Wednesday 31 May 2017

MARYAMA SARAUNIYA..22,23

[5/14, 4:31 PM] Ummi Shatu🏻: *_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*


   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

     _Dedicated to Maryam Qaumi_💕

  _Wannan Shafin nakine yar uwa rabin jiki Khairat Dandawakee keda duk k'awayenki.._

    *_22_*


   ~~~Ganin tayi shiru ta shiga duniyar tunani yasa anty maijidda fahimtar cewa akwai wani abu dake damunta,

"Maryama meyake damunki ne? Ki fada min mana, nifa mamanki ce haifarki ne kawai banyi ba, wallahi dake da dan da nahaifa acikina duk daya nake ganinku babu banbanci..."

"Anty maijidda wallahi nima ina son nayi auren to amma wanda nake son aurar ne shikuma bani yake soba asalima ya tsaneni, rabona dashi anfi shekara daya da rabi..." Nan ta kwashe labarin komai ta sanar da anty maijidda,

Zuba mata ido anty maijidda tayi tana kallonta cikin tausayawa amma sai ta dake domin tana son karfafa mata gwiwa har ta samu wanda take so ta aura,

Dan haka cikin sigar lallashi anty maijidda tace,

"Haba maryama to kuma menene na daga hankali? Ki kalli fa irin baiwar kyau da Allah yayi miki, wallahi babu wani d'a namiji da zai ce bakiyi masa ba sai dai idan har yasan bazai sameki ba,

Kina da baiwar da kowanne namiji zai so ya mallakeki dan haka ko kaffara bazanyi ba idan na rantse miki kan shima shaddad din yana sonki, yatafi da tabon sonki acikin zuciyarsa, son da yake miki ma koke bakya yi masa, kuma koda bai fito ya furta miki ba afili to azuciyarsa hakane,

Dan haka ki kwantar da hankalinki ki nutsu Ki saurareni domin zan doraki akan hanya wacce zata kaiki ga muradinki har burinki ya cika,

Nafarko dai sai kin zama mai hakuri da juriya domin hakuri shine matakin da yake kai bawa ga kowanne irin nasara, idan kika kasance mai hakuri da juriya to wallahi zaki kai ga nasara, ba yanzu ba ko bayan aurenku da shaddad to sai kin zama mai hakuri da juriya, bari nabaki misali, zakiga akwai matan da suke zaune lafiya agidan mazajensu ko kansu ba aji amma idan zama ya hadaku dasu zaka fahimci tsananin hakurinsu ne yakaisu ga wannan matsayin wanda har ake yimusu kallon marassa matsala agidan aure, dan haka samun nasararki yanada alaka ga hakurinki da kuma juriyarki,

Abu nagaba kuma shine ki zama mai zurfin ciki marar tona sirrinta ko kuma matsalarta, dayawa daga cikin mata zaki samu bamuda sirri idan abu yana damun mu to sai kowa yaji bama iya rike abin acikin ranmu, to ki zama mai rike sirrinki duk abinda ya dameki Allah zaki fadawa sannan awurinsa zaki nemi sauki,

Wadannan abubuwan guda biyu sune masomin samuwar nasararki, sannan insha Allah a wannan zaman da zamuyi dake zan koyar dake abubuwa da dama kama tun daga kan girki, kula da maigida,gyaran jiki da sauransu, sai abu na karshe shine ilmin addini, ya zama dole maryama ki shiga makarantar islamiyya har yanzu baki makaraba,idan kika shiga makaranta zaki karu da abubuwa da dama kafin kibar garinnan, kin san kowanne namiji baya son jahilar mace domin tarbiyar yaransa zata samu nakasu,ita mace duk kyanta duk arzikinta duk kyawun nasabarta to mutukar bata da ilmin addini to wallahi ansamu matsala..."

Ajiyar zuciya maryama tayi sannan ta bude bakinta dakyar tayi magana,

"Nagode anty maijidda sannan insha Allah zanyi yadda kikace.."

"Yawwa 'yata, insha Allah sai kin mallaki abinda kike so"

Murmushi maryama tayi acikin zuciyarta tana addu'ar Allah ya amsa,

"Yawwa tunda kinzo sai ki rubuta min maganin ciwon baya wallahi bayana ciwo yake, baby likita.."

Murmushi maryama tayi saboda jin yanda anty maijidda tayi maganar cikin barkwanci.

  Tunda maryama tazo gidan anty maijidda tare suke shiga kitchen kullum su shirya abinci banda drinks kala kala da take koya mata gashi babu kunya ko wani abun ta hadawa mijinta da ita kanta sai tafito ta fada mata amfaninsa da kuma dalilin yinsa,

Satinta biyu da zuwa suka fara fita ganin gari, sune wurin shakatawa da super market da duk wani wuri wanda masu son bude ido suke ziyarta,gashi duk lokacin da suka fita to maryama bata dawowa sai da sabon saurayi,

Yauma kamar kullum agajiye suka dawo daf da sallar magrib, hannun maryama dauke suke da ledojin ice cream da cake ga wata ledar kuma mai dauke da dambun nama dan gaske,

Tunda suka fito daga exclusive supermarket wani guy yake faman binta ganin taki kulashi yasashi shiga motarshi kirar Lexus ya biyosu, har gida ya bisu amma ita sam bai burgeta ba, dakyar anty maijidda ta lallabata taje ta saurareshi nan dinma duk fuskarta babu walwala,

Bayanin kanshi yayi mata yace sunanshi mufid kallonshi kawai take kyakkyawa ne kuma daga gani dan manyan mutane ne amma bata jin zata iya amincewa ta aureshi, nan yabata phone number dinshi ta karba tana yatsina fuska, ganin kamar atakure take yasashi yi mata sallama ya tafi,

Tafiya take tana tsaki har ta shiga falon inda anty maijidda ke zaune tana cin dambun naman da suka shigo dashi,

"Yata mai farin jini wannan kuma waye? Ni ai da shi dinma kika aura.."

"Tab haba anty maijidda ni wallahi sai navy.."

Dariya anty maijidda tayi ta bugeta akafada cikin wasa,

"To shima ai naga dan gayune kakkarfa.."

"Kinga anty ni idan kina da pad kibani kawai uzuri gareni.."

"Kashhh ai kuwa saura kwaya daya kuma ina jin guda bakwai ne aciki da kamar tun dazu muka yi maganar ai da mun siyo wani, koda yake dayanma ai zai isheki.."

"Anty wallahi yayi min kadan"

"Kai maryama har kwana nawa kikeyi?"

"Kwana takwas anty"

Ido anty maijidda ta zaro tana kallonta,

"Kwana takwas? Amma idan kinyi aure zaki rinka shan maganin da zai rage miki kwanakin ko? Ai wannan kwanakin yayi yawa maryama gashi maza basa so saboda takura suke.."

Sunkuyar da kanta tayi saboda kunya ita kuma anty maijidda sam babu boye boye komai fada take yi afili baro baro....



*_Ummi Shatu_*
[5/14, 4:31 PM] Ummi Shatu🏻: *_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*

   _*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_


    _Dedicated to Maryam Qaumi_💕

   _*23*_

aishaummi.blogspot.com

  ~~~Jin tayi shiru yasa anty maijidda taci gaba da fadin,

"Kidaina wani kunya da nuku nuku maryama, ba abin kunya bane dan kin san wadannan abubuwan,

Ni kinganni nan tun kafin nayi aure lokacin ina budurwa nasan abubuwa da yawa wadanda suka shafi al'amuran aure wallahi, ba laifi bane dan budurwa ta samu ilmi na rayuwar aure amma sai kiji wasu suna cewa wai yan matan yanzu menene basu saniba ai practical ne kawai basu yiba amma sun san komai, to wannan din shine daidai domin yanada kyau budurwa tasan hakan tun kafin tayi aure ba wai sai lokacin da tayi auren sannan zata fara tunanin tayaya zan zauna da mijina ko kuma me mijina ya kamata inyi masa ba,

Wallahi maryama nasan abubuwa da dama ina budurwa wanda wasu matan auren da yawa basu saniba kuma zurfi acikin karatun addini shine yakaini ga wannan matakin, saboda alokacin nakasance ma'abociyar karance karancen littattafan addini da sauraren wa'azozi wadanda malaman addini sukayi akan rayuwar aure, amma mu yanzu sai muke ganin abin banbarakwai idan budurwa tasan abubuwan da suka shafi, sai mu rinka yi mata kallon yar duniya ko kuma ai yar iskace, to wallahi ba iskanci bane kuma ba mummunar wayewa bace asalima wannan itace wayewa irin wacce musulunci ya tanada mutukar ba ta mummunar hanya tasan hakanba, shiyasa nake cewa zaki shiga islamiyya domin ina son ki kara samun gogewa da wasu tarin ilmin wanda ya shafi lamarin aure duk da nasan kin san dayawa daga cikinsu tunda ke likita ce amma wannan wanda zaki samu a makaranta daban yake,

Kuma nasan zakiyi alfahari dani koba yanzu ba saboda zaki gane cewar nayi miki babban gata wurin doraki akan turba mai kyau, sannan ko bayan kinyi aure zaki ji dadin zama da mijinki batare da matsala ba,

Shiyasa kika ga tunda nake babu wurin wacce nake zuwa neman shawarar wai ya zan yi inbawa mijina kulawa, domin nadade da sanin abubuwan da maza keso da wanda bakya so, shiyasa nazama star mai haskawa awurin mijina"

Dafa kafadar maryama anty maijidda tayi sannan taci gaba,

"Yanda nasamu fada awurin mijina kema haka nake miki fata yata, amma sai kin nutsu sannan kuma kin jajurce, akwai wa'azi dayawa da malamai suka yi akan yammata da masu shirin shiga dakin miji musamman dan abasu wani ilimi na yanda zasu kula da mazajensu ya kamata ki nemesu ki adana kuma ki rinka saurara sannan kinga idan har hakan ba abune mai kyau ba to da malamai basu bata lokacin su sun zauna sun rubuta ba, kamar yadda nafada miki ba iskanci bane kuma ba abin kunya bane saboda acikin magabata ma ansamu matar da tayiwa yarta nasiha tabata shawarwari lokacin da zata kaita dakin miji, hatta yanda yadace ta kula da mijinta da irin yanda zata faranta ran mijinta da abinda zata yimasa lokacin rayuwar auratayyarsu duk sai da wannan matar ta koyar da yarta,kuma hakanne ya kamata ko wacce uwa ta zama, mu rashin zurfafa awurin karance karancen addini da sauraren malamai duk shine ya mayar damu baya har muke aibanta abinda yake mai kyau,wallahi indai yarinya mai addini ce hadisin zadiz zaujaini kadai ya isa ya sanar da ita ilmin aure dan haka yana da kyau mu tashi mu nemi ilmi,

Wadannan kwanakin kamar yanda nafada miki sunyi yawa maryama musamman ma awurinki keda kike saka ran cewar zaki auri soja, kin san karfin sha'awar sojoji tafi ta sauran maza saboda su yanayin motsa jikinsu da shan wahalarsu, idan normal namiji zai bukaceki adare sau biyu to soja sai dai sau uku ko hudu, kinga kuwa indai hakane bazaku shirya dashi ba mutukar kina yin period har tsawon kwanaki takwas, wani namijin ma ko kwana hudu kikeyi sai kinga ya shiga damuwa, yanzu dai nasan bakya gane abinda nake sanar dake sai dai idan lokacin yayi zaki fahimta"

Mikewa maryama tayi cikeda jin kunyar anty maijidda ta nufi bedroom taje ta dauko pad din ta shiga dakinta,

Wanka tayi ta shirya cikin wasu pink din riga da wando masu laushi ta koma falo inda anty maijidda ke zaune tana kallon _Dhoom_ a tashar mbc Bollywood,

Zama tayi ta dauki robar dambun nama ta bude tafara tsakura tana ci,

"Maryama mai zaki dan dafa mana muci?"

"Duk abinda kikace anty"

"To dafa mana taliya sai ki danyi mana sos da kifi.."

"To anty.."

Tashi tayi ta ajiye dambun naman da take ci ta nufi cikin kitchen, tana ji wayarta na kara amma ko ta kula saboda tasan samarin dake damunta kullum ne,

Binta da kallo anty maijidda tayi fuskarta dauke da murmushi saboda da saninta take saka maryama aiki kamar su girki da sauransu saboda tana son kiwar dake tattare da ita ta ragu sannan idan tana yawan yin girki akai akai to hakan zai sata ta goge ta kware afannin girkin shiyasa yanzu yawancin girkin ita take barwa tayi musu kuma alhamdulillah tun ba ayi nisa ba har maryaman tafara kwarewa sabanin da wanda babu abinda ta iya ko dafa ruwan zafi ma wahala yake mata saboda ita tunda ta taso agidansu kuku ne yake dafa musu duk abinda zasu ci,

Jin karar wayar maryama yayi yawa ya cikawa anty maijidda kunne yasata dauka ta kaimata kitchen din,

"Ungo phone dinki samarinki sai cika min kunne suke da kira.."

Hannunta ta tsame daga robar da take wanke kifi sukumbiya da ruwan kal saboda magance karninsa,

Daga wayar tayi tana murmushi saboda ganin dr fahad ne wanda ke kiranta,

Makale wayar tayi akafadarta tafara amsawa yayinda anty maijidda ta juya ta fita daga cikin kitchen din,

"Hello fahad...." Tafada tareda jan sunan,

"Hy maryama ta, yakike?"

Murmushi tayi "lafiya lau fahad ya aiki?"

"Alhamdulillah maryama, ya lagos"

"Lfy, ni ina abuja ma nazo hutu"

"Ahh daidai kenan, zanzo miki mu gaisa sai mu gama maganar bikinmu ko, saboda nidai na kosa.."

Tana jin haka ta bata fuska kamar yana ganinta saboda ita ta tsani taji anyi mata zancen aure mutukar ba za a danganta maganar auren da shaddad ba,

"Ok, to kabari zan kiraka yanzu ina kitchen ne"

"Me ake dafa mana sarauniya?"

"Cikin kosawa da maganar ta amsa masa, "ina wanke kifine so we will talk later.."

"Ok queen bye"

Ajiye wayar tayi tana tsaki, "yara kanana basu taka kara sun karya ba suce wai kaine Sa,an aurensu saboda tsabar rashin kunya, ko idan sun aureni ina zasu kaini oho.."

Da haka ta samu ta kammala girkin tana yi tana ta korafi ita kadai,

A babban farantin tangaran ta zuba musu abincin itada anty maijidda ta fita,

A inda ta tafi tabar ta anan ta sameta tana rikeda remote tana rage volume din tv,

Ajiye abincin tayi wanda yaketa faman kamshi domin sos din tasha curry kala kala,

Fara cin abincin sukayi, girkin ya danyi sai dai kuma akwai yan kura kurai wanda ba arasa ba nan anty maijidda ta danyi mata gyaran da yadace saboda gaba....


*_Ummi A'isha_*

MARYAMA SARAUNIYA.. 20,21

[5/13, 7:16 AM] Ummi Shatu

*_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*


   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*


     _Dedicated to Maryam Qaumi_💕

  _Fatan alkairi agareki kawata fiddausi sodangi, nasan kema masoyiyar maryama sarauniya ce shiyasa nabaki wannan shafin kyauta keda maryama Abdul takwarar maryama sarauniya.._


    *_20_*

aushaummi.blogspot.com

   ~~~Wani wahalallen barcine yayi gaba da ita, hatta acikin mafarkin ma in banda mafarkin shaddad babu abinda takeyi,

Mafarki take wai gashi nan ta ganshi awani gari wanda bata san kowanne bane, tana tsaye kan wani tsauni shikuma yana can nesa da ita, ahankali ahankali sai kara yimata nisa yake da haka har ta daina hangoshi,

Tashi tayi firgigit daga baccin da take duk tabi ta hada zufa kamar wacce ta kwara ruwa ajikinta,

"Me wannan mafarkin yake nufi kenan? Kodai shaddad yayi min nisan da bazan iya kamoshi ba har abada?"

Dafe kanta tayi wanda ke barazanar rabewa gida biyu,

"Ya Allah ka sassauta min, nasan hakkin shaddad ne yake bibiyata, hakkin sharrin da nayi masa ne shiyasa Allah ya jarrabeni da tsananin sonshi..."

K'walla ce ta cika mata idonta ta dauki wayarta dake ajiye agefen gado tafara trying din number dinsa amma kamar kullum yau ma wayar akashe take, cigaba da kira tayi har ba adadi daga karshe ta jefar da wayar akan gado ta kifa kanta jikin pillow tana hawayen bakin ciki masu cikeda nadama tareda dana sani,

Dakyar ta iya saita kwakwalwarta ta tashi idanuwanta jajur ta lallaba ta sauka k'asa inda Dada ke zaune akan carpet yana cin abincin dare,

Ganinta yasashi sanin ba kalau ba domin fuskarta da idanuwanta sun sanar dashi hakan,

"Daughter..." Yafada cikeda kulawa,

"Na'am Dada" ta amsa masa tana runtse idonta saboda ciwon da kanta yake yi mata,

"Bakida lafiya ne?"

Daga masa kai tayi sannan tace, "kaina ne yake ciwo.."

"To kinsha magani?"

"Ehh nasha.."

Tashi Dada yayi yabar abincin da yake ci yakoma kusa da ita ya zauna,

"Mai sunan mama kodai kinada damuwa ne kika boye min?

Idan akwai abinda yake damunki ki sanar dani domin nine mahaifinki baki da kowa sai ni, sannan bakida wanda yafini dan haka karki rufe min abinda ke damunki"

Hannuwanshi duka guda biyu ta kama ta rirrike sai ga hawaye yana bin kuncinta wanda yayi mutukar razana Dada domin sam yasan maryama ba mai saurin kuka bace sannan akwaita da dauriya tun tana yarinya karama, ita dai barta da shagwaba amma tanada dauriya akan komai,

Hankalinsa ne yaji ya tashi saboda bai saniba ko wani abune yake damunta haka wanda har yasata kuka,

"Mai sunan mama kodai mahaifiyarki kika tuno?"

K'wallar idonta ta share ta girgiza masa kai,

"To meyake damunki har yasaki kuka? Ko kina son zuwa kiga yan uwan mahaifiyarki ne?"

Nanma kai ta girgiza masa alamun a'a, take taga hankalinsa yayi kololuwar tashi nan kuma taji tsoron kar hawan jininsa ya tashi dan haka tayi gaggawar rarrashin tata zuciyar,

Murmushin dole tayi idanuwanta sun kada sunyi ja,

"Father babu fa abinda yake damuna, jikinane duk nake jinsa a daddaure amma yanzu na wartsake.."

"A,a daughter nasan abinda ke damunki, tunowa kikayi da mahaifiyarki shiyasa kikayi kuka, kiyi hakuri kiyi mata addu'a akan Allah yayi mata rahama yakai haske kabarinta,

Keda ko zama da itama bakiyi ba bare har kisan halayenta da dabi'unta da mu'amalarta,

Nida nazauna da ita ni nasan wacece ita,ni nasan wacece maryama, shiyasa bazan taba iya mantawa da maryama ba domin nagartacciyar mace ce mai hakuri mai fara,a mai son mutane sannan mai tsananin biyayya ga mijinta, sunanta kadai idan naji yakan sani farin ciki, maryama ta zauna dani a lokacin da banida arziki banida abin duniya a lokacin da ban mallaki komai ba, gashi dadin dadawa sunan mahaifiyata gareta shiyasa dan haka ko sunanta bana kira wannan dalilin ne ma yasa kema na kiraki da maryama na rada miki sunanta kuma sunan mahaifiyata,

Maryama ta nuna min dukkan soyayya ta duniya sannan ta rayu dani cikin kwanciyar hankali, lokacin bana zama agida kullum ina can jeji yawon yake yake haka zan tafi nabarta babu ko aike sai nadade zan dawo amma bata taba damuwa ba, ko mahaifiyata ce tazo ta tambayeta ko da wani abu sai tace babu.."

Shafa kan maryama yayi yana kokarin boye yar kwallar da ta taru a gefen idonsa,

"Ke kadaice yar da ta haifa a duniya kuma ta mutu wurin kawoki duniya dan haka kema kiyi koyi da ita ko kinyi aure kiyi kokarin rufe sirrin mijinki kinji mamana..."

D'aga kai maryama tayi tana murmushi, "insha Allah Dada nayi maka alkawarin zanyi irin abinda mahaifiyata tayi, bazaka taba jin na kawo maka karar mijina ba.."

"Allah yayi miki albarka mai sunan mama.."

"Amin father"

Tashi tayi taje ta hau kan exercise machine ta kunna tafara yi domin tana son ta warware ta rabu da damuwar dake damunta ko dan lafiyar Dada,

Tana daga kan exercise machine din shikuma Dada yana zaune a falo yana bata labarin kuruciyarta, murmushi tayi saboda jin yace tun tana rarrafe take kaunar butterfly shiyasa ma kusan duk kayan wasanta masu adon butterfly yake siyo mata,

Dawowa kusa dashi tayi ta zauna hannunta rikeda battle water mai sanyi,

"Father ashe na dade ina son butterfly.."

"Zan fito miki da wasu hotuna wanda aka yimiki kina karama lokacin hatta rigarki zanen butterfly ne ajiki"

Dariya tayi ta jingina ajikinsa, ko babu komai labaran da yabata yasata jin damuwarta ta ragu, sun raba dare suna hira da Dada kafin daga bisani ta shiga dakinta ta kwanta,

Kamar kowanne dare yauma kasa bacci tayi sai tsananin tunanin shaddad da yake addabar zuciyarta.

Haka taci gaba da kasancewa kullum cikin bege da kaunar shaddad amma har yau babu alamun sake ganinshi atare da ita,

Kullum cikin damuwa take sanin idan ta zauna agida damuwa ce zata yimata yawa yasata take fita aiki amma kowa yasanta da yaganta yanzu yasan akwai abinda yake damunta, akwana atashi har saida akayi shekara daya da yan watanni amma kullum son shaddad sake shiga zuciyarta yake, sam takasa cire tunaninsa aranta, wani lokacin ma idan ta zauna tana tunaninsa sai ta ringa cewa kila ma yanzu haka shi har yayi aure,

Samari bawai ta rasasu bane kawai har yanzu shaddad zuciyarta ke muradi,

Yauma kamar kullum cikin bacci shaddad yazo mata har yana cemata zata ganshi sannan zata hadu dashi amma sai taje wani gari,

"Wanne garinne shaddad?"Kafada min ko inane zanzo.."

Yabude baki kenan zai fada mata tayi firgigit ta tashi....



*_Ummi A'isha_*🏻
[5/13, 7:16 AM] Ummi Shatu🏻:

*_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*


    _*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_


    _Dedicated to Maryam Qaumi_💕

 
   _Anty maijidda musa your page done start...._

    *_21_*

aishaummi.blogspot.com


    ~~~Shiru tayi tana bin jikinta da kallo yanda duk tabi ta hada gumi, tagumi tayi tana son tuna inda ya dace tatafi neman shaddad ko Allah zaisa ta dace ta hadu dashi, amma zuciyarta taji ciwon rashin fada matan da baiyi ba, shekara daya kenan harda yan watanni tana fama da radadin soyayyarsa acikin ranta amma bata san inda zata sameshi ba,

Tashi tayi ta shiga bathroom tayi wanka ta fito, blessing tagani tana kokarin fito mata da kayan da zata sa,

"Blessing ki fito min da kayana ki dauko babbab akwati ki shirya min su saboda gobe zanyi tafiya.."

"To anty.." Blessing ta amsa mata,

Shiryawa tayi tafito das da ita domin dama maryama badai kyau ba,komai tasa yimata kyau yake yi musamman ma bakaken kaya,

Falon Dada ta shiga ta zauna tana jiranshi yafito, bata jima da zama ba sai gashi ya fito cikin shirin fita wurin aiki,

"Father... Ina kwana"

"Lafiya lau mai sunan mama, har anfito?"

"Wallahi nafito Dada, zanje asibiti ne saboda ina son na rubuta leave with out pay..."

"Saboda me?" Yayi mata tambayar yana kallonta,

"Dada ina son zuwa wurin yan uwan mahaifiyata ne kuma zan dan jima acan.."

Ajiyar zuciya ya sauke yayi dan murmushi,

"Za kije zumunci kenan,dama ai rabonki da can tun farkon dawowarki daga Malaysia, yakamata kije kam"

"Insha Allah gobe zan tafi"

"Da wuri haka? Har kin gama shiryawa?"

Kai ta daga masa,"nagama father.."

"To Allah ya kaiki lafiya"

"Amin dada"

Tare suka fita ita ta dauki motarta ta nufi asibiti shikuma driver yajashi suka tafi office dinshi.

  Tana zuwa agurguje ta dudduba marassa lafiya taje round ta fito, wasikar daukar hutun ta rubuta ta dauka da kanta ta nufi office din shugaban asibitin,

Kasancewar shima yana sonta sannan ya dade yana bibiyarta kan ta bashi dama ya aureta yasa atake awurin yayi approving yabata, babu wanda ta fadawa ta kwaso duk wasu kayanta dake cikin office din ta koma gida,

Akwatuna biyu manya manya sai da aka cika su da kayanta ahakanma dayawa barinsu zatayi bazata tafi dasu ba,

Tunda ta dawo shirya kayan suke itada blessing har magrib tayi a lokacin dada ya dawo,

Wurinshi taje ta zauna suka fara hira anan yake sanar da ita cewar yasa an yanko mata ticket din jirgi, zata bi jirgin karfe 9 nasafe,

Murnar da tayi gani take kamar ma har ta mallaki shaddad din, daren ranar tsananin murna bai barta tayi bacci ba.

  Washe gari misalin karfe 8:30 tabar gida su dada suka rakata airport harda su blessing, wata kwalla ce ta siraro ta gefen idonta lokacin da suke yin sallama da dada domin idan ba dole ba bata son yin nesa dashi, sakin hannunshi tayi taje ta shiga cikin jirgin suna tsaye suna kallonta,

"Mamana kenan duk lokacin da za ayi tafiya sai anyi kuka, haka ma lokacin da tana karatu duk hutun da take zuwa idan zata koma to da kuka take komawa..."

Dada yace dasu blessing yana murmushin karfin hali domin shima zuciyar tasa a karye take.

K'arfe tara da rabi su maryama suka sauka a birnin abuja,

Taxi ta samu ta hau aka kaita har kofar gidan kanwar mahaifiyarta wanda ke cikin unguwar Yar adu'a housing estate, tana gaba mai gadi yana binta da kayanta har cikin gidan,

Tana kitchen tana hada abincin karyawa taga shigowar maryama, cikin sauri ta fito tana fadin,

"Oyoyo maryama.."

Rungume juna suka yi cikin farin ciki, har suka shiga cikin falon basu iya sakin juna ba,

"Anty maijidda yau kin ganni nasamu zuwa.."

"Naganki maryama ai gara da kikazo amma kya yi shiru ki kyalemu bakya ziyartar mu?"

Murmushi maryama tayi tana kallonta saboda bata da maraba da mahaifiyarta kamarsu daya sak,

"Anty maijidda ina yaran naji gidan shiru.."

"Maryama ai babu kowa agidan nan sai ko ke yanzu da kikazo duk sun tafi boarding school"

"Lallai anty kinyi kokari.."

"To bari na karasa shirya mana abincin nakawo dama oga baya nan bai kwana agari ba.."

Tashi tayi ta shiga kitchen ta karasa hada musu abinci ta fito dashi,

Dumamen tuwon shinkafa miyar agushi da tea sannan ga soyayyen dankali da miyar hanta,

"Kai anty duk wadannan kayan kuma a ina zamu durasu?"

Dariya anty maijidda tayi tana kallonta "maryama kenan ai dan oga baya nanne da yana nan to da sai nayi masa girkinshi daban"

"Lallai kina kokari gashi bakida yar aiki.."

"Ai shi baya son yar aiki maryama sannan nima nafi son nayi komai da kaina.."

Murmushi maryama tayi domin dama can tasan anty maijidda kwararriya ce wurin iya tarairayar miji da bashi kulawa shiyasa har yau mijinta ya kasa karo mata abokiyar zama,

"Yanzu maryama wa kika tsayar a matsayin mijin da zaki aura? Ina nufin waye proposed dinki domin yanzu ya kamata ki fara maganar aure tunda kin kammala karatu har kina yin aiki duk wata kina karbar salary, to yakamata kuma yanzu kifara shirin tunkarar shiga gidan miji domin yanzu shekarunki 30 babu watanni, dan haka ki nutsu ki zabo nagari mai kyawawan halaye wanda zakiji dadin zama dashi..."

Shiru maryama tayi sai dai maganar da anty maijidda tayi ya soso mata wurin da yake yi mata kekayi nan tafara shawara da zuciyarta kan shin ta sanar da anty maijidda abinda ya fito da ita daga gida ko kuma tayi shiru??


*_Ummi Shatu_*

MARYAMA SARAUNIYA.. 16,17,18,19

*_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*



   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

   
_Dedicated to Maryam Qaumi_💕

  *_Gaisuwa mai tarin yawa ga Maryam s Bello da Aysha garkuwa, tabbas ku masoyana ne na hak'ik'a dan haka wannan shafin na badashi tukwici agareku daku da duk wani wanda yake jin yana son ummi Shatu_*

aishaummi.blogspot.com

     _*16*_

~~~Tagaban gidansu maryama yawuce yana jin wani bacin rai yana ziyartar zuciyarshi,ko daga ido bai yi y kalli gidanba har yayi nisa dashi amma acikin zuciyarsa damuwace kwance saboda yasan mahaifin maryama ya kullace shi acikin ransa domin yana tsananin son yar tashi sannan ya daukeshi kamar dan cikinsa yabashi dukkan yarda sai dai kuma daga karshe yaci amana,

Tamkar marar jini ajiki haka yake takawa har ya karasa fita daga cikin barikin, taxi ya tara ya shiga ya tasamma tashar mota.

***

  Tsalle ta doka ta fad'a kan gado ta kwanta tana shakar daddadar iskar air condition din dake ratsata, yanzu kam ranta yayi mata fari kuma hankalinta ya kwanta sakamakon mayarwa da shaddad martanin abinda yayi mata da tayi,

Bargo ta jawo ta rufe jikinta ta lumshe idanuwanta tana jin wani irin farin ciki yana ziyartar zuciyarta,

Rungume daya daga cikin manyan teddy din dake kan gadon nata tayi tana murmushi,

"Wai har ni wannan yaron zai daga hannu ya mara sannan ya kirani da karuwa..., sannan kuma har ya tsammaci zama lafiya, wallahi bazai yiyuba, yanzu nasan na tabbatar masa da cewa ni karuwar ce kamar yadda yace.."

Duk wadannan maganganun tana yinsu ne acikin zuciyarta fuskarta kunshe da fara'a, ranta fari tas bacci ya kwasheta.

  Washe gari kamar kullum haka ta tashi tana zuba mulki tayi wanka ta shirya kuku ya hada mata abincinta kamar yadda ya saba, wata red din gown tasaka mai adon duwatsu ta yafa dan siririn mayafin rigar tana ta faman zuba kamshi,ga yar siririyar barimar gold tasaka acikin hudar hancinta domin tana tsananin son kwalliyar hanci,

Falon Dada ta nufa tana tafe tana taunar chewing gum, zaune ta iskeshi ya kammala breakfast yana jiran driver yazo ya kaishi office, zama tayi agefenshi tana dan murmushi,

"Good morning father.."

"Morning daughter, har anfito?"

"Nafito Dada.."

"Gashi kuma babu mai kaiki office, koda yake kibari idan driver na yazo sai mu fita tare muyi dropping dinki"

"Babu komai dada kabarshi ma zanyi driving da kaina yau..."

"To shikenan dama ina son kifara driving din saboda bana son nasake baki wani drivern asamu wata matsalar"

"To Dada, insha Allah ma daga yau ni zan rinka kai kaina office ina dawowa.."

"Idan kikayi hakan nima hankalina zai fi kwanciya"

Murmushi tayi ta mike tsaye, "Dada bari naje natafi.."

"To mai sunan mama sai kin dawo sannan daga yanzu zuwa yamma zan turo miki kudin da kika nema harda kari.."

"Dada rencen kabani?" Ta tambaya tana dariya wanda har saida kyawawan fararen hakoranta suka fito waje,

"Kyauta nabaki daughter saboda ina son ki samu ki kammala ginin asibitin naki.."

"Ai dada akwai saura sosai yau idan natashi daga office zan biya nadubo ginin, nagode sosai dada Allah ya kara girma da lafiya.."

"Amin mai sunan mama"

Fita tayi fuskarta kunshe da murmushi, har cikin motarta blessing ta rakata tana dauke da hang bag dinta da sauran kayan tarkacenta nazuwa office,

Bakin glass tasaka ta daura belt ta tashi motar, sosai motar tayi mata kyau kuma ta karbeta, ahankali tafara driving tabar harabar wurin ta nufi asibiti.

  Tunda shaddad yabar Lagos bai ko je gidaba ya tafi Benin domin abubuwan dasu gudanar awurin masu muhimmanci ne, dadin dadawa kuma za abasu training na sati biyu shiyasa ma baiyi yunkurin zuwa gidaba, kullum da haushin abinda maryama tayi masa yake kwana yake tashi gaba daya yakasa mantawa da ita balle ya manta da abinda tayi masa, zuciyarsa duk lokacin da ta tuno masa da abin sai yaji kamar zata hudo kirjinsa tafito waje, ahaka ya daure ya kammala wannan training din ya nemi izinin zuwa gida kuma cikin sa'a ya samu, shiryawa yayi ya hari gida saboda yanada abu mai muhimmnanci da yake son aiwatarwa.

   K'arfe Biyar daidai maryama ta fito daga cikin office dinta ta nufi packing space domin daukar motarta, dr sameer ne ya biyota a baya yana tsayar da ita,

"Ranki ya dade har zaki fita..?"

Murmushi tayi ta bude motarta ta dafa murfin kofar motar ta dage glass dinta dake sanye afuskarta ta mayar dashi kan goshinta,

"Wallahi har zan fita dr, ina sone nafara zuwa wurin ginin hospital dina da akeyi acan agege"

"To Allah yabada nasara, dama kawai zuwa nayi nace miki wani abu idan kin bani dama sai na fada.."

"Nabaka dama dr kafadi ko menene.."

Sai da ya danyi murmushi sannan yace, "kinyi kyau yau, sannan da ace zaki bani dama to da na aureki na kasance dake har abada.."

Murmushi tayi ta shiga cikin motar ta zauna, tana kokarin daura belt ta kalleshi,

"Dr kenan zandai baka damar nan in gani.."

"Amma kuwa da kin gama yimin komai"

Rufe kofar tayi tana murmushi ta tashi motarta ta fita tana yi masa bye bye, can agege ta nufa wani katon daji inda ake gina mata asibitin yara wanda yake mai girman gaske, kasancewar ginin katone yasa ko rabi ba ayiba, fita tayi ta dan dudduba takoma cikin mota ta nufi gida, tana zuwa gida ta sake yin wanka ta tsuke tafito domin zuwa stadium,

Kullum haka take bata da lokacin hutu sai week end sai dai tunda samari suka yi yunkurin keta mata mutuncinta har yau bata sake komawa club ba.

  Lamurranta kawai take aiwatarwa hankali kwance kuma yanzu tafara ji a zuciyarta cewar zata zabi daya daga cikin samarinta dr sameer ko da yazeed ta aura saboda shi dr naz da fahad duk yara ne amma har yanzu  zuciyarta ta gaza tantance mata wanda ya dace ta aura, batun shaddad kuwa tuni har ta mance dashi saboda yanzu a kalla za ayi kimanin watanni biyu da tafiyarsa daga gidansu.

   Fitowarta kenan daga wanka ta danyi abubuwan da zatayi ta fesa turare ta saka rigar bacci pink colour light, rigar bata da nauyi sannan iyakacinta gwiwarta,

Kwanciya tayi ta kunna air condition ta kashe wuta, babu bata lokaci bacci yace muje zuwa, can cikin dare tana tsaka da bacci taji kamar motsin ana daure mata hannu ta baya, sake gyara kwanciyarta tayi, abu sai kara gaba yake sai jin kafafunta tayi suma a daure, kafin ta iya saita tunaninta har andaure mata baki, a lokacin tsoro da razani suka dirar mata, ihu take son yi amma babu hali, tana ji aka dauketa aka dorata akafada akayi waje da ita cikin sand'a,

Hankalinta idan yayi dubu to duk yagama tashi sannan gashi garin bakikkirin yake da duhu kasancewar anyi ruwan sama gashi babu wuta kuma ankashe injin da aka kunna tun karfe 1,

Wani lallausan hannune ke rikeda ita sannan ga wani kamshi mai dadi da sanyi da take shaka, zuciyarta sai harbawa take a tamanin musamman ma dataga an nufi dajin kare kukanka da ita wanda ke cikin barikin daga can karshe gashi yayi nisa da gidajen cikin barikin ko kashe mutum za a iya yi batare da an saniba,

Kan wani yayi taji an jefata tareda take kafafuwanta, idanuwanta ta runtse dan tsananin azaba, ahankali taji an matso saitin fuskarta, fitila ya kunna ya haska mata fuskarsa take taji tana shirin sakin fitsari a wando saboda ganinshi, idanuwanta ta zazzaro saboda tsananin firgici,

Daurin da yayiwa hannunta da kafarta ya kunce yasake saka kafarshi ya take kafarta, kyallen da ya daure bakinta yakunce mata ya kura mata ido,

Ita dinma kallonshi take fuskarta cikeda tsoro tana kokarin ja da baya sai dai amma takasa saboda ya take mata kafafu wanda take ji kamar ya karya mata su, cikin rawar jiki take kallonshi tana rufe bakinta, ba kowa bane illa shaddad, yana sanye da bakin wando da bakar riga ajiki an rubuta Nigerian Navy,

"Kinyi min sharrin fyade ko? To yau zanyi miki na gaske in yaso sai mahaifinki yasa aharbeni, yau zanyi miki abinda baki taba ji ba ko acikin tarihi so kishirya..."

D'aga mata kafarta yayi daga takewar da yayi take tafara jada baya tana girgiza masa kai cikin rawar murya mai hadeda tsoro tareda firgici tafara magana,

"Dan Allah dan annabi kayi hakuri, dan Allah karka keta min alfarmata...."

"Shhhhhh...." Yadora hannunshi akan bakinsa,

"Karki kuskura ki hadani da Allah saboda yau sai na nuna miki cewar ke karamar karuwa ce, zan nuna miki ke ba kowa bace.."

Ganin yafara kokarin kunce belt din wandonshi yasata cigaba da matsawa baya tana runtse idonta gashi duk tabi ta kukkuje jikinta sai jini ne yake fita, yana fara dosota ta sake yin baya tana shirin yin kuka....

*_Ummi Shatu_*🏻
*_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*



     *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*


    _Dedicated to Maryam Qaumi_💕

   _Kuna raina akoda yaushe, Basma er lele, Nasma mai Kano, Umma yahaya musa (marubuciyar goyon kaka), tareda Baby Rasheed...nagode muku Allah yabar zumunci._

aishaummi.blogspot.com

   *_17_*


~~~Ja da baya take yana binta tana sake jada baya yana sake matsowa da haka har taje ta tokaru da wani katon ice,

"Dan Allah kayi hakuri, wallahi bazan sake ba..." Tafada idanuwanta sunyi jajur suna shirin fitar da hawaye,

K'afarsa yasa ya take kafarta guda daya nan taji wani radadi ya shigeta, babu shiri ta bude baki da niyyar kwalla ihu,

Cikin sauri ya katseta,

"Shhhhh, idan kika sake kika yimin ihu wallahi sai na lahira yafiki jin dadi,kin yimin karya kince zanyi raping dinki to yanzu zanyi raping din naki dagaske...."

Hannu tasa ta toshe bakinta tafara jijjiga masa kai alamun yayi hakuri kar ya aikata abinda yake shirin aikatawa,

Kafarta ya kama yajawota gabanshi ya direta, rufe idanuwanta tayi saboda ganin abinda ke shirin faruwa gashi ita ba wani iya addu'o'i tayiba balle ta karanto,

Shi kuwa shaddad zuciyarshi sai angazashi take tana zugashi akan ya aikata hakan amma kuma wani bangaren na daya zuciyar tashi sai hanashi take tana cewa,

"Haba shaddad kai da baka taba aikata zinaba koda wasa meyasa yanzu zaka aikata baka tsoron haduwarka da ubangiji? Ko baka tsoron daukar cuta ajikinta tunda dai ba kamilalliya bace ita..."

Shawarar zuciyarsa yabi na kawai ya kyaleta saboda ko yanzu yasan ta gane kuskurenta sannan ta fahimci shi ba sa'anta bane tunda gashi nan har hakuri take bashi,

Mayar da belt dinshi yayi ya daura yana kallonta, jikinta inbanda rawa kamar mazari babu abinda yake yi ta runtse idanuwanta ta gagara budesu,

"Mtsssss Allah ya sawwake na hada jiki da karuwa irinki wacce take bibiyar maza kala- kala,na tabbata idan na kusanceki sai na dauki cututtuka barkatai...."

Shureta yayi da kafarsa nan ta fadi sharaffff, ko kallonta bai sake yiba ya juya yayi tafiyarsa mintuna kadan ta daina hangoshi, duk irin radadi da ciwon da jikinta yake yi mata hakan bai hanata tashi da rugawa aguje ba, gudu take iya fin karfinta kamar zata kifa,tana ji tana tattaka abubuwa masu tsini suna shige mata cikin kafarta amma hakan baisa tafasa gudun ba,

Ko alamar shaddad bata gani bare ta saka ran zai sake biyota, kafin ta karasa gida tagama jigata,

Kamar yadda shaddad yabar gidan haka ta sameshi a bude nan ta lallaba ta shige tayi gaggawar hawa sama ta fada dakinta, kan gado tafada ta kankame jikinta wuri guda tana kakkarwa,

Gaba daya jinta take ta kasa tuna koda abu guda daya saboda tsananin tsoro da razani hadida fargaba da suka dabaibayeta,

Ta dade sosai kafin tasamu tadawo cikin nutsuwarta, ganin abinda yafaru take yi kamar acikin mafarki aka yishi,

Sai alokacin ciwon da jikinta yake yi yadawo sabo nan kafafunta wanda shaddad ya tattaka suka dauki ciwo gashi ko ina na jikinta radadi yake yi mata musamman ma tafin kafarta wanda bai saba jin wahala ba gashi yau ta tattaka k'aya da sauran abubuwa masu shiga k'afa,

Tana nan akwance tana tuna yanda abubuwan suka faru har ta jiyo an shiga masallaci sallar asuba,

"Shin yakamata na sanarwa da father wannan abun da yafaru kuwa..?" Ta tambayi kanta, juyawa tayi ta sake gyara kwanciyarta,

"Idan har nafadawa Dada wannan abun to nasan bazai taba hakura ba har sai ya dauki mummunan mataki akan shaddad gara kawai nayi shiru nayi hakuri sannan nabar abin acikin zuciyata ni kadai.."

Wuta ta kunna saboda taji alamun ankawo, kallon jikinta tayi duk yanda rigar baccinta tayi kaca kaca da kasa da tab'o,

"Ohhhh yaron nan gaskiya yanada karfi... Kalli fa rik'o daya yayi min nakasa k'wacewa.."

Haka tayita maganganu ita kadai amma ta rigada ta yankewa kanta hukunci cewar bazata sanar da kowa abinda shaddad yayi mata ba har mahaifinta tunda dai Allah ya taimaketa bai yi mata komai ba.

   Bandaki ta shiga ta tari ruwan zafi cikin baho ta surka da na sanyi tashiga tayi wanka ta gasa jikinta sosai saboda ko ina ciwo yake yimata,

Alwala tayi ta fito tayi salla sannan ta dauko first aid box dinta ta duba magungunan da ya dace da ita a yanzu wanda ya kamata tasha,

Zab'a tayi ta dauki ruwa dake ajiye agefen gadonta tasha taja bargo ta lulluba lokaci kadan zazzabi ya hau jikinta ga wani irin ciwo da kanta yake yi...


*_Ummi A'isha_*
*_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*



    _*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*


    _Dedicated to Maryam Qaumi_💕

    _Gaisuwa mai yawa ga masoyiyar ummi A'isha, wato Meenah 4eva tareda Khadija Magaji bk,da duk masoyana gaba daya.._

    *_18_*

aishaummi.blogspot.com

~~~Kwana tayi da zazzabi ajikinta ga matsanannacin ciwon kai dake addabarta,

Misalin karfe 10 nasafe Dada ya shigo dakin nata saboda har ya kammala shirin tafiya office rashin jin motsinta yasashi zuwa dubawa yagani ko lafiya,

Ido ta bude tasake rufe jikinta sosai da bargo domin bata son dada ya ga ciwukan dake jikinta,

"Daughter lafiya kuwa?" Dada yafada yana karasawa gaban gadon,

"Dada bana jin dadine yau dinnan da zazzabi natashi ga wani irin ciwon kai.."

Kanta dada ya dafa yana yimata sannu, kuku ya kira yace ya dan hado mata wani abun taci sai tasha magani, kasancewar akwai wurinda zaije shiyasa yatafi batare da ya tsaya yaga taci abincin ba,

Dakyar tasamu ta tashi ta zauna saboda radadin da jikinta keyi mata musamman ma tafin kafarta da kafofinta,

Blessing ce ta kawo mata indomie wacce aka dafa da naman kaza da kwai,

"Sorry anty, meya samu jikinki haka?"

Harara ta wullawa blessing sannan ta nuna mata hanyar fita da hannunta,

"Zo ki fice min adaki, kar ki sake ki dawo har sai idan nice na nemeki..."

Sum sum blessing ta fice daga cikin dakin tabarta tana cin indomie din data kawo mata,

Abincin take ci tana ganin shaddad yana yi mata gizo, wani irin masifaffen tsoronshi ne yake shigarta wanda ta kasa sanin dalili gefe daya kuma tunanin ta yadda akayi har ya shigo gidan yafita da ita take yi,

"Koda yake babu mamaki tunda shi ba bak'on gidan bane" ta fadi hakan acikin zuciyarta,

Abincin ta ture gefe ta dauki robar ruwa ta fara sha kafin daga baya ta debi magunguna ta sha.

  Kwananta biyu akwance tana zazzabi kafin ta Samu ta warware, office ta koma taci gaba da zuwa aikinta saboda yanzu ta dawo normal sai dai amma duk wanda yasanta ada idan yaganta ayanzu zai fahimci canjin dake tare da ita, domin yanzu bata doguwar magana gashi jikinta yayi sanyi komai asanyaye take aiwatar dashi duk da cewar dama can haka take da rashin son hayaniya to yanzu har gara da,

Tun ranar da shaddad yaso yayi mata wannan cin mutuncin tun aranar taso ta yakice tunaninshi amma hakan ya faskara,

A kowanne lokaci cikin ganin kyakkyawar fuskarshi take acikin zuciyarta, da farko tayi zaton abin na wasane sai daga baya ta fahimci ba haka bane,

Gaba daya yanzu tunanin shaddad yagama zame mata dimin da'iman daga baya dakanta ta fahimci cewar tashiga tarkon so da kauna, ganin zata yiwa kanta illa yasata nemanshi a waya amma abin haushi koda ta kira bata sameshi ba saboda wayar akashe take.

"Yanzu ya zanyi ni maryama...?"

Ta tambayi kanta tana tallafe da kumatunta acikin office dinta bayan ta kammala duba marassa lafiyar dake ziyartar office din nata,

"Guy dinnan nasan bazan taba samunsa ba domin ba zai iya aurena ba saboda haushina yake ji, kawai abinda yafi shine nabawa dr sameer ko dr yazeed dama na auri daya daga cikinsu,

Kai sai dai kuma gaskiya ni basuda wasu qualities din da nake son mijina ya mallaka,

Shaddad dai shi kadai shine namijin da nake ganin zai iya dani sannan zanji dadin zama dashi duk da nasan baya sona baya kaunata, asalima babu macen da yafi tsana irina...

Waima duk ba wannan ba yanzu a ina zan ganshi har na mallakeshi....?"

Wadannan sune tarin maganganun da take tayi acikin zuciyarta ita kadai sai kace zautacciya...

Sake gyara zamanta tayi ta dafe kanta ta zubawa teburinta idanu,

"Nifa ko sanin garinsu ma banyi ba yanzu wa zan tunkura da tambayar inda yake?"

Dabarace ta fado mata, "koda yake nasan ada shi mutumin dada ne babu mamaki watikil ya taba sanar da dada sunan garinsu, bari idan nakoma gida zan tambayi dada"

Mikewa tayi jikinta babu kwari tamkar marar lafiya ta nufi dakin yara, round tayi ta dudduba marassa lafiyar ta kammala ta fito domin yau bata jin zata iya kaiwa yamma acikin asibitin, gida kawai take son tafiya domin ta samu dada ta tambayeshi labarin shaddad......

*_Ummi Shatu_*
[5/12, 10:18 AM] Ummi Shat🏻: *_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*



    *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

   _Dedicated to Maryam Qaumi_💕

   _*19*_

aishaummi.blogspot.com

   ~~~Jikinta a sabule ta tashi ta fita tana rikeda key din motarta tana faman karkadashi sai dai kuma duk jikinta a sanyaye yake, babu wanda tayiwa sallama ta bude motarta ta shiga domin bata son damuwa,

Driving take hankalinta kwance idanuwanta na bisa titi, wayarta ta dauka ta kira dada ta tambayeshi ko yana gida, cikin sa'a yace mata yana gida tun rana ya dawo,

Katse wayar tayi ta sake bawa motar wuta ta nufi gida cikeda kwarin gwiwar abinda take son aikatawa,

Lokacin da ta shiga gida falon dada ta shiga direct ta iskeshi zaune yana rikeda jaridar daily trust yana karantawa, zama tayi ta yaye gyalen dake kanta ta kalli Dada,

"Barka da hutawa dada.."

"Yawwa barka da dawowa mai sunan mama, ya aikin?"

"Lafiya lau dada..."

Shiru tayi tafara nazarin ta inda ya kamata ta fara, can dai ta daure tayi magana,

"Uhm Dada nace nikuwa wannan sojan wanda da ya yake kaini asibiti da d'an wanne garine...?"

Dago da idonshi yayi daga kan magazine din da yake karantawa ya kalleta,

"Daughter meya faru? Lafiya kuwa?"

"Lafiya lau Dada dama musu muke yi da dr naz shine nace zan tambayeka.."

"Shi nazirun ina yace garinsu?"

Dan jim tayi kafin tabada amsa,

"Cewa yayi wai dan katsina ne.."

Jijjiga kai Dada yayi,

"Bana jin wannan yaron dan katsina ne sai dai ko wajen kano ko Kaduna amma ni gaskiya ban taba tambayarshi sunan garinsu ba.."

Murmushin yake maryama tayi ta mike tana kallon dada,

"Dada bari na shiga ciki nayi wanka..."

Dakinta ta shiga ta zauna ta rafka uban tagumi,tunani take shin yanzu awurin wa zata iya samo labarin shaddad da garin da yake?

Ganin bata samu mafita ba yasata tashi ta cire kayan jikinta ta shiga wanka, ko acikin bathroom dinma ganin shaddad tayi yana yimata gizo, dakyar ta samu ta kammala wankan ta fito ta zauna domin shiryawa,

Komai nata cikin sanyi takeyi domin damuwar dake kwance cikin zuciyarta tafi gaban wasa,

Doguwar riga brown colour tasa ta yafa mayafi ta dauki key din mota ta fita, headquarter din sojoji take son zuwa domin bincikawa ko Allah zaisa ta dace tasamu wanda ya sanshi,

Koda taje cikin rashin sa'a babu wani bayani ko kwaya daya data samu saboda sojojin da ake turowa nan Allah ne kadai yasan adadinsu,

Cikeda takaici da bacin rai hadeda kunar zuci ta fito ta koma gida, wani irin jiri taji yana daukarta sama sama wanda har yana barazanar kayar da ita, dakyar ta fara dafa bango ta samu ta haura zuwa dakinta,

Har wani kai kawo take ji numfashinta yake yi kamar zai fita daga jikinta babu shiri ta kwanta akan gado ta dafe goshinta tana kallon sama nan da nan taga dakin ya fara juya mata,

Runtse idanuwanta tayi wadanda suka kada suka yi jajur duk da tsananin farin da suke dashi,

Gaba daya ta gagara samun nutsuwarta balle tasan abinda ya kamata tayi, blessing ce ta turo kofa ta shigo tana dauke da kayan sawar maryama wanda aka wanke aka goge, drewar taje tafara jerasu daya bayan daya amma kuma sai take jin kamar nishi nishi,da sauri ta waiwaya ga maryama,

Ganinta tayi dafe da goshinta idanuwanta arufe tana yin numfashi sama sama,

Matsawa tayi kusa da ita, "sannu anty..."

Kai kawai maryama ta daga mata ta yi mata nuni da ta dauko mata first aid box dinta,

Cikin gaggawa blessing taje ta kinkimo mata shi ta kawo mata, dakyar ta iya yunkurawa ta tashi zaune ta bude box din ta dauki magani, da gudu blessing taje ta dauko mata ruwa roba daya ta kawo mata, maganin tasha ta zame ta sake kwanciya tana jin zuciyarta tana bugawa da sauri saboda tsananin soyayyar shaddad dake azalzalarta, jitake kamar ba zata iya rayuwa ba mutukar bata mallakeshi ba mallaki na har abada.......








*_Ummi Shatu_*

MARYAMA SARAUNIYA.. 14,15

[5/9, 9:42 AM] Ummi Shatu🏻: *_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*



   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*


     _Dedicated to Maryam Qaumi_💕


       *_14_*

aishaummi.blogspot.com

   ~~~Rufuwa samarin suka yi akanta suna kokarin rabata da sutturar dake jikinta, jin idan batayi dagaske ba zasu cimma manufarsu akanta yasata dagewa ta ciji hannun wanda ya toshe mata bakin babu shiri yayi azamar sakinta, wata kara mai karfi ta k'walla tareda kiran sunan shaddad akaro nafarko acikin rayuwarta,

"Shaddad...." Tafada cikin karaji,

Shaddad yana cikin mota zaune sai kunnensa yajiyo karar da maryama ta kwalla, bai gasgata cewar itace ba har sai da yaji ta ambaci sunanshi, cikin azama ya fito daga motar ko kulleta bai tsaya yiba ya nufi inda yake jiyo sautin muryarta, gashi ko ina na club din duhune dim babu haske ko kadan sai ko na farin wata,

Bayan club din ya nufa jikinsa har wani rawa yake saboda tsananin gigita, yana zuwa ya iske samari fal sunyi mata runfa har sun kusa rabata da sutturar dake jikinta, bindigarsa ya ciro ya harbi sama ji kake, tauuuu...!!

Babu bata lokaci samarin suka baje kowa yayi ta kansa, maryama dake kwance sai faman kankame jikinta take yi ta samu ta mike da kyar sai layi take tana tangadi kamar wacce tasha kayan maye,

Ko kallonta baiyiba ya juya yafara tafiya, da saurinta tabi bayanshi batare data tsaya daukar gyalenta ba wanda yafadi awurin,

Jikake garammm lokacin da ya shiga motar ya rufeta,

"Washhhh...!" Tafada tana runtse idonta bayan ta danna kafafunta domin dama can ciwo suke yimata kuma gashi yanzu an tattaka mata su,

Kallonta yayi zuciyarsa na radadi da tafarfasa wanda bai san dalili ba,

"Sunyi miki wani abune?" Ya tambayeta yana kallonta cikeda tsana,

Kai ta girgiza masa alamun a'a, bai sake magana ba ya kunna motar suka bar wurin,

Tsaki yaja mai karfin gaske sannan yafara magana cikin zafin rai,

"Ni ban taba ganin mahaukaciya, marar tunani, jahila, marar kamun kai irinki ba, kowacce mace tana adana halittar da Allah yayi mata, tana kare mutuncinta amma banda ke, ke kullum burinki shine ki bayyanar da surar da Allah yayi miki..."

Dauke kanta tayi alamun maganganun nashi basu shigeta ba, nan yaci gaba,

"In banda iskanci da rashin ilmi da rashin sanin yakamata ina macen kirki da zuwa club, mace indai ta arziki ce babu abinda ya danganta ta da club, idan kina ganin hakan kamar wayewa ne ko kuma wata burgewa ce to wallahi kinyi kuskure domin ba hali ne mai kyau ba, duk macen dake zuwa wannan wurin karuwa ce..."

Cikin razani ta juyo tana kallonsa lokaci guda fuskarta ta sauya,

"Wacece karuwan??"

Ta fada cikin bacin rai da masifa,

"Ke mana, keda mecece idan ba karuwa ba, bakida maraba da karuwai..."

Nunashi tayi da yatsa, "karka kara kirana da karuwa.."

Packing din motar yayi agefen titi ya juya yana kallonta cikin bacin rai,

"Idan ankiraki da karuwan me kika isa kiyi? Kinada wani sunan ne bayada wannan? Ke karuwace cikakkiya..."

"Naji ni karuwace amma da kanwarka ko yayarka muke karuwancin tare..."

Tun kafin ta karasa rufe bakinta ya dauketa da wani gigitaccen mari wanda yayi barazanar makantar da ita domin lokaci guda ta nemi ganinta ta rasa sannan taji kanta ya dauki ciwo yana barazanar barin jikinta ga wani jiri da yafara daukarta,

Nunata yayi da dan yatsa,

"Ki iya bakinki, ni duk dangina babu yan iska sannan babu karuwai aciki..."

Dakyar ta iya bude idonta ta kalleshi tana mai jin wani bakin ciki yana shigarta sanadiyyar marin da yayi mata domin tunda take a duniya babu namijin da yataba gigin kai hannunsa fuskarta da sunan mari amma yau wannan yaron da baifi Sa,anta ba wai shine ya mareta,

"Ka mareni..?"

"An mareki din ko zaki ramane?" Yabata amsa yana huci,

"Wallahi sai na rama, bazaka taba marina kuma ka zauna lafiya ba, kamar yadda kace ni karuwace to zan nuna maka cewar ni din karuwarce cikakkiya kamar yadda kafada, wallahi bazan yarda ba..."

Tafada idanuwanta sun kada sunyi jajur, fuskarta kuwa har ta kumbura musamman barin da ya mareta, hatta hakorinta dake barin sun kumbura sun fara yimata ciwo,

"Karki fasa ki rama idan baki ramaba ke ba yar halak bace.." Yafada yana huci,

Murmushin takaici tayi ta gyara zamanta tana shafa kuncinta da ya Mara,

"Sai na nuna maka kai yarone karami, wallahi sai na koyar dakai babban darasi.."

"Karki fasa.."

Bata kara magana ba shima bai sake koda kallonta ba ya figi motar, suna zuwa gida yayi packing ya cilla mata key din motar kan cinyarta ya fita yayi gaba ransa yana wani irin zafi,

Har lokacin maryama na dafe da kuncinta tana kallonsa zuciyarta tana yimata wani irin kuna sakamakon marin da shaddad yayi mata gashi wai ita ya kalla ya kira da karuwa,

Fita tayi ta rufe motar tabarta anan ta shiga cikin gida, bedroom dinta ta shiga ta kunna wuta ta karasa gaban mudubi tana bin fuskarta da kallo....


*_Ummi A'isha_*🏻
[5/9, 9:42 AM] Ummi Shatu🏻: *_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*

   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Dedicated to Maryam Qaumi_💕


   *_15_*

~~~ Ji take kamar ta fashe da kuka sai dai kuma ta dauki alwashin bazata taba yiwa wannan yaron kuka ba kome zaiyi mata,

Kallon fuskarta taci gaba dayi wanda take a kumbure sannan ga shatin yan yatsun shaddad nan sun fito rado rado ajiki,

Girgiza kai tayi ta Shiga bathroom tayi wanka tafito, rigar baccinta ta zira ta fiddo kwalabin benalin guda hudu ta shanye saboda jin ranta take yana sake dagule mata,

Babu bata lokaci bacci yayi gaba da ita, da safe kuwa da wani irin zazzabi ta tashi ajikinta wanda tasan marin da shaddad yayi matane sanadinshi,

Ko tashi kasawa tayi har saida blessing ta shigo ta taimaka mata ta rakata toilet tayi wanka tafito, har lokacin fuskarta tana nan a kumbure,

Komawa tayi ta sake lwanciya ta lulluba tana mai jin tsanar shaddad acikin ranta,

Wuni guda tana kwance bata ci komai ba dakyar ta iya tashi tasha ruwan tea ta kwanta, koda shaddad yazo kaita office blessing cemasa tayi bata da lafiya, kafada kawai ya daga alamun ko oho yayi tafiyarsa.

Da yamma misalin karfe 5 dr naz yazo gidan duba maryaman, har dakinta ya shiga shida blessing domin ganin jikin nata, blessing ya tambaya ko tasha magani tace a'a nan yafara yimata magana,

"Haba dr ya za ace bakida lafiya amma bakisha maganiba? Meyasa?"

Dakyar ta bude idonta wadanda suke jajur ta kalleshi,

"Zansha dr so nake sai natashi lokacin naji karfin jikina.."

"To bari nayi miki allura inyaso idan kika tashi sai kisha magani.."

Dakyar ta yarda dr naz yayi mata allurar a hannu saboda tana tsananin tsoron allura ko kadan bata sonta,

Murmushi dr naz yayi yana kallonta bayan ya zare allurar daga jikinta,

"Ke baki son allura amma kuma kinfi kowa yiwa mutane allura,koda yake ashe fa ance doctors sunfi tsoron allura.."

Kwanciya tayi tasake lulluba, "nagode likita"

Sallama yayi mata yatafi, ahaka tasake kwana da zazzabin gashi jini har yataru a idonta guda daya wanda shaddad ya mareta, washe gari ma sai da dr naz yasake dawowa yayi mata allurar.

Sai da ta kwana uku tana zazzabi kafin ta dan warware,akwana na hudune ta shirya fita office, koda shaddad yazo kaita bata musaba ta shiga suka tafi yakaita ya sauketa sai dai amma ko k'ala bata shiga tsakaninsu ba, lokacin da ta tashi ma haka ya koma ya daukota,

Kullum haka yake kaita ya daukota sai dai babu kalmar dake hadasu,shi dai yanzu yagama sanin wacece maryama, kaf halayenta babu wanda bai saniba hatta shaye shayen datake yasani

Ranar juma'a da daddare mahaifinta yadawo daga tafiyar da yayi zuwa saudiyya, shaddad yayi mutukar mamaki jin bata sanar da Dada cewar ya mareta ba, harkarta kawai taci gaba dayi,

Tana zaune afalon dada da medical glass a idonta gabanta kuma laptop dintace ajiye tana kallon wani american film _iron man_,sanye take da pink colour din doguwar riga mai hannun shimi kanta babu dan kwali, gefenta kuma Dada ne zaune yana cin tuwon alkama miyar kubewa danya, hira suke yi ita tana kallon film din data kunna shikuma Dada yana kallon tv,

"Father zan samu rancen kudi.."

Kafin yabata amsa shaddad yaturo kofa ya shigo hannunsa rikeda envelope babba,

Zama yayi suka gaisa da dada ya mika masa envelope din,

"Mai sunan mama me zakiyi da kudi idan nabaki rence?" Dada yafada yana bude envelope din da shaddad yabashi,

"Dada ginin asibitina da aka fara yifa ya tsaya gashi ko rabi ba ayiba kuma wallahi banida kudi, shine nake son ka ara min 3 millions adan kara tsayin ginin.."

Dariya dada ya danyi yaciro zungureriyar takardar dake nade cikin envelope din yafara dubawa,

"Daughter dama shi gini ai sai da kudi, shiyasa nace miki kibari sai kin tara kudi sosai sai kiyi ginin amma haka kawai kika tsiri gini ba kadanba bayan baki tara kudiba.."

Juyawa yayi ga shaddad ya kalleshi,

"Masu tafiya Niger delta dinnan aka turo, jiyama munyi meeting kan cewa za atura sojoji ta ruwa zuwa Benin to amma bana jin za atura dakai.."

"Ah ranka yadade ai da antura ni nima ina son zuwa kawai dai matsalar banida lafiya ne dan zazzabi ne ke damuna"

Shaddad yafada yana murmushi,

"Allah yabada lafiya, ga maryama nan ai sai tayi maka allura ko?"

Girgiza kai yayi "nasha magani ai Yallabai"

Tashi Dada yayi ya shiga cikin bedroom dinshi,

"Nima dama ba yimaka allurar zanyi ba, maza nawa nagani irinka atube..?" Yajiyo muryar maryama tana yimasa gatsali,

Ko saurarenta baiyiba yamaida hankalinsa kan tv,amma aranshi cewa yake,

"Dama nasan ai kin ga maza irina dayawa tsirara koda baki fada ba.."

Bai sake kallon inda take ba har dada yafito suka gama abinda zasuyi yayi masa sallama yatafi.

Yau kimanin sati uku kenan da marin maryama da shaddad yayi,

Yana kwance adakinsa yana bacci yaji karar wayarshi, hannu ya mika ya katse kiran, nan aka sake kira, sai da aka kira wurin sau biyar sannan yatashi yana dubawa, bakuwar number yagani nan ya kalli agogo,karfe 2 nadare,

Kara wayar yayi a kunnenshi nan yaji muryar mace tana kuka,

"Shaddad ka taimaka min Dada babu lafiya kazo mu kaishi asibiti, dan Allah kayi sauri ko motsi bayayi gashi acikin dakina, wayyo nashiga uku..."

Ko ba afada masa ba yasan maryama ce saboda ya gane muryarta,dagashi sai dogon wando da singileti ta maza ko neman riga bai tsaya yiba ya fita da sauri, tsabar gaggawa ma agida yabar wayar tashi,

Yana zuwa gidan ana dauke wuta, acikin duhun yasamu ya kutsa ya tasamma dakin maryama, yana shiga yafara jiyo shesshekar kukanta,

"Maryam, kunna fitila mana, ina Yallabai din yake, maryam kunna haske.."

Yana wadannan maganganun yana tafiya domin karasawa gadonta, caraf yaji an makaleshi tareda jefashi kan gadon, nan ta haye jikinsa ta kwalla kara mai mutukar karfi,

Kansa ne ya daure gaba daya yana tunanin to meye yake shirin faruwa, makalkaleshi yaji ta sakeyi tana ihu, kafin yayi wani yunkuri har dada ya shigo cikin dakin kuma daidai lokacin NEPA suka dawo da wuta mai karfin gaske, mirginawa tayi karkashinsa ya zama shine asamanta,

Duk gashin kanta ya tarwatse, rigarta anfara yagata,tana rungume dashi sai ihu take kwallawa,

Tsayawa dada yayi yana kallon shaddad fuskarsa a daure, kafin wani lokaci har gidan yacika da mazauna barikin wadanda suka shigo domin bayar da taimako saboda sun jiyo karar maryama,

Tashi tayi dagudu taje ta tsaya a bayan dada tana kuka,

"Wayyo dada nashiga uku.."

Shikam shaddad yama kasa motsi yana zaune akan gadon kansa a daure,

Wata tsawa dada ya daka masa mai sa firgici,

"Kai shaddad ashe bakada mutunci ban saniba? Yar tawa kwaya daya zaka lalatawa rayuwa kayi mata fyade? Na daukeka kamar dan da nahaifa acikina shine zaka yimin mummunar sakayya? To daga yau sai yau karka sake shigo min cikin gidana sannan babu kai babu yata, kuma sai kabar garin nan agobe ba jibiba, sannan sai na dauki mummunan mataki akanka..., get out!"

Tashi shaddad yayi batare da yayi magana ba sai dai idanuwansa sun kada sunyi jajur, ko musu baiyiba domin yasan zaiyi wahala a yarda dashi kasancewar ankamashi red handed, wato dumu dumu,

Daga idanuwansa yayi ya kalli maryama wadda ke tsaye tana yimasa murmushin mugunta sai yanzu yagane ashe makirci ta shirya masa,

Fita yayi daga gidan cikeda kunya da takaici domin yasan yanzu duk jama'ar wurin zasu daina ganin kimarshi sannan sun gama yadda cewar kwadayine yakaishi dakin maryama har yaso yimata fyade,

Gida yakoma yanemi wuri ya zauna yana kukan zuci, ji yake kamar ya kira mahaifiyarshi ya sanar da ita halin da ya shiga sai dai kuma baya son ya daga mata hankali, wayarshi ce tadauki ruri yadaga batare da yayi magana ba,

"Hello, yanzu nasan kagama tabbatar da cewa maryama cikakkiyar karuwace kamar yadda ka fada....."

Kit ya katse wayar yana rike da kanshi, har gari yawaye idonshi biyu, shiryawa yayi ya tattara kayansa domin yasan yau zai bar garin Lagos koda baya so saboda zai bi sahun wadanda za atura Benin,

Fita yayi zuwa headquarter amma duk inda ya gifta maganarshi akeyi cewar yaje yiwa maryama fyade, abokinshi Abbas ne kawai ya tareshi da maganar yace yasan bazai aikata hakaba, nan ya kwashe duk abinda yafaru ya fadawa Abbas,

Posting letter dinshi yaje ya karba saboda dama an rigada an buga sai dai kawai arubuta sunan mutum abashi yayi signing,

Barikin yakoma ya tattara komai nasa ya fito yana mai yiwa barikin kallon karshe saboda yasan shida sake dawowa ciki har abada...


*_Ummi A'isha_*

MARYAMA SARAUNIYA.. 14,15

[5/9, 9:42 AM] Ummi Shatu🏻: *_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*



   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*


     _Dedicated to Maryam Qaumi_💕


       *_14_*

aishaummi.blogspot.com

   ~~~Rufuwa samarin suka yi akanta suna kokarin rabata da sutturar dake jikinta, jin idan batayi dagaske ba zasu cimma manufarsu akanta yasata dagewa ta ciji hannun wanda ya toshe mata bakin babu shiri yayi azamar sakinta, wata kara mai karfi ta k'walla tareda kiran sunan shaddad akaro nafarko acikin rayuwarta,

"Shaddad...." Tafada cikin karaji,

Shaddad yana cikin mota zaune sai kunnensa yajiyo karar da maryama ta kwalla, bai gasgata cewar itace ba har sai da yaji ta ambaci sunanshi, cikin azama ya fito daga motar ko kulleta bai tsaya yiba ya nufi inda yake jiyo sautin muryarta, gashi ko ina na club din duhune dim babu haske ko kadan sai ko na farin wata,

Bayan club din ya nufa jikinsa har wani rawa yake saboda tsananin gigita, yana zuwa ya iske samari fal sunyi mata runfa har sun kusa rabata da sutturar dake jikinta, bindigarsa ya ciro ya harbi sama ji kake, tauuuu...!!

Babu bata lokaci samarin suka baje kowa yayi ta kansa, maryama dake kwance sai faman kankame jikinta take yi ta samu ta mike da kyar sai layi take tana tangadi kamar wacce tasha kayan maye,

Ko kallonta baiyiba ya juya yafara tafiya, da saurinta tabi bayanshi batare data tsaya daukar gyalenta ba wanda yafadi awurin,

Jikake garammm lokacin da ya shiga motar ya rufeta,

"Washhhh...!" Tafada tana runtse idonta bayan ta danna kafafunta domin dama can ciwo suke yimata kuma gashi yanzu an tattaka mata su,

Kallonta yayi zuciyarsa na radadi da tafarfasa wanda bai san dalili ba,

"Sunyi miki wani abune?" Ya tambayeta yana kallonta cikeda tsana,

Kai ta girgiza masa alamun a'a, bai sake magana ba ya kunna motar suka bar wurin,

Tsaki yaja mai karfin gaske sannan yafara magana cikin zafin rai,

"Ni ban taba ganin mahaukaciya, marar tunani, jahila, marar kamun kai irinki ba, kowacce mace tana adana halittar da Allah yayi mata, tana kare mutuncinta amma banda ke, ke kullum burinki shine ki bayyanar da surar da Allah yayi miki..."

Dauke kanta tayi alamun maganganun nashi basu shigeta ba, nan yaci gaba,

"In banda iskanci da rashin ilmi da rashin sanin yakamata ina macen kirki da zuwa club, mace indai ta arziki ce babu abinda ya danganta ta da club, idan kina ganin hakan kamar wayewa ne ko kuma wata burgewa ce to wallahi kinyi kuskure domin ba hali ne mai kyau ba, duk macen dake zuwa wannan wurin karuwa ce..."

Cikin razani ta juyo tana kallonsa lokaci guda fuskarta ta sauya,

"Wacece karuwan??"

Ta fada cikin bacin rai da masifa,

"Ke mana, keda mecece idan ba karuwa ba, bakida maraba da karuwai..."

Nunashi tayi da yatsa, "karka kara kirana da karuwa.."

Packing din motar yayi agefen titi ya juya yana kallonta cikin bacin rai,

"Idan ankiraki da karuwan me kika isa kiyi? Kinada wani sunan ne bayada wannan? Ke karuwace cikakkiya..."

"Naji ni karuwace amma da kanwarka ko yayarka muke karuwancin tare..."

Tun kafin ta karasa rufe bakinta ya dauketa da wani gigitaccen mari wanda yayi barazanar makantar da ita domin lokaci guda ta nemi ganinta ta rasa sannan taji kanta ya dauki ciwo yana barazanar barin jikinta ga wani jiri da yafara daukarta,

Nunata yayi da dan yatsa,

"Ki iya bakinki, ni duk dangina babu yan iska sannan babu karuwai aciki..."

Dakyar ta iya bude idonta ta kalleshi tana mai jin wani bakin ciki yana shigarta sanadiyyar marin da yayi mata domin tunda take a duniya babu namijin da yataba gigin kai hannunsa fuskarta da sunan mari amma yau wannan yaron da baifi Sa,anta ba wai shine ya mareta,

"Ka mareni..?"

"An mareki din ko zaki ramane?" Yabata amsa yana huci,

"Wallahi sai na rama, bazaka taba marina kuma ka zauna lafiya ba, kamar yadda kace ni karuwace to zan nuna maka cewar ni din karuwarce cikakkiya kamar yadda kafada, wallahi bazan yarda ba..."

Tafada idanuwanta sun kada sunyi jajur, fuskarta kuwa har ta kumbura musamman barin da ya mareta, hatta hakorinta dake barin sun kumbura sun fara yimata ciwo,

"Karki fasa ki rama idan baki ramaba ke ba yar halak bace.." Yafada yana huci,

Murmushin takaici tayi ta gyara zamanta tana shafa kuncinta da ya Mara,

"Sai na nuna maka kai yarone karami, wallahi sai na koyar dakai babban darasi.."

"Karki fasa.."

Bata kara magana ba shima bai sake koda kallonta ba ya figi motar, suna zuwa gida yayi packing ya cilla mata key din motar kan cinyarta ya fita yayi gaba ransa yana wani irin zafi,

Har lokacin maryama na dafe da kuncinta tana kallonsa zuciyarta tana yimata wani irin kuna sakamakon marin da shaddad yayi mata gashi wai ita ya kalla ya kira da karuwa,

Fita tayi ta rufe motar tabarta anan ta shiga cikin gida, bedroom dinta ta shiga ta kunna wuta ta karasa gaban mudubi tana bin fuskarta da kallo....


*_Ummi A'isha_*🏻
[5/9, 9:42 AM] Ummi Shatu🏻: *_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*

   *_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

    _Dedicated to Maryam Qaumi_💕


   *_15_*

~~~ Ji take kamar ta fashe da kuka sai dai kuma ta dauki alwashin bazata taba yiwa wannan yaron kuka ba kome zaiyi mata,

Kallon fuskarta taci gaba dayi wanda take a kumbure sannan ga shatin yan yatsun shaddad nan sun fito rado rado ajiki,

Girgiza kai tayi ta Shiga bathroom tayi wanka tafito, rigar baccinta ta zira ta fiddo kwalabin benalin guda hudu ta shanye saboda jin ranta take yana sake dagule mata,

Babu bata lokaci bacci yayi gaba da ita, da safe kuwa da wani irin zazzabi ta tashi ajikinta wanda tasan marin da shaddad yayi matane sanadinshi,

Ko tashi kasawa tayi har saida blessing ta shigo ta taimaka mata ta rakata toilet tayi wanka tafito, har lokacin fuskarta tana nan a kumbure,

Komawa tayi ta sake lwanciya ta lulluba tana mai jin tsanar shaddad acikin ranta,

Wuni guda tana kwance bata ci komai ba dakyar ta iya tashi tasha ruwan tea ta kwanta, koda shaddad yazo kaita office blessing cemasa tayi bata da lafiya, kafada kawai ya daga alamun ko oho yayi tafiyarsa.

Da yamma misalin karfe 5 dr naz yazo gidan duba maryaman, har dakinta ya shiga shida blessing domin ganin jikin nata, blessing ya tambaya ko tasha magani tace a'a nan yafara yimata magana,

"Haba dr ya za ace bakida lafiya amma bakisha maganiba? Meyasa?"

Dakyar ta bude idonta wadanda suke jajur ta kalleshi,

"Zansha dr so nake sai natashi lokacin naji karfin jikina.."

"To bari nayi miki allura inyaso idan kika tashi sai kisha magani.."

Dakyar ta yarda dr naz yayi mata allurar a hannu saboda tana tsananin tsoron allura ko kadan bata sonta,

Murmushi dr naz yayi yana kallonta bayan ya zare allurar daga jikinta,

"Ke baki son allura amma kuma kinfi kowa yiwa mutane allura,koda yake ashe fa ance doctors sunfi tsoron allura.."

Kwanciya tayi tasake lulluba, "nagode likita"

Sallama yayi mata yatafi, ahaka tasake kwana da zazzabin gashi jini har yataru a idonta guda daya wanda shaddad ya mareta, washe gari ma sai da dr naz yasake dawowa yayi mata allurar.

Sai da ta kwana uku tana zazzabi kafin ta dan warware,akwana na hudune ta shirya fita office, koda shaddad yazo kaita bata musaba ta shiga suka tafi yakaita ya sauketa sai dai amma ko k'ala bata shiga tsakaninsu ba, lokacin da ta tashi ma haka ya koma ya daukota,

Kullum haka yake kaita ya daukota sai dai babu kalmar dake hadasu,shi dai yanzu yagama sanin wacece maryama, kaf halayenta babu wanda bai saniba hatta shaye shayen datake yasani

Ranar juma'a da daddare mahaifinta yadawo daga tafiyar da yayi zuwa saudiyya, shaddad yayi mutukar mamaki jin bata sanar da Dada cewar ya mareta ba, harkarta kawai taci gaba dayi,

Tana zaune afalon dada da medical glass a idonta gabanta kuma laptop dintace ajiye tana kallon wani american film _iron man_,sanye take da pink colour din doguwar riga mai hannun shimi kanta babu dan kwali, gefenta kuma Dada ne zaune yana cin tuwon alkama miyar kubewa danya, hira suke yi ita tana kallon film din data kunna shikuma Dada yana kallon tv,

"Father zan samu rancen kudi.."

Kafin yabata amsa shaddad yaturo kofa ya shigo hannunsa rikeda envelope babba,

Zama yayi suka gaisa da dada ya mika masa envelope din,

"Mai sunan mama me zakiyi da kudi idan nabaki rence?" Dada yafada yana bude envelope din da shaddad yabashi,

"Dada ginin asibitina da aka fara yifa ya tsaya gashi ko rabi ba ayiba kuma wallahi banida kudi, shine nake son ka ara min 3 millions adan kara tsayin ginin.."

Dariya dada ya danyi yaciro zungureriyar takardar dake nade cikin envelope din yafara dubawa,

"Daughter dama shi gini ai sai da kudi, shiyasa nace miki kibari sai kin tara kudi sosai sai kiyi ginin amma haka kawai kika tsiri gini ba kadanba bayan baki tara kudiba.."

Juyawa yayi ga shaddad ya kalleshi,

"Masu tafiya Niger delta dinnan aka turo, jiyama munyi meeting kan cewa za atura sojoji ta ruwa zuwa Benin to amma bana jin za atura dakai.."

"Ah ranka yadade ai da antura ni nima ina son zuwa kawai dai matsalar banida lafiya ne dan zazzabi ne ke damuna"

Shaddad yafada yana murmushi,

"Allah yabada lafiya, ga maryama nan ai sai tayi maka allura ko?"

Girgiza kai yayi "nasha magani ai Yallabai"

Tashi Dada yayi ya shiga cikin bedroom dinshi,

"Nima dama ba yimaka allurar zanyi ba, maza nawa nagani irinka atube..?" Yajiyo muryar maryama tana yimasa gatsali,

Ko saurarenta baiyiba yamaida hankalinsa kan tv,amma aranshi cewa yake,

"Dama nasan ai kin ga maza irina dayawa tsirara koda baki fada ba.."

Bai sake kallon inda take ba har dada yafito suka gama abinda zasuyi yayi masa sallama yatafi.

Yau kimanin sati uku kenan da marin maryama da shaddad yayi,

Yana kwance adakinsa yana bacci yaji karar wayarshi, hannu ya mika ya katse kiran, nan aka sake kira, sai da aka kira wurin sau biyar sannan yatashi yana dubawa, bakuwar number yagani nan ya kalli agogo,karfe 2 nadare,

Kara wayar yayi a kunnenshi nan yaji muryar mace tana kuka,

"Shaddad ka taimaka min Dada babu lafiya kazo mu kaishi asibiti, dan Allah kayi sauri ko motsi bayayi gashi acikin dakina, wayyo nashiga uku..."

Ko ba afada masa ba yasan maryama ce saboda ya gane muryarta,dagashi sai dogon wando da singileti ta maza ko neman riga bai tsaya yiba ya fita da sauri, tsabar gaggawa ma agida yabar wayar tashi,

Yana zuwa gidan ana dauke wuta, acikin duhun yasamu ya kutsa ya tasamma dakin maryama, yana shiga yafara jiyo shesshekar kukanta,

"Maryam, kunna fitila mana, ina Yallabai din yake, maryam kunna haske.."

Yana wadannan maganganun yana tafiya domin karasawa gadonta, caraf yaji an makaleshi tareda jefashi kan gadon, nan ta haye jikinsa ta kwalla kara mai mutukar karfi,

Kansa ne ya daure gaba daya yana tunanin to meye yake shirin faruwa, makalkaleshi yaji ta sakeyi tana ihu, kafin yayi wani yunkuri har dada ya shigo cikin dakin kuma daidai lokacin NEPA suka dawo da wuta mai karfin gaske, mirginawa tayi karkashinsa ya zama shine asamanta,

Duk gashin kanta ya tarwatse, rigarta anfara yagata,tana rungume dashi sai ihu take kwallawa,

Tsayawa dada yayi yana kallon shaddad fuskarsa a daure, kafin wani lokaci har gidan yacika da mazauna barikin wadanda suka shigo domin bayar da taimako saboda sun jiyo karar maryama,

Tashi tayi dagudu taje ta tsaya a bayan dada tana kuka,

"Wayyo dada nashiga uku.."

Shikam shaddad yama kasa motsi yana zaune akan gadon kansa a daure,

Wata tsawa dada ya daka masa mai sa firgici,

"Kai shaddad ashe bakada mutunci ban saniba? Yar tawa kwaya daya zaka lalatawa rayuwa kayi mata fyade? Na daukeka kamar dan da nahaifa acikina shine zaka yimin mummunar sakayya? To daga yau sai yau karka sake shigo min cikin gidana sannan babu kai babu yata, kuma sai kabar garin nan agobe ba jibiba, sannan sai na dauki mummunan mataki akanka..., get out!"

Tashi shaddad yayi batare da yayi magana ba sai dai idanuwansa sun kada sunyi jajur, ko musu baiyiba domin yasan zaiyi wahala a yarda dashi kasancewar ankamashi red handed, wato dumu dumu,

Daga idanuwansa yayi ya kalli maryama wadda ke tsaye tana yimasa murmushin mugunta sai yanzu yagane ashe makirci ta shirya masa,

Fita yayi daga gidan cikeda kunya da takaici domin yasan yanzu duk jama'ar wurin zasu daina ganin kimarshi sannan sun gama yadda cewar kwadayine yakaishi dakin maryama har yaso yimata fyade,

Gida yakoma yanemi wuri ya zauna yana kukan zuci, ji yake kamar ya kira mahaifiyarshi ya sanar da ita halin da ya shiga sai dai kuma baya son ya daga mata hankali, wayarshi ce tadauki ruri yadaga batare da yayi magana ba,

"Hello, yanzu nasan kagama tabbatar da cewa maryama cikakkiyar karuwace kamar yadda ka fada....."

Kit ya katse wayar yana rike da kanshi, har gari yawaye idonshi biyu, shiryawa yayi ya tattara kayansa domin yasan yau zai bar garin Lagos koda baya so saboda zai bi sahun wadanda za atura Benin,

Fita yayi zuwa headquarter amma duk inda ya gifta maganarshi akeyi cewar yaje yiwa maryama fyade, abokinshi Abbas ne kawai ya tareshi da maganar yace yasan bazai aikata hakaba, nan ya kwashe duk abinda yafaru ya fadawa Abbas,

Posting letter dinshi yaje ya karba saboda dama an rigada an buga sai dai kawai arubuta sunan mutum abashi yayi signing,

Barikin yakoma ya tattara komai nasa ya fito yana mai yiwa barikin kallon karshe saboda yasan shida sake dawowa ciki har abada...


*_Ummi A'isha_*

MARYAMA SARAUNIYA.. 12,13

[5/7, 8:20 PM] Ummi Shatu: *_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*


    _*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

    _Dedicated to Maryam Qaumi_💕

  _Gaisuwar fatan alkairi agareki Khadijat Buba, naci karo da sakonki kuma nagode, hakika nima ina yinki kamar yadda kike yina.._


   *_12_*

aishaummi.blogspot.com

   ~~~Tashin motar shaddad yayi batare da yako dubi Inda takeba, amma ta gefen idonshi yana kallonta tana dagawa alhaji bashir hannu ta cikin glass,

Sake hade fuska tayi ta bata rai saboda jin shaddad yanata aikin jan tsaki shikadai, maimakon ma ta zauna shiru sai ta dauki wayarta tafara kiran fahad abokinta,

Yana jinta ta karaci wayarta tagama lokacin da suka shiga cikin barikin, packing yayi ta bude ta fita shikuma ya shigar da motar cikin garage,

Ko cikin gidan nasu bai koma ba ya mikewarsa gidanshi domin yagama gajiya gashi ransa abace yake saboda ayanda ya fuskanta ana neman takura masa ta hanyar tirsasashi ya rinka bautawa maryama bayan kuma ita ba kintsattsiya bace, tsaki yasake ja ya bude gidan ya shiga,

Gefen katifarshi yaje ya zauna yafara rage kayan jikinshi yana yi yana tsaki har yagama cirewa,

Wani dogon tsakin yasake ja ya kwanta agefen katifar, tunani yake yi shima fa kila yanada nasa kason zunubin tunda shine ya dauketa ya kaita guest house din,

Haka yayita tunane tunane har yasamu yayi bacci. Washe gari kuwa bai fita da wuriba saboda sai misalin karfe 11:30,kansa tsaye ya shiga gidan yana sanye da jar riga da brown din wando fuskarshi babu annuri, a falon kasa ya iske maryama zaune daga ita sai rigar bacci wata Christian tana yimata kitso akanta, duk da bai san kallonta amma sai da ya dan sake dubanta domin ganin gashin kanta yayi shuri guda sai dai zuciyarshi tafi aminta da cewar na dokine ake kara mata saboda yawan gashin ya isa,

Wucewa yayi falon Dada Wanda shi tuntuni ma ya dade da fita daga gidan amma maryama tana kallonshi ta rabu dashi domin aganinta shine yafi cancanta da yafara yimata magana amma kawai tsabar isa da gadara yazo ya wani wuce kansa tsaye sai kace gidanshi,

Sai da shaddad ya shiga falon sannan ya tabbatar da cewa Dada baya nan, fitowa yayi hannayenshi acikin aljihunsa da niyyar barin gidan,

"Am kaga, kajirani na shirya yanzu zaka kaini office.."

Yajiyo muryarta cikin gadara da sigar bada umarni tana yi masa magana, batare da ya juyoba yawuce abinshi ya fita,

Tsaki taja ta mike tana karkade jikinta saboda angama yimata kitson domin manya manya ne ba kanana ba, bedroom dinta ta shiga ta shiga bathroom, wanka tayi ta fito tana daure da towel kamar wacce aka cewa ta leka window sai ta nufi wurin taje ta dauke labulen dake jiki ta leka, shaddad ta hango zaune asaman motarta sai cilla key din motar yake sama yana cafewa ba karamin kyau yayi ba gashi komai nashi yana yine cikin zafi zafi irin na jajartattun mazaje, amma shi bai ganta ba,

Sakin labulen tayi ta dawo tsakiyar dakin tafara shiryawa, wata shudiyar doguwar riga roba tasaka wacce ta kamata tayi mata das sannan ta bayyanar da shape din jikinta a fili,

Komai kalar shudi tasaka kama tun daga barimar kunnenta harta kan hancinta har zuwa takalmi da jaka,

Fuska a yatsine tafito tana kiran blessing domin ta dauko mata kayanta tabita dashi,

Shaddad yana zaune yana ganin fitowarta sai faman shan shan kamshi take tana wani bata rai,

"Banza karuwa..." Yafada acikin zuciyarsa amma afili sai yasake daure fuskarsa saboda shi yanzu ya tsani koda ganin fuskarta ne saboda duk farar fatar datake da ita to shi bakikkirin yake ganinta,

Sauka yayi daga saman motar ya bude ya shiga, itama cikeda takama tabude gaba ta zauna tana sake shan kunu,

Kiran fahad ne ya shigo wayar tata nan ta dauka cikeda yanga, tana gama waya dashi kiran dr naz ya shigo,

"Hello naz.." Tafada tana kallon fuskarta ajikin mudubin motar,

"Dr yau ko bazaki shigo bane? Gashi inata kiranki number busy dawa kike waya..?"

Sai da ta dan yi dariya kafin tabashi amsa saboda jin yanda yayi maganar sai kace wani shine gaba da ita,

"Dr naz kenan gani nan ahanya nataho nida driver na, sannan wayar da kaga inayi ba kowa bane fahad ne shikuwa kasan friend dinane ba saurayi na bane kawai mun zauna room daya dashi ne a Malaysia har muka gama karatu.."

"Iya matsayinsa kenan?" Dr naz yasake tambayarta,

"Wallahi matsayinshi kenan, lokacin da naje ban samu accommodation bane so sai yace min kawai naje muyi sikwatin so kawai sai nayarda muka zauna room daya har muka gama karatu, so yanzu yakirani ne yana fada min zai shigo Lagos gobe.."

"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un.. Lallai yarinyar nan yar duniyace ta karshe, ko kunya bataji take fadin cewa ta zauna daki daya da namiji,namijin da mijinta ba sannan ba muharraminta ba" shaddad yafada acikin zuciyarsa, nan yasoma hango irin dukan da zaiyi mata da ace kanwarsa ce ita,

Jijjiga kai yayi yaci gaba da tukinshi baima san lokacin data gama wayarba, har sukaje asibitin bai kalli saitin datake ba saboda yaki jinin kallon fuskarta,

Bude motar tayi tafita tana takawa cikeda rangwada, yana zaune yana jiran azo a daukar mata kayanta har Joseph yazo ya kwashi kayan ya tafi,

Fisgar motar shaddad yayi ya tasamma head quarter dinsu ta sojoji yana zuwa yasamu Abbas wanda aka daukesu tare kuma tare sukayi passing out dashi,

"Abbas nifa nakusa barin garin nan, gaskiya dole nanemi canji saboda zaman garin nan bai dace daniba"

Dariya Abbas yayi ya kama hannun shaddad,

"Haba Navy, wai Kai sai yaushe idonka zai bude ne? Kai da yakamata kayi murna saboda ankawoka nan babu wanda kasani babu wanda ya sanka kaci karenka babu babbaka"

"Wallahi bazan iyaba, nidai kawai burina nasamu transfer domin rayuwar mutanen nan kwata kwata bata dace daniba"

Matsawa abbas yayi kusa dashi yafara magana ahankali,

"Naga wata sarauniyar kyawawan mata agidan oga ance yarshi ce, meyasa bazaka shigar da kanka wurinta ba kasamu ka kwashi rabonka.."

"Allah ya sawwaka wallahi, me zanyi da ita? Yarinyar da bata da maraba da karuwa.."

"Ai wayewar kenan Navy, kaine bazaka ganeba"

Shaddad bai sake magana ba yabar wurin domin yasan idan zancen yayi nisa to ranshi ne zai baci a banza.

K'arfe biyar daidai yaje dauko maryama, yanata zaune zaman jiranta ga kayanta Joseph ya kawo amma ita din kuma taki fitowa, fitowa yayi a fusace ya nufi office din nata saboda yafi minti goma sha biyar yana zaman jiranta,

Ko izini bai nemaba ya bunka kai cikin office din, tsaye yaganta tana gyara rigar jikinta gefe kuma dr naz ne yake tsaye yana gyara belt din wandonshi,

Hada ido sukayi shida ita ya sakar mata wata muguwar harara sannan yaja kofar da karfi jikake gammm ya rufe ya tafi,

Cikin halin ko in kula suka fito itada dr naz yana mai gyara necktie din dake daure a wuyanshi,

Ko a kasan takalminta babu kunya ta bude motar ta shiga kafin ta rufe kofar tuni har shaddad ya figi motar yayi gaba, sake jin kyamarta yayi saboda abinda idanuwanshi suka gane masa yanzu,

Suna zuwa gida yasake ganin wani ikon Allah domin fahad ne yazo wanda take kira da room partner dinta, hannunta cikin nashi suka shiga cikin gidan, wanka kawai tayi ta shirya cikin riga da wando tafito zasu fita club ita da fahad din,coke mai sanyi ta dauko ta ciro wasu kwayoyi guda biyu ta jefa aciki tareda ballo wasu manyan tablet guda biyu ta afa abakinta ta korasu da coke,

"Kefa yar kwayace har yanzu ashe kina sha.." Fahad yace da ita yana murmushi,

"Ai dole sai da tsaro room partner, yaushe zan daina? Ai na kariyane ko ka manta"

Dariya suka saka dukkaninsu harda tafawa taja hannunshi domin tafiya, duk wadannan maganganun a kunnen shaddad suka yisu nan yabisu da kallon takaici.......



_*Ummi Shatu*_
[5/7, 8:20 PM] Ummi Shatu🏻: *_MARYAMA SARAUNIYA..!!_*



    *_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_


    _Dedicated to Maryam Qaumi_💕

  *_13_*

aishaummi.blogspot.com

~~~Bin bayansu da kallo shaddad yayi cikeda tsana da kyamatar hali irin nasu,

Janye jikinsa yayi yakoma ya nufi gida batare da ya shiga koda gidansu maryaman ba.

   Abangaren maryama kuwa tunda suka fita cinema suka fara zuwa itada fahad suka yi kallo na dan wani lokaci daga nan kuma suka fito suka tasamma club nan suka dade suna hirarsu sannan suna ganin abubuwan dake faruwa awurin,

Sai da misalin karfe 12 nadare harda yan mintuna sannan suka nufo gida, suna tafe suna hirarsu itada fahad wani lokacin idan hira tayi dadi har tafawa suke yi,

Gida ya kawota ya sauketa sannan yakoma domin zuwa masaukinsa wato murna hotel.

  Washe gari da safe  maryama ta sauko kasa ta shiga kitchen tana tsarawa kuku irin abubuwan da take son ya shiryawa fahad na karyawa,

Daki ta koma ta shiga wanka  tafito tasoma shiryawa, fahad ne yayi mata waya cewar ya karaso gidan dan haka tabashi izinin ya karasa dakin ya sameta,

Kayanta ta saka green din t shirt da skirt high waist ja,

Tana kokarin daura sarka a kafarta fahad ya turo kofar dakin ya shigo,

Murmushi ya aika mata dashi itama ta mayar masa da martani,

"Kinyi kyau sannan kinyi min laifi fa maryama.."

"Nagode fahad, laifin me kuma nayi maka?"

"Tunda nazo gidan nan baki hadani da dady dinki ba why?"

Murmushi tayi ta dauki dan karamin gyalenta ta yane kanta dashi ta juya tana kallonshi,

"Haba fahad kai ai ba bako bane agidan nan kazama dan gida, jiya lokacin da kazo dada baya nan yaje abuja sai asuba suka dawo, so yanzu after kayi breakfast zamuje ku gaisa.."

"Yawwa ko kefa sarauniyar mata, nagode da wannan damar da kika bani"

Murmushi ta saki na kasaita takama hannunshi suka fara saukowa daga kan matattakalar bene suna gangarowa kasa, daidai lokacin kuma shaddad shima yasako kai ya shigo cikin falon,

Dauke kai maryama tayi tasake makale hannun fahad acikin nata tana murmushi,

"Fahad kafata ciwo take wallahi.." Tafada cikin yatsina fuska,

Kan dining table suka karasa yaja mata kujera ta zauna sannan shima ya zauna kusa da ita,

"Maryama ciwon kafar nan nakifa akwai matsala, tun jimawa nafada miki"

Kallonshi tayi tana tsiyayar tea acikin wani dan karamin glass cup,

"Kai ai fahad maganarka bata da alaka da ciwon dake damuna, nafada maka dada ma haka yake fama dashi shiyasa last time nace mishi yaje saudiyya yaga dr.."

"Ayya to Allah yabashi lafiya, amma ke din dai yakamata nayi checking dinki before natafi"

Yace da ita yana dan murmushi kasancewar shima likitan matane, jin tayi shiru yasashi soko wani zancen,

"Maryama wai sai yaushe kika shirya aurata ne? Nafada miki dad dina ya matsa min da maganar aure nikuma kece macen da nake son mallaka a matsayin mata..."

Shiru tayi ta kura masa ido tana kallonshi yayinda shi dinma itan yake kallo, dan kyau fahad kyakkyawa ne sannan ga aji gashi dan masu kudi, to ita matsalar shine yayi mata yaro dayawa domin shi dinma irinsu dr naz ne yara, ita kuma a burinda take dashi tafi son auren namiji dan shekar 35 zuwa 40 aganinta kuma a ra'ayinta shine daidai da ita amma wadannan mitsi mitsin yaran ina zasu kaita?,

Pork ta dauka ta cakulo dankali takai bakinta tana kallonshi,

"Haba maryama say something please..."

Batare data zare cokalin daga bakinta ba ta langwabar da kanta gefe tana yimasa murmushi,

Ita gaba daya ma bata san auren namijin da yake yawan mu'amala da mata shiyasa duk taki auren doctors din asibitin su dake tururuwar sonta, shi kansa fahad din bata da sha'awar aurenshi saboda likitane yana mu'amula da mata sosai.

Hannunshi yakai ya rike pork din ya cireshi daga cikin bakinta,

"Nadai fahimci kawai ni dinne baki so ko maryam?"

Girgiza masa kai tayi tana murmushi,

"Ba haka bane fahad, yanzu dai kaci abinci idan kakoma gida zamuyi magana through call.."

"Hmm kullum dai haka kike cemin gaskiya nafara kosawa da wannan jan ran da kike yimin.."

"Haba fahad nace zamuyi magana, yanzu kaci abinci kawai.."

Badan yasoba haka ya hakura yaci gaba da cin abincin har suka kammala tayi masa jagora wurin dada suka gaisa lokacin shaddad yana zaune suna yin brreakfast in banda harara babu abinda ke hadashi da maryama har shi fahad dinma ji yake ya tsaneshi, fahad ne yatashi zai fita domin tafiya nan maryama tabishi ta rakashi,

Hannunta ya kama yana kallonta,

"Wancan guy din waye shi?"

Tab'e baki tayi, "driver nane.."

"Wai dagaske?"

"Dagaske mana, wani abune yafaru?"

"A,a babu komai"

"Shikenan tunda babu komai, sai munyi waya.."

Sakin hannunta yayi ya wuce ya nufi motarshi, tana tsaye awurin har saida taga fitarshi sannan ta koma cikin gida,

Takalmi tasaka tafita da wayarta a hannu ta shiga falon Dada tana yiwa shaddad kallon tara saura kwata,

"Father bari naje asibiti.."

Cikin fara'a da kulawa ya kalleta, "adawo lafiya mai sunan mama, Allah yabada sa'a"

"Amin father, thank you" tafada tareda mikewa tana kallon shaddad,

"Am muje ko"

Bai ko kalleta ba ya mike yayi gaba ta mara masa baya, so take ta kamoshi amma takasa domin kafin tayi taku daya shi yayi biyar, babu shiri ta hakura domin har tafara yin haki,

Motar ta shiga ta zauna tana dan daddanna kafafunta dake yimata ciwo,blessing nagama ajiye kayan shaddad ya fisgi motar, idanuwanta ne suka sauka akan hannuwanshi dake rike da sitiyarin motar,fatarshi luwai luwai take gwanin kyau ga gashi kwance ajiki, dauke idonta tayi daga kallonshi, har sukaje asibitin bai kalleta ba asalima lokacin da yayi packing kawar da kanshi gefe yayi har saida ta fice.

Da daddare misalin karfe 7 tace tana son zuwa stadium kallon ball, wata harara ya cilla mata sannan yayi magana,

"Ke nifa ba dan iska bane kin gane? Ki nemi mai kaiki stadium amma baniba.."

Dada tayiwa waya ta fada masa shikuma ya kira shaddad yace ya kaita, bama stadium ba duk wurinda take so ya rinka kaita,

Matsu tasha cikin jeans da t shirt da bakar hula facing cap,tasha bakin combos tafito, yana kallonta ta mirror din jikin motar lokacin da take tahowa,

"Karuwar banza karuwar wofi, Allah ya wadaran halinki" yafadi hakan acikin zuciyarshi,

Shiga tayi ta zauna tana faman taunar chewing gum, ko kallonshi ita dinma batayi ba ta dauke kanta tana kallon mirror,

Kaita stadium din yayi ya zauna acikin mota yana jiranta, sai wurin karfe 8 sannan aka gama wasan ya dauketa zasu koma gida,

"Ina son zan sai plate din wrestling" tace dashi tana tauna chewing gum din dake bakinta, bai bata amsaba amma ya nufi wurinda zasu iya samun Kaset din sai dai mamaki ya kamashi mutuka, shin ita wannan yarinyar wai duk dabi'unta irin na mazane? Itace kallon kwallo itace hawa bike itace kallon wrestling to ko shi da yake namiji ma wadannan abubuwan basu dameshi ba amma ita tana mace tana abubuwa irin na maza, da kanta tafita ta siyo Kaset din ta dawo cikin motar ya maida ita gida.

Haka rayuwar taci gaba da tafiya atsakaninsu kullum shaddad ne ke kaita office ya daukota sannan wani lokacin kuma har club yake kaita, yau ma akan hanyarsu ta dawowa daga asibiti ta yamitsa fuska tana yi masa magana,

"Anjima zaka kaini stadium da karfe 6"

Bai amsa ba dama tasan ba amsawar zaiyi ba, tana komawa gida ta shirya tana jiransa bai zoba gashi dada baya nan yatafi saudiyya ganin likita,

Cika tayi fam saboda tasan tayi missing din wannan wasan, karfe 8 shaddad din yazo ganin haka yasata fita tace yakaita club saboda bata son ta kyaleshi haka bai wahala ba duk tsiya dai sai ta fitar dashi awannan daren koda baya so,

Baiyi musuba ya dauketa suka fita zuwa club din, sanye take da wani damammen wando da riga body hug ita dinma ta kamata sosai, dan karamin gyale ta dora akanta kawai daga nan bata kara komai ba,

Lokacin da sukaje club din packing yayi tafita ta shiga ciki shikuma ya zauna acikin motar ya kunna radio yana sauraren wa'azi.

Maryama na shiga cikin club din taganshi cikeda maza da yanmata ashe wasu students ne yan university suke party awurin, tunda ta shigo samari ke kallonta domin ta hadu tayi awon gaba da imaninsu,

Can tasamu wuri ta zauna, diffff aka dauke wuta kafin tayi wani motsi tuni har an toshe mata baki anyi sama da ita, kokawa take iya karfinta domin kwatar kanta amma takasa kasancewar mazan da suka rufu akanta sunfi biyar,

Can bayan club din suka kaita suka ajiye sannan suka fara kokarin aiwatar da mummunan kudirinsu akanta....

  _Wayyo maryama maza zasuyi mata aika aika.._




*_Ummi A'isha_*