Thursday 26 January 2017

RUWAN KASHE GOBARA...! 75

*RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_


  *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_

   aishaummi.blogspot.com

   *_75_*

~~~Tsayawa Lamido yayi a k'ofar gidan yana jiran fitowar yaya hussain amma acikin zuciyarsa yana jin radadin maganganun da yaya hussain ya jefeshi dasu,

A fusace yaya hussain ya shiga cikin gidan inda ikhlas ke tsaye a tsakar gida ta kasa karasawa cikin falon domin maganganun da yaya hussain ya fadawa lamido sunyi mutukar girgiza ta,

Tana jin tahowarshi tayi saurin shigewa cikin falon kamar an jehota,

"Lafiya..?" Farida matarshi ta fada tana kallon ikhlas,

"Wannan yarinyar ban san cewa shashasha bace sai yau, in banda rashin hankali meye nata na bin shi..?" Yaya hussain ya fada yana huci,

"Kayi hakuri dai dan Allah, abi komai a sannu" farida tace dashi cikin sanyayyiyar murya, juyawa yayi ya fita a fusace, nan farida ta juyo tana duban ikhlas,

"Haba ikhlas meyasa zaki bishi kamar baki da wayo? Kefa kike bani labarin irin wulakancin da yayi miki agidanshi, meyasa bazaki tsaya kija ajinki ba a matsayinki na ya mace ai ya kamata ace kinja masa aji bawai daga baki hakuri zaki hakura ba.."

Kallonta ikhlas tayi idonta cike da kwalla "anty farida ya kuke so nayi ne dan Allah? Yazo ya bani hakuri kuma har kuka ya tisani agaba yana yimin idan ban kulashi ba yaya zanyi..."

"Babu wani kuka kedai kawai kinyi missing din mijinki shiyasa kika bishi"

Juyawa tayi ta fita domin tasan idan ta zauna farida ta rinka tsokanarta kenan. Lamido kam yana nan tsaye har yaya hussain ya fito ya wuceshi fuskarshi babu fara'a, bin bayanshi lamido yayi har zuwa gidan ammi, babu alamun tsoro ko fargaba yasaka kai ya shiga cikin gidan, yaya hussain na zama shikuma yana shigowa, mikewa tsaye yaya hussain yayi yana huci,

"Waye ya baka izinin shigo mana cikin gida? Ka gaggauta fita mana daga gida"

Ammi ce ta fito daga cikin daki saboda jiyo maganar Hussain da tayi,

"Hussain me yake faruwa ne...?"

Ganin lamido da tayi ya sata janyo tabarma ta fara kokarin shimfida masa tana cewa,

"Bako muka yine?"

"Ammi karki saurareshi domin ikhlas ba zata koma gidanshi ba"

"Haba hussain ya isa haka mana, kayi hakuri muji abinda ke tafe dashi"

Zama Lamido yayi amma ranshi ya fara baci da maganganun da Hussain ke yaba masa, zama ammi tayi suka fara gaisawa da lamido, hussain kuwa har lokacin sai masifa yake zubawa har hajiya ta shigo dauke da sadiq a hannunta ai sadiq yana ganin lamido ya fara tsalle kamar zai fado,

Karbarshi lamido yayi yana murmushi, zama hajiya tayi ammi ta fara kora mata jawabin abinda ya faru nan hajiya tace to sai abawa lamido matarsa su tafi tunda gashi har yazo  biko da kansa, fada hussain ya tayar shi a lallai ikhlas ba zata koma gidan lamido ba, da kyar hajiya da ammi suka shawo kanshi suka bashi hakuri ya yarda cewar ikhlas zata koma amma da sharadin ko yaya lamido ya sake yi mata wulakanci ko ya fifita matanshi akanta to ta dawo gida kuma wallahi ba zata koma ba har abada, akan wannan sharadin hussain ya amince da komawar ikhlas, suna nan zaune bayan an sasanta ikhlas ta shigo sai rrrakubewa take yi domin kunyar su ammi da hajiya take yi saboda bin lamido da tayi,

"Ke idan zaki shigo ki shigo ba ason munafurci, kizo ki tattara kayanki kibi mijinki kuje can ku karata" hajiya tace da ita cikin daga murya,

"Hajiya munafurcin me nayi kuma" ikhlas ta fadi cikeda kunya bayan ta shiga cikin dakin,kukan da sadiq ya fara yine saboda ganinta da yayi ya sata juyawa ta karbeshi daga hannun lamido ta shige cikin dakin ammi ta zauna tana yiwa sadiq magana,

"Saddiqun abba jiya na barka acikin maraici ko? Allah sarki yarona kayi hakuri abbanka ne ya jawo maka..."

Tana daga cikin daki tana jinsu suka gama sasantawa da zummar gobe lamido zai zo su tafi, karar shigowar text massage cikin wayarta taji tana dubawa taga lamido ne ya turo mata sako kamar haka,

   _pretty shine ko sallama babu ko? To ai ni ban sallameki ba kika tafi amma shikenan  na tafi,ki shirya da wuri gobe domin da sassafe zamu tafi, sai kinji wayata nagode da kulawar da kika bani, I know zanyi mutukar missing dinki yau, i love you....!_

Murmushi tayi bayan ta gama karanta sakon nashi, sadiq ta kwantar ta tashi ta fara harhada kayanta tana shiryawa acikin akwati har ammi da hajiya suka shigo,

"Kin dawo?" Hajiya ta tambayeta tana rike habarta,

"Ke yarnan wato shine kika bi mijinki ko sallama babu ko? Anata kokarin a kwato miki yancinki amma ke bakya gani, to ai shikenan sai ki shirya ku tafi dama ba mune muka je muka daukoki ba kece nan kika zo da kafarki"

Shiru ikhlas tayi bata tanka ba domin ta fuskanci cewar duk abinda zata fada musu ba ganewa zasu yi ba saboda basu san tsakaninta da lamido ba, sam ba zata iya jurar ganinshi cikin damuwa ba mutukar tanada ikon rabashi da damuwar,itadai ammi na jinsu batace dasu komai ba har hajiya ta gama bambaminta ta tafi,

Har tsawon lokaci ikhlas na zaune ta kasa daga kanta ta kalli ammi, murmushi ammi tayi tai gyaran murya tasoma yi mata fad'a akan idan ta koma yola ta yi hakuri ta zauna da kishiyoyinta da mijinta lafiya sannan ta zama mai rufe sirrin mijinta acikin kowanne lokaci.

Kammala shirya kayanta tayi wuri daya, acikin daren yaya hussain ya kawo mata abdallah domin suyi sallama, k'in bin yaya Hussain abdallah yayi yace awurin ikhlas zai kwana hakan kuwa akayi domin rungumeshi tayi ajikinta ahaka suka yi bacci.

Washe gari da safe da wuri ta tashi ta shirya ta shirya sadiq sannan ta shirya abdallah domin akwai school yaya hussain zai zo ya kaishi, su abdallah na tafiya lamido yazo, agurguje suka gaggaisa dasu ammi ya dauki kayan ikhlas da sadiq ya fita, sallama tayiwa su ammi da dukkan mutanen gidan ta fita wurin lamido, dakyar ta lallabashi ya kaita gidan yayunta tayi sallama da matansu ta fito, nan suka dauki hanyar yola lamido sai hira yake yi mata.

Karfe 2 na rana suka shiga cikin garin yola, kai tsaye gida suka wuce, itace ta fara shiga cikin gidan nan ta ganshi babu alamun mutum aciki tasan duk yanda aka yi fadila da ihsan suna makaranta, bedroom dinta ta karasa lamido yana biye da ita dauke da kayanta a hannunshi, ajiye mata kayan yayi yai mata sallama ya fita domin yanada abubuwa da yawa wadanda zai gudanar a kamfaninshi,

Zama ikhlas tayi ta gyara part dinta sosai ta shiga kitchen ta dafa jalop din taliya da kifi, tana kokarin fitowa daga cikin kitchen din fadila ta shigo rikeda littattafai a hannunta,

"Ashe kun dawo? Sannu da zuwa" fadila tace da ita tana yayyatsina fuska,

"Ehh mun dawo, barka da dawowa" ikhlas ta bata amsa daga nan kowa ya wuce sashensa ba tare da sun kara yin wata magana ba.

Tunda ikhlas ta shiga daki bata sake fitowa ba har dare yayi, shi kanshi lamidon shima bai samu damar dawowa gidan ba sai bayan sallar magrib, kansa tsaye dakinsa ya shiga yayi wanka ya fito gashi wata irin yunwa yake ji domin rabonshi da abinci tun safe, salla yayi ya nufi dakin ikhlas,

Tana zaune agefen gado tana turawa yaya Hussain text lamido ya shiga cikin dakin, kamshin turarenshi kawai taji ta gane zuwanshi, dago da kanta tayi ta kalleshi, yasha kyau cikin farar t shirt wacce aka rubuta home boy ajiki da bakin wando,

Murmushi ya sakar mata ya karasa cikin dakin ya je kusa da sadiq yana kallonshi,

"Saddiquna har kayi bacci? Yau ban ganka sosai ba aiki ya rikeni"

Dagowa yayi daga kallon sadiq ya kalli ikhlas, "pretty yunwa nake ji kinada abinci ki bani?"

"Akwai abinci bari na baka" tashi tayi taje ta zubo mishi abincin data dafa da rana tazo ta ajiye mishi, hannunta ya rike yana kallon fuskarta,

"Tsaya ki bani mana..."

Zama tayi ta soma bashi a baki yana ci amma sai shhhhh yake yi alamun akwai yaji a abincin,

"Abban sadiq gaskiya ka fiya raki da yawa naga babu wani yaji sosai"

"Haka dai kika ce" ya bata amsa yana wasa da zoben dake sanye cikin dan yatsanta,

Murmushi tayi ta dauko masa juice ta tsiyaya masa,makale kafada yayi,

"Ni dai wallahi na bakinki nake so.." Lallabashi taci gaba dayi domin ta fuskanci lamido tamkar yaro yake sai da rarrashi, da wayo da dabara ta samu ya gama cin abincin yasha juice,

Cikinta ya shafo, "ki rage cin yaji kinga kinada juna biyu.."

Saurin kallonshi tayi sai kuma tayi murmushi, "wanne irin juna biyu kuma?" Ta tambayeshi,

"Wanda kike dashi"

Yabata amsa yana matsawa kusa da ita, murmushi tayi ta rike hannunshi,

"To wallahi ni banida wani juna biyu saboda dazun nan ma..."

Bude idonshi yayi sosai yana kallonta "dazu me? Bako kika yi? To wallahi kice masa ya koma,wai ma tsaya yanzu kina nufin duk wannan zazzabin da kika rink'a goga min dama ba ciki ne dake ba...?"

"Na goga maka zazzabi kodai ka goga min..?"

"Kece kike goga min ni kar kiyi min sharri, wallahi kece.."

Dariya tayi ta fara tattare kayan da yaci abincin ta fita, binta yayi ya kama hannunta zuwa babban falo inda su fadila suke zaune suna kallo,

Agefensu ya zauna ita kuma ta zauna a gefenshi, dukkaninsu sunsha kwalliya musamman ma ihsan wacce taci gayu cikin riga da wando,

Bayani yayi musu sosai akan su zauna lafiya banda fada banda daukar magana sannan girki zasu rinka yin kwana daya daya, nan ya tambayesu ko akwai mai magana acikinsu sukace babu amma yau ya kwana a dakin ikhlas in yaso washe gari sai afara rabon kwanan, ba karamin dadi lamido yaji ba,

Tashi ikhlas tayi ta koma dakinta ta barshi zaune awurinsu fadila suna hira, wanka ta shiga tayi ta fito ta zauna ta fara tsarawa fuskarta kwalliya, jagira, jan baki, kwalli, lip glow, powder, mascara, eye shadow duk sai da ta sakawa fuskarta cikin wannan daren domin tana son yau ta burge lamido, turare kuwa kamar barinshi akayi ajikinta domin ko wanne bangare na jikinta kamshine ke tashi na daban, wata light purple din rigar bacci ta saka mai dan siririn hannu wacce bata da nauyi,gashi ta gyara gashin kanta ta tufkeshi wuri guda,

Tana zaune tana feeding din sadiq ya shigo cikin dakin yana sanye cikin kayan bacci riga da wando,

"Woww..." Yafadi ahankali bayan ya zauna a kusa da ita,

"Kinyi kyau pretty na sai kace wacce zata je dinner"

Murmushi ikhlas tayi ta fara masa idanuwanta batare da tayi magana ba nan yaji ya sake rikicewa, da kanshi ya dauki sadiq ya kaishi cikin dan karamin gadonshi ya kwantar dashi ya koma gareta.

Tun misalin karfe 8 ikhlas tayi wanka ta shirya tayi kwalliya sosai ta saka wata koriyar atamfa tasha dauri bayan ta game dukkan sassan jikinta da turare, gefen lamido taje ta zauna ta kwantar da kanta akan gadon bayanshi,

Hannunta ya riko ya soma kissing dinshi har lokacin idonshi a rufe yake,

"Abban sadiq ka tashi.."

"Me zanyi idan na tashi?" Ya tambayeta idonshi arufe,

"Shirin office"

"Ba yanzu ba"

"Sai yaushe?" Ta sake tambayarshi,

"Sai 10 lokacin nagama ganawa dake"

Murmushi tayi ta matsa hannunshi "to ka tashi kaje ka gaisa da matanka karsu fita school baku gaisa ba.."

Sai a lokacin ya bude idonshi domin har ga Allah ya manta dasu saboda idan yana tare da ikhlas dinshi mantawa yake yi da kowacce mace,

Zaune ya tashi yana binta da kallo domin ba karamin kyau tayi ba tasha ado sosai gashi har sarka da awarwaro ta saka,

"Kinyi kyau, zo muje ki rakani mu gaisa da su ihsan"

Tashi tayi ta bishi suka fita ita ihsan har ta tafi makaranta lokacin ita kuma fadila ta fito zata tafi, yana jikin ikhlas rungume da ita suka gaisa da fadila ta juya ta wuce ta fita, dakinshi suka shiga acan suka sake bude sabon babin soyayya.

Sai karfe 11 lamido ya samu ya fita wanda ahakan ma da kyar ya iya daurewa ya fice, amma koda yaje office dinma bini bini sai ya kirata awaya yaji muryarta, har ya taso daga office ya dawo gida hankalinsa na ga ikhlas, yau kam a dakin fadila yake dan haka duk sai ikhlas taji ta shiga damuwa amma haka ta daure suka yi sallama dashi ya tafi. Daren ranar daga shi har ita basuyi baccin kirki ba gari yana wayewa ya nufi dakinta tana zaune tana yiwa sadiq wanka tasha kwalliya sosai cikin shadda orange colour wacce tasha dinkin sirfani,dagowa tayi ta kalleshi tana murmushi,

"Abban sadiq har ka tashi?"

Kiss yayi mata a kumatu yace "dama nazo ganinku ne tunda kuna lafiya shikenan"

"Lafiya lau muke abban sadiq"

Mikewa yayi ya fita ya nufi dakinshi.

Haka rayuwarsu taci gaba da tafiya cikin farin ciki da kulawa da juna domin ikhlas tana mutukar kulawa da lamido kullum cikin yi masa kwalliya take kala kala, gaba daya ta gama mamaye zuciyarsa da soyayyarta domin duk cikin matanshi yafi sonta yafi kaunarta kowanne lokaci cikin begenta yake,

Tafiya ce ta kamashi zuwa abuja nan ya fara ahiri yaso ya tafi da ikhlas amma taki saboda bata son matanshi su gane tafisu fada awurinshi ko kuma yafi fifitata akansu, tsayawa yayi yaki koda kallonta ya juyar da kanshi yana kallon wani wuri ita ikhlas sai hakan da yayi ya sake burgeta tana tsaye ta jingina da bangon falonta kallonshi kawai take yi yasha kyau sosai cikin jar t shirt mai zagayayyen wuya da bakin wando ya daura jan agogo da jan takalmi sauciki ga kuma lollypop a bakinshi yana sha,sunfi minti biyar a tsaye amma yaki kallonta, juyawa yayi ya shiga cikin dakinta ya yiwa sadiq kiss a kumatunshi ya fito, sai da yazo daf da ita zai gifta tayi saurin shiga gabanshi ta rungumeshi, wata sanyayyiyar ajiyar zuciya ya sauke amma sai bai nuna mata yaji dadin hakan da tayi ba,

"Haba handsome kar kayi fushi dani mana.."

Maimakon ya bata amsa saima kawar da kanshi da ya sake yi,jin yaki kulata ya sata kai masa kiss a bakinshi bayan ta cire lollypop din da yake tsotsa, yana jinta tana kissing din lips dinshi amma bai mayar mata da martani ba, dauke bakinta tayi daga kan nashi tana zumbura baki,

"Mantawa ma nayi nai kissing din bakinka bayan bani kadai ce dashi ba"

Nan dinma shirun yayi mata bai tanka ba amma acikin zuciyarshi dariya yake yi mata sakamakon abinda yaji ta fadi,

"Koda yake ya na iya, babu yanda zanyi dole haka zan daure.."

Bakinshi ta sake kamawa tafara kissing dinshi har na tsawon wani lokaci kafin ta sakeshi, duk wannan abun da tayi da fushi suka rabu dashi saboda yana jin haushin bata bishi ba amma ita sam bata so wannan tafiyar tashi ba domin jikinta yayi sanyi kwatankwacin irin sanyin da yayi ranar da Abubakar sadiq zai bar duniya....



*_Ummi Shatu_*

RUWAN KASHE GOBARA.. 74

*RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_


   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_

aishaummi.blogspot.com

   *_74_*

~~~Cikin sauri ya kamo hannunta ya janyota baya yana murmushi, ita dinma murmushin take yi tana kallonshi,

"Ke ba zaki yi wankan bane?"

Kai ta daga masa,

"Why?" Ya tambayeta yana kokarin saka kwayar idonshi cikin nata,

"Ni nayi wanka dazu.." Ta bashi amsa, sakin hannunta yayi ya wuce cikin bathroom din yana murmushi kamar wanda aka yiwa bushara da aljannah yau haka yake jinsa,

Bakin gadon ta koma ta zauna tana jiran fitowarsa amma kuma duk atakure take domin bata taba zuwa hotel ba sai yau gashi ta taho su ammi basu sani ba yanzu idan ta koma ko me zatace musu?

Tana cikin wannan tunanin Lamido ya fito ya zauna a bayanta, juyawa tayi ta kalleshi yanda ya matseta sosai,

"Ya akayi?" Ta tambayeshi,

"Kije kiyi wankan" ya mayar mata da amsa,

"Ikon Allah nifa nace maka nayi wanka.."

"Allah sai kinyi wankan nan kinji dai nace Allah" ya fada tareda fara kokarin cire hijabin jikinta,

"Yau naji ikon Allah, wai jikinka ko nawa?"

"Nawa" ya fada yana kashe mata idonshi guda daya,

"Ko ni zanyi miki?"

"A'a nagode" ta fada da sauri,

"To tashi kije kiyi"

Mikewa tayi ba dan taso ba ta nufi cikin toilet din tana cicccije lebe domin bata so,

Rigarshi yasaka ya fita yaje motarshi ya dauko yar karamar jakar kayanshi da ya zo da ita ya koma dakin, towel ya ciro ya nufi bathroom din domin kai mata,

"Abban sadiq nidai gaskiya ka fita..." Ta fada cikin shagwaba,

"Towel fa na kawo miki, shikenan na fita" lankaye mata towel din yayi ya fita ya koma cikin dakin ya kishingida akan gado yana sauraren fitowarta.

Ta dade acikin bathroom din kafin ta fito tana daure da towel dinshi tasaka hijab tana rikeda kayanta a hannu, bakin gadon taje ta zauna tana goge jikinta da dan kwalin kayanta,

Tashi zaune Lamido yayi ya matsa kusa da ita,

"Kawo na tayaki.."

Kafin tayi magana har ya cire hijabin jikinta, bakin gashin kanta ya zubawa idanu yana kallo domin yana mutukar burgeshi, man shafawarshi ta dauka zata shafa nan yayi caraf ya rike hannunta,

"Ai cemiki nayi zan tayaki"

Kwace man yayi ya fara shafa mata ita kam duk yabi yasata jin kunya wanda shi kanshi ya lura da hakan domin kunyarta tana mutukar sake rikitashi, ahankali ya sake matsawa jikinta yace,

"Shy girl..."

Kasa jiyowa tayi domin salon shafa man da yake yi mata dabanne.

  Tashi zaune tayi tana bin dakin da kallo amma babu lamido, kasa kunne tayi sosai nan ta jiyo motsinshi a toilet, murmushi tayi ta shafi kumatunta da hannunta domin yau Lamido ya sakata tayi rayuwa mai dadi mai dauke da tsantsar nishadi aciki wacce bata taba yin irinta ba,

Motsin fitowarshi taji ta dan daga idonta ta kalleshi daga shi sai farin gajeren wando yana sharce ruwan dake jikin sumar kanshi,saurin dauke idonta tayi daga kanshi,

Gaban dressing mirror ya karasa ya fara kokarin shiryawa, babu zato ya hangota ta cikin mirror din tana zaune ta kura masa ido tana kallonshi,

"Yaya dai?" Ya tambayeta bayan shima ya bude manyan idanuwanshi akanta, girgiza masa kai tayi alamun babu komai,

"To ki tashi mana, ko kina sone na fita na barki ke daya a dakin?"

Cikin sauri ta tashi tana girgiza masa kanta ta shiga cikin bathroom tayi wanka ta fito lokacin Lamido yana tsaye yana salla, wuceshi tayi taje ta bude jakar kayanshi ta dauko farar t shirt mai gajeren hannu da blue din jeans ta saka ta dauki hijab itama ta fara sallar, domin sun makara sosai,

Lokacin data idar Lamido yana zaune ya kafeta da ido yana jiran ta, koda tayi sallama suna hada ido ya sakar mata hararar wasa,

"Kinga kin sakani banyi salla akan lokaci ba..."

Dauke kanta tayi daga kallonshi ta mike tsaye, "tunda ni na hanaka to kazo ka mayar dani gida saboda karka rasa ta isha kamar yadda ka rasa ta magrib"

Tashin shima yayi ya isa inda take ya kamo hannuwanta yana kallon kyakkyawan bakinta mai dauke da fararen hakora sosol hadida zagayayyen lips jajaye,

"Idan kin tafi dawa zan zauna?"

"Sai ka zauna kai kadai"

Murmushi yayi ya dauki key din motarshi  yaja hannunta,

"Kayan nan sunyi miki kyau ko nabar miki ne?" Ya fada cikin zolaya,

"Babu wani kyau kawai dai kana zugani ne" tace dashi a shagwabance,

"To naji kibari yanzu muje mu dawo inyaso sai kiyi min shagwabar"

Langabe kai tayi "kai abban sadiq dan Allah nidai na yafe"

Kokarin rufe dakin yayi bayan sun fita ya juyo yana kallonta "see you idle girl har kin fara k'orafi?"

"Ehh na yarda, nidai ka kaini gida yanzu nasan sadiq yana can ya tashi yanata kuka.."

"Babu wani kuka,bayan kin koya masa shan madara saboda rashin kirki"

Hannunta ya kama suka fita har inda ya ajiye motarshi ta shiga suka tafi wurin cin abinci,

"Preety ya kamata ki sakeni haka fa saboda gaskiya na jigatu"

Kawar da kanta tayi gefe "ni na isa na rikeka kai da kake da mata 3 kana niyyar yin ta hudu"

Murmushi yayi ya riko hannunta "inada mata uku amma kuma duk ciki nafi ji dake..."

"Ni kar kayi min dadin baki, idan kaje wurin wata matar taka ma nasan abinda yafi haka zaka fada mata"

Shiru yayi yaci gaba da driving din yana nazarinta, a dan zaman da suka yi dashi ya fuskanci cewar ita mace ce mai kishi sai dai tanada kokarin boye hakan amma wani lokacin kuma yanayin furucinta yana bayyanar da abinda yake cikin zuciyarta,

Murmushi mai sanyaya zuciya yayi "kenan tana kishina?" Ya tambayi kanshi acikin zuciyarshi,

"Pretty kenan! Ko da wasa karki sakawa ranki cewar zan iya fadawa wata mace maganganu masu kama da wanda na fada miki, ki yarda dani"

Daidai lokacin yayi packing agefen titi daidai wani wurin sayar da abinci da kayan makulashe,

"Ki zauna anan bari naje na siyo mana abinci"

"Ka taho min da ice cream"

Bakinta ya kaiwa kiss yana fadin "ai wannan bakin naki yana son ice cream,duk abinda kike so yau zan samo miki domin banida abinda zan iya biyanki farin cikin da kika bani"

Hannunta ta saka ta kare fuskarta, zame hannun nata yayi, "kin san how many marks kika samu?"

Sake rufe fuskarta tayi tana murmushi, ahankali ya rada mata,

"100/100 is your marks"

"Dan Allah ka bari" tafada tana murmushi,

"Shikenan tunda bakya so" yace da ita ahankali,

Sakinta yayi ya fita  daga cikin motar yana murmushi kamar yadda itama take murmushi, binshi tayi da kallo har ya shige cikin shagon, mintuna kadan sai gashi ya fito rikeda ledodi, cikin motar ya shiga ya mika mata kayan, ledar farko ta bude shawarma ta gani,hannu yasa ya gutsuro ya mika mata,

"Bude bakinki kici pretty" yace da ita yana kokarin saka mata acikin bakinta,

Bude bakinta tayi tareda lumshe idonta take Lamido yafara ciyar da ita abincin har sai da kawar ta kanta tace ta koshi, dayar ledar ya bude ya ciro robar ice cream ya mika mata,

"Zaki sha..?"

Cikin sauri ta daga masa kai alamun ehhh, mika mata yayi ya tsaya yana kallonta yana jiran yaga ta fara sha, tunanin ranar da suka sha soyayya a yola ya fara yi ranar da ya kaisu shan ice cream sam ya kasa mantawa da wannan ranar domin ranace wacce bazai iya mantawa da ita ba, gaba daya ya gama shagala da tunanin da yake yi babu zato yaji ikhlas na shafe masa kumatunshi da ice cream din hannunta,

Murmushi yayi ya riketa "kema kina son mu maimaita yanayin rannan ko? Nima ina bukatar hakan pretty, ina son hakan ta sake faruwa.."

Kankameta yayi suka fara kokawa ya kwace ice cream din hannunta ya fara Shafa mata a fuskarta, sun dade acikin wannan yanayi kafin daga bisani ya dauketa zuwa inda suka fito suna zuwa kan gado ya fada ya kwanta ya lumshe  idanuwanshi. Kusa dashi taje ta zauna tana jin sonshi yana yawo acikin jinin jikinta,

"Abban sadiq bacci zakayi?"

Mirginawa yayi ya zagayeta da hannuwanshi yana kallonta,

"Bacci yanzu? Ai yau babu baccin da zanyi"

"Idonka biyu zaka zauna har gari ya waye?" Ta jefa masa tambayar bayan ta zuba masa ido,

"Zancen kike so amma harke a rashin baccin" ya fada tareda sakinta ya koma ya kwanta, bathroom ta tashi ta shiga saboda batayi sallar isha ba, yana daga kwance yana kallonta har ta idar da sallar tazo kusa dashi ta kwanta.

  Har gari ya waye rana ta fito lamido yana manne da ita ya kasa matsawa daga kusa da ita ga wani dan malalacin zazzabi dake rinjayarshi daga shi har ita jikinsu ya danyi zafi kadan, wurin karfe 8 ya mike ya shiga toilet  yayi wanka ya fito ya shirya ya saka coffee colour din t shirt da bakin wando, agefen gadon ya zauna ya kunna wayarshi yana duba sakonnin da suka shigo wanda na matanshi ne sai xahar wacce itama ta turo nata sakon,

Ahankali ikhlas ta bude idonta tana kallonshi, ba karamin kyau taga yayi mata ba domin fuskarshi har wani irin sheki take yi,

Zuba mishi ido tayi taci gaba da kallon kyakkyawar fuskarshi wanda ko kadan shi bai san tana yi ba domin duk a tunaninshi bacci take yi, kallonshi take yi sosai acikin zuciyarta tana tunanin duk wanda yaga lamido kallon saurayi zai yi masa domin babu wanda zaiyi tunanin cewar yayi auren fari balle har ace yana da mata uku,

Babu zato caraf suka hada ido dashi, saurin dauke kanta tayi daga kallonshi, ahankali ya matsa kusa da ita ya kamo hannunta yana kallon beautiful face dinta,

"Pretty kin tashi?" Yace da ita yana bin kunshin dake tafin hannunta da kallo,

Kai ta daga masa alamun ehh,

"Sorry ki tashi kiyi wanka"

Juyar da kanta ta sake yi, murmushi yayi ya juyo da fuskarta da hannunshi,

"Ki tashi ki shirya, kinji?"

"To ka daina kallo na" ta fada cikin shagwaba,

"To na daina" ya bata amsa bayan ya juya mata baya, tashi tayi ta sauka daga kan gadon tana cewa,

"Kar ka bude idonka please"

Hannuwanshi ya saka ya rufe idanuwanshi yana murmushi,

"Bazan bude ba wuce"

Sauri tayi ta shige cikin toilet din tana lekenshi, sai da yaji shigarta cikin bathroom din sannan ya bude fuskarshi, order din abinci yayi musu kafin ta fito daga wanka har an kawo abincin ajiyewa yayi ya fita domin sauran wayoyinshi suna cikin mota.

Fitowa tayi ta shirya ta fesa turarenshi ta saka kayanta, dan karamin tsaki tayi domin babu kayan kwalliya ita kuma tana son tayiwa lamido kwalliya domin ya taba fada mata cewar yana so,

Ranta a dan bace tana daura dankwali ya shigo cikin dakin, agabanta ya tsaya yana kallonta,

"Menene ya batawa pretty na rai?"

"Babu komai" ta bashi amsa tana girgiza masa kanta,

"Da akwai pretty, ki fada min ko inyi miki kuka.."

Hakan da yafada ne ya sata yin murmushin da bata shirya ba "saboda baka gajiya da kuka?"

Ta tambayeshi tana murmushi, hannunta ya kama zuwa wurinda ya ajiye musu abincin da aka kawo musu,

"Naji dadi tunda na ganki kina murmushi, kici gaba da yin murmushi domin yana yiwa fuskarki kyau"

Wani murmushin ta sake yi, zaunar da ita yayi ya bude breakfast din ya fara bata a baki, shine ya ciyar da ita har sai da ta koshi sannan ta tashi ta koma kan gadon ta kwanta babu jimawa bacci ya dauketa, komawa yayi ya zauna ya dan ci abincin kadan sannan ya koma kusa da ita ya kwanta, wunin ranar sunyi shine manne da juna har sai da yamma tayi sannan ta saka masa darun sai ya mayar da ita gida, ba dan yaso ba haka ya dauketa suka nufi gidan,

Yana rike da hannunta yana driving da daya hannun sai labari yake bata wai wani lokaci sunyi dare shida bash police suka taresu zasu tafi dasu police station wasu karnuka suka fito sunfi guda talatin nan police din suka baje suka barsu shida bash,

Dariya sosai ikhlas take yi domin labarin yayi mutukar bata dariya sannan bata taba tsammanin lamido ya iya surutu haka ba sai yau domin baya yi, har sukaje kofar gidan yaya hassan dariyar take yi, amma sai dariyar tata ta yanke saboda ganin yaya Hussain tsaye fuskarshi a murtuke sai muzurai yake yi,

Jiki asabule ta fito daga cikin motar, shima lamido fitowar yayi ya nufi yayan nata wanda daga gani babu tambaya domin kamarsu kusan daya da ita,

"Ke daga ina kike? A ina kika kwana? Dama ashe ke sokuwace shashasha ban sani ba?" Yaya Hussain ya fada cikin masifa,

"Um yaya dama, dama abban sadiq ne yazo shine...." Ta bashi amsa cikin rawar murya,

"Shine kika bishi ko? Saboda bakida zuciya baki san ciwon kanki ba, mutumin da ya gama wulakantaki agidanshi ya nuna miki cewar bai damu dake ba shine har yanzu zai zo yayi miki dadin baki ki yarda? To bari in fada miki kiji irin wadannan yan duniyar sun wuce duk inda kike tunani kuma wallahi ko bana nan ban yarda ki sake kulashi ba balle har ki bishi kinji dai na fada miki, dalla wuce ciki kibar nan ko na bugeki.."

Juyawa yayi ga lamido wanda yake tsaye yana kallonshi,

"Kai kuma ina mai gargadinka da ka fita daga harkar yarinyar nan domin muddin ina raye to bazata koma gidanka ba garama ka saketa ka daina batawa kanka lokaci idan kuma baka saketa ta dadin rai ba to kasani zaka saketa ta cikin bacin rai da tashin hankali"

Yana kaiwa nan ya juya yabar lamido awurin ya nufi cikin gida wurin ikhlas....!



_*Ummi Shatu*_

RUWAN KASHE GOBARA.. 74

*RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_


   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_

aishaummi.blogspot.com

   *_74_*

~~~Cikin sauri ya kamo hannunta ya janyota baya yana murmushi, ita dinma murmushin take yi tana kallonshi,

"Ke ba zaki yi wankan bane?"

Kai ta daga masa,

"Why?" Ya tambayeta yana kokarin saka kwayar idonshi cikin nata,

"Ni nayi wanka dazu.." Ta bashi amsa, sakin hannunta yayi ya wuce cikin bathroom din yana murmushi kamar wanda aka yiwa bushara da aljannah yau haka yake jinsa,

Bakin gadon ta koma ta zauna tana jiran fitowarsa amma kuma duk atakure take domin bata taba zuwa hotel ba sai yau gashi ta taho su ammi basu sani ba yanzu idan ta koma ko me zatace musu?

Tana cikin wannan tunanin Lamido ya fito ya zauna a bayanta, juyawa tayi ta kalleshi yanda ya matseta sosai,

"Ya akayi?" Ta tambayeshi,

"Kije kiyi wankan" ya mayar mata da amsa,

"Ikon Allah nifa nace maka nayi wanka.."

"Allah sai kinyi wankan nan kinji dai nace Allah" ya fada tareda fara kokarin cire hijabin jikinta,

"Yau naji ikon Allah, wai jikinka ko nawa?"

"Nawa" ya fada yana kashe mata idonshi guda daya,

"Ko ni zanyi miki?"

"A'a nagode" ta fada da sauri,

"To tashi kije kiyi"

Mikewa tayi ba dan taso ba ta nufi cikin toilet din tana cicccije lebe domin bata so,

Rigarshi yasaka ya fita yaje motarshi ya dauko yar karamar jakar kayanshi da ya zo da ita ya koma dakin, towel ya ciro ya nufi bathroom din domin kai mata,

"Abban sadiq nidai gaskiya ka fita..." Ta fada cikin shagwaba,

"Towel fa na kawo miki, shikenan na fita" lankaye mata towel din yayi ya fita ya koma cikin dakin ya kishingida akan gado yana sauraren fitowarta.

Ta dade acikin bathroom din kafin ta fito tana daure da towel dinshi tasaka hijab tana rikeda kayanta a hannu, bakin gadon taje ta zauna tana goge jikinta da dan kwalin kayanta,

Tashi zaune Lamido yayi ya matsa kusa da ita,

"Kawo na tayaki.."

Kafin tayi magana har ya cire hijabin jikinta, bakin gashin kanta ya zubawa idanu yana kallo domin yana mutukar burgeshi, man shafawarshi ta dauka zata shafa nan yayi caraf ya rike hannunta,

"Ai cemiki nayi zan tayaki"

Kwace man yayi ya fara shafa mata ita kam duk yabi yasata jin kunya wanda shi kanshi ya lura da hakan domin kunyarta tana mutukar sake rikitashi, ahankali ya sake matsawa jikinta yace,

"Shy girl..."

Kasa jiyowa tayi domin salon shafa man da yake yi mata dabanne.

  Tashi zaune tayi tana bin dakin da kallo amma babu lamido, kasa kunne tayi sosai nan ta jiyo motsinshi a toilet, murmushi tayi ta shafi kumatunta da hannunta domin yau Lamido ya sakata tayi rayuwa mai dadi mai dauke da tsantsar nishadi aciki wacce bata taba yin irinta ba,

Motsin fitowarshi taji ta dan daga idonta ta kalleshi daga shi sai farin gajeren wando yana sharce ruwan dake jikin sumar kanshi,saurin dauke idonta tayi daga kanshi,

Gaban dressing mirror ya karasa ya fara kokarin shiryawa, babu zato ya hangota ta cikin mirror din tana zaune ta kura masa ido tana kallonshi,

"Yaya dai?" Ya tambayeta bayan shima ya bude manyan idanuwanshi akanta, girgiza masa kai tayi alamun babu komai,

"To ki tashi mana, ko kina sone na fita na barki ke daya a dakin?"

Cikin sauri ta tashi tana girgiza masa kanta ta shiga cikin bathroom tayi wanka ta fito lokacin Lamido yana tsaye yana salla, wuceshi tayi taje ta bude jakar kayanshi ta dauko farar t shirt mai gajeren hannu da blue din jeans ta saka ta dauki hijab itama ta fara sallar, domin sun makara sosai,

Lokacin data idar Lamido yana zaune ya kafeta da ido yana jiran ta, koda tayi sallama suna hada ido ya sakar mata hararar wasa,

"Kinga kin sakani banyi salla akan lokaci ba..."

Dauke kanta tayi daga kallonshi ta mike tsaye, "tunda ni na hanaka to kazo ka mayar dani gida saboda karka rasa ta isha kamar yadda ka rasa ta magrib"

Tashin shima yayi ya isa inda take ya kamo hannuwanta yana kallon kyakkyawan bakinta mai dauke da fararen hakora sosol hadida zagayayyen lips jajaye,

"Idan kin tafi dawa zan zauna?"

"Sai ka zauna kai kadai"

Murmushi yayi ya dauki key din motarshi  yaja hannunta,

"Kayan nan sunyi miki kyau ko nabar miki ne?" Ya fada cikin zolaya,

"Babu wani kyau kawai dai kana zugani ne" tace dashi a shagwabance,

"To naji kibari yanzu muje mu dawo inyaso sai kiyi min shagwabar"

Langabe kai tayi "kai abban sadiq dan Allah nidai na yafe"

Kokarin rufe dakin yayi bayan sun fita ya juyo yana kallonta "see you idle girl har kin fara k'orafi?"

"Ehh na yarda, nidai ka kaini gida yanzu nasan sadiq yana can ya tashi yanata kuka.."

"Babu wani kuka,bayan kin koya masa shan madara saboda rashin kirki"

Hannunta ya kama suka fita har inda ya ajiye motarshi ta shiga suka tafi wurin cin abinci,

"Preety ya kamata ki sakeni haka fa saboda gaskiya na jigatu"

Kawar da kanta tayi gefe "ni na isa na rikeka kai da kake da mata 3 kana niyyar yin ta hudu"

Murmushi yayi ya riko hannunta "inada mata uku amma kuma duk ciki nafi ji dake..."

"Ni kar kayi min dadin baki, idan kaje wurin wata matar taka ma nasan abinda yafi haka zaka fada mata"

Shiru yayi yaci gaba da driving din yana nazarinta, a dan zaman da suka yi dashi ya fuskanci cewar ita mace ce mai kishi sai dai tanada kokarin boye hakan amma wani lokacin kuma yanayin furucinta yana bayyanar da abinda yake cikin zuciyarta,

Murmushi mai sanyaya zuciya yayi "kenan tana kishina?" Ya tambayi kanshi acikin zuciyarshi,

"Pretty kenan! Ko da wasa karki sakawa ranki cewar zan iya fadawa wata mace maganganu masu kama da wanda na fada miki, ki yarda dani"

Daidai lokacin yayi packing agefen titi daidai wani wurin sayar da abinci da kayan makulashe,

"Ki zauna anan bari naje na siyo mana abinci"

"Ka taho min da ice cream"

Bakinta ya kaiwa kiss yana fadin "ai wannan bakin naki yana son ice cream,duk abinda kike so yau zan samo miki domin banida abinda zan iya biyanki farin cikin da kika bani"

Hannunta ta saka ta kare fuskarta, zame hannun nata yayi, "kin san how many marks kika samu?"

Sake rufe fuskarta tayi tana murmushi, ahankali ya rada mata,

"100/100 is your marks"

"Dan Allah ka bari" tafada tana murmushi,

"Shikenan tunda bakya so" yace da ita ahankali,

Sakinta yayi ya fita  daga cikin motar yana murmushi kamar yadda itama take murmushi, binshi tayi da kallo har ya shige cikin shagon, mintuna kadan sai gashi ya fito rikeda ledodi, cikin motar ya shiga ya mika mata kayan, ledar farko ta bude shawarma ta gani,hannu yasa ya gutsuro ya mika mata,

"Bude bakinki kici pretty" yace da ita yana kokarin saka mata acikin bakinta,

Bude bakinta tayi tareda lumshe idonta take Lamido yafara ciyar da ita abincin har sai da kawar ta kanta tace ta koshi, dayar ledar ya bude ya ciro robar ice cream ya mika mata,

"Zaki sha..?"

Cikin sauri ta daga masa kai alamun ehhh, mika mata yayi ya tsaya yana kallonta yana jiran yaga ta fara sha, tunanin ranar da suka sha soyayya a yola ya fara yi ranar da ya kaisu shan ice cream sam ya kasa mantawa da wannan ranar domin ranace wacce bazai iya mantawa da ita ba, gaba daya ya gama shagala da tunanin da yake yi babu zato yaji ikhlas na shafe masa kumatunshi da ice cream din hannunta,

Murmushi yayi ya riketa "kema kina son mu maimaita yanayin rannan ko? Nima ina bukatar hakan pretty, ina son hakan ta sake faruwa.."

Kankameta yayi suka fara kokawa ya kwace ice cream din hannunta ya fara Shafa mata a fuskarta, sun dade acikin wannan yanayi kafin daga bisani ya dauketa zuwa inda suka fito suna zuwa kan gado ya fada ya kwanta ya lumshe  idanuwanshi. Kusa dashi taje ta zauna tana jin sonshi yana yawo acikin jinin jikinta,

"Abban sadiq bacci zakayi?"

Mirginawa yayi ya zagayeta da hannuwanshi yana kallonta,

"Bacci yanzu? Ai yau babu baccin da zanyi"

"Idonka biyu zaka zauna har gari ya waye?" Ta jefa masa tambayar bayan ta zuba masa ido,

"Zancen kike so amma harke a rashin baccin" ya fada tareda sakinta ya koma ya kwanta, bathroom ta tashi ta shiga saboda batayi sallar isha ba, yana daga kwance yana kallonta har ta idar da sallar tazo kusa dashi ta kwanta.

  Har gari ya waye rana ta fito lamido yana manne da ita ya kasa matsawa daga kusa da ita ga wani dan malalacin zazzabi dake rinjayarshi daga shi har ita jikinsu ya danyi zafi kadan, wurin karfe 8 ya mike ya shiga toilet  yayi wanka ya fito ya shirya ya saka coffee colour din t shirt da bakin wando, agefen gadon ya zauna ya kunna wayarshi yana duba sakonnin da suka shigo wanda na matanshi ne sai xahar wacce itama ta turo nata sakon,

Ahankali ikhlas ta bude idonta tana kallonshi, ba karamin kyau taga yayi mata ba domin fuskarshi har wani irin sheki take yi,

Zuba mishi ido tayi taci gaba da kallon kyakkyawar fuskarshi wanda ko kadan shi bai san tana yi ba domin duk a tunaninshi bacci take yi, kallonshi take yi sosai acikin zuciyarta tana tunanin duk wanda yaga lamido kallon saurayi zai yi masa domin babu wanda zaiyi tunanin cewar yayi auren fari balle har ace yana da mata uku,

Babu zato caraf suka hada ido dashi, saurin dauke kanta tayi daga kallonshi, ahankali ya matsa kusa da ita ya kamo hannunta yana kallon beautiful face dinta,

"Pretty kin tashi?" Yace da ita yana bin kunshin dake tafin hannunta da kallo,

Kai ta daga masa alamun ehh,

"Sorry ki tashi kiyi wanka"

Juyar da kanta ta sake yi, murmushi yayi ya juyo da fuskarta da hannunshi,

"Ki tashi ki shirya, kinji?"

"To ka daina kallo na" ta fada cikin shagwaba,

"To na daina" ya bata amsa bayan ya juya mata baya, tashi tayi ta sauka daga kan gadon tana cewa,

"Kar ka bude idonka please"

Hannuwanshi ya saka ya rufe idanuwanshi yana murmushi,

"Bazan bude ba wuce"

Sauri tayi ta shige cikin toilet din tana lekenshi, sai da yaji shigarta cikin bathroom din sannan ya bude fuskarshi, order din abinci yayi musu kafin ta fito daga wanka har an kawo abincin ajiyewa yayi ya fita domin sauran wayoyinshi suna cikin mota.

Fitowa tayi ta shirya ta fesa turarenshi ta saka kayanta, dan karamin tsaki tayi domin babu kayan kwalliya ita kuma tana son tayiwa lamido kwalliya domin ya taba fada mata cewar yana so,

Ranta a dan bace tana daura dankwali ya shigo cikin dakin, agabanta ya tsaya yana kallonta,

"Menene ya batawa pretty na rai?"

"Babu komai" ta bashi amsa tana girgiza masa kanta,

"Da akwai pretty, ki fada min ko inyi miki kuka.."

Hakan da yafada ne ya sata yin murmushin da bata shirya ba "saboda baka gajiya da kuka?"

Ta tambayeshi tana murmushi, hannunta ya kama zuwa wurinda ya ajiye musu abincin da aka kawo musu,

"Naji dadi tunda na ganki kina murmushi, kici gaba da yin murmushi domin yana yiwa fuskarki kyau"

Wani murmushin ta sake yi, zaunar da ita yayi ya bude breakfast din ya fara bata a baki, shine ya ciyar da ita har sai da ta koshi sannan ta tashi ta koma kan gadon ta kwanta babu jimawa bacci ya dauketa, komawa yayi ya zauna ya dan ci abincin kadan sannan ya koma kusa da ita ya kwanta, wunin ranar sunyi shine manne da juna har sai da yamma tayi sannan ta saka masa darun sai ya mayar da ita gida, ba dan yaso ba haka ya dauketa suka nufi gidan,

Yana rike da hannunta yana driving da daya hannun sai labari yake bata wai wani lokaci sunyi dare shida bash police suka taresu zasu tafi dasu police station wasu karnuka suka fito sunfi guda talatin nan police din suka baje suka barsu shida bash,

Dariya sosai ikhlas take yi domin labarin yayi mutukar bata dariya sannan bata taba tsammanin lamido ya iya surutu haka ba sai yau domin baya yi, har sukaje kofar gidan yaya hassan dariyar take yi, amma sai dariyar tata ta yanke saboda ganin yaya Hussain tsaye fuskarshi a murtuke sai muzurai yake yi,

Jiki asabule ta fito daga cikin motar, shima lamido fitowar yayi ya nufi yayan nata wanda daga gani babu tambaya domin kamarsu kusan daya da ita,

"Ke daga ina kike? A ina kika kwana? Dama ashe ke sokuwace shashasha ban sani ba?" Yaya Hussain ya fada cikin masifa,

"Um yaya dama, dama abban sadiq ne yazo shine...." Ta bashi amsa cikin rawar murya,

"Shine kika bishi ko? Saboda bakida zuciya baki san ciwon kanki ba, mutumin da ya gama wulakantaki agidanshi ya nuna miki cewar bai damu dake ba shine har yanzu zai zo yayi miki dadin baki ki yarda? To bari in fada miki kiji irin wadannan yan duniyar sun wuce duk inda kike tunani kuma wallahi ko bana nan ban yarda ki sake kulashi ba balle har ki bishi kinji dai na fada miki, dalla wuce ciki kibar nan ko na bugeki.."

Juyawa yayi ga lamido wanda yake tsaye yana kallonshi,

"Kai kuma ina mai gargadinka da ka fita daga harkar yarinyar nan domin muddin ina raye to bazata koma gidanka ba garama ka saketa ka daina batawa kanka lokaci idan kuma baka saketa ta dadin rai ba to kasani zaka saketa ta cikin bacin rai da tashin hankali"

Yana kaiwa nan ya juya yabar lamido awurin ya nufi cikin gida wurin ikhlas....!



_*Ummi Shatu*_

RUWAN KASHE GOBARA.. 74

*RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_


   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_

aishaummi.blogspot.com

   *_74_*

~~~Cikin sauri ya kamo hannunta ya janyota baya yana murmushi, ita dinma murmushin take yi tana kallonshi,

"Ke ba zaki yi wankan bane?"

Kai ta daga masa,

"Why?" Ya tambayeta yana kokarin saka kwayar idonshi cikin nata,

"Ni nayi wanka dazu.." Ta bashi amsa, sakin hannunta yayi ya wuce cikin bathroom din yana murmushi kamar wanda aka yiwa bushara da aljannah yau haka yake jinsa,

Bakin gadon ta koma ta zauna tana jiran fitowarsa amma kuma duk atakure take domin bata taba zuwa hotel ba sai yau gashi ta taho su ammi basu sani ba yanzu idan ta koma ko me zatace musu?

Tana cikin wannan tunanin Lamido ya fito ya zauna a bayanta, juyawa tayi ta kalleshi yanda ya matseta sosai,

"Ya akayi?" Ta tambayeshi,

"Kije kiyi wankan" ya mayar mata da amsa,

"Ikon Allah nifa nace maka nayi wanka.."

"Allah sai kinyi wankan nan kinji dai nace Allah" ya fada tareda fara kokarin cire hijabin jikinta,

"Yau naji ikon Allah, wai jikinka ko nawa?"

"Nawa" ya fada yana kashe mata idonshi guda daya,

"Ko ni zanyi miki?"

"A'a nagode" ta fada da sauri,

"To tashi kije kiyi"

Mikewa tayi ba dan taso ba ta nufi cikin toilet din tana cicccije lebe domin bata so,

Rigarshi yasaka ya fita yaje motarshi ya dauko yar karamar jakar kayanshi da ya zo da ita ya koma dakin, towel ya ciro ya nufi bathroom din domin kai mata,

"Abban sadiq nidai gaskiya ka fita..." Ta fada cikin shagwaba,

"Towel fa na kawo miki, shikenan na fita" lankaye mata towel din yayi ya fita ya koma cikin dakin ya kishingida akan gado yana sauraren fitowarta.

Ta dade acikin bathroom din kafin ta fito tana daure da towel dinshi tasaka hijab tana rikeda kayanta a hannu, bakin gadon taje ta zauna tana goge jikinta da dan kwalin kayanta,

Tashi zaune Lamido yayi ya matsa kusa da ita,

"Kawo na tayaki.."

Kafin tayi magana har ya cire hijabin jikinta, bakin gashin kanta ya zubawa idanu yana kallo domin yana mutukar burgeshi, man shafawarshi ta dauka zata shafa nan yayi caraf ya rike hannunta,

"Ai cemiki nayi zan tayaki"

Kwace man yayi ya fara shafa mata ita kam duk yabi yasata jin kunya wanda shi kanshi ya lura da hakan domin kunyarta tana mutukar sake rikitashi, ahankali ya sake matsawa jikinta yace,

"Shy girl..."

Kasa jiyowa tayi domin salon shafa man da yake yi mata dabanne.

  Tashi zaune tayi tana bin dakin da kallo amma babu lamido, kasa kunne tayi sosai nan ta jiyo motsinshi a toilet, murmushi tayi ta shafi kumatunta da hannunta domin yau Lamido ya sakata tayi rayuwa mai dadi mai dauke da tsantsar nishadi aciki wacce bata taba yin irinta ba,

Motsin fitowarshi taji ta dan daga idonta ta kalleshi daga shi sai farin gajeren wando yana sharce ruwan dake jikin sumar kanshi,saurin dauke idonta tayi daga kanshi,

Gaban dressing mirror ya karasa ya fara kokarin shiryawa, babu zato ya hangota ta cikin mirror din tana zaune ta kura masa ido tana kallonshi,

"Yaya dai?" Ya tambayeta bayan shima ya bude manyan idanuwanshi akanta, girgiza masa kai tayi alamun babu komai,

"To ki tashi mana, ko kina sone na fita na barki ke daya a dakin?"

Cikin sauri ta tashi tana girgiza masa kanta ta shiga cikin bathroom tayi wanka ta fito lokacin Lamido yana tsaye yana salla, wuceshi tayi taje ta bude jakar kayanshi ta dauko farar t shirt mai gajeren hannu da blue din jeans ta saka ta dauki hijab itama ta fara sallar, domin sun makara sosai,

Lokacin data idar Lamido yana zaune ya kafeta da ido yana jiran ta, koda tayi sallama suna hada ido ya sakar mata hararar wasa,

"Kinga kin sakani banyi salla akan lokaci ba..."

Dauke kanta tayi daga kallonshi ta mike tsaye, "tunda ni na hanaka to kazo ka mayar dani gida saboda karka rasa ta isha kamar yadda ka rasa ta magrib"

Tashin shima yayi ya isa inda take ya kamo hannuwanta yana kallon kyakkyawan bakinta mai dauke da fararen hakora sosol hadida zagayayyen lips jajaye,

"Idan kin tafi dawa zan zauna?"

"Sai ka zauna kai kadai"

Murmushi yayi ya dauki key din motarshi  yaja hannunta,

"Kayan nan sunyi miki kyau ko nabar miki ne?" Ya fada cikin zolaya,

"Babu wani kyau kawai dai kana zugani ne" tace dashi a shagwabance,

"To naji kibari yanzu muje mu dawo inyaso sai kiyi min shagwabar"

Langabe kai tayi "kai abban sadiq dan Allah nidai na yafe"

Kokarin rufe dakin yayi bayan sun fita ya juyo yana kallonta "see you idle girl har kin fara k'orafi?"

"Ehh na yarda, nidai ka kaini gida yanzu nasan sadiq yana can ya tashi yanata kuka.."

"Babu wani kuka,bayan kin koya masa shan madara saboda rashin kirki"

Hannunta ya kama suka fita har inda ya ajiye motarshi ta shiga suka tafi wurin cin abinci,

"Preety ya kamata ki sakeni haka fa saboda gaskiya na jigatu"

Kawar da kanta tayi gefe "ni na isa na rikeka kai da kake da mata 3 kana niyyar yin ta hudu"

Murmushi yayi ya riko hannunta "inada mata uku amma kuma duk ciki nafi ji dake..."

"Ni kar kayi min dadin baki, idan kaje wurin wata matar taka ma nasan abinda yafi haka zaka fada mata"

Shiru yayi yaci gaba da driving din yana nazarinta, a dan zaman da suka yi dashi ya fuskanci cewar ita mace ce mai kishi sai dai tanada kokarin boye hakan amma wani lokacin kuma yanayin furucinta yana bayyanar da abinda yake cikin zuciyarta,

Murmushi mai sanyaya zuciya yayi "kenan tana kishina?" Ya tambayi kanshi acikin zuciyarshi,

"Pretty kenan! Ko da wasa karki sakawa ranki cewar zan iya fadawa wata mace maganganu masu kama da wanda na fada miki, ki yarda dani"

Daidai lokacin yayi packing agefen titi daidai wani wurin sayar da abinci da kayan makulashe,

"Ki zauna anan bari naje na siyo mana abinci"

"Ka taho min da ice cream"

Bakinta ya kaiwa kiss yana fadin "ai wannan bakin naki yana son ice cream,duk abinda kike so yau zan samo miki domin banida abinda zan iya biyanki farin cikin da kika bani"

Hannunta ta saka ta kare fuskarta, zame hannun nata yayi, "kin san how many marks kika samu?"

Sake rufe fuskarta tayi tana murmushi, ahankali ya rada mata,

"100/100 is your marks"

"Dan Allah ka bari" tafada tana murmushi,

"Shikenan tunda bakya so" yace da ita ahankali,

Sakinta yayi ya fita  daga cikin motar yana murmushi kamar yadda itama take murmushi, binshi tayi da kallo har ya shige cikin shagon, mintuna kadan sai gashi ya fito rikeda ledodi, cikin motar ya shiga ya mika mata kayan, ledar farko ta bude shawarma ta gani,hannu yasa ya gutsuro ya mika mata,

"Bude bakinki kici pretty" yace da ita yana kokarin saka mata acikin bakinta,

Bude bakinta tayi tareda lumshe idonta take Lamido yafara ciyar da ita abincin har sai da kawar ta kanta tace ta koshi, dayar ledar ya bude ya ciro robar ice cream ya mika mata,

"Zaki sha..?"

Cikin sauri ta daga masa kai alamun ehhh, mika mata yayi ya tsaya yana kallonta yana jiran yaga ta fara sha, tunanin ranar da suka sha soyayya a yola ya fara yi ranar da ya kaisu shan ice cream sam ya kasa mantawa da wannan ranar domin ranace wacce bazai iya mantawa da ita ba, gaba daya ya gama shagala da tunanin da yake yi babu zato yaji ikhlas na shafe masa kumatunshi da ice cream din hannunta,

Murmushi yayi ya riketa "kema kina son mu maimaita yanayin rannan ko? Nima ina bukatar hakan pretty, ina son hakan ta sake faruwa.."

Kankameta yayi suka fara kokawa ya kwace ice cream din hannunta ya fara Shafa mata a fuskarta, sun dade acikin wannan yanayi kafin daga bisani ya dauketa zuwa inda suka fito suna zuwa kan gado ya fada ya kwanta ya lumshe  idanuwanshi. Kusa dashi taje ta zauna tana jin sonshi yana yawo acikin jinin jikinta,

"Abban sadiq bacci zakayi?"

Mirginawa yayi ya zagayeta da hannuwanshi yana kallonta,

"Bacci yanzu? Ai yau babu baccin da zanyi"

"Idonka biyu zaka zauna har gari ya waye?" Ta jefa masa tambayar bayan ta zuba masa ido,

"Zancen kike so amma harke a rashin baccin" ya fada tareda sakinta ya koma ya kwanta, bathroom ta tashi ta shiga saboda batayi sallar isha ba, yana daga kwance yana kallonta har ta idar da sallar tazo kusa dashi ta kwanta.

  Har gari ya waye rana ta fito lamido yana manne da ita ya kasa matsawa daga kusa da ita ga wani dan malalacin zazzabi dake rinjayarshi daga shi har ita jikinsu ya danyi zafi kadan, wurin karfe 8 ya mike ya shiga toilet  yayi wanka ya fito ya shirya ya saka coffee colour din t shirt da bakin wando, agefen gadon ya zauna ya kunna wayarshi yana duba sakonnin da suka shigo wanda na matanshi ne sai xahar wacce itama ta turo nata sakon,

Ahankali ikhlas ta bude idonta tana kallonshi, ba karamin kyau taga yayi mata ba domin fuskarshi har wani irin sheki take yi,

Zuba mishi ido tayi taci gaba da kallon kyakkyawar fuskarshi wanda ko kadan shi bai san tana yi ba domin duk a tunaninshi bacci take yi, kallonshi take yi sosai acikin zuciyarta tana tunanin duk wanda yaga lamido kallon saurayi zai yi masa domin babu wanda zaiyi tunanin cewar yayi auren fari balle har ace yana da mata uku,

Babu zato caraf suka hada ido dashi, saurin dauke kanta tayi daga kallonshi, ahankali ya matsa kusa da ita ya kamo hannunta yana kallon beautiful face dinta,

"Pretty kin tashi?" Yace da ita yana bin kunshin dake tafin hannunta da kallo,

Kai ta daga masa alamun ehh,

"Sorry ki tashi kiyi wanka"

Juyar da kanta ta sake yi, murmushi yayi ya juyo da fuskarta da hannunshi,

"Ki tashi ki shirya, kinji?"

"To ka daina kallo na" ta fada cikin shagwaba,

"To na daina" ya bata amsa bayan ya juya mata baya, tashi tayi ta sauka daga kan gadon tana cewa,

"Kar ka bude idonka please"

Hannuwanshi ya saka ya rufe idanuwanshi yana murmushi,

"Bazan bude ba wuce"

Sauri tayi ta shige cikin toilet din tana lekenshi, sai da yaji shigarta cikin bathroom din sannan ya bude fuskarshi, order din abinci yayi musu kafin ta fito daga wanka har an kawo abincin ajiyewa yayi ya fita domin sauran wayoyinshi suna cikin mota.

Fitowa tayi ta shirya ta fesa turarenshi ta saka kayanta, dan karamin tsaki tayi domin babu kayan kwalliya ita kuma tana son tayiwa lamido kwalliya domin ya taba fada mata cewar yana so,

Ranta a dan bace tana daura dankwali ya shigo cikin dakin, agabanta ya tsaya yana kallonta,

"Menene ya batawa pretty na rai?"

"Babu komai" ta bashi amsa tana girgiza masa kanta,

"Da akwai pretty, ki fada min ko inyi miki kuka.."

Hakan da yafada ne ya sata yin murmushin da bata shirya ba "saboda baka gajiya da kuka?"

Ta tambayeshi tana murmushi, hannunta ya kama zuwa wurinda ya ajiye musu abincin da aka kawo musu,

"Naji dadi tunda na ganki kina murmushi, kici gaba da yin murmushi domin yana yiwa fuskarki kyau"

Wani murmushin ta sake yi, zaunar da ita yayi ya bude breakfast din ya fara bata a baki, shine ya ciyar da ita har sai da ta koshi sannan ta tashi ta koma kan gadon ta kwanta babu jimawa bacci ya dauketa, komawa yayi ya zauna ya dan ci abincin kadan sannan ya koma kusa da ita ya kwanta, wunin ranar sunyi shine manne da juna har sai da yamma tayi sannan ta saka masa darun sai ya mayar da ita gida, ba dan yaso ba haka ya dauketa suka nufi gidan,

Yana rike da hannunta yana driving da daya hannun sai labari yake bata wai wani lokaci sunyi dare shida bash police suka taresu zasu tafi dasu police station wasu karnuka suka fito sunfi guda talatin nan police din suka baje suka barsu shida bash,

Dariya sosai ikhlas take yi domin labarin yayi mutukar bata dariya sannan bata taba tsammanin lamido ya iya surutu haka ba sai yau domin baya yi, har sukaje kofar gidan yaya hassan dariyar take yi, amma sai dariyar tata ta yanke saboda ganin yaya Hussain tsaye fuskarshi a murtuke sai muzurai yake yi,

Jiki asabule ta fito daga cikin motar, shima lamido fitowar yayi ya nufi yayan nata wanda daga gani babu tambaya domin kamarsu kusan daya da ita,

"Ke daga ina kike? A ina kika kwana? Dama ashe ke sokuwace shashasha ban sani ba?" Yaya Hussain ya fada cikin masifa,

"Um yaya dama, dama abban sadiq ne yazo shine...." Ta bashi amsa cikin rawar murya,

"Shine kika bishi ko? Saboda bakida zuciya baki san ciwon kanki ba, mutumin da ya gama wulakantaki agidanshi ya nuna miki cewar bai damu dake ba shine har yanzu zai zo yayi miki dadin baki ki yarda? To bari in fada miki kiji irin wadannan yan duniyar sun wuce duk inda kike tunani kuma wallahi ko bana nan ban yarda ki sake kulashi ba balle har ki bishi kinji dai na fada miki, dalla wuce ciki kibar nan ko na bugeki.."

Juyawa yayi ga lamido wanda yake tsaye yana kallonshi,

"Kai kuma ina mai gargadinka da ka fita daga harkar yarinyar nan domin muddin ina raye to bazata koma gidanka ba garama ka saketa ka daina batawa kanka lokaci idan kuma baka saketa ta dadin rai ba to kasani zaka saketa ta cikin bacin rai da tashin hankali"

Yana kaiwa nan ya juya yabar lamido awurin ya nufi cikin gida wurin ikhlas....!



_*Ummi Shatu*_

RUWAN KASHE GOBARA..!73

*RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_

   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

      _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_

      _Fatan alkairi gareku masu sunan k'awata,Khadija Ahmad (Kdeey) & Khadija Magaji bk,ina gaisheku aduk inda kuke._

  aishaummi.blogspot.com

    *_73_*

~~~D'agowa da kanta tayi ta kalleshi yanda ya rank'wafo kusa da ita har tana jin fitar numfashinsa,

Matsawa tayi ta koma gefen gadon ta zauna tana kallonshi, ko shakka ba tayi abinda ya fad'a mata d'azu gaskiyane har cikin ranshi sai dai bata son ta karbi ban hakurinsa cikin gaggawa gudun kar asake maimata gidan jiya,

"Kazo ka mayar dani gida..." Tace dashi ahankali bayan ta dauke idonta daga kallonsa,

Kusa da ya ita ya matsa ya zauna yana mai kallon kwayar idonta,

"Preety... Kece fa da bakinki kikace in baki hakkinki kamar yadda nake bawa kowacce mace acikin Gidana, to yanzu na shirya baki hakkin naki harma da sauran bashin da kike bina..."

Ji tayi kamar k'asa ta bud'e ta shiga dan kunya domin lokacin da ta furta masa hakan hankalinta ya gushe ne shiyasa, saurin kawar da kanta daga barin da yake tayi tana jin zuciyarta tana bugawa ahankali ahankali,

Binta da kallo ya fara yi wanda da bai samu zarafin yiba sai yanzu, idonshi ne ya kai kan jan lallen dake zane a tafin hannunta kasancewar ana igobe sunan matar yaya hassan anyi musu kunshi itada mai jego, ahankali ya mika hannunshi ya kamo nata ya soma bin kunshin da kallo,

"Woww.." Ya fad'a ahankali, hannunta ta fara k'ok'arin k'wacewa amma ta kasa saboda ya rik'eshi gam acikin nasa,

"Ka sakar min hannuna" tace dashi ba tare da ta jiyo ba,

Murmushi Lamido ya yi ya sake matsawa kusa da ita hadida rungumeta ta baya ya d'ora kanshi akan kafad'arta,

"Ikhlas banida bakin da zan baki hakuri domin nasan laifina mai girman gaske ne agareki amma duk da haka zance kiyi hakuri ki yafe min wallahi ina sonki, so mai tsanani"

Zoben hannunta ya kamo yana murzawa "kinga wannan zoben? Nine na saka miki shi bayan na cire wanda yake jikin dan yatsanki.."

Jikin ikhlas ne yayi sanyi aranta ta fara tunanin ashe kenan Lamido shine silar warkewarta domin tabbas shine mutumin da ya rabata da zoben da anty nafi ta bata ta saka acikin yatsanta wanda sakamakon haka ciwon hauka ya kamata,

Lumshe idanuwanta tayi ta yi luf ajikinsa tana sauraron kalaman da yake sanar da ita,

"Ina rokonki da ki yafe min duk abubuwan da suka faru, duk abubuwan da nayi miki laifinki ne saboda kece kika tilastani yin hakan amma wallahi ba dan bana sonki nayi miki ba"

Juyowa yayi da ita tana fuskantarsa, "nasan abinda nayi miki da ciwo da zafi da bacin rai amma ki daure ki yafe min please, ina sonki ikhlas, ina sonki fiyeda kowacce mace a duniya ki rike wannan a ranki kece macen da na fara so a duniya kuma har gobe baki sauya min ba dan haka ki daure ki yafe min..."

Hannuwanshi yasa ya tallafo kumatunta yana kallonta,

"Kin yafe min? Uhmm?"

Lumshe idanuwanta tayi tana jin lauassasun hannunshi bisa kuncinta ba tare da tayi magana ba,

"Ko baki yafe min bane..?" Ya sake tambayarta,

D'aga masa kanta tayi alamun ehhh,

Murmushi yayi ya dauketa cancak ya d'orata ajikinshi ya rungumeta tsamtsam yana jin wani irin farin ciki yana ratsashi,

"To me kike son inyi miki ki yafe min? Ko sai na biyaki bashinki sannan zaki yafe min?" Ya rada mata acikin kunnenta,

Kunya yasata ji dan haka tayi gaggawar cusa kanta cikin kirjinshi,

"Hakika yau ina cike da farin ciki domin na dade ina burin zuwan wannan ranar, ranar da zamu fuskanci juna nida ke ikhlas, babu shakka Allah ya soni da rahama shiyasa ya cika min burina ya mallaka min ke a matsayin mata"

Ikhlas dai lukus tayi acikin jikin Lamido ta kasa koda kwakkwaran motsi,

"Ka maida ni gida kaga yanzu sadiq ya tashi"

"Ai keda komawa gida sai gobe garama ki kirasu awaya ki fada musu"

"Yi hakuri dan Allah, daga fitowa sai ajini shiru ban koma ba?" Tace dashi fuskarta a shagwabe,

Wayarshi ya ciro daga cikin aljihun wandonshi ya mika mata,

"Ungo ki kirasu ki fada musu" ya dagota daga jikinshi yana mika mata wayar,

Fuskarta ta kawar taki amsar wayar, "kinga idan baki karba ba har na kashe wayar nan ba sake kunnawa zanyi ba sai gobe"

K'in karb'a tayi ta sake d'auke kanta hakan da tayi ya sake bawa Lamido sha'awa,

"Idan na k'irga 10 baki karb'a ba kashe wayata zanyi kuma babu ruwana tunda laifinki ne..."

Nan dinma shirun ta sake yi dan haka ya fara k'irgawa "1...,2..3...4...5...6...7...8..9..."

Kafin yace 10 tayi saurin mik'a hannunta ta kamo phone din,

Murmushi yayi ya rik'e hannunta wanda baya gajiya da kallonsa akoda yaushe domin kyaun da yayi,

"Ashe kina ji ai na dauka bakya ji"

Damk'a mata wayar yayi acikin hannunta yana kallon fuskarta,

Anty Farida matar yaya Hussain ta kira amma shiru bata daga ba hakan yasata tura mata text massage, massage din yana tafiya ta mika masa wayar idonta yana kallon k'asa,

Lollypop din da yake sha ya mik'a mata zai saka mata acikin bakinta,kawar da kanta tayi,

"Ni bazan sha kayan yara ba.." Ta fadi cikin shagwaba,

"Ni naji ni yaronne, nagode"

"Ni ai ba da kai nake ba saboda ban isa na cewa mai mata hud'u yaro ba"

Murmushi yayi ya riko hannunta "ni mata na uku ai banyi ta hudun ba ko?"

D'auke kanta ta sake yi bata amsa masa ba,hakan ya sashi sakar mata da dan malalacin murmushi,

"Nagaji sosai saboda driving din da nayi daga yola zuwa nan pls taimaka min nayi wanka kinji"

Kallonshi tayi saboda yanda ya langab'ar da kanshi kamar wani k'aramin yaro,

"Please pretty na" ya sake fada yana sake langab'ewa, kwayar idonta ta sauke akasa domin yau ta fuskanci Lamido shagwaba yake ji ba kad'an ba, yau yarintarshi ce ta tashi,

"Ko naje na hada ruwan da kaina?" Ya sake tambayarta, tashi tayi ba tare da ta sake kallonshi ba ta nufi cikin bathroom din kafin ta fito har ya cire kayanshi ya rage daga shi sai gajeren wando, tana fitowa suka yi karo a kofar toilet din yana kokarin shiga, dafe goshinta tayi,

"Washhh..!" Da sauri ya rikota jikinshi yana kallon goshin nata,

"Am sorry my dear..." Yace da ita ahankali, harararshi ta danyi tafara kokarin barin wurin,kunnuwanshi ya kama da hannunshi,

"Double sorry preety"

Juyawa tayi fuskarta dauke da murmushi....



   _masu karatu kuyi hakuri na yau babu yawa kun san jiki da jini kwana biyun nan lafiya bata isheni ba ina fata zaku yimin uzuri._

_Gaisuwa mai tarin yawa gareku Hajjaju & fa'iza nagode sosai da kulawarku._


*_Ummi Shatu_*

RUWAN KASHE GOBARA...! 72

*RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_

  *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_

aishaummi.blogspot.com


   *_72_*

~~~Ihu ihsan ta fasa itada fadila suka zube awurin suna burburwa yayinda bash yayi mutuwar tsaye, wani babban likita ne ya fito ya dakawa nurse din tsawa,

"Waye ya fada miki cewar ya mutu?"

Cikin inda inda nurse din tace "am sorry sir"

Juyawa yayi gurinsu fadila yace dasu "patient dinku bai mutu ba yana nan araye kuma insha Allah zamu bashi kyakkyawar kulawa har ya samu lafiya" yana gama fadin haka ya shiga cikin dakin da lamido yake.

Tsayawa suka yi cirko cirko suna jiran likitan da ya shiga duba lamido ya fito amma shiru bai fitoba har fiyeda tsawon awa daya, kuka sosai fadila da ihsan keyi rarrashin duniya bash yayi musu amma basu iya yin shiru ba,

Jungum jungum suka yi har wani lokaci, bash yana son ya kira baffa ya sanar dashi abinda yake faruwa amma baya son ya tayar musu da hankali dan haka yaja bakinsa yayi shiru, sai wurin karfe 2 nadare sannan likitan ya fito ya wucesu, zumbur dukkaninsu suka tashi suka bishi suna tambayarshi ya jikin marar lafiyar? Babu wata ingantacciyar amsa da likitan ya basu hakan ya sasu garzayawa dakin da lamido ke kwance duk ya fige yayi wani iri kamar wanda ya shekara yana jinya, gaban gadon ihsan da fadila suka karasa suna wani sabon kukan.

Kwana suka yi suna kuka har gari ya waye gashi har lokacin lamido baiyi koda motsi ba sai dai numfashi, ganin gari ya waye yasa bash tafiya gidan baffa, sashen innah ya shiga ahanya suka yi kicibus hannunta dauke da kulolin abinci tana kokarin zuwa sashen baffa,

"A'a bashir yanzu kake tafe? Sannu da zuwa.." Innah tace dashi tareda komawa da baya ta ajiye kayan dake hannunta,

"Ehh wlh innah, nine" bash ya fada yana sosa keyarshi,

Tsugunnawa yayi ya gaisheta ya dan fara inda inda domin ya rasa ta inda zai sanar da ita rashin lafiyar lamido,

"Bashir lafiya kuwa...?"

"Wallahi innah ba lafiya ba, lamido ne bashida lafiya tun jiya da daddare, a asibiti muka kwana nida su fadila.."

"To ni me zanyi muku kuma? Lamido bashida hali bashari, akan matarshi ne wai tatafi gida amma ai da laifinsa tunda..."

"Innah dan Allah kiyi hakuri muje kiga halin da yake ciki, wallahi lamido yana cikin wani hali"

"Jeka fadawa baffa tukunna inyaso muji abinda zai ce"

Mikewa bash yayi ya nufi sashen baffa innah kuma tana tsaye tayi suman tsaye kamar wacce aka dasa awurin, tana nan tsaye sai ga baffa ya shigo shida bash,

"Kina ina? Fito mu tafi muje mu ganoshi, lafiya ai ita ake yiwa" baffa ya fadi,

Shiga daki innah tayi ta janyo mayafinta ta fito suka fita, baffa sai tambayar bash yake yi da yaushe abin ya faru? Yanzu awanne hali lamido yake? Inna kuwa tafi kowa shiga cikin damuwa da haka suka karasa asibitin,

Dakin da lamido yake ciki suka shiga yana kwance ana kara masa ruwa fuskarshi tayi fayau, ga ihsan da fadila agefe sunata sharar kwalla idanuwansu duk sunyi luhu luhu, suna ganin innah suka tashi sukaje suka rungumeta suka fara wani sabon kukan, ita kanta innah sai da tayi kwalla saboda tausayi irin na uwa da d'a,suna cikin wannan hali likita ya shigo ya sake dubashi ya fita, bin bayan likitan Baffa yayi zuwa office dinshi ya tambayeshi abinda yake damun lamido,

"Alhaji damuwa da bacin rai shine abinda ke damunsa gashi dama yanada hawan jini.." Inji likitan ya bawa baffa amsa, mamakine ya kama baffa jin cewar Lamido yanada hawan jini domin bai taba saniba tashi yayi ya fita ya koma wurinsu bash.

A asibitin suka wuni har dare ya sake yi su ihsan kuwa har lokacin kayan baccine ajikinsu sun kasa tafiya su cire domin gani suke yi idan sun tafi kafin su dawo lamido ya mutu, koda dare yayi ma haka innah tayi tayi dasu akan suje gida su kwana amma fur suka ki suka ce anan zasu kwana.

Har akayi kwana uku Lamido bai san a inda yake ba, akwana na hudune ya dan bude idonsa amma baya gane kowa domin dishi dishi yake gani gashi kansa sai juyawa yake yi kamar hajijiya, duk da haka su innah ba karamin murna suka yi ba ganin ya bude idonsa,

Satin lamido daya a asibiti baffa ya kira bash ya tambayeshi dangane da maganar fyaden da lamido yayiwa ikhlas shekaru shida da suka wuce,

Nan bash ya zayyane komai sannan ya k'ara da cewa,

"Wallahi baffa lamido yana tsananin son ikhlas domin tun wannan lokacin ya kamu da Sonta bashida wata magana sai tata kullum burinshi ya ganta ya aureta kuma ta sanadiyyarta y kamu da ciwon hawan jini lokacin da marigayi ya aureta.."

Tausayin lamido ne ya rufe baffa domin abin a tausaya masa ne yayi dawainiya da son ikhlas na tsawon shekaru, ita kuwa innah harda kukanta saboda tausayin autan danta, tunda baffa yaji wannan maganar daga bakin bash ya cewa innah washe gari da sassafe zai tafi Maiduguri bikon ikhlas, hakan kuwa aka yi da sassafe ya tafi Maiduguri shida drivern shi,bayan sallar azahar suka karasa gidansu ikhlas.

Sun samu tarba sosai awurin ammi da hajiya, ikhlas dai dakyar kunya ta barta ta je ta gaishe da baffa sannan ta koma daki ta kwanta tana tuna lamido da irin wulakancinshi da rayuwar soyayyar da sukayi lokacin da bata tare agidanshi ba,

Waya ammi tayiwa hassan da Hussain akan suzo ayi maganar bikon ikhlas amma koda suka zo Hussain cewa yayi ikhlas ba zata koma ba domin wulakancin da lamido yayi mata yayi yawa maimakon ya barta da babban tabon da ya ji mata acikin zuciyarta na fyaden da yayi mata,shi dai baffa hakuri kawai yake basu bashida ta cewa, da kyar aka samu aka shawo kan yaya Hussain ya yarda cewar zata koma amma ba yanzu ba sai ta huta tukunna, duk da haka baffa yayi murna kuma yaji dadi domin dama baya son araba auren, a yammacin ranar su baffa suka koma yola amma har ya tafi basu nuna mishi abdallah ba.

Abu kamar wasa sai da lamido yayi sati uku a asibiti kafin hankalinsa ya dawo jikinsa ya fara samun nutsuwarshi,yana tuno da abinda ya faru ya kalli innah yana hawaye,

"Innah tana ina? Ba zata dawo ba ko? Ni dama nasan na rasata har abada"

"Zata dawo lamido ka kwantar da hankalinka tana nan dawowa" innah tace dashi cikin tausayawa,

"Dan Allah innah karku rabani da ita..." Yafada yana kokarin tsayar da kwallar dake bin kuncinshi,

"Babu wanda zai rabaku lamido, kayi hakuri kaji" innah tace dashi tana shafar sumar kanshi,

Sudai su fadila suna zaune suna jinsu amma basu tanka ba domin dama sun dade da gane cewar lamido yagama matowa akan ikhlas, haka suka ci gaba da zaman jinyarshi aranar da daddare xahar tazo dubashi ita da suhaimat nan aka shiga kallon kallo tsakaninta da su fadila amma kuma basuji haushinta sosai ba kamar yadda suke jin haushin ikhlas saboda sun fahimci cewar lamido yafi son ikhlas fiyeda kowacce mace acikinsu, basu wani jima ba suka tafi, washe gari da safe lamido ya dage shi lallai sai likita ya bashi sallama domin Maiduguri yake son tafiya wurin ikhlas, sallamarshi likitan yayi bawai dan ya gama warkewa ba, suka koma gida aka ci gaba da kulawa dashi.

Ikhlas kuwa yanzu hankalinta ya kwanta har ta danyi kiba kadan domin kullum tana tsakiyar hajiya da ammi suna hira ko ta tafi gidan yayunta susha hira wani lokacin har dare take kaiwa acan sai kwanciyar baccine yake dawo da ita gida, kullum tana ganin kiran lamido amma bata dauka ga text massage dinshi wanda kullum sai ya aiko mata fiyeda guda biyar amma ko sau daya bata taba gwada mayar mishi da reply ba gashi duk massages din na bada hakurine da na soyayya sai dai duk da haka wani lokacin tana jin kewarshi na damunta, amma har yanzu yaya Hussain bai ce ga ranar da zata koma ba domin shi ba danma baffa yaje biko ba to da niyyarshi ya raba auren,cikin haka matar yaya hassan ta haihu ta haifi yara biyu maza, murna awurin ikhlas kamar zata yi me,nan suka shiga budiri domin can ta tattara ta koma ta tare.

Kwanan lamido 5 da sallamowa daga asibiti ya fara shirin tafiya Maiduguri domin yaji dan sauki, yanzu kam ya shirya duk abinda za ayi sai dai ayi amma dole sai ya dawo da matarsa,sallama yayiwa su fadila da innah ya tafi.

A ranar da yaje aranar su ikhlas ke aikin suyar naman sunan matar yaya hassan sadiq kuma ta kaiwa ammi shi ta goyashi,gidansu ya fara zuwa ya aika akirata akace bata nan tana gidan yaya has an dan haka ya tafi can, suna tsaka da aikin yaro ya shigo yace wai ikhlas tazo inji yayanta, duk atunaninsu Hussain ne dan haka ta tashi ta fita da hijabinta a hannu aranta tana cewa,

"Naga dazun nan yaya Hussain yabar gidannan, yanzun ko me ya faru kuma?"

Tana fita taga mota irin tashi Lexus baka, jin yayi horn ya sanyata zuwa jikin motar ta bude ta Shiga, wani sanyin kamshine mai dadi ya bugeta, wa zata gani?

Lamido tagani sanye cikin farar shadda yar ubansu wacce tasha dinki mai aji, kanshi babu hula yayi mugun kyau hannunshi rikeda alewar lollypop yana tsotsa, kafeta yayi da ido yana kallonta domin har tayi dan kumatu alamun hankalinta ya kwanta,

Hade rai ikhlas tayi ta dauke kanta ta fara kokarin bude kofar motar,

"Haba pretty.." Yace da ita a hankali bayan ya matsa kusa da ita sosai,

"Malam ka bude min kofa zan fita, idan kuma takardar sakin ne ka kawo da kanka to ka bani saboda tafiya zanyi" ta fada cikin fada,

"Ba divorce letter na kawo miki ba pretty, apologise letter na kawo miki" ya fadi ahankali bayan ya zare lollypop din dake bakinshi,

"Dan Allah kiyi hakuri karki fita daga cikin rayuwata, ina yi miki tsananin son da koni ban san adadinshi ba, trust me pretty ban taba son wata ya mace ba wlhi sai ke, akanki na fara so kuma akanki na gama shi domin har yau babu macen da ta taba burgeni sama dake, sonkine yayi sanadiyyar da na kamu da hawan jini, rabuwa dake kamar rabuwa da numfashi nane domin you are my life.... I love you...!" Ya karasa maganar yana kallon fuskarta,

"Hmm nifa duk ba wannan na tambayeka ba.." Ikhlas ta fadi cikin gatsali,

"I know, kaiwai dai ina fada miki ne saboda kisan irin matsayinki awurina pretty, wallahi duk maganganun nan da nake gaya miki babu karya aciki,nafara sonki tun ranar da na fara ganinki, wannan tafiyar da kikayi kika barni har a asibiti ta sakani kwanciya saboda kece rayuwata kece farin cikina, kece burina, you are my everything..." Wasu zafafan hawayene suka gangaro daga cikin idonshi hakan yayi mutukar bawa ikhlas mamaki, shiru tayi ta kasa magana amma ta gama yarda da maganar da yake fada mata gaskiyace babu karya ko kadan aciki sannan son da yake yi mata bana yaudara bane sone tsaftatacce wanda babu algus aciki,amma duk da haka sai ta sake b'ata fuska ta hada girar sama da k'asa,

"Ni bance ka soni ba kuma bana son ka soni har abada, matanka dai wadanda kake so kake kauna to kaci gaba da sonsu da nuna musu kaunar...."

Murmushi yayi ya kalleta har lokacin fuskarshi d'auke take da tsadadden murmushi,maganganunta kamar da alamun kishi aciki, jikinta ya sake matsawa ta yadda har tana jiyo saukar numfashinsa akan fuskarta,

"Ko ki yarda ko karki yarda nidai ke kadai nake so kuma akanki zuciyata tasan zafin so, duk abubuwan da suka faru tsakaninmu wallahi laifinki ne, ikhlas ki tausaya min haka mana, so kike ciwon sonki ya kasheni? Idan ba so kike na mutu da sonki ba ya kamata ki yafe min haka domin kaunarki da sonki sun gama illata rayuwata..."

Kallonshi tayi ta gefen ido kawai sai ganinshi tayi ya sunkuyar da kai ya dafe goshinsa wanda da alama kuka yake yi, wani irin tausayinshi taji yana ratsata tun daga babban dan yatsan kafarta har zuwa tsakiyar kanta sannan ga wani irin shauki dake fisgarta, kasa magana tayi amma tana jin tausayinshi acikin ranta, sunfi minti goma suna zaune shiru babu wanda ya sake kwakkwaran motsi. Sai da lamido yayi kukanshi ya gama sannan ya zaro farin hankicif daga aljihunsa ya goge fuskarsa ya juya yana kallonta,

"Ki bani dama zan wanke laifin da nayi miki" yace da ita ahankali gashi muryarshi har ta dan dishe saboda kukan da yayi,

Tana jinshi ya kunna motar ya fara kokarin barin wurin amma bata iya hanashi ba, lollypop dinshi ya mayar cikin bakinshi yana driving yana sha, har sukaje Roxy hotel dake cikin birnin garin Maiduguri,

"Zo muje" yace da ita bayan yayi packing, babu musu ta fito ta bishi,tana tsaye tana kallonshi yaje ya biya kudin daki ya karbo key din dakin yazo ya kama hannunta suka wuce,

Room 90 shine dakin da ya bude suka shiga, kallonshi tayi ba karamin kyau yayiba shi dinma ita yake kallo da lollypop a bakinshi,

"Abban sadiq wai me zamu yi anan? Dan Allah nidai ka maida ni gida.."

Kallonta yayi ya dan sakar mata murmushi ya matsa kusa da ita

"Zan biyaki bashinki ne, duk kwanakin da nayi ba tare dake ba zan biyaki kayanki duka a yau...".



*_Ummi Shatu_*

RUWAN KASHE GOBARA...! 72

*RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_

  *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_

aishaummi.blogspot.com


   *_72_*

~~~Ihu ihsan ta fasa itada fadila suka zube awurin suna burburwa yayinda bash yayi mutuwar tsaye, wani babban likita ne ya fito ya dakawa nurse din tsawa,

"Waye ya fada miki cewar ya mutu?"

Cikin inda inda nurse din tace "am sorry sir"

Juyawa yayi gurinsu fadila yace dasu "patient dinku bai mutu ba yana nan araye kuma insha Allah zamu bashi kyakkyawar kulawa har ya samu lafiya" yana gama fadin haka ya shiga cikin dakin da lamido yake.

Tsayawa suka yi cirko cirko suna jiran likitan da ya shiga duba lamido ya fito amma shiru bai fitoba har fiyeda tsawon awa daya, kuka sosai fadila da ihsan keyi rarrashin duniya bash yayi musu amma basu iya yin shiru ba,

Jungum jungum suka yi har wani lokaci, bash yana son ya kira baffa ya sanar dashi abinda yake faruwa amma baya son ya tayar musu da hankali dan haka yaja bakinsa yayi shiru, sai wurin karfe 2 nadare sannan likitan ya fito ya wucesu, zumbur dukkaninsu suka tashi suka bishi suna tambayarshi ya jikin marar lafiyar? Babu wata ingantacciyar amsa da likitan ya basu hakan ya sasu garzayawa dakin da lamido ke kwance duk ya fige yayi wani iri kamar wanda ya shekara yana jinya, gaban gadon ihsan da fadila suka karasa suna wani sabon kukan.

Kwana suka yi suna kuka har gari ya waye gashi har lokacin lamido baiyi koda motsi ba sai dai numfashi, ganin gari ya waye yasa bash tafiya gidan baffa, sashen innah ya shiga ahanya suka yi kicibus hannunta dauke da kulolin abinci tana kokarin zuwa sashen baffa,

"A'a bashir yanzu kake tafe? Sannu da zuwa.." Innah tace dashi tareda komawa da baya ta ajiye kayan dake hannunta,

"Ehh wlh innah, nine" bash ya fada yana sosa keyarshi,

Tsugunnawa yayi ya gaisheta ya dan fara inda inda domin ya rasa ta inda zai sanar da ita rashin lafiyar lamido,

"Bashir lafiya kuwa...?"

"Wallahi innah ba lafiya ba, lamido ne bashida lafiya tun jiya da daddare, a asibiti muka kwana nida su fadila.."

"To ni me zanyi muku kuma? Lamido bashida hali bashari, akan matarshi ne wai tatafi gida amma ai da laifinsa tunda..."

"Innah dan Allah kiyi hakuri muje kiga halin da yake ciki, wallahi lamido yana cikin wani hali"

"Jeka fadawa baffa tukunna inyaso muji abinda zai ce"

Mikewa bash yayi ya nufi sashen baffa innah kuma tana tsaye tayi suman tsaye kamar wacce aka dasa awurin, tana nan tsaye sai ga baffa ya shigo shida bash,

"Kina ina? Fito mu tafi muje mu ganoshi, lafiya ai ita ake yiwa" baffa ya fadi,

Shiga daki innah tayi ta janyo mayafinta ta fito suka fita, baffa sai tambayar bash yake yi da yaushe abin ya faru? Yanzu awanne hali lamido yake? Inna kuwa tafi kowa shiga cikin damuwa da haka suka karasa asibitin,

Dakin da lamido yake ciki suka shiga yana kwance ana kara masa ruwa fuskarshi tayi fayau, ga ihsan da fadila agefe sunata sharar kwalla idanuwansu duk sunyi luhu luhu, suna ganin innah suka tashi sukaje suka rungumeta suka fara wani sabon kukan, ita kanta innah sai da tayi kwalla saboda tausayi irin na uwa da d'a,suna cikin wannan hali likita ya shigo ya sake dubashi ya fita, bin bayan likitan Baffa yayi zuwa office dinshi ya tambayeshi abinda yake damun lamido,

"Alhaji damuwa da bacin rai shine abinda ke damunsa gashi dama yanada hawan jini.." Inji likitan ya bawa baffa amsa, mamakine ya kama baffa jin cewar Lamido yanada hawan jini domin bai taba saniba tashi yayi ya fita ya koma wurinsu bash.

A asibitin suka wuni har dare ya sake yi su ihsan kuwa har lokacin kayan baccine ajikinsu sun kasa tafiya su cire domin gani suke yi idan sun tafi kafin su dawo lamido ya mutu, koda dare yayi ma haka innah tayi tayi dasu akan suje gida su kwana amma fur suka ki suka ce anan zasu kwana.

Har akayi kwana uku Lamido bai san a inda yake ba, akwana na hudune ya dan bude idonsa amma baya gane kowa domin dishi dishi yake gani gashi kansa sai juyawa yake yi kamar hajijiya, duk da haka su innah ba karamin murna suka yi ba ganin ya bude idonsa,

Satin lamido daya a asibiti baffa ya kira bash ya tambayeshi dangane da maganar fyaden da lamido yayiwa ikhlas shekaru shida da suka wuce,

Nan bash ya zayyane komai sannan ya k'ara da cewa,

"Wallahi baffa lamido yana tsananin son ikhlas domin tun wannan lokacin ya kamu da Sonta bashida wata magana sai tata kullum burinshi ya ganta ya aureta kuma ta sanadiyyarta y kamu da ciwon hawan jini lokacin da marigayi ya aureta.."

Tausayin lamido ne ya rufe baffa domin abin a tausaya masa ne yayi dawainiya da son ikhlas na tsawon shekaru, ita kuwa innah harda kukanta saboda tausayin autan danta, tunda baffa yaji wannan maganar daga bakin bash ya cewa innah washe gari da sassafe zai tafi Maiduguri bikon ikhlas, hakan kuwa aka yi da sassafe ya tafi Maiduguri shida drivern shi,bayan sallar azahar suka karasa gidansu ikhlas.

Sun samu tarba sosai awurin ammi da hajiya, ikhlas dai dakyar kunya ta barta ta je ta gaishe da baffa sannan ta koma daki ta kwanta tana tuna lamido da irin wulakancinshi da rayuwar soyayyar da sukayi lokacin da bata tare agidanshi ba,

Waya ammi tayiwa hassan da Hussain akan suzo ayi maganar bikon ikhlas amma koda suka zo Hussain cewa yayi ikhlas ba zata koma ba domin wulakancin da lamido yayi mata yayi yawa maimakon ya barta da babban tabon da ya ji mata acikin zuciyarta na fyaden da yayi mata,shi dai baffa hakuri kawai yake basu bashida ta cewa, da kyar aka samu aka shawo kan yaya Hussain ya yarda cewar zata koma amma ba yanzu ba sai ta huta tukunna, duk da haka baffa yayi murna kuma yaji dadi domin dama baya son araba auren, a yammacin ranar su baffa suka koma yola amma har ya tafi basu nuna mishi abdallah ba.

Abu kamar wasa sai da lamido yayi sati uku a asibiti kafin hankalinsa ya dawo jikinsa ya fara samun nutsuwarshi,yana tuno da abinda ya faru ya kalli innah yana hawaye,

"Innah tana ina? Ba zata dawo ba ko? Ni dama nasan na rasata har abada"

"Zata dawo lamido ka kwantar da hankalinka tana nan dawowa" innah tace dashi cikin tausayawa,

"Dan Allah innah karku rabani da ita..." Yafada yana kokarin tsayar da kwallar dake bin kuncinshi,

"Babu wanda zai rabaku lamido, kayi hakuri kaji" innah tace dashi tana shafar sumar kanshi,

Sudai su fadila suna zaune suna jinsu amma basu tanka ba domin dama sun dade da gane cewar lamido yagama matowa akan ikhlas, haka suka ci gaba da zaman jinyarshi aranar da daddare xahar tazo dubashi ita da suhaimat nan aka shiga kallon kallo tsakaninta da su fadila amma kuma basuji haushinta sosai ba kamar yadda suke jin haushin ikhlas saboda sun fahimci cewar lamido yafi son ikhlas fiyeda kowacce mace acikinsu, basu wani jima ba suka tafi, washe gari da safe lamido ya dage shi lallai sai likita ya bashi sallama domin Maiduguri yake son tafiya wurin ikhlas, sallamarshi likitan yayi bawai dan ya gama warkewa ba, suka koma gida aka ci gaba da kulawa dashi.

Ikhlas kuwa yanzu hankalinta ya kwanta har ta danyi kiba kadan domin kullum tana tsakiyar hajiya da ammi suna hira ko ta tafi gidan yayunta susha hira wani lokacin har dare take kaiwa acan sai kwanciyar baccine yake dawo da ita gida, kullum tana ganin kiran lamido amma bata dauka ga text massage dinshi wanda kullum sai ya aiko mata fiyeda guda biyar amma ko sau daya bata taba gwada mayar mishi da reply ba gashi duk massages din na bada hakurine da na soyayya sai dai duk da haka wani lokacin tana jin kewarshi na damunta, amma har yanzu yaya Hussain bai ce ga ranar da zata koma ba domin shi ba danma baffa yaje biko ba to da niyyarshi ya raba auren,cikin haka matar yaya hassan ta haihu ta haifi yara biyu maza, murna awurin ikhlas kamar zata yi me,nan suka shiga budiri domin can ta tattara ta koma ta tare.

Kwanan lamido 5 da sallamowa daga asibiti ya fara shirin tafiya Maiduguri domin yaji dan sauki, yanzu kam ya shirya duk abinda za ayi sai dai ayi amma dole sai ya dawo da matarsa,sallama yayiwa su fadila da innah ya tafi.

A ranar da yaje aranar su ikhlas ke aikin suyar naman sunan matar yaya hassan sadiq kuma ta kaiwa ammi shi ta goyashi,gidansu ya fara zuwa ya aika akirata akace bata nan tana gidan yaya has an dan haka ya tafi can, suna tsaka da aikin yaro ya shigo yace wai ikhlas tazo inji yayanta, duk atunaninsu Hussain ne dan haka ta tashi ta fita da hijabinta a hannu aranta tana cewa,

"Naga dazun nan yaya Hussain yabar gidannan, yanzun ko me ya faru kuma?"

Tana fita taga mota irin tashi Lexus baka, jin yayi horn ya sanyata zuwa jikin motar ta bude ta Shiga, wani sanyin kamshine mai dadi ya bugeta, wa zata gani?

Lamido tagani sanye cikin farar shadda yar ubansu wacce tasha dinki mai aji, kanshi babu hula yayi mugun kyau hannunshi rikeda alewar lollypop yana tsotsa, kafeta yayi da ido yana kallonta domin har tayi dan kumatu alamun hankalinta ya kwanta,

Hade rai ikhlas tayi ta dauke kanta ta fara kokarin bude kofar motar,

"Haba pretty.." Yace da ita a hankali bayan ya matsa kusa da ita sosai,

"Malam ka bude min kofa zan fita, idan kuma takardar sakin ne ka kawo da kanka to ka bani saboda tafiya zanyi" ta fada cikin fada,

"Ba divorce letter na kawo miki ba pretty, apologise letter na kawo miki" ya fadi ahankali bayan ya zare lollypop din dake bakinshi,

"Dan Allah kiyi hakuri karki fita daga cikin rayuwata, ina yi miki tsananin son da koni ban san adadinshi ba, trust me pretty ban taba son wata ya mace ba wlhi sai ke, akanki na fara so kuma akanki na gama shi domin har yau babu macen da ta taba burgeni sama dake, sonkine yayi sanadiyyar da na kamu da hawan jini, rabuwa dake kamar rabuwa da numfashi nane domin you are my life.... I love you...!" Ya karasa maganar yana kallon fuskarta,

"Hmm nifa duk ba wannan na tambayeka ba.." Ikhlas ta fadi cikin gatsali,

"I know, kaiwai dai ina fada miki ne saboda kisan irin matsayinki awurina pretty, wallahi duk maganganun nan da nake gaya miki babu karya aciki,nafara sonki tun ranar da na fara ganinki, wannan tafiyar da kikayi kika barni har a asibiti ta sakani kwanciya saboda kece rayuwata kece farin cikina, kece burina, you are my everything..." Wasu zafafan hawayene suka gangaro daga cikin idonshi hakan yayi mutukar bawa ikhlas mamaki, shiru tayi ta kasa magana amma ta gama yarda da maganar da yake fada mata gaskiyace babu karya ko kadan aciki sannan son da yake yi mata bana yaudara bane sone tsaftatacce wanda babu algus aciki,amma duk da haka sai ta sake b'ata fuska ta hada girar sama da k'asa,

"Ni bance ka soni ba kuma bana son ka soni har abada, matanka dai wadanda kake so kake kauna to kaci gaba da sonsu da nuna musu kaunar...."

Murmushi yayi ya kalleta har lokacin fuskarshi d'auke take da tsadadden murmushi,maganganunta kamar da alamun kishi aciki, jikinta ya sake matsawa ta yadda har tana jiyo saukar numfashinsa akan fuskarta,

"Ko ki yarda ko karki yarda nidai ke kadai nake so kuma akanki zuciyata tasan zafin so, duk abubuwan da suka faru tsakaninmu wallahi laifinki ne, ikhlas ki tausaya min haka mana, so kike ciwon sonki ya kasheni? Idan ba so kike na mutu da sonki ba ya kamata ki yafe min haka domin kaunarki da sonki sun gama illata rayuwata..."

Kallonshi tayi ta gefen ido kawai sai ganinshi tayi ya sunkuyar da kai ya dafe goshinsa wanda da alama kuka yake yi, wani irin tausayinshi taji yana ratsata tun daga babban dan yatsan kafarta har zuwa tsakiyar kanta sannan ga wani irin shauki dake fisgarta, kasa magana tayi amma tana jin tausayinshi acikin ranta, sunfi minti goma suna zaune shiru babu wanda ya sake kwakkwaran motsi. Sai da lamido yayi kukanshi ya gama sannan ya zaro farin hankicif daga aljihunsa ya goge fuskarsa ya juya yana kallonta,

"Ki bani dama zan wanke laifin da nayi miki" yace da ita ahankali gashi muryarshi har ta dan dishe saboda kukan da yayi,

Tana jinshi ya kunna motar ya fara kokarin barin wurin amma bata iya hanashi ba, lollypop dinshi ya mayar cikin bakinshi yana driving yana sha, har sukaje Roxy hotel dake cikin birnin garin Maiduguri,

"Zo muje" yace da ita bayan yayi packing, babu musu ta fito ta bishi,tana tsaye tana kallonshi yaje ya biya kudin daki ya karbo key din dakin yazo ya kama hannunta suka wuce,

Room 90 shine dakin da ya bude suka shiga, kallonshi tayi ba karamin kyau yayiba shi dinma ita yake kallo da lollypop a bakinshi,

"Abban sadiq wai me zamu yi anan? Dan Allah nidai ka maida ni gida.."

Kallonta yayi ya dan sakar mata murmushi ya matsa kusa da ita

"Zan biyaki bashinki ne, duk kwanakin da nayi ba tare dake ba zan biyaki kayanki duka a yau...".



*_Ummi Shatu_*

RUWAN KASHE GOBARA...! 72

*RUWAN KASHE GOBARA...!*🔥
  _(Labari mai tab'a zuciya)_

  *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Sadaukarwa ga k'awata *KHADIJA SIDI*_

aishaummi.blogspot.com


   *_72_*

~~~Ihu ihsan ta fasa itada fadila suka zube awurin suna burburwa yayinda bash yayi mutuwar tsaye, wani babban likita ne ya fito ya dakawa nurse din tsawa,

"Waye ya fada miki cewar ya mutu?"

Cikin inda inda nurse din tace "am sorry sir"

Juyawa yayi gurinsu fadila yace dasu "patient dinku bai mutu ba yana nan araye kuma insha Allah zamu bashi kyakkyawar kulawa har ya samu lafiya" yana gama fadin haka ya shiga cikin dakin da lamido yake.

Tsayawa suka yi cirko cirko suna jiran likitan da ya shiga duba lamido ya fito amma shiru bai fitoba har fiyeda tsawon awa daya, kuka sosai fadila da ihsan keyi rarrashin duniya bash yayi musu amma basu iya yin shiru ba,

Jungum jungum suka yi har wani lokaci, bash yana son ya kira baffa ya sanar dashi abinda yake faruwa amma baya son ya tayar musu da hankali dan haka yaja bakinsa yayi shiru, sai wurin karfe 2 nadare sannan likitan ya fito ya wucesu, zumbur dukkaninsu suka tashi suka bishi suna tambayarshi ya jikin marar lafiyar? Babu wata ingantacciyar amsa da likitan ya basu hakan ya sasu garzayawa dakin da lamido ke kwance duk ya fige yayi wani iri kamar wanda ya shekara yana jinya, gaban gadon ihsan da fadila suka karasa suna wani sabon kukan.

Kwana suka yi suna kuka har gari ya waye gashi har lokacin lamido baiyi koda motsi ba sai dai numfashi, ganin gari ya waye yasa bash tafiya gidan baffa, sashen innah ya shiga ahanya suka yi kicibus hannunta dauke da kulolin abinci tana kokarin zuwa sashen baffa,

"A'a bashir yanzu kake tafe? Sannu da zuwa.." Innah tace dashi tareda komawa da baya ta ajiye kayan dake hannunta,

"Ehh wlh innah, nine" bash ya fada yana sosa keyarshi,

Tsugunnawa yayi ya gaisheta ya dan fara inda inda domin ya rasa ta inda zai sanar da ita rashin lafiyar lamido,

"Bashir lafiya kuwa...?"

"Wallahi innah ba lafiya ba, lamido ne bashida lafiya tun jiya da daddare, a asibiti muka kwana nida su fadila.."

"To ni me zanyi muku kuma? Lamido bashida hali bashari, akan matarshi ne wai tatafi gida amma ai da laifinsa tunda..."

"Innah dan Allah kiyi hakuri muje kiga halin da yake ciki, wallahi lamido yana cikin wani hali"

"Jeka fadawa baffa tukunna inyaso muji abinda zai ce"

Mikewa bash yayi ya nufi sashen baffa innah kuma tana tsaye tayi suman tsaye kamar wacce aka dasa awurin, tana nan tsaye sai ga baffa ya shigo shida bash,

"Kina ina? Fito mu tafi muje mu ganoshi, lafiya ai ita ake yiwa" baffa ya fadi,

Shiga daki innah tayi ta janyo mayafinta ta fito suka fita, baffa sai tambayar bash yake yi da yaushe abin ya faru? Yanzu awanne hali lamido yake? Inna kuwa tafi kowa shiga cikin damuwa da haka suka karasa asibitin,

Dakin da lamido yake ciki suka shiga yana kwance ana kara masa ruwa fuskarshi tayi fayau, ga ihsan da fadila agefe sunata sharar kwalla idanuwansu duk sunyi luhu luhu, suna ganin innah suka tashi sukaje suka rungumeta suka fara wani sabon kukan, ita kanta innah sai da tayi kwalla saboda tausayi irin na uwa da d'a,suna cikin wannan hali likita ya shigo ya sake dubashi ya fita, bin bayan likitan Baffa yayi zuwa office dinshi ya tambayeshi abinda yake damun lamido,

"Alhaji damuwa da bacin rai shine abinda ke damunsa gashi dama yanada hawan jini.." Inji likitan ya bawa baffa amsa, mamakine ya kama baffa jin cewar Lamido yanada hawan jini domin bai taba saniba tashi yayi ya fita ya koma wurinsu bash.

A asibitin suka wuni har dare ya sake yi su ihsan kuwa har lokacin kayan baccine ajikinsu sun kasa tafiya su cire domin gani suke yi idan sun tafi kafin su dawo lamido ya mutu, koda dare yayi ma haka innah tayi tayi dasu akan suje gida su kwana amma fur suka ki suka ce anan zasu kwana.

Har akayi kwana uku Lamido bai san a inda yake ba, akwana na hudune ya dan bude idonsa amma baya gane kowa domin dishi dishi yake gani gashi kansa sai juyawa yake yi kamar hajijiya, duk da haka su innah ba karamin murna suka yi ba ganin ya bude idonsa,

Satin lamido daya a asibiti baffa ya kira bash ya tambayeshi dangane da maganar fyaden da lamido yayiwa ikhlas shekaru shida da suka wuce,

Nan bash ya zayyane komai sannan ya k'ara da cewa,

"Wallahi baffa lamido yana tsananin son ikhlas domin tun wannan lokacin ya kamu da Sonta bashida wata magana sai tata kullum burinshi ya ganta ya aureta kuma ta sanadiyyarta y kamu da ciwon hawan jini lokacin da marigayi ya aureta.."

Tausayin lamido ne ya rufe baffa domin abin a tausaya masa ne yayi dawainiya da son ikhlas na tsawon shekaru, ita kuwa innah harda kukanta saboda tausayin autan danta, tunda baffa yaji wannan maganar daga bakin bash ya cewa innah washe gari da sassafe zai tafi Maiduguri bikon ikhlas, hakan kuwa aka yi da sassafe ya tafi Maiduguri shida drivern shi,bayan sallar azahar suka karasa gidansu ikhlas.

Sun samu tarba sosai awurin ammi da hajiya, ikhlas dai dakyar kunya ta barta ta je ta gaishe da baffa sannan ta koma daki ta kwanta tana tuna lamido da irin wulakancinshi da rayuwar soyayyar da sukayi lokacin da bata tare agidanshi ba,

Waya ammi tayiwa hassan da Hussain akan suzo ayi maganar bikon ikhlas amma koda suka zo Hussain cewa yayi ikhlas ba zata koma ba domin wulakancin da lamido yayi mata yayi yawa maimakon ya barta da babban tabon da ya ji mata acikin zuciyarta na fyaden da yayi mata,shi dai baffa hakuri kawai yake basu bashida ta cewa, da kyar aka samu aka shawo kan yaya Hussain ya yarda cewar zata koma amma ba yanzu ba sai ta huta tukunna, duk da haka baffa yayi murna kuma yaji dadi domin dama baya son araba auren, a yammacin ranar su baffa suka koma yola amma har ya tafi basu nuna mishi abdallah ba.

Abu kamar wasa sai da lamido yayi sati uku a asibiti kafin hankalinsa ya dawo jikinsa ya fara samun nutsuwarshi,yana tuno da abinda ya faru ya kalli innah yana hawaye,

"Innah tana ina? Ba zata dawo ba ko? Ni dama nasan na rasata har abada"

"Zata dawo lamido ka kwantar da hankalinka tana nan dawowa" innah tace dashi cikin tausayawa,

"Dan Allah innah karku rabani da ita..." Yafada yana kokarin tsayar da kwallar dake bin kuncinshi,

"Babu wanda zai rabaku lamido, kayi hakuri kaji" innah tace dashi tana shafar sumar kanshi,

Sudai su fadila suna zaune suna jinsu amma basu tanka ba domin dama sun dade da gane cewar lamido yagama matowa akan ikhlas, haka suka ci gaba da zaman jinyarshi aranar da daddare xahar tazo dubashi ita da suhaimat nan aka shiga kallon kallo tsakaninta da su fadila amma kuma basuji haushinta sosai ba kamar yadda suke jin haushin ikhlas saboda sun fahimci cewar lamido yafi son ikhlas fiyeda kowacce mace acikinsu, basu wani jima ba suka tafi, washe gari da safe lamido ya dage shi lallai sai likita ya bashi sallama domin Maiduguri yake son tafiya wurin ikhlas, sallamarshi likitan yayi bawai dan ya gama warkewa ba, suka koma gida aka ci gaba da kulawa dashi.

Ikhlas kuwa yanzu hankalinta ya kwanta har ta danyi kiba kadan domin kullum tana tsakiyar hajiya da ammi suna hira ko ta tafi gidan yayunta susha hira wani lokacin har dare take kaiwa acan sai kwanciyar baccine yake dawo da ita gida, kullum tana ganin kiran lamido amma bata dauka ga text massage dinshi wanda kullum sai ya aiko mata fiyeda guda biyar amma ko sau daya bata taba gwada mayar mishi da reply ba gashi duk massages din na bada hakurine da na soyayya sai dai duk da haka wani lokacin tana jin kewarshi na damunta, amma har yanzu yaya Hussain bai ce ga ranar da zata koma ba domin shi ba danma baffa yaje biko ba to da niyyarshi ya raba auren,cikin haka matar yaya hassan ta haihu ta haifi yara biyu maza, murna awurin ikhlas kamar zata yi me,nan suka shiga budiri domin can ta tattara ta koma ta tare.

Kwanan lamido 5 da sallamowa daga asibiti ya fara shirin tafiya Maiduguri domin yaji dan sauki, yanzu kam ya shirya duk abinda za ayi sai dai ayi amma dole sai ya dawo da matarsa,sallama yayiwa su fadila da innah ya tafi.

A ranar da yaje aranar su ikhlas ke aikin suyar naman sunan matar yaya hassan sadiq kuma ta kaiwa ammi shi ta goyashi,gidansu ya fara zuwa ya aika akirata akace bata nan tana gidan yaya has an dan haka ya tafi can, suna tsaka da aikin yaro ya shigo yace wai ikhlas tazo inji yayanta, duk atunaninsu Hussain ne dan haka ta tashi ta fita da hijabinta a hannu aranta tana cewa,

"Naga dazun nan yaya Hussain yabar gidannan, yanzun ko me ya faru kuma?"

Tana fita taga mota irin tashi Lexus baka, jin yayi horn ya sanyata zuwa jikin motar ta bude ta Shiga, wani sanyin kamshine mai dadi ya bugeta, wa zata gani?

Lamido tagani sanye cikin farar shadda yar ubansu wacce tasha dinki mai aji, kanshi babu hula yayi mugun kyau hannunshi rikeda alewar lollypop yana tsotsa, kafeta yayi da ido yana kallonta domin har tayi dan kumatu alamun hankalinta ya kwanta,

Hade rai ikhlas tayi ta dauke kanta ta fara kokarin bude kofar motar,

"Haba pretty.." Yace da ita a hankali bayan ya matsa kusa da ita sosai,

"Malam ka bude min kofa zan fita, idan kuma takardar sakin ne ka kawo da kanka to ka bani saboda tafiya zanyi" ta fada cikin fada,

"Ba divorce letter na kawo miki ba pretty, apologise letter na kawo miki" ya fadi ahankali bayan ya zare lollypop din dake bakinshi,

"Dan Allah kiyi hakuri karki fita daga cikin rayuwata, ina yi miki tsananin son da koni ban san adadinshi ba, trust me pretty ban taba son wata ya mace ba wlhi sai ke, akanki na fara so kuma akanki na gama shi domin har yau babu macen da ta taba burgeni sama dake, sonkine yayi sanadiyyar da na kamu da hawan jini, rabuwa dake kamar rabuwa da numfashi nane domin you are my life.... I love you...!" Ya karasa maganar yana kallon fuskarta,

"Hmm nifa duk ba wannan na tambayeka ba.." Ikhlas ta fadi cikin gatsali,

"I know, kaiwai dai ina fada miki ne saboda kisan irin matsayinki awurina pretty, wallahi duk maganganun nan da nake gaya miki babu karya aciki,nafara sonki tun ranar da na fara ganinki, wannan tafiyar da kikayi kika barni har a asibiti ta sakani kwanciya saboda kece rayuwata kece farin cikina, kece burina, you are my everything..." Wasu zafafan hawayene suka gangaro daga cikin idonshi hakan yayi mutukar bawa ikhlas mamaki, shiru tayi ta kasa magana amma ta gama yarda da maganar da yake fada mata gaskiyace babu karya ko kadan aciki sannan son da yake yi mata bana yaudara bane sone tsaftatacce wanda babu algus aciki,amma duk da haka sai ta sake b'ata fuska ta hada girar sama da k'asa,

"Ni bance ka soni ba kuma bana son ka soni har abada, matanka dai wadanda kake so kake kauna to kaci gaba da sonsu da nuna musu kaunar...."

Murmushi yayi ya kalleta har lokacin fuskarshi d'auke take da tsadadden murmushi,maganganunta kamar da alamun kishi aciki, jikinta ya sake matsawa ta yadda har tana jiyo saukar numfashinsa akan fuskarta,

"Ko ki yarda ko karki yarda nidai ke kadai nake so kuma akanki zuciyata tasan zafin so, duk abubuwan da suka faru tsakaninmu wallahi laifinki ne, ikhlas ki tausaya min haka mana, so kike ciwon sonki ya kasheni? Idan ba so kike na mutu da sonki ba ya kamata ki yafe min haka domin kaunarki da sonki sun gama illata rayuwata..."

Kallonshi tayi ta gefen ido kawai sai ganinshi tayi ya sunkuyar da kai ya dafe goshinsa wanda da alama kuka yake yi, wani irin tausayinshi taji yana ratsata tun daga babban dan yatsan kafarta har zuwa tsakiyar kanta sannan ga wani irin shauki dake fisgarta, kasa magana tayi amma tana jin tausayinshi acikin ranta, sunfi minti goma suna zaune shiru babu wanda ya sake kwakkwaran motsi. Sai da lamido yayi kukanshi ya gama sannan ya zaro farin hankicif daga aljihunsa ya goge fuskarsa ya juya yana kallonta,

"Ki bani dama zan wanke laifin da nayi miki" yace da ita ahankali gashi muryarshi har ta dan dishe saboda kukan da yayi,

Tana jinshi ya kunna motar ya fara kokarin barin wurin amma bata iya hanashi ba, lollypop dinshi ya mayar cikin bakinshi yana driving yana sha, har sukaje Roxy hotel dake cikin birnin garin Maiduguri,

"Zo muje" yace da ita bayan yayi packing, babu musu ta fito ta bishi,tana tsaye tana kallonshi yaje ya biya kudin daki ya karbo key din dakin yazo ya kama hannunta suka wuce,

Room 90 shine dakin da ya bude suka shiga, kallonshi tayi ba karamin kyau yayiba shi dinma ita yake kallo da lollypop a bakinshi,

"Abban sadiq wai me zamu yi anan? Dan Allah nidai ka maida ni gida.."

Kallonta yayi ya dan sakar mata murmushi ya matsa kusa da ita

"Zan biyaki bashinki ne, duk kwanakin da nayi ba tare dake ba zan biyaki kayanki duka a yau...".



*_Ummi Shatu_*