yawan gaske, tun abin baya damunta har yafara damunta domin akwai lokacin da suka fita dashi ita da waleeda ta rakasu zai kaita shopping lokacin da sukaje shopping din suna gab da kammalawa wata budurwa tazo anan yatafi wurinta ya barsu nadiya, tun daga irin tsaiwar da sukayi da budurwar zaka fuskanci cewar saurayi da budurwa ne baya ga haka kuma sai kwantar da murya yake yi duk da dai nadiya bata jin abinda yake fada amna tagane cewar hakuri yake bawa yarinyar, anan ya kirgo kudi ya bata yadawo wurinsu nadiya wacce tagama shakar bacin rai,

Ko takansa nadiya bata bi ba taja hannun waleeda suka fita sai shine ya dauko kayan da suka siya bayan yabiya kudin,

Motarshi ya bude ya saka kayan sannan su nadiya suka shiga suka zauna, baiyi magana ba itama nadiyan haka nan yaja motar suka tafi,

Tana kallonsa anata kiranshi awaya yana katsewa daga baya kuma ya dauka yace zai kira anjima,

Wani haushine ya cika mata ciki domin koda yaushe ahaka yake ayita kiransa awaya yana rejecting ko kuma ya dauka yace zai kira ko ba afada mata ba tasan cewa yanmata ne ke kiransa domin yaya kabeer kyakkyawan namijine mai jida kyau da kuruciya sannan ga abin hannu domin aikin da yake yi da turawa yasamu nasibi sosai acikinsa sannan gashi da ilmi wannan dalilin ne yasa yasamu karbuwa sosai ake damawa dashi har kasashen waje suke fita aiki shiyasa kowacce mace zata yi burin mallakarsa,

Babu wanda yayi magana acikinsu har sukaje gida amma kafin su karasa an kirashi awaya yafi sau 30 wanda kusan duk kiran na yanmata ne,

Waleeda yabawa kayan ya rike hannun nadiya tamau tayadda bazata iya kwacewa ba, sai da yaga waleeda ta fita sannan ya sawa motar lock ya kalleta....


*_Ummi Shatu_*🏻
[7/14, 9:19 PM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
     _(Labarin k'auna)_


   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*

   *11*

~~~D'auke kai nadiya tayi ranta fal da takaici ita yanzu jin yaya kabeer take yafara fita aranta saboda kule kulen yanmatanshi, baya minti biyar sai mace ta kirashi sannan takasa gane alakarshi da wadannan tulin yanmatan,

"Yan matanah.." Muryarshi ta katse mata tunanin da takeyi,

Sam kin juyawa ta kalleshi tayi maimakon hakama sai kokarin kwace hannunta da ya rike tafara yi,

"Juyo mana kiji abinda zan fada miki yanmata na"

Nan dinma dai sake kawar da kanta tayi bata juya ta kalleshi ba ita bakin cikin da takeyi shine yanzu saura yan watanni kadan tayi candy kuma da zarar tagama school bikinsu za ayi ita dashi to haka zaije yana yimata wadannan kule kulen yan matan sai kace wani marar aji?

"Haba nadiya ta, ya kamata ki kasance mai yimin uzuri da afuwa akoda wanne lokaci, dan Allah ki saurareni kiji.."

Jin ya hadata da Allah yasata juyawa ta kalleshi,

"Ina jinka"

"Nadiya nifa wadda kika ganni da ita ba budurwata bace kanwar abokina ce, abokin nawa ma yanzu ba a kasar nan yakeba to shine tace wai in dan taimaka mata saboda sha'anin karatu dalilin dayasa kenan kika ga na dauki kudi nabata amma tunda bakiji dadiba kiyi hakuri.."

Shiru ta danyi na dan wasu sakanni tana nazari, nadiya yarinyace mai wayo da basira da kaifin kwakwalwa shi kansa ya shaida haka sannan gata da saurin gano abu shiyasa wani lokacin har tsoron yimata karya yake yi domin atake zata gane kuma tafada masa sai dai kawai yaji tace "yaya KB nagane logic din.."

Dagowa tayi ta kalleshi suka hada idanu abinda bai taba faruwa ba domin tsananin kunyarsa da takeji baya barinta ta iya hada idanu dashi,

"Yaya KB idan har wannan budurwar kanwar abokinka ce baka da alaka da ita meyasa zaku ware ku koma wuri daya bazaku gaisa ku tattauna agabanmu ba?

Meyasa zaku rinka maganganu kasa kasa alamun bakwa son kowa yaji abinda kuke cewa ciki har dani wacce kake shirin zama MIJINA SIRRINA, ni aganina ai duk wani abu wanda ya shafeka nima ya shafeni babu boye boye a tsakaninmu.."

"Hakane nadiya, amma kisani komai yana son sirri, yanzu yarinyar nan da agabanku ne bazata iya rokona kudin ba saboda bani kadai bane.."

"To amma da kuka gama yaya kabeer meyasa ko gaisawa baka kawota munyi ba a matsayina na kanwarka mai shirin zama matarka sirrinka?"

"Ohhh nadiya kin fiya rigima, ki yarda dani wannan yarinyar banida alaka da ita"

"To naji nayarda amma masu kiranka awaya tun dazu sukuma suwaye?"

Sumar kanshi ya shafa kafin yabata amsa "yan companynmu ne"

"Yan campanynku ne amma shine ka gagara daukar wayar saboda ina wurin?"

"Amma dai ai kinga driving nake ko"

Murmushin takaici ta danyi saboda har yanzu bata yarda da abinda yafada ba, "yaya kabeer gaskiya nidai bana jin dadin wannan abinda kakeyi, idan har zaka aureni to meye naka na kule kulen yanmata? Nasan dama tunda kana da kyau da kudi yanmata dole zasu soka to amma ai wannan ba yana nuna cewar ka sakar musu fuska kayita kulasu ba.."

"Wai nadiya yaushe muka fara yar haka dakene? Kodai wasu kika samu suke zugaki awaje?"

"Ko kadan ba maganar zuga bace yaya kabeer maganace ta gaskiya nidai bana son wannan kula yanmatan da kakeyi"

"Shikenan naji kuma zan kiyaye, shikenan?"

"Shikenan, bude min zan fita"

Juyo da fuskarta yayi yana murmushi,

"To ai baki tabbatar min da cewa mun shirya din ba"

"Mun shirya karka damu"

"To sai yaushe?"

"Sai da daddare idan kadawo"

"To kiyi min dan murmushi nagani mana"

Yanda yayi maganar ne yasata yin murmushin ba tareda ta shirya ba, nan ya bude mata kofar ta fita ta shiga gida, ko mama bata fadawa abinda ya faru ba tabar maganar aranta shi dinma da yadawo da daddare bata nuna masa ba.

  Kwana biyu da faruwar haka yace ta shirya zai zo ya kaita wurin mama su gaisa, nan ta shirya taci ado cikin wani swiss material blue, tasa mayafi da takalmi blue da jaka, ba karamin kyau tayi ba nan yazo suka tafi tareda su husna wadanda zasu rakata dama ka'idar gidan duk inda zataje to dasu husna take tafiya ko walida idan kuma basa nan to Amira ko amir acikinsu wani zai rakata,

Yana driving suna hira har suka hau titin da zai sadasu da unguwar, suna karya kwana sukaga wasu yan mata tsaye a bakin titi su biyu sunci uwar kwalliya, har ya dan gotasu sukaji maganar daya daga cikin yan matan tana tsayar dashi,

"KB, kb, kb.."

Packing yayi agefen titi ya dubi nadiya, "ina zuwa 2 minutes"

Bata cemasa kala ba har yafice tana ganinsu ta cikin mirror shida yan matan sai dariya sukeyi, shida yace tabashi minti biyu saida ya shafe fiyeda minti 15 awurinsu nan ran nadiya yabaci,

Dakyar suka rabu da yanmatan nan yadawo cikin motar yana shafa sumar kanshi,

"Yanmata na kiyi hakuri nasan nayi laifi amma ki yafe min kannen wani abokina ne.."

Ko ci kanka bata cemasa ba saboda shiru ma amsa ce da haka suka karasa gidansu, tun da mama taji sallamar nadiya tafara yimata lale sannu da zuwa, ba karamin dadi nadiyan tajiba domin mama tana mutukar kaunarta kamar zata goyata duk lokacin data ganta,

Kafin wani lokaci ancikata da kayan cima kala kala, mama sai janta take da hira tana tambayarta mutanen gidansu su mama dasu Amira,

Duk kannensa sai da sukazo suka gaggaisheta bayan duk sun girmeta babu sa'anta A'isha ce ma dai zasu danyi kusan sa'anni da ita amma daga Muhammad har fati sun girme mata sosai,

Kasa kasa ta kalli kabeer nan taga yamaida hankalinsa kacokan akan wayarsa wanda ko ba afada mata ba tasan chaten yake yi....

*_Ummi Shatu_*
[7/14, 9:19 PM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*

   *12*

~~~Wani b'acin raine ya sake rufe nadiya amma bata bari kowa ya fahimta ba, nan ta zauna agidan har sai da sukayi sallar mangariba sannan tayiwa mama sallama cewar zata tafi tareda fito da sabulun wanka wanda ta kawowa Maman ta bata,

"Ah haba nadiya harda wahala? Ai nice zan baki bake zaki baniba, haba nadiya keda ba ma'aikaciya ba bamai Sana'a ba kuma shine harda dorawa kai wahala?"

Maman tafada zuciyarta cikeda murna, cikin hanzari ta shiga daki ta dauko wata leda ta bawa husna tana fadin,

"To ga wannan babu yawa, agaida mama dakyau dasu Amira nagode madalla Allah yabar zumunci, Allah ya nuna mana wannan lokaci yasa ayi damu, agaida Alhaji dakyau.."

Godiya nadiya tayiwa mama sannan tafita, wani abin haushi kuma tana fita taga yaya kabeer tsaye ajikin motarsa shida wata budurwa wacce bata santa ba,

Kamar tasaka ihu haka nadiya taji ita sai yanzu take gane yaya kabeer, yanzu take fahimtar koshi waye, mutumne shi mai yawan kule kulen yanmata shiyasa har tafara kokarin janye zuciyarta daga gareshi domin gaskiya bazata juri wannan halayyarba,

Fuskarta babu yabo babu fallasa ta karasa wurin ta bude gaban motar ta shiga tana kallonsu ta cikin glass din motar,

"Shikenan zee sai munyi magana kigaida gida"

Yafada tareda bude kofar motar ya shiga,

"Wannan wata yarinyace acan gaba damu kadan to kwana biyu bamu haduba sai yau shine muka tsaya muka gaisa"

Yace da nadiya yana kokarin tada motar,

Ko kala nadiya bata furta masa ba saboda abin yana cin zuciyarta sosai, duk tulin yanmatan nan na yaya kabeer ko mata goma aka bashi damar ya aura tasan sai wasu dole sunyi saura to bare mata hudu kacal aka halasta masa,

Zuciyarta kamar zata fashe dan bacin rai sukaje gida, fitowa tayi zata shiga cikin gida yayi saurin shan gabanta,

"Wai nadiya dan Allah meyasa kike son sauyawa ne daga yanda nasanki zuwa wata tadaban? Meyasa kike son yiwa soyayyarmu illah? Dan Allah nadiya kidaina bata ranki akan duk wata mace da zakiga na tsaya da ita, ki dauka afadin duniyar nan babu wata mace sai ke, kisawa ranki cewar kowacce mace abayanki take, ke kadai nake gani a matsayin matar aurena dan haka ki daina damuwa kina bata ranki"

"Naji.." Shine kawai abinda nadiya tafada ta gegeshi zata wuce nan yayi saurin janyota wanda har sai da tafada jikinsa batare da ta shirya ba nan ya riketa yaki sakinta,

Jinta tayi cikin wani irin sabon yanayi saboda tunda take da yaya kabeer haka bata taba faruwa a tsakaninsu ba tasan dai sau mafiyan lokuta yana rike mata hannu ko yaja hancinta ko kuma yaja mata kunne amma bai taba gwada rungumeta ajikinsa ba sai yau,

Jin tana neman shagala yasata yin hanzarin zamewa,

"Ai nace maka na hakura ko?"

"To ai gani nayi kamar ba har zuciyarki ba shiyasa"

Murmushi tayi masa irin wanda zai tabbatar masa da cewar da gaske ta hakuran, nan ya karasa sakinta ta shiga gida, tun daga lokacin maganar ta wuce awurinta domin adaren ranar ma raba dare suka yi suna hira awaya.

  Haka komai yaci gaba da gudana batare da nadiya ta sake nunawa kabeer damuwarta ba saboda bata son yasata acikin jerin mata masu korafi da rashin hakuri, koda yaushe tana lura dashi domin tana son ganewa ko ya sauya ko kuma yana nan kamar da,

Kamar da din kuwa yake babu abinda ya sauya na daga kule kulen yanmatan da yake yi, wayo tayi masa ta karbi wayarsa aro tace zata kira kawarta nan ta shige dakin mama taje ta fara duban wayar ai kuwa sai da taji kamar zuciyarta zata buga domin bacin rai saboda massages ne na yanmata, da hotunansu kaca kaca,

Shi kansa kabeer sai da jikinsa yabashi cewar nadiya bincike ta tafi yimasa awaya bawai kawarta zata kiraba kamar yadda tace nan ya tashi ya tsaya yana jiran fitowarta Amma shiru sai da ta shafe fiyeda mintuna talatin adakin mama tagama duba wayarsa ciki da waje sannan ta fito, da mamakinsa sai yaga fuskarta asake babu alamun damuwa anan ya danji dama dama saboda watakil zarginsa bai zama gaskiya ba kila ba bincike tayi masa a waya ba,

Bashi wayar tayi suka dan taba hira ya tafi, yana tafiya nadiya taje tasamu mama wadda ke kitchen tana tuka tuwo, tsayawa nadiya tayi abayan mama,

"Mama.."

"Na'am.."

"Mama nafasa auren yaya kabeer"

"Saboda me?" Mama ta tambayeta cikeda razani bayan ta juyo tana kallonta,

"Mama haka kawai"

Rufe tukunyar mama tayi ta juyo tana kallon nadiya har na tsawon wani lokaci,

"Nadiya lafiyarki kalau kuwa? Anya babu abinda yake damunki?"

"Mama lafiyata lau, babu abinda yake damuna, nidai kawai yanzu bana son yaya kabeer abar maganar auren nan kawai ni yanzu karatu ma nake sonyi ina gama secondary zan tafi jami'a"

Tsayawa kawai mama tayi tana kallonta cikeda mamaki domin sam nadiya bata taba nuna sha'awar ta na cigaba da karatu ba sannan tun farko ita ta nace ta nuna kabeer takeso shiyasa itama Maman har ta hakura ta amince ta mara mata baya ta yadda take tayata to amma abin tambayar shine yanzu wanne abu kabeer yayi mata har take neman canja ra'ayi akansa....?


*_Ummi A'isha_*
[7/14, 9:19 PM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


   *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO.*

  *13*

~~~Jan hannunta mama tayi zuwa cikin dakinta suka zauna agefen gado,

"Nadiya idan da wani abu ki fada min saboda bazai yiyu haka kawai babu dalilin komai ki sauya ra'ayinki akan kabeer ba bayan kuma ada babu wanda kikeso kamarsa,

Idan kawayene suke zugaki to ki sani zasu kaiki ne kawai su baroki, idan kuma kuruciyace ke daukarki to kisani zaki cuci kanki wanda bazaki gane hakan ba sai nan gaba zaki fahimci cewar kin yiwa kanki illah domin Allah ya baki dama ya zabar miki miji nagari wanda ya dace dake amma kinki amincewa,

Idan kuma fada kukayi dashi to ki sanar min sai nakirashi naji menene ba'asi daga karshe na daidaitaku domin daga ke har kabeer ni dayane awurina babu banbanci.."

Tunda mama tafara wannan maganar nadiya tafara zubar da hawaye wanda bata san dalili ba, jin mama tayi shiru yasata yin magana cikin kuka,

"Mama nidai kawai yanzu bana sonsa ne wallahi nafasa aurensa.."

"Nadiya kin taba ganin anfasa aure babu dalili? Karfa ki manta yau saura watanni biyu kacal ki kammala karatunki kuma kin sani kina gamawa ko wata daya bazaki kara agidan nan ba za a aurar dake saboda kece kika nuna haka tun farko, tun da fari ke kika nuna aure kikeso idan kin gama secondary har abbanki ya ji ya kuma yarda dan haka yanzu bakida bakin da zakice kin fasa"

Kukan nadiya ne ya karu,

"Mama wallahi nidai nafasa auren yaya kabeer, ni bana sonsa yanzu"

"Ai nadiya ko bakya son kabeer yanzu tunda ada kin soshi dole ki aureshi, idan har abbanki ma yaji wannan maganar to kisani sai ranki ya baci dan haka ina mai shawartarki da kiyi gaggawar watsi da wannan hudubar ta shaidan.."

Mama na kaiwa nan ta mike tayi ficewarta saboda ita atunaninta kawaye nadiya tasamu a makaranta suke hure mata kunne dan haka tayi komawarta kitchen taci gaba da aikinta tabar nadiya nata faman kuka,

Har mama tagama tuwon abba yadawo nadiya na daki tanata faman kuka, sai da abba ya tambayi mama cewar ina nadiya sannan ta tuna ashe tabarta adaki nan ta tashi taje dakin nata tana shiga ta sameta tanata kuka bata daina ba,

"Ke har yanzu kukan kike yi? To kici gaba dayi karki daina". Mama tafada tareda sake fita takoma wajen abba,

Tun daga nan nadiya ta sauya kwata kwata, gaba daya haushin yaya kabeer takeji idanma yazo gidan bata saurararsa har sai idan mama na wurin, ko waya yanzu ta daina yi dashi idanma ya kira bata dauka dama kuma wayar mamace ita bata da waya har yanzu,

Gaba daya abinda ke faruwa Mama tasani amma har yau shi abba bai saniba shima kuma kabeer gidansu basu saniba, yayinda ita kuma nadiya tafara rubuta jarabawar fita domin har sun fara practical,

Lokacin da abba yaga sun fara practical tuni yabada order din gado tun daga kasar Italy, kaya aka kawo shiryayyu kama tun daga kan gado, kujeru, dining table da sauran kayan kawata gida hatta kayan kitchen an siyo, nan hankalin nadiya ya tashi saboda ganin wadannan kayan dan haka ta saka mama agaba tana yimata kuka akan ita wallahi yanzu bata son yaya kabeer karatu zatayi, da abin ya ishi mama sai taje ta fadawa abba tace ga nadiya can tasata agaba tana yimata kuka akan wai bata son aure karatu take so,

Amir abba ya tura ya kirata ta shigo idanuwanta jajur alamun tasha kuka ta koshi,

"Nadiya meyake faruwane? Naji mamanki tace kinzo da sabuwar magana"

"Abba ni yanzu nafasa auren yaya kabeer karatu nakeso"

"Ai nadiya ko agidan mijinki zaki iya yin karatu har kikai matsayin professor dan haka kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki kinji, shi aure baya hana karatu sannan karatu baya hana aure za a iya hada duka biyun, kabeer yayanki ne ba bare bane dan haka bazai cutar dakeba"

"Abba ni kawai auren ne yanzu bana so"

"Nadiya kefa da kanki kika kawo min kabeer kikace shi kikeso nikuma nabashi ke tareda yimasa alkawarin aure sai yanzu kuma yaji na canja magana? Ai aure tsakaninki da kabeer babu fashi, insha Allah kina gama makaranta da sati biyu zan daura miki aure akaiki dakin mijinki kamar yanda nayi alkawari ko bayan raina kar afasa"

Hawayene suka cigaba da ambaliya akan kumatun nadiya nan Abba yace tatashi tatafi, tashi tayi tafita taje taci gaba da kukanta adakinta,

Tsakanin d'a da uwa sai Allah nan itama mama taji hankalinta yatashi dan haka tabi bayan nadiya, adaki ta isketa tana kuka dan haka tazauna akusa da ita ta dafata,

"Nadiya kiyi shiru kinji, ki saurareni kiji abinda zan fada miki, tun farko nadiya kece kikace kabeer kikeso wanda nikuma banso hakanba saboda wasu abubuwa da na hango amma ganin hankalinki ya karkata akansa yasa na amince saboda ki samu abinda kikeso, to yanzu idan muka Mara miki baya muka hanaki auren kabeer duniyace zata zagemu, shi kansa abbanki indan har na goya miki baya zaiga laifina, zaice saboda kabeer ba dangina bane shiyasa nake kin aurenku dashi,

Dan haka ki nutsu kiyi hakuri kibarwa Allah ikonsa kedai kawai kici gaba da addu'a kinji"

Tashi zaune nadiya tayi tafara share hawayen fuskarta tana kallon mama......


*_Ummi Shatu_*
[7/16, 7:30 AM] Ummi A'isha🏻: [7/16, 7:29 AM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


    *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*


     _Gaisuwa da babbar murya ga masoyan mijina sirrina ina gaisheku aduk inda kuke, sannan ina taya kawata Batool Mamman marubuciyar littafin al'adun wasu murnar samun karuwa da mukayi, Allah ya raya mana boy cikin addinin islama yasa yayiwa addinin Allah hidima.._


   *14*

~~~Kallon mama tayi bayan ta share hawayen dake gudana akan fuskarta, sannan ta bude baki dakyar tace,

"Shikenan mama naji nayarda zan auri yaya kabeer kamar yadda kukeso.."

"Ai bamu mukeso ba nadiya, kece kike so bawai auren dole zamuyi miki ba, yau da ace bakece kika fito kika nuna kabeer a matsayin wanda kikeso ki aura ba to da ko yace yana sonki bazan goyi bayan abashi aurenki ba mutukar bakya sonshi, to amma BAKIN ALKALAMI ya bushe dan haka kiyi hakuri ki rungumi kaddara saboda kabeer shine mijinki..."

Jijjiga kai nadiya tayi, "to mama, amma gaskiya yaya kabeer yanada wata dabi'a wacce kowacce macen kirki bazata so mijinta ya kasance haka ba, yaya kabeer shegen son kula yan matanshi yayi masa yawa baya minti biyar sai kinji mace ta kirashi nikuma abin yana bani haushi"

Dafa kafadarta mama tayi tana murmushi,

"Haba nadiya, yanzu dama akan wannan zaki fasa auren kabeer? Ai wannan duk abune mai sauki da zarar kunyi aure duk zai manta da wadannan yan matan suma kuma zasu daina saurararsa su daina kulashi indai sukaji cewar yayi aure, wannan ba komai bane face halayya da dabi'un matasan zamani yawanci haka suke sai kiga wani ma yatara yan mata fiyeda goma kuma kowacce yana ikirarin cewar budurwarsa ce sonta yake.."

Murmushi nadiya tayi na karfin hali, itama Maman murmushi tayi ta mike tsaye amma duk maganganun nan tayi sune kawai saboda ta kwantarwa da 'yarta hankali,

"Ki saki ranki kinji karki sake nuna masa damuwarki ko bacin ranki akan haka, sannan tun daga yanzu ki zama mace mai daukar mijinta a matsayin sirrinta wacce bata fallasa asirin mijinta, ki koyi rufawa miji asiri kinji, bawai komai zaka rinka fada wanda ya shafi mijinka ba, shi aure da kike ganinsa nadiya zallar hakurine acikinsa dole sai ka koyi hakuri ka ji kaki ji kagani kaki gani sannan dole sai ka zama mai kawaici da mantuwa kar kayita tara laifukan da ake yi maka mutukar zakayi haka to bazaku taba zama lafiya da abokin zamanka ba domin koda yaushe mai laifine awurinka.."

"To mama"

Juyawa mama tayi ta fita, tabbas maganganun mama sun saukar mata da nutsuwa da kwanciyar hankali nan da nan ta nemi damuwarta ta rasa nan tafara harkokinta kamar yadda ta saba ta dauko comprehensive book dinta ta bude domin karantawa bayan taje sunci abinci da mama da kannenta,

Waleeda ce ta shigo da gudu tana rikeda wayar mama a kunnenta,

"Yaya kabeer ga anty nadiyan.."

Karbar wayar tayi tana murmushi,

"Yaya KB"

"Ranki ya dade, haka akeyi kuma gaba daya sai kibi ki manta da kabeer dinki? Anya kuwa kinyiwa yayanki halacci?"

"Haba yaya kabeer ni na isa, waneni da mantawa da yayana, mijina sirrina..."

Yanda tayi maganar ne yasashi yin dariya,

"Kajita kamar gaske alhalin kin manta dani asalima fushi kikeyi dani bayan nikuma baki sanar dani laifina ba"

"Yaya kabeer kenan wannan maganar ai tawuce so karma kace zaka tadata.."

Ajiyar zuciya ya saki mai mutukar karfi,

"Wato nadiya nikaina ban san irin son da nake yimiki ba shiyasa da kika juya min baya gaba daya hankalina ya kasa kwanciya.."

"Ayya yaya kabeer ai nace maka yawuce ko"

"Nagode matata, yanzu me kike shirya mana nadangane da hidimar bikinmu?"

"Yaya kabeer ai shiri yana wurinka sai yadda kace.."

"A'a yadda kikace dai gimbiya.."

Murmushi tayi saboda yaushe rabonta da su zauna suyi waya ta minti biyu da yaya kabeer,

"Yanzun me kakeyi ne?"

Kin ganni adakina na tura A'isha taje ta kawo min abinci.."

"Allah sarki gwauro.." Tafada cikin tsokana,

"Gwauraye dai har dake ai ko ke ba gwauruwa bace?"

"Gaskiya ba ita bace.."

"Nima ai ba gwauron bane tunda inada matata nadiya saura lokaci kankani ta zama mallakina nakaita gidana, nakaita dakina...."

Katseshi tayi ta hanyar cewa,

"To ya isa yaya kabeer basai ka lissafa ba"

Dariya yayi, "shikenan tunda kin hanani fadar sirrin zuciyata.."

"Ba hanaka nayi ba amma basai ka fada ba dai, yanzu kabani labarin abinda kake shirya mana na biki"

  Sun dade tare awaya suna tattaunawa har zuwa wani lokaci, koda gari ya waye ma shine yazo ya kaita makaranta domin ranar tanada paper,

Daga nan komai yaci gaba da tafiya yadda akeso domin sun shirya yanzu maganar bikinsu kawai suka saka agaba,

Kamar da yanzun ma koda yaushe kabeer yana kan hanyar zuwa gidansu nadiya,

Ita kuma nadiya yanzu gaba daya kanta ya dauki zafi saboda jarabawar da takeyi gashi gida sai shirye shiryen biki ake tayi mama kullum cikin fita take tana zuwa siyayyar abubuwan da ba asiya ba,

Suma gidansu kabeer din ba abarsu a bayaba wurin shirye shiryen bikin domin har sun kammala hada lefe akwatuna bakwai masu tsananin kyau da tsada,

Saura paper biyu nadiya ta gama jarabawarta aka kai lefenta, sai kawai dawowa tayi daga makaranta ta tarar da kaya makota sun shiga sunata gani,

Mamakine ya kamata saboda yaya kabeer ne fa ya daukota daga makaranta ya kawota gida amma shine bai fada mata ba?

Ai mutane naganinta suka hau guda suna cewa "ga amarya ga amarya.."

Ko takan kayan bata bi ba tawuce daki tana kokarin cire takalminta,

Dakin mama taje ta dauki wayarta ta kira kabeer,

"Yaya kabeer shine ko ka fada min ankawo kayan nan ko? Sai kawai zuwa gida nayi natarar mutane na kallo"

"Yi hakuri mantawa nayi, haba yanmata na ai kin san dai haka kawai bazan ki fada miki ba"

"Shikenan dai nagode"

Katse wayar tayi tatafi taje tayi wanka ta shirya, bata samu damar ganin kayanba sai da dare yayi bayan ankaiwa abba yagani,

Komai da aka saka acikin akwatinan sunyi mata domin babu na banza gaba daya masu tsadane.

Haka aci gaba da shirye shirye shiryen biki, musty abokin yaya kabeer shine babban abokin ango dan haka shine akan komai,

Ayanda angwayen suka tsara za agudanar da kamu da walima sai dinner aranar da aka daura aure bayan ankai amarya dakin mijinta, ita dai nadiya duk abubuwan da suka shirya bata da matsala domin yanzu bikin saura sati biyu saboda yaune zata zana jarabawarta ta karshe,

Kayan taya murna sosai yaya kabeer ya hado mata su greeting card, calendar, memo, key holder, handkerchiefs da sauran kayayyaki tududu wanda har mama sai da tayi masa fada tace shi da hidimar biki take gabansa meya aikeshi wannan aiki,

Aranar da su nadiya suka gama jarabawar tun daga ranar kawayenta yan class dinsu suke zuwa su rakata rabon iv card domin har yaya kabeer ya buga ya basu,

Shirye shiryen da ake gudanarwa agidansu nadiya sai wanda yagani domin gaba daya angyara gidan anyi sabon fenti abba ya zubawa mama sabbin furnitures nadiya nagani ta hau dariya tana cewa,

"Mama Ashe kema kin zama amaryar tunda harda sabbin kaya"

"Ahh nazama kam, gani uwar amarya sannan kuma amarya.."

Kullum musty ne ke kaisu rabon iv card din itada kawayenta har suka kammala nan kuma tafara sintirin zuwa gyaran jiki wurin kawata KHADIJA SIDI domin kwararriyace wurin fito da amare,

Cikin kwana biyu kacal da fara gyaran jikin nadiya tayi kyau tayi sumul fatarta ta sake gyaruwa ta dawo kamar bayan kwado dan tsananin laushi da taushi....

*_Ummi Shatu_*🏻
[7/16, 7:29 AM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
        _(Labarin k'auna)_


  *_NA_*

*UMMI A'ISHA*

® *HASKE WRITERS ASSO.*


  *15*

~~~A daren ranar kabeer yazo gidan, ganin nadiya yayi gaba daya ta sauya masa kamanni saboda tsananin kyawun da fatar jikinta tayi, gyaran jikin ba karamin karbarta yayiba ya fito da ita sosai sai kace balarabiya,

"Yan matana.. Irin wannan kyau haka, ai da ahanya na hadu dake sai kiwuce nawuce domin bazan iya ganeki ba... Wow"

Murmushi nadiya tayi, "kai yaya kabeer harda su tsokana haka"

Sajen dake kewaye afuskarshi ya shafa yana cigaba da kallonta tacikin hasken kwan lantarkin da ya haskesu,

"Allah ba wasa ba kin sauya min gaba daya, kinyi wani irin kyau Wanda ada banma san kina dashiba sai yanzu nagani"

"Ohhh yau dai yaya kabeer tsokana yakeji dan haka bari nayi shiru nabarshi yayi tsokanarsa yagama"

"A'a babu wani tsokana fa"

Dariya tayi ta kalleshi, "yawwa namanta ban fada makaba su zarah maina suna nemanka saboda wai hall din da kukace za ayi dinner acan ba lallai ya isa ba.."

"Jama'ar taku har nawace da bazai isaba? Zai isa harma yayi saura kudai kawai ku zama ready.."

"Shikenan to zamu zama ready din kamar yadda kace"

Murmushi yayi ya dan matsa kusa da ita, "har kin fara kamshin amarcin ne? Naji sai wani rikitaccen kamshine yake faman tashi.."

Juyawa tayi tawuce tana dariya tana fadin "yaya kabeer kaganka ko... Hmmm"

Tun daga wannan ranar basu sake haduwa sunyi mintuna biyar atare ba saboda gaba daya abubuwa sunyiwa kowannensu yawa musamman ma kabeer,

Tun ana saura kwana biyu biki gidansu nadiya yafara cika da yan uwa musamman ma yan uwan mama wadanda suka zo daga kura domin mama haifaffiyar garin kura ce,

Aranar musty yazo yakai su nadiya kunshi da saloon, basu suka dawo gidaba sai dare lokacin har yan jere sun dawo sunata faman koda gidan da irin daular da aka ajiye aciki,ita dai nadiya najinsu batayi koda tari ba saboda dama kabeer ya nuna mata gidan awaya lokacin da yayi yayi da ita suje tagani taki sai ya dauko mata hoton gidan awayarsa yakawo mata tagani, gida kam ya tsaru babu karya kamar a turai domin gidane irin tsarin na turawa.

Saura kwana daya afara shagalin biki mahaifiyar kabeer ta aikowa da nadiya wani kayataccen leshi mai tsadar gaske a dinke tace tasa ranar kamu, ita kam nadiya koda yaushe aranta tana jin cewar tayi sa'ar uwar miji mai sonta da kaunarta,

Ranar kamu ba karamin kyau nadiya tayiba tafito sosai domin wani leshi ne ajikinta golden da gwaggwaro shima golden sai takalmi da jaka,

Nadiya tayi kyau iya kyau nan aka kwashesu zuwa wani hall wanda acan za ayi shagalin kamun, daf da za atashi angwaye suka zo nan kabeer yakasa rufe bakinsa sai fara'a yaketa faman zabgawa yasha wani yadin boyel brown da hula sai kamshine yake tashi ajikinsa, hotuna kam da video sun shasu babu adadi har su kabeer din suka tafi nan taron ya watse kowa ya koma gidansa yayinda su nadiya da sauran dangi sukuma suka koma gida.

  Washe gari da misalin karfe 2 aka daura auren kabeer da nadiya akan sadaki dubu 30 kamar yanda waliyyinsa ya bayar wato mahaifin nadiya, shikuma mahainsa yayiwa nadiya walinci, ana tashi daga wurin daurin aure suka wuce wurin walimar da abokanshi suka shirya masa nan akaje aka debo su nadiya ita da kawayenta,

Yau dinma nadiya ba karamin kyau tayiba cikin wani jan leshi gashi an lullube jikinta gaba daya da lifayya wadda daga ganin adon dake jikinta kasan naira tayi kuka,

Wa'azi aka gudanar awurin walimar sannan akaci aka sha, ango shima ba abarshi abaya ba wurin zuba kyau domin wata lafiyayyar farar shadda yasha wadda taji dinki mai tsada,

Karfe hudu aka tashi daga walimar aka maida su nadiya gida, suna zuwa gida suka tarar da har anfara harhada kayan da za akai nadiya dasu domin abba yace ana yin sallar mangariba aje akaita,

Ai kuwa nadiya najin haka sai kuka nan mama tazo ta kama hannunta suka nufi falon abba,

Nan suka zauna tanata gursheken kuka,

"Nadiya kiyi hakuri kidaina kuka kinji domin kowacce mace hakace take faruwa da ita arayuwarta mutukar wannan ranar tazo, nidai abinda zance miki shine kiyi hakuri kibi mijinki sau da kafa kiyi masa biyayya,ki zama mace tagari mai rufa asirin mijinta, ina miki addu'ar Allah yabaki rayuwa mai dadi agidan mijinki yasa ta silarshi ki shiga aljanna, Allah yayi miki albarka"

"Amin amin, sannan kuma banda kazanta nadiya, banda rashin kunya, banda biye makota ana gulma, banda tona asirin miji, duk abinda yasaki kiyi abinda ya hanaki ki hanu, Allah yayi miki albarka yabaki yaya nagari" mama ta dora bayan abba yagama, nan mama ta kamata ta maidata inda ta daukota, da kuka da komai nadiya tasamu tayi wanka ta fito ta shirya lokacin har yan daukar amarya sunzo dan haka babu bata lokaci aka fita da ita aka saka a mota aka nufi gidan mijinta da ita lokacin ba afi karfe 7 nadare ba,

Suna zuwa kuma aka fara shirye shiryen tafiya dinner, angama shiryata kenan ango ya shigo cikin wani sky blue din yadi marar kauri, itama kuma dama shigar blue tayi nan suka bada kala,

Sai faman murmushi yake yimata amma ita duk idonta yayi ja saboda kukan da tasha gwanin ban tausayi, hannunta ya kama suka fita yana yimata magana ahankali,

"Menene yasaki kuka yanmata na? Ko kukan rabuwa dasu mamane? Kiyi hakuri kinji ai baku rabuba zaki rinka zuwar musu.."

Ita nadiya dai bata yi magana ba saboda tasan tana bude bakinta to fashewa da kuka zatayi dan haka taja bakinta tayi shiru,

Iya kawatuwa wurin dinner din ya kawatu yasha decoration  blue colour,nan aka fara gudanar da abinda za ayi gadan gadan,

Daga nadiya har kabeer sunsha ruwan nairori wasu ma masu yimusu likin ita nadiya ba saninsu tayiba kawai dai tasan gayyar kabeer ce musamman ma wasu yanmata wadanda suka daddage sunata zubar musu da ruwan nairori,

Karfe 12 aka tashi daga dinner din aka kwashi mutane zuwa gida, nadiya ita da kawayenta suna motar musty shine yakaisu gida yana zuwa yace kawayen su fito zai mayar dasu gidansu nan suka yi masa caaaah wai bazasu tafiba sai anbasu kudin siyan baki, cheque din 20,000 ya rubuta musu yabasu sannan suka yarda suka hakura suka fito bayan sun gama tsokanar nadiya wacce ke lullube ta tukunkune agefen gado tana risgar kuka...

*_Ummi Shatu_*🏻
[7/16, 7:29 AM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


   *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO.*

  *16*

~~~Sai da akayi kamar mintuna ishirin da tafiyarsu zarah maina tafara jiyo karar mota alamun yaya kabeer ya karaso gidan,

Sake gyara mayafinta tayi ta lulluba tana sauraren shigowarsa minti kadan kuwa sai gashi ya shigo hannuwansa dauke da ledoji manya guda biyu,

Ajiye ledodin yayi ya karasa wurinda take ya zauna akusa da ita yana murmushi,

"Yanmata nah.."

Shiru nadiya tayi takasa ko motsi ganin haka yasashi dagota zuwa jikinsa,

"Kidaina kukan haka kinji? Maza tashi kije kiyi alwala kizo muyi salla"

Batayi musuba ta mike taje ta shiga toilet din dake cikin dakin tayi alwala tafito tazo ta iskeshi yana jiranta nan yajasu salla sukayi sallar nafila raka'a biyu kamar yadda sunnah ta koyar,

Ledodin da ya shigo dasu yajawo ya bude ya fito da gasasshiyar kaza da snacks da drinks masu mutukar sanyi, "yan matana jeki kitchen ki dauko mana flate da wuka da cups.."

"Yaya kabeer ban san inda kitchen din yakeba.."

Jin abinda tace yasashi murmushi ya tashi dakansa yaje ya dauko yadawo ya zauna,

"Ga kaza zoki ci kinji yanmata na"

Duk da cewar nadiya najin yunwa sosai amma sai taji bazata iya cin kazar ba saboda kunyarshi dan haka ta jijjiga kai cikin dashewar murya tace,

"Nakoshi.."

Jan kazar yayi gabansa ya zage yafara cin abarsa batare da ya sake magana ba nan nadiya ta sake jin daci aranta saboda halin ko in kular da ya nuna mata,

Tana kallonsa yagama cin kazar ya dauki juice yasha ya mike,

"To tashi muje ki kwanta.."

Tashi tayi yabi bayanta zuwa kan lafiyayyen Italian bed din da aka kafa mata acikin dakin.

***

  K'arfe 8 nasafe nadiya ta farka duk jikinta sai faman yimata ciwo yake saboda gajiyar biki wacce ta hadar mata da gajiyar da yaya kabeer ya tara mata adaren jiya,

Dubashi tayi amma baya cikin dakin nan ta yunkura dakyar ta sauka daga kan gadon ta shiga toilet tasamu tayi wanka ta fito in banda yunwa babu abinda takeji nan tayi salla ta shirya ta zauna tayi tagumi tana jiran dawowarsa amma shiru babu alamunsa,

Ganin har karfe goma da rabi tayi bai dawoba gashi tana jin rsananin yunwa yasata tashi taje ta dauko guntun snacks din da ya bari adaren jiya tafara ci tana ci tana hawaye saboda bakin cikin rashin ganin yaya kabeer,

Ita abinda yasata kuka ma shine yasan irin yanayin da yatafi ya barta aciki maimakon ya tsaya ya tarairayeta yabata kulawa ya taimaka mata ya nuna mata soyayya kamar yadda kowacce amarya take samu daga angonta washe garin ranar da aka kaita amma ita yayi tafiyarsa yabarta bata samu wannan kulawar ba,

Sannan ko acikin littattafan da take karantawa tana jin irin zumudin da angwaye keyi tareda nunawa amarensu soyayya amma ita sam bata samu haka ba, da kuka tagama cin snacks din ta tashi tafita tana tafiya dakyar, gidan tabi ta ga yanda aka tsarashi dan kyau kam gida yayi kyau sai dai fatan Allah yasa tasamu farin ciki mai dorewa acikinsa,

Ganin dagaske yaya kabeer baya cikin gidan yasata komawa falo ta zauna zuciyarta nata tunanin inda yatafi, "kodai abinci yatafi siyo mana?"

Nan ta zauna ita kadai har yan gidansu suka zo su waleeda da yan uwan mama, ananne ta dan sake taji dadi ana jimawa kuma sai ga yan gidansu yaya kabeer dauke da kulolin abinci,mintuna kadan sai ga kawayenta suma nan taji tasamu saukin damuwar dake addabar zuciyarta,

Gidanta cika yayi sosai da mutane nan kawayenta suka sata ta sake yin wanka tasha kwalliya domin yan unguwa sai shigowa ganin amarya suke yi,

Wuni guda cur babu kabeer babu alamunsa sannan ko waya bai yimata ba dadi daya taji shine kawayenta da kannenta har dare suka kai agidan sai daf da sallar isha sannan suka tafi, nan kuma tsoro ya tisata agaba sa'arta daya ma da akwai wuta,

Atsorace taci gaba da zama acikin gidan har karfe 9 nadare sai lokacin taji karar mota alamun dawowar yaya kabeer....

  _Gaisuwa ga masoya masu bibiyar labarin hakika kune abin alfaharina...._


*_Ummi Shatu_*: [7/17, 8:23 AM] Ummi A'isha🏻: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
       _(Labarin k'auna)_



   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.* _(home of expert writers)_


   *17*

   _Wannan shafin nabaku shi kyauta k'awayen arziki, Cwt Kausar luv, Besty phertymah Xarah, Fido sodangi k'awata tareda dukkanin d'aukacin masoyanku masu sonku suna bibiyar rubutunku akoda yaushe...._


~~~Tashi tsaye tayi ta karasa bakin kofar falon domin taroshi amma koda taje sai tayi turus saboda ganin irin kallon da yayi mata,

"Yaya kabeer sannu da zuwa.." Tace dashi jikinta asanyaye,

"Yawwa..." Shine kawai abinda yace yabi ta gefenta yawuce batare da yasake koda kallonta ba,

Tamkar gunki haka nadiya ta zama sai ido da tabishi dashi,

Abubuwa biyune suke daure mata kai ahalin yanzu, nafarko fitar sassafen da yayi ko tashi bai bari tayiba sannan tunda ya fita bai dawo gidanba sai yanzu, sannan yanzun ma da yadawo babu fara'a babu magana mai dadi kenan da saninsa yatafi ya barta yayi biris da ita ko waya bai yimata yaji yanda ta wuni ba tunda yafi kowa sanin acikin yanayin da yatafi ya barta,

"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un..." Shine kawai abinda ta iya furtawa taje kan kujera ta zauna hawaye nata faman ambaliya akan kumatunta,

Tunani daya takeyi Allah yasa ba irin wannan mummunan zaman zasuyi ita da yaya kabeer ba, burinta daya Allah yasa bazai sauya mata daga yaya kabeer dinta mai sonta mai kaunarta mai damuwa da ita akoda yaushe ba,

Kukan zuci taci gaba dayi har na tsawon wani lokaci nan ta tashi ta bishi cikin daki ga mamakinta akwance ta sameshi yanata faman daddanna wayarsa wadda da alama chaten yakeyi,

A dan nesa dashi ta zauna tana kallonsa,

"Yaya kabeer lafiya kuwa yau ka tashi tun sassafe ka fita baka dawoba sai yanzu..?"

"Lafiya lau" ya amsa mata atakaice,

Dan shiru tayi nawani lokaci sannan tasake magana,

"Yaya kabeer ga abinci can nakawo maka?"

"Ke dan Allah ki kyaleni idan ina jin yunwar ai zan fada miki haba, ke wacce irin yarinyace kin tisani agaba sai surutu kike yimin? Kin tambayeni ina natafi dasafe kinzo kuma kina sake yimin nonsense question.."

Binsa da kallo kawai nadiya ta tsaya yi saboda yadda ya fututtuke yana balbala masifa kamar wacce ta watsa masa wuta, ko a mafarki akace mata yaya kabeer zaiyi haka bazata taba amincewa ba amma sai gashi azahiri tagani,

"Allah yabaka hakuri yaya kabeer.." Tafada idonta cikeda kwalla,

Tashi tayi tawuce taje ta dauki zani ta shiga bathroom tayi wanka ta fito tazo ta shirya tasaka kayan bacci ta kwanta,

Bata san iya adadin lokacin da ya kwashe yana chaten dinsa ba.

  Yauma kamar jiya haka tasake tashi da ciwon jiki, jikinta duk yayi tsami amma koda ta duba gefenta sai taga wayam babu yaya kabeer babu alamunsa,

Zama tayi akan gadon tana tunani, to wannan wacce irin rayuwace? Dama haka auren yake? Miji sam bazai zauna agidansa tare da matarsa ba,

Nan da nan hawaye suka fara zubowa daga idanuwanta ita sai yanzu tagane dalilin mama da kullum idan tatashi yimata fada akan aure take cemata tayi hakuri domin gaba daya auren babu komai acikinsa face hakuri to dama wannan hakurin ne?

Share hawayenta tayi ta tashi ta dingisa zuwa cikin toilet tayi wanka tafito tayi salla ta shirya ta fita falo gidan babu komai na abinci sai ko danye sannan gas dinma ba aduro ba gashi babu kalanzir idan risho tace zata kunna, in banda yunwa babu abinda takeji,

Tana zaune afalo taga an kawo wuta nan taje ta jona electric cooker ta dora indomie ta dafa ta zo falo ta zauna taci tana gamawa ta tashi ta gyara gidan tasake yin wanka,

Tana daki tana kwalliya taji sallamar yan gidansu nan tafita cikeda murna domin su waleeda ne da sauran yan biki sukazo yimata sallama saboda ayau zasu tafi,

Ba karamin dadi tajiba nan ta hanasu waleeda tafiya tace sai yamma tayi hakane saboda tana son ta ragewa kanta zaman kadaicin da zata yi, daidai lokacin sallar azahar suma kannen kabeer suka zo gidan, nan suka zo mata da abinci wainar shinkafa da miyar agushi wai inji mama,ita dai nadiya tasan tayi sa'ar uwar miji amma abisa dukkan alamu batayi sa'ar mijiba,

Nan suka wuni dasu fati da su husna kannenta sai mangariba sannan suka tafi ai kuwa suna tafiya ta shiga damuwa domin gidan tsitttt yake sai ita kadai kwal kamar mayya.

Yauma kamar Jiya yaya kabeer bashi yadawo gidan ba sai da misalin karfe 10:30 lokacin nadiya har bacci ya dauketa akan kujera tana zaune ta kifa kanta akan hannun Kujerar da take kai....


*_Ummi Shatu_*
[7/17, 8:23 AM] Ummi A'isha: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
       _(Labarin k'auna)_

  *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*

  *18*

~~~Sai da yafi minti 20 da dawowa sannan nadiya tafarka nan tsoro ya sake kamata domin duk a zatonta bai dawoba amma kuma tana jiyo kamar motsi acikin dakinta,

Tashi tayi tanufi hanyar dakin tana magana "waye..?"

Shiru taji dan haka ta sadada ta shiga, tana shiga taga yaya kabeer ne yake tsane jikinsa yafito daga wanka,

"Yaya kabeer kaine kadawo ashe.. ?"

"Nine" yabata amsa, sanin yanda suka yi jiya yasata yin shiru bata sake magana ba, nan itama taje tayi wankan ta shirya ta kwanta,

Tunani ne ya mamaye zuciyarta saboda gaba daya yaya kabeer ya bata mamaki bata taba tsammanin cewar irin wannan rayuwar zasuyi dashiba, ita a zatonta irin rayuwar soyayyar da ake rubutawa acikin littafi zasuyi ashe abin ba haka bane sai yanzu tagane cewar rayuwar datake karantawa a littafi tasha banban da abinda ke faruwa azahiri amma ita bata fahimci hakanba sai yanzu,

Da wadannan tunanin bacci yayi awun gaba da ita, kasancewar tasamu tayi isasshen bacci yasata tashi da wuri domin ta riga kabeer tashi, Salla tayi ta zauna tana karatun alqur'ani har yaya kabeer din yatashi,

Gaisheshi tayi bayan ya idar da salla nan yace ta dora masa ruwan zafi tace babu gas kuma babu kalanzir,

Fita yayi can sai gashi da gas din da kayan tea yazo ya ajiye mata nan taje ta kunna wuta ta dafa masa ruwan zafin sannan ta dafa ruwan tea, wanka yayi ya fito yasha tea din akaro nafarko da yaci wani abu agidan,

Yana kammalawa ya kada rigarsa yafita bai sake waiwayar gidanba hatta kayan miya sai aike yayo mata,

Jalop din taliya da shinkafa tayi ta zuba a food flaks ta ajiye taje tayi wanka, tana fitowa taji wayarta na kara nan taga mamace murna sosai ta shiga yi ta dauka suka gaisa nan mama ta harhadata dasu waleeda dasu amir suka gaisa sai da suka gama gaisawa da kowa sannan mama takoma gefe,

"Nadiya ai babu matsalar komai ko? Naji tunda aka kaiki baki kiraniba sannan baki kira abbanki ba"

"Ehh mama wallahi wayar tawace babu kudi.."

Dan dam mama tayi sannan tace "to shikenan, ina kabeer din ko ya fita?"

"Ehh ya fita mama"

"To shikenan, ayita hakuri dai nadiya, zaman aure dan hakurine Allah yabaku zaman lafiya"

"Amin mama" nadiya tafada tana hawaye domin ita yanzu sai take jin cewar rayuwar gidansu tafi ta gidanta dadi domin da agidane da tuni yanzu tana can cikin kannenta yan uwanta suna wasa da dariya wani lokacin ma harda mama da abba acikin wasan amma nan gashi tazo rayuwarta atakure,

Sai da suka jima da mama suna hira sannan sukayi sallama ta ajiye wayar tazauna agefen gado tasha kukanta ta koshi ta share hawayenta tasoma shiryawa lokacin ba afi karfe 2 narana ba, tana gab da kammala shirinta taji karar shigowar text nan ta dauka ta duba tana budewa taga mamace ta turo mata katin waya har na dubu daya,

"Allah sarki mama.." Tafada idonta cikeda kwalla,

Falo ta koma bayan tayi salla tajona kayan kallo ta kunna tafara kallon wata tasha, tunowa da tayi cewar tana karantawa acikin littattafai tana jin irin yanda mata ke kulawa da mazajensu yasata daukar wayarta ta kira yaya kabeer,

Kamar bazai dauka ba sai kuma taji ya daga,

"Hello nadiya.."

Jin ya ambaci sunanta yasanya ta mamaki domin ada yanmatana yake kiranta amma yanzu tadawo nadiya,

"Yaya kabeer kana inane?"

"Ban gane ina inaba, sai kace wani yaronki zaki wani tambayeni ina ina? Menene? Me zanyi miki?"

Jikinta ne yafara rawa saboda jin masifar da yake yimata,

"Babu komai dama dai bugowa nayi inji lafiyarka.."

Bai sake bata amsaba ya katse wayar Kitttt,

Har lokacin da ya kashe wayar jikinta rawa yake domin fada yake yimata bil hakki da gaskiya,

Tagumi tayi tana rike da wayar tagagara koda motsi tana tunanin yanda yaya kabeer ya zama ahalin yanzu.

Wuni tayi acikin damuwa abincin ma bata iya ciba saboda ita kadaice masu zuwar matan ma yau babu wanda ya lekota dan haka tawuni sukuku har dare sai wurin karfe goma yaya kabeer ya dawo,

Sannu da zuwa tayi masa taje ta kinkimo abincin data dafa ta kawo masa,

"Yaya kabeer ga abincin.."

"Ke kinci?"

"A'a kai nake jira.."

"To danme zaki jirani? Agidanku mahaifiyarki tare kikaga sunaci da mahaifinki? Nace agidanku haka akeyi? Karki sake wani jirana akan abinci, idan kin dafa kayanki kici kawai basai kin jiraniba kin gane?"

Tsallake abincin yayi ya wucewarsa zuwa cikin daki yabarta sakare tana hawaye, jan abincin tayi ta dan tsakura a flate tafara ci tana hawaye har ta gama.

  Washe gari da sassafe yace taje ta dafa masa ruwan wanka zai fita, nan ta shiga kitchen ta dauki ashana kenan ta hango wani murgujejen bera nan ta yarda ashanar tayi daki da gudu domin tana tsananin tsoron bera,

"Menene?"

"Yaya kabeer bera ne acikin kitchen din.."

"Akan beran zaki fasa dafa min ruwan wanka? Ke wacce irin sakarya ce marar sanin abinda ya kamata? Look kinga nifa bazan dauki wannan sakarcin na banza da wofiba..."

Bathroom ya shige ya doko kofar yanata bala'i, falo ta koma ta zauna, tana zaune ya fito cikin shirinsa nafita yasaka kai yafice bai ko kalleta ba.........




*_Ummi Shatu_*🏻
[7/17, 8:23 AM] Ummi A'isha: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
       _(Labarin k'auna)_



   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

® *HASKE WRITERS ASSO.*


   *19*

~~~Bin bayanshi da kallo tayi sannan cikin damuwa tace,

"Adawo lafiya"

Bai amsata ba ya karasa ficewa, haka nadiya ta zabga tagumi tana tunanin makomar rayuwarta.

  Cikin wannan hali suka yi sati biyu koda yaushe idan kabeer yasa kafa yabar gidan da safe baya dawowa sai karfe 10 nadare, tunda akayi bikinsu basu taba zama da nadiya sunyi hira na minti daya ba, sai dai idan har fad'a zaiyi mata,

Koda yaushe ita kuma tana kokarin nuna kulawarta agareshi domin tana yimasa waya taji yanda ya wuni wani lokacin ya dauka yana tsaki wani lokacin kuma yaki dauka,

Tana zaune taci kwalliya amma gani daya zaka yimata kasan cewar akwai abinda yake damunta yaya kabeer ya shigo, lokacin karfe 5 na yamma,

Abinci ta kawo masa ya zauna ya danci ya tashi ya shiga cikin daki, wayarsa da yabari afalon ne tasoma kara nan nadiya ta dauka da niyyar kai mishi ai kuwa sai gashi ya fito, fautar wayar yayi yafara yimata fada,

"Uban waye yasaki ki daukar min waya? Danme zaki taba min waya? Karki kuskura nasake ganinki kin taba min wayata..."

Yana gamawa yawuce fuuhhhhh yakoma daki mintuna kadan yazo yawuceta yabar gidan daga nan bai sake dawowaba sai 11 nadare.

  Haka rayuwar nadiya da yaya kabeer ta kasance koda yaushe babu dadi, tsakaninta dashi babu kulawa, babu magana mai dadi, babu tausasawa, babu nuna soyayya babu komai, kullum cikin yimata fada yake, idan ta kirashi awaya ya hauta da fada idan bataci abinciba ta jirashi yazo yayita fada da haka har suka debe watanni biyu da bikinsu, mai karatu acikin watanni biyun nan nadiya bata da wani labari mai dadi wanda zata bayar dangane da rayuwar aure, ko kadan bata san dadin aureba sai sabanin haka,

Kasancewar bata cikin kwanciyar hankali yasata ta rame ta kanjale domin kullum cikin kuka da damuwa take, lokacin da takai kimanin watanni uku babu kadan mama tazo mata,

Tsayawa mama kawai tayi tana kallonta saboda ganin irin yanda ta rame ta zabge, ita mama da atunaninta zata zo ta iske nadiya tayi kiba ta hada jiki amma sai taga sabanin haka sai dai batayi magana ba domin tayi zaton ko dai har nadiyan tasoma laulayi ne,

Nan mama ta kusan wuni agidan amma abin mamaki harta taho bata ga kabeer ya koma ba,duk sai bata kawo komai aranta ba saboda tasan irin soyayyar dake tsakanin kabeer din da nadiya.

  Acikin satin da mama tazo itama maman su yaya kabeer tazo taga gida, sosai mamanshi keson nadiya domin har kayan makulashe ta kawo mata irinsu alawar madara, gullisuwa, tsami gaye,yashin madina, hanjin ligidi da sauransu haka ta kawo matasu cikin leda viva,bata jima dayawa ba tatafi,

Tun daga nan nadiya bata sake ganin kowa nagida ba sai dai mamanta kullum tana kiranta su gaisa da ita sannan ta hadata da kannenta su gaisa haka kuma duk satin duniya sai mama ta turo mata kati na dubu daya ko na 750 dama shi yaya kabeer babu ruwanshi da batun wayarta ko wani abin bukatarta kullum da safe da zarar ya kada rigarsa yafita sai dare.

  Haka nadiya taci gaba da zaman hakuri zaman da babu komai acikinsa face damuwa da bacin rai har ta debe watanni shida lokacin dai ya kaita gidansu sau daya haka itama yakaita tagaida mamanta sau daya daga nan sai dai su waleeda suzo mata a weekend su wuni shiyasa har burin zuwan weekend take domin abba yana kawo mata su, duk ranar da suka zo wuni take cikin farin ciki shiyasa bata barinsu su tafi sai dare yayi.

Cikin wannan yanayi nadiya tafara amai wanda abisa dukkan alamu na laulayin cikine, kabeer ko ajikinsa babu abinda ya dameshi,

Lokacin ma da ya shigo ya isketa tana aman kallonta yayi yace,

"Ke cikine dake ko?"

Daga nan bai sake magana ba yayi tafiyarsa yawuce ciki yabarta tana faman kwarara amai,

Satinta biyu tana zazzabi atafe daga karshe zazzabin ya kwantar da ita, nan ya dauketa yakaita asibiti likita yana dubata yace cikine da ita na wata biyu, ga mamakinta sai taga yana murna harda bawa likita tukwici, daga nan ya daukota suka dawo gida bayan ya biya ta kasuwa ya siyo mata fruits su lemo da ayaba da makamantansu,

Tunda suka dawo gida kuma yarage fada da masifar da yake yimata yafara dan kula da ita, komai tace tana so baya k'i shiyasa lokaci kankani tayi kyau tayi kiba saboda hankalinta ya dan fara kwanciya,

Yanzu abu dayane ke damunta shine wayar da yaya kabeer ya tsiri yi acikin kowanne dare, koda yaushe ta bude idonta sai tajiyoshi yana waya, kusan kwana yake yana yin waya da wadda bata san ko wacece ba, bayaga haka kuma ko wacce safiya ta Allah sai yafita da sassafe yana tafiya inda bata san ko inaneba,

Wannan dalilinne yasa yau ta daura aniyar tambayarshi inda yake zuwa, tana kwance afalo ya shigo lokacin misalin karfe 9 nasafe, akusa da ita ya zauna nan ta yunkura ta tashi dakyar,

"Yaya kabeer wai ina kake zuwa da sassafe ne?"

"Nadiya shamsiyya nake zuwa nake kaiwa makaranta, baki Santa ba ko? Yar kanwar mamace to shine aka kawota gidanmu dan tayi karatu.."

"Amma yaya kabeer fisabilillahi sai kaine zaka rinka kaita makarantar? Kullum fa da karfe 6 kake fita, haba dan Allah, gaskiya nidai wannan abun yana bata min rai.."

Mikewa yayi yashiga cikin daki baiyi magana ba, nan ran nadiya ya baci domin tagane cewar tsakaninsa da shamsiyyan akwai wani abu, tana ganinsa yazo ya sake fita bayan yayi shirin office,

Tagumi ta zabga tayi shiru, wayarta ce ta soma kara nan ta dauka taga bakuwar number ce,

"Assalamu akaikum"

Daga daya bangaren aka amsa sallamarta tana jin muryarsa ta ganeshi ba kowa bane face yaya Kamal dan gidan wan mama wanda suke zaune agarin tofa....

*_Ummi Shatu_*
[7/17, 8:23 AM] Ummi A'isha: *MIJINA SIRRINA...!*🌹
      _(Labarin k'auna)_


   *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_

® *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of experts writers)_

*20*

~~~Nan suka fara gaisawa cikeda zumudi domin rabonta dashi tun tana JSS lokacin da yake zuwa gidansu hutu, Allah ya hada jininta dashi sosai,

Hirace ta barke tsakaninsu nan yafara tambayarta ya rayuwar auren nasu, tsakaninta da yaya kamal babu boye boye sannan ayanda take jin zuciyarta sam bazata ji sauki ba har sai ta amayar da abinda ke cikin zuciyarta dan haka ta fara zayyane masa damuwarta tun daga washe garin ranar da aka kawota har yau,

Hakuri kamal yafara bata cikeda tausayinta,

"Nadiya kiyi hakuri, ki dauki Dangana sannan kisani komai na duniya mai wucewa ne sannan babu abinda yake dawwama a duniya,

Dadi baya taba dawwama haka shima wuya da damuwa basa dawwama,

Farin ciki baya dawwama kamar yanda bakin ciki baya taba dawwama,

Kisakawa ranki cewar ibada kike yi domin zaman aure ibadane haka kuma abayan kowanne tsanani to da akwai sauki haka alqur'ani ya sanar damu,

Kiyi hakuri kici gaba da yiwa mijinki biyayya karki gaji sannan karki daina,

Kidauka cewar bautar Allah kikeyi sannan aljanna kike nema kin san kuwa samun aljanna ba abune mai sauki ba dole sai ansha wahala sai anshiga damuwa,

Haka kuma kamar yadda baki taba fadawa kowa ba saini to kiyi hakuri kisake daurewa karki fadawa kowa wannan maganar domin sirrinki ne keda mijinki ta shafa kinji..?"

"Naji yaya kamal.."

Nan yaci gaba da bata shawarwari akalla sai da suka shafe awanni yana yimata nasiha gamida bata hakuri tareda tausar zuciyarta akan taci gaba da jurewa gamida hakuri,

Ko ba komai taji dadin shawarwarin da yaya kamal yabata tareda bada hakuri domin idan abu yana damunka kasamu wanda ka fadawa har yabaka hakuri dadi kakeji koda bai baka komai ba.

  Nan taci gaba da rainon cikin da yake tareda ita shikuma kabeer bai fasa halinshi na daka sammako ya fita da sassafe ba wai shamsiyya yar uwarsa yake kaiwa makaranta sannan ga wayar dare da ya kware akanta kamar gwauro marar iyali,

Juyi nadiya tayi nan tajiyo muryarsa kasa kasa afalo yana maganganu ahankali wanda daga ji wayar tasa yake yi, yunkurawa tayi ta tashi dakyar ta fita falon nan ta hangoshi akwance cikin kujera kamar ba dareba sai wayarsa yake,

"Yaya kabeer..."

Juyowa yayi tareda katse wayar yana cewa "i will call you back latter..."

Tashi yayi yana kallon nadiya,tamkar zai hauta da duka haka yayi yabude babin masifa,

"Menene? Acikin tsohon daren nan zakizo kina kirana, me zanyi miki? Ba tambayarki nakeba, nace uban me zanyi miki, wannan wanne irin rashin mutunci ne, da rana ba abar mutum ya hutaba haka da daddare ma baza abarshi ya hutaba.."

"Haba yaya kabeer, yanzu me yayi zafi da zaka fara fada da daddaren nan, ni idan nice na bata maka rai kayi hakuri, gani nayi abinda kake yi bai daceba sannan bai kamata ba, ya za ayi ni ka baroni acikin daki sannan kazo nan ka zauna kana waya, idan wayarka zakayi ai sai kayi da rana tun kana waje amma bawai sai kadawo cikin gida..."

Katseta yayi cikin wata irin tsawa,

"Ke karki kuskura kiyi min iyayi kin gane ko,kece ma zaki tsara min yanda zan rinka gudanar da rayuwata?, saboda gaki uwata ko? To bari kiji.."

Bai karasa ba yaga ta rike cikinta tareda faduwa akasa nan da nan yaga tafara murkususu jini yana bin kafafuwanta, iya tashi hankalinsa kam ya tashi domin yana mutukar son cikin dake jikinta nan yaji ya shiga rudu,

Dakyar ya iya kokarin daukarta yakaita cikin mota yanufi asibiti da ita wanda yake can gaba dasu kadan,

Cikin wani daki aka sata nan likitoci suka yi cahhhh akanta suna dubata daga karshe dai sunaji suna gani babu yanda zasu iya cikin dake jikinta ya zube,

Kabeer yayi mutukar bakin ciki lokacin da yaji cewar cikin ya zube, nan ya zauna acikin asibitin har gari ya waye sannan ya tafi gidansu yaje ya sanarwa da mamanshi, hankali tashe mama ta bishi zuwa asibitin bayan tasaka A'isha ta hadowa nadiya tea da sauran kayan karyawa,

Tunda mamanshi taje itace take kula da nadiya domin tana mutukar sonta ko kadan bata son damuwarta shiyasa kullum cikin yimata hidima take, karfe 8 daidai yaje ya dauko A'isha da shamsiyya zuwa asibitin ita nadiya sai yau taga shamsiyyan ma domin akomai tasan tayiwa shamsiyyan nisa amma da yake namiji ba dan goyo bane shine yaya kabeer yake neman fifita shamsiyyan akanta,

Nan sukayi mata sannu mama ta taimaka mata ta tashi ta hada mata tea sannan ga farfesun kayan ciki da soyayyen kwai ta bata taci takoma ta kwanta, sai da wurin karfe 11 sannan yaje gidansu nadiya yafada nan mama ta rude ta shirya tatafi asibitin amma da taje sai taji hankalinta ya kwanta saboda tasamu maman kabeer na kula da nadiya,ita nadiyan ma lokacin bacci takeyi, nan su mama suka shiga gaisawa tareda jajantawa juna.

Kwanan nadiya takwas a asibitin aka sallameta bayan anyi mata wankin ciki nan Maman kabeer tace maman nadiya tatafi da ita Gida tunda likitoci sunce ta dan samu hutu banda aikin wahala, ita abinda yasa bazata tafi da nadiya gidanta ba tasan idan sunje bazata sake kamar gidansu ba amma idan gidansu ne zatafi sakewa,

Nan mama ta yarda suka tafi da nadiya bayan sun biya ta gidanta sunje sun daukar mata kayan sawarta, komawar nadiya gida ba karamin kwanciyar hankali ta samuba domin cikin sati biyu tayi kiba tayi kyau jikinta ya dawo saboda mamanta tana mutukar kula da ita sannan babu abinda takeyi daga kallo sai ko taci abinci ta kwanta, gashi yanzu babu damuwa babu bacin rai bp dinta ma da yahau ya sauka, babu abinda takeyi ko mama tagani tana aiki idan tace zata tayata sai taki, sai dai ta zauna tayita kallo idan kuma su husna sun dawo daga makaranta suyita hira suna sata dariya domin suna nan har yanzu da halinsu na sa'insa, idan yamma tayi kuma abba yadawo to bazai shigo haka ba sai ya tahowa da nadiya wani abu na kwadayi, yana dawowa kuma zasu tattara su koma falonsa hatta abinci tare za ahadu aci, ana ci ana hira shiyasa nadiya ta kwammace gara rayuwar gida sau dubu data gidan aurenta.

  Yaya kabeer ma yana zuwa dubata lokaci zuwa lokaci sannan yana kawo mata abubuwan bukata, har nadiya ta Karaci zamanta agidansu tafara shirin komawa gidanta bata taba fadawa mama matsalarta ba ko kuma damuwarta ba duk da tasan tana cikin damuwa sannan babu wanda yafi cancanta da jin damuwarta sama da mahaiifiyarta amma bata taba sanar da mama ba, tasan ita babu wani jin dadi ko farin ciki kwaya daya da zata iya fada wanda tasamu agidan aure to ina dadin ma yake auren dako amarci ba asamu anyiba matsalolin rayuwa suka taru suka yimasa illa,

Watanta biyu agidansu sannan takoma gidan yaya kabeer bayan abba ya bata kudi har dubu hamsin yasaka mata acikin account yace idan tana da damuwa sai ta dauka tayi amfani dashi,

Tunda ta koma gidan yaya kabeer yasamu abinda yayi missing shikenan suka dawo yar gidan jiya, baya zama agida idan yafita tun safe sai dare, baya zama suyi hira da ita to bai zauna agidan bama bare suyi hirar, wayar cikin dare, fita sassafe kai shamsiyya makaranta, ita dai nadiya kawai zaman hakuri take nan tasake rarramewa, damma dai yaya kamal dan uwanta yana kiranta awaya koda yaushe yana kwantar mata da hankali, da haka kwanaki masu yawa suka shude nan tasake samun wani cikin tafara laulayi ganin haka yasa yaya kabeer fara bata yar kulawa saboda cikin da yake jikinta,

Kamar wancan lokacin yanzun ma tayi kiba tayi kyau saboda hankalinta ya dan kwanta, sannan kuma fitar da yakeyi sassafe zuwa kai shamsiyya makaranta ahalin yanzu yadaina wayar tsakar daren ce dai har yanzu yanayi,

Daga mamanta har Maman shi kowacce na taka muhimmiyar rawa wurin ganin sun bata kulawa domin kullum cikin yimata aiken kayan dadi suke, haka kawai zataga mamanshi ta aiko A'isha kanwarshi ta kawo mata abun kwadayi, ko kuma taga Amira kanwarta mama ta aikota, yanzu bata da damuwa sosai saboda shima yaya kabeer din yarage masifar da yake yimatay,nan hankalinta ya kwanta tayi kyau sosai kowa yaganta yanzu yasan tasamu kwanciyar hankali sabanin da.

  Cikinta yagirma ya shiga wata bakwai sannan yayi kato kamar wadda zata haifi yaya hudu, karfe biyu da rabi na dare ta farka tana jin yunwa da kishin ruwa dama tunda cikin yafara girma take tashin dare cin abinci da shan ruwa, yaya kabeer tajiyo afalo yana aikin wayar tasa ta dare kamar yadda ya saba, nan ta yunkura dakyar ta fita falon ranta idan yayi dubu ya baci take zufa ta rufeta jininta yahau mutuka saboda dama ta dade da kamuwa da hawan jini nan hawan jinin ya tashi jikinta yahau rawa,

"Yaya kabeer..."

Takira sunanshi cikin radadin ciwo, saurin tashi yayi ya katse wayar amma kafin yakarasa wurinta har ta sulale ta yanke jiki tafadi cikin daukewar numfashi.......


*_Ummi Shatu_*