Thursday 5 January 2017

MACE GUDA DAYA TILO

[3/11, 4:49 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO... 1⃣

  Na
UMMI A'ISHA


   Matashin saurayine sanye da kayan yan bautar kasa (N. Y. S. C) kayan sunyi mutukar yimasa kyau, tsaye yake agaban allo yana yiwa dalibai yan department of sociology lecture din biology, a jami'ar tarayya dake jihar bauchi, kowanne dalibi ya nutsu yana sauraron lecture din domin babu karya malamin akwai iya darasi kuma akwai zakin murya radau,wannan shine shigarsa hall din na 3 ,yauma kamar kullum ya kwashe fiyeda awa 1 yana yimusu lecture akan introduction to biology, kwas kwas sukaji tafiyar takalmi alamun ana shigowa cikin hall din, hankalin kowa yakoma kanta, jiyowa shima yayi yabita da kallo daga sama har kasa, farace sosai dan har yellow take dan tsabar fari, bata da tsayi sosai amma tana da dan jiki, idanuwanta manya ne farare tas,tanada dogon hanci da dan mitsitsin baki, tana sanye da wani pink din leshi da mayafinsa takalmin kafarta kuwa mai dan karen tsinine shima pink hannunta rike da jaka pink colour, kanta tsaye ta nufi inda zata zauna, he! Taji malamin ya fada ko jiyowa batayi ba taci gaba da tafiyarta.
[3/11, 6:16 PM] Ummi A'isha: MACE GUDA DAYA TILO...2⃣

Na
UMMI A'ISHA

   Cike da haushi yabi bayanta yasha gabanta tare da nuna mata hanyar fita get out from my class taji yafada, idanuwanta ta bude sosai tafara kallonsa farine tas dogo mai tsananin kyau yana da idanuwa sosai hancinsa tamkar biro kuma yana da yar kiba daidai misali ita kanta tasan yanada kyau kuma ya hadu kallon banza ta wurga masa tare da Jan wani dogon tsaki, mamaki ne ya kamashi dan babu macen da ta taba yi masa tsaki sai wannan yarinyar yar rainin hankali, tsawa ya daka mata yace who are you dazaki shigo min class yanzu? Me kike takama dashi? Ke yar gidan uban waye? Gaba daya ajin yayi tsit kowa ya zuba ido yana kallonsu domin idan da sabo to sun gama sabawa da halin wannan dalibar wani mugun kallo ya bita dashi sannam yace oya carry your legs and get out from my class tun kafin na wulakanta ki, ni banma taba ganin wannan fuskar taki acikin class dina ba, ita kuwa gaba daya bakin cikin duniya yagama rufeta batare da tace masa ko kala ba tajuya tafice daga cikin hall din zuciyarta cike da bacin rai, lalle gayen nan yau xan nuna masa ko ni wacece zaisan dani da sauran matan da yasaba yiwa wulakanci akwai banbanci ayau sai naga waye ubansa a kasar nan.
[3/11, 6:18 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

3⃣

Na
UMMI A'ISHA

     Dawowa yayi yahau kan step din yaci gaba da lecture din daya keyi, Director din makarantar ne yashigo cikin hall din shida mukarrabansa nan da nan idon kowa ya koma kansu wanda ciki harda shi kansa malamin, dasauri director din yazo gabansa yana cewa me yahadaka da wannan yarinyar junaida mukhtar? Kasan ko wacece ita? Bude baki copper din yayi tareda niyyar yin magana amma cikin tsawa director din ya katse shi tare da cewa look Lamin kaifa ba staff dinmu bane service kawai kazo yi dan haka mun dakatar dakai daga wannan aikin,yanzu ka biyoni office inada magana dakai yana kaiwa nan ya juya yafita shida wadanda suka rakoshi, ajin kuwa tsit kakeji kamar ruwa yacisu shi kuwa malamin wanda aka kira da lamin kayansa yashiga tattarawa ya rufe laptop dinsa ya saka acikin jakarta ya yiwa daliban sallama wadanda akalla zasu kai kimanin dari biyu kasancewar combined lecture ne
[3/11, 6:22 PM] Ummi A'isha: MACE GUDA DAYA TILO

4⃣

Na
UMMI A'ISHA

  Gaba daya yan ajin jikinsu yayi sanyi domin wannan bashine karo na farko da dalibar tayi sanadiyyar korar malaman makarantar ba, ahankali ya gama hada kayansa cikin jakar ya dauka ya rataya akafadarsa ya sauko ya futa daga cikin hall din, yana fita hall din ya cika da surutun daliban dake ciki, wasu tausaya masa suke wasu kuma bakin cikin tafiyarsa suke yayinda wasu kuma suke Allah wadai da halin wannan dalibar mai suna junaida mukhtar. Kansa tsaye ya nufi admin block,office din director ya shiga suna zaune shida students affairs da registerer da hed of department can gefe kuma wannan kyakkyawar yarinyar ce zaune tana kallonsa, da sallama yashiga suka amsa tareda nuna masa kujerar da zai zauna, yana zama director yafara balbale shi da fada tareda cewa yazama dole kabata hakuri kuma ka nemi afuwarta akan abinda yafaru dazu baki ya bude cike da mamaki wai shine zai bawa wannan yarinyar hakuri instead ace itace zata nemi afuwarshi kallo yabisu dashi daya bayan daya sannan yace impossible yaza ayi ace nine zan bata hakuri bayan itace tayi min laifi? Head of department ne ya katse shi ta hanyar cewa kasan yar gidan waye kuwa? Ko yar gidan waye wlhi bazan bata hakuri ba kallonsa suka farayi cike da mamaki director yace to ai kuwa tunda bazaka bata hakuri ba yazama dole kabar makarantar nan ayau.
[3/11, 6:23 PM] Ummi A'isha: MACE GUDA DAYA TILO

5⃣

Na
UMMI A'ISHA

    Mamakine karara ya bayyana akan fuskarsa domin kuwa babu dalilin da zaisa akoreshi akan kawai ya hukunta dalibarsa wacce ta karya dokarsa, wata xungureriyar takarda director ya miko masa yace gashi ka zaba acikin biyu nafarko ko kabawa junaida hakuri ko kuma ayau dinnan ka bar mana makarantar nan domin bazamu zuba maka ido ka yimana sanadin aikinmu ba, wannan yarinyar babanta shine permanent secretary na education kuma shine Head of service na wannan state din dan haka kazabi daya, shiru lamin yayi yana tunani wato dan babanta ne head of service shikenan sai ta raina mutane? Shi ai ya zata duk wannan kafafar da take babanta ne governor dama head of service ne kawai? Wani guntun tsaki yaja aransa yace lallai nima dan bakusan waye ni ba shiyasa kuke neman wulakanta ni,ni ai ubana yafi nata matsayi tunda secretary to the state government ne kaf state dinmu ubana shine na 3 daga governor sai deputy sai ubana amma ban taba nunawa ba registerer ne ya katse masa tunani ta hanyar cewa lamin kaifa muke jira kayi magana kallonsu yayi sannan ya juya ya kalli yarinyar yace wlhi bata isa nabata hakuri ba nazabi barin makarantar, takardar ya karba ya tashi yafita daga cikin office din ya nufi motarsa wadda ke ajiye awurin da aka tanada domin ajiye motoci.
[3/22, 7:56 PM] Ummi A'isha🏻: [3/15, 7:05 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

6⃣

Na
UMMI A'ISHA


   Motarsa kirar Toyota corolla yabude ya shiga ya fita daga cikin makarantar ,gudu yake shararawa sosai kamar wadda zai tashi sama yafita daga garin bauchi ya nufi birnin yola. Karfe 3 dai dai yashiga cikin yola Chief olusegun obasanjo housing estate ya nufa, ahankali yake tukin har ya iso tangamemen gidan nasu wanda yake cikin jerin gwanon gidajen, hon yayi mai gadi ya bude masa gate din yashiga cikin gidan securities sai daga masa hannu suke yi ajiye motar yayi a muhallinsa sannan ya tasamma cikin gidan, babban falon gidan ya shiga daya daga cikin kannenshi ya hango kwance cikin luntsumemiyar kujera tana kallon Indian film sallama yayi dasauri ta dago tana cewa oyoyo yaya lamin karasowa ciki yayi yana cewa wacece? Hasna ce ko husna? Murmushi itama tayi tace yaya kenan wai kai meyasa baka ganemu? Dariya yayi mata sannan yace to mummy da daddy ma basa ganeku balle ni da bani na haifeku ba dariyar itama tayi sannan tace to husna ce hasna na kitchen tana yimana fried indomie murmushi yayi yace sarakan kwadayi kenan ina mummy? Mummy tana side din dad tabashi amsa mikewa yayi ya nufi side dinshi.
[3/15, 7:08 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

7⃣

Na UMMI A'ISHA

  Dakinsa yashiga ya zauna ya zubawa carpet din dake malale acikin dakin ido, tunanin matakin da zai dauka akan wannan yarinyar shin me take takama dashi? Yanzu kenan duk burin da ya dauka ya rushe? Babban burinsa shine yayi lecturing lokacin service dinsa domin yana kaunar koyarwa a jami'a amma yau gashi wata MACE GUDA DAYA TILo tayi masa sanadi ta rusa masa duk budget dinsa ai kuwa yazama tilas ya rama wannan wulakancin da tayi masa da wannan shawara ya tashi ya shiga hadadden toilet dinsa yayi wanka ya fito yashirya cikin wata green din t shirt mai hoton heart ajiki sai blue din jeans ya taje sumar kansa ya fesa turaren smart collection ya fito, falon mummynsa ya wuce yana shiga ya tarar da ita zaune cikin kawatacciyar shiga tana waya gefenta yan biyunta ne zqune suna cin indomie,kusa dasu yaje yazauna yana fadin hasna kin gama girkin dasauri kanwar tasa ta kalleshi tana fadin lah yaya lamin yaushe ka dawo? Ban jima da dawowa ba ya bata amsa dai dai lokacin mummyn tasu ta gama wayar ta kalleshi tana cewa babana saukar yaushe? Wlh dazu nadawo mummy daddy yana gari kuwa? Kallonsa tayi tace bakuyi waya bane? Dazun nan yadawo daga Holland kaje ka sameshi yana falo mikewa yayi ya nufi falon mahaifin nasa.
[3/15, 7:12 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

8⃣

Na UMMI A'ISHA


    Ahankali yake ratsa falikan har ya isa na mahaifin nasa ya sameshi zaune yana hutawa sallama yayi masa sannan ya nemi wuri ya zauna yafara gaida shi cikin murmushi mahaifin nasa ya amsa sannan yace lamin har kadawo daga bauchin? Jikinsa asanyaye yace dady sun sallameni sunce sai dai naje wani wurin nayi service din kallonsa mahaifin nasa yayi sannan yace laifin me kayi musu? Kansa ya sunkuyar kasa sannan yace babu laifin komai daddy to yanzu ya zakayi? Ya tambayeshi dama daddy cewa nayi yanzu zan koma can N. Y. S. C Secretariat din na sanar musu inyaso sai ayi posting dina Bayero university kano ina ganin hakan zaifi, to shikenan Allah yasa hakan shi yafi alkhairi mahaifin nasa yace dashi amin ya amsa sannan yatashi ya fita daga cikin falon. Ita kuwa junaida tana tashi daga office din director tashiga sabuwar motarta kia 1 door ta nufi gidansu dake unguwar area 7 tana isa ta wuce dakinta ta jefar da jakarta, mayafinta, takalminta, wayarta ta haye gadonta ta kwanta rufe idonta keda wuya tafara ganin wannan saurayin matashin yana yimata gizo gaskiya babu karya ya hadu zuciyarta taji tafara dukan uku uku kamar zata tsage, idanuwanta ta bude sannan ta mayar ta rufe still shi din dai take gani lokacin da yake yayyafa mata masifa acikin hall din.
[3/15, 7:13 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

9⃣

Na UMMI A'ISHA


     Zaune ta tashi cikin sauri, Fara zagaya cikin dakin nata tayi sannan ta saki wani kayataccen murmushi toilet ta shiga ta silla wanka sannan ta fito ta sanya wata doguwar riga ta shan iska ta nufi falo acan ta hango mahaifiyarta zaune tana kallo karasawa tayi cike da shagwaba ta fada kan cinyarta tana cewa umma nifa yunwa nake ji dasauri takalleta tace haba autana me yasa kike son zama da yunwa kira tafara kwallawa daya daga cikin yan aikin gidan dagudu ta runtumo tazo ta durkusa agabansu kallon junada ta yi tace auta me zaki ci?? A yangance tace ta dafa min indomie with egg da sauri mai aikin ta tashi ta nufi kitchen domin aiwatar da abinda aka sata ita kuma taci gaba da zubawa uwar shagwaba.
[3/15, 7:15 AM] Ummi A'isha: MACE GUDA DAYA TILO..

1⃣0⃣

Na UMMI A'ISHA

    Tun da sassafe lamin ya baro garin Adamawa ya nufi bauchi gudu yake babu kakkautawa ya kure A. C din motar ya kunna wakar no one be like you yana saurare amma acan kasan ransa kuwa abinda zai aiwatar kawai yake tunani. Karfe takwas ya shiga cikin bauchi dan haka wani guest house ya zarce inda zai huta. Sai 10 ya fito yashiga cikin garin kofar jami'ar yaje ya yi packing yana ganin shige da ficen daliban yana nan xaune acikin motarsa ya rurrufe glass din wanda ya kasance mai mutukar duhu ne na waje baya ganin na ciki sai na cikine ke hango na waje, wata mota pink colour ya hango tana tahowa kirar new discussion R888 sai datazo saitinsa sannan yaga ashe wannan yarinyarce junada aciki tasha ado tamkar wata sarauniya komai blue nan da nan ta kutsa kan motar tata cikin makarantar shi kuwa murmushin mugunta yayi tareda fadin yarinya kin tabo gidan rina dan haka zaki yi bayani.
[3/22, 7:56 PM] Ummi A'isha🏻: [3/17, 9:52 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..

1⃣1⃣

Na
UMMI A'ISHA
     Yana nan zaune har ya hango adam dama shi yake jira, Adam daya daga cikin dalibansa ne wanda yafara koya musu kuma course mate din junada mukhtar ne shigowa motar adam din yayi sannan yafara gaida lamin ta hanyar cewa morning sir, morning lamin din ya amsa yace dama zuwa nayi kabani duk labarin da kasani akan wannan yarinyar junada mukhtar murmushi Adam yayi sannan yafara bashi labarin. Alhaji mukhtar Magashi shine mahaifinta kuma asalinsu yan garin bauchi ne cikin karamar hukumar Giyade babanta ya rike madafan iko da yawa daga karshe aka bashi mikamin head of service na wannan jahar matarsa 1 da yaransu uku junada ce yar auta sai yayunta maza guda 2 Khalid da Amir, yar gatace ta karshe kasancewar ita kadai ce mace kuma gata yar auta komai daka sani na rayuwa yimata ake bata da wata matsala sai kwaya daya.
[3/17, 9:54 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

1⃣2⃣

Na
UMMI A'ISHA
   Matsalarta shine bata son karatu ko kadan gata shagwababbiya ce ta karshe amma duk da haka mahaifinta yana hukuntata idan ta aikata ba dai dai ba sai dai ita mahaifiyarta tafi batata don bata tsawatar mata idan tayi ba dai ba, tunda muka shigo makarantar nan bata zuwa lecture sai time din data gadama, bata respecting din malamai balle yan uwanta dalibai bata da lokacin tsayawa tayi karatu amma kuma babu malamin da ya isa yabata carry over saboda director yana daure mata gindi, yana iya korar mutum akanta saboda kawai yana jin tsoron kar ta fadawa mahaifinta abashi query bayan kuma shi mahaifinta ba irin wadannan mutanen bane masu zarmewa akan yayansu, ka ganta nan har muka shiga level 300 bata taba samun carry over ba alhalin kuma ba karatun takeyi ba. Wani matashin murmushi lamin yayi tabbas yanzu ya samu hanyar da zai rama abunda tayi masa ta hanya mai sauki juyawa yayi ga Adam yayi masa godiya sannan ya yi masa sallama yatashi motarsa ya bar wurin, garin kano ya nufa yana tafe yana nishadi ya kunna wakar you are my African queen ahaka har ya isa B. U. K.
[3/17, 9:56 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..

1⃣3⃣

Na
UMMI A'ISHA


   Yana isa ya kai takardunsa cikin sa'a sukayi accepting dinsa musamman ma da suka ga cewar ba a Nigeria yayi karatunsa ba a Malaysia yake yi, psychology department suka turashi suka bashi yan level 100 inda zai daukesu Biology, sati 1 suka bashi tareda bashi inda zai zauna amma bai karbi masaukin ba kasancewar yanada inda zai zauna. Karfe 4 yagama abinda zaiyi yabar cikin makarantar ya nufi yola. Bai isa garin yola ba sai kimanin karfe 7 nadare yana zuwa mahaifinsa ma na karasowa dan haka cikin gidan ya shiga yajira karasowar mahaifin nashi wanda bodyguard dinsa suka ysnyameshi kamar wanda za adauke,da fara'arsa ya tari dan nasa yana fadin tafiya tayi sauri my son dafatan andace? Murmushi yayi sannan yace yes dad sunyi accepting dina dafa kafadarsa uban yayi tareda jan hannunsa suka jera suna tafiya tamkar wasu abokai har suka karasa cikin falon uban sannan shi lamin din ya juya ya wuce side din mummy yana shiga ya tarar da babban yayansa yana zaune yana cin abinci akan dinning wajensa yakarasa yabashi hannu suka gaisa sannan shima ya nemi wuri ya zauna yace broz nabar bauchi university fa na koma kano murmushi yayan nasa yayi wanda suke mutukar kama amma shi bakine sabanin lamin wanda yake fari sol, dubansa yayi yace to nidai ina baka shawara wlhi babu kai babu yan matan jami'a, dan nasan halinka da shegen neman mata.
[3/17, 9:59 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

1⃣4⃣

Na
UMMI A'ISHA

    Kai ko tsoron Allah bakaji balle tsoron wadannan cutukan na zamani, rai lamin yabata sannan yace kaifa kanada takurawa wlh shigowar mahaifiyarsu ne yasashi yin shiru domin baya son taji zancen da yakeyi kasancewar yanada yakinin duk gidan babu wanda yasan yana neman mata in banda yayan nasa cikeda murna tace sannu babana shima cikin sigar shagwaba yace yawwa mummy dama nazo miki da wani albishir murmushi tayi tace to Allah yasa alkhairi ne ai kuwa mummy alkhairi ne kuma nasan zakiyi farin ciki sosai kallonsa suka tsaya yi itada yayan nasa tace to fadi inji cikin farin ciki yace na samo matar aure a bauchi dan haka kisanar da dad aje a tambayo min domin aure nake so, wani farin cikine ya lullube uwar tace to Allah yasa albarka kuma naji dadi bayan kagama karatu za ayi bikin? Dasauri yace no nanda 3 months nake so ayi cikin mamaki tace to zai yiwu ahada da na abdulrahman yayankane? Yes mum haka nake so ayi cikin fara'a tace to Allah ya yarda tatashi ta fita daga cikin falon. Yayansa ne ya kalleshi yace ai gara kayi auren yafi maka amma kana yaronka dakai sai jarabar mata just 26 years? Koni da nake 29 bana bin mata sai kai? Cikin kunkuni lamin ya mike yabar cikin falon ya nufi side dinshi aransa kuwa fadi yake wannan dinma da zanyi ai na ramuwar gayya zanyi bana Allah bane.
[3/17, 10:00 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

1⃣5⃣

Na UMMI A'ISHA

   Yana shiga hadaden dakinsa wanda ya kawatu mutuka da kayan alatun more rayuwa ya fada saman gado ya jawo wayarsa BlackBerry B210 Vicky yakira daya daga cikin yanmatansa ringing 2 ta dauka cikin harshen turanci tafara gaida shi murmushi yayi yace nayi missing dinki daga can kamar zatayi kuka tace nafika damuwa da rashinka kusa dani yanzu yaushe zakazo? Silin din dakin ya kurawa ido yace gaskiya Vicky zaki dade baki ganni ba amma next week zan shigo kano to idan nazo i will call you murmushi tayi tace ok sai najika i luv you, luv you too ya amsa mata ya ajiye wayar ko minti 2 ba ayiba wayar tasa tasoma ruri hannu ya mika ya dauko yana dubawa yaga Jenifer ce cikin murmushi yaje hello madam j how are you? Daga can ta amsa da fine my Prince.
[3/22, 7:56 PM] Ummi A'isha🏻: [3/22, 4:21 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..

1⃣6⃣

Na
UMMI A'ISHA

  Kamar zata saka kuka tace yaushe zamu hadu? Wani malalacin murmushi yayi sannan yace very soon but yanzu ina yola ne kin san babu halin kizo amma idan nasamu time zanzo dakaina cike da jin dadi tace to ina jiranka i love you me too yabata amsa ya kife wayar. Daya wayar tashi ce ta soma kara ya dauka ya duba sunan Mary yaga ajikin screen din cikin sauri ya daga yace hello my Mary yakike? Daga can tace abnormal murmushi ya aika mata dashi yace what's wrong? Cikin shesshekar kuka tace kamanta dani kwana biyu baka nemana rarrashinta yafara yi domin duk cikin yanmatan sa itace star yafi ji da ita domin Mary akwai kyau ga diri shiyasa ma yafi sonta fiyeda sauran dakyar ya samu ya lallasheta tadaina kukan sannan yayi mata alqawarin zai tura mata kudi ta account dinta sai ta yanki ticket din jirgi daga Lagos tazo kano ta sameshi saida yayi da gaske sannan ta hakura sukayi sallama yana ajiye wayar yaga yayansa daga bakin kofa yana tsaye yana kallonsa fuskarsa babu walwala yace lamin abinda kakeyi baka kyautawa wai kai me yayan arnan nan suke baka ne ka manne musu? Wlh kaji tsoron Allah dan babu mamaki yanzu yana fushi dakai kuma inajin ma har giya kana sha sai asannan lamin yayi magana yace ni babu abinda nake sha nasan dai ina neman mata amma bana shan ko sigari balle giya.
[3/22, 4:22 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

1⃣7⃣

Na
UMMI A'ISHA

  Harara ya wurga masa sannan yace kalli lips dinka yadda sukayi ja ahaka xakace min baka shan giya na yarda? Kallonsa yayi yace yaya sai dai idan sharri zaka yimin amma wlh bana shan giya hararsa ya kuma yi yace kaji dashi dai ya juya yayi ficewarsa shi kuwa lamin tashi yayi ya shiga toilet domin watsa ruwa. Abangaren junada kuwa tun ranar data sa aka kori lamin duniya tayi mata zafi domin ta tsinci kanta dumu dumu cikin kaunarsa gashi bata san a inda yake ba bare tasa anemo mata shi, yauma ranta abace ta shirya cikin wani brown din material ta nufi sch amma sam zuciyarta babu dadi gaba daya ranta abace yake kuma ko yaya ta rufe idanuwanta shi take gani abinda yafi tsaya mata arai shine yadda kullum sai tayi mafarkin kyakkyawar fuskarshi, ranta ajagule ta fito daga dakinta ko ummarta bata yiwa sallama ba ta fita sabuwar motarta Prado baka ta dauka ta nufi makarantar zuciyarta cike da fatan dama taga wannan matashin saurayin.
[3/22, 4:24 PM] Ummi A'isha: MACE GUDA DAYA TILO...

1⃣8⃣

Na
UMMI A'ISHA


Da wannan tunanin ta isa cikin makaranta kowa mamakin canjawarta yake tun ranar da abin yafaru bata kara yiwa kowa maganar bacin rai ba sannan yanzu ta daina makara da wuri take zuwa school sabanin da dasai lokacin data gadama kuma babu wanda ya isa ya hanata shiga lecture, ahankali tashiga hall din ta zauna ziciyarta cike da dana sanin fadawa director datayi har aka kori wannan dan bautar kasar da haka tagama sauraron lectures din ta tashi ta tafi gida. Shi kuwa lamin tuni yafara zuwa lecturing a kano B. U. K wani dan madaidaicin gida ya kama a unguwar jan bulo kabuga tuni budurwarsa Vicky ta yi masauki agidan tana tafiya Mary tazo, haka ya rinka sheke ayarsa batare da iyayensa sun sani ba dama ko lokacin da yake Malaysia haka haka yake ajiyesu agidansa daga wannan ta tafi wannan zatazo. Yan matan jami'a kuwa ba acewa komai domin ganinshi kyakkyawa mai class kuma ga kudi nan da nan suka Fara cusa kansu wurinsa sai dai har yanzu babu wadda ta samu shiga domin shi baya harka da hausawa duk yan matansa Christian ne babu musulma ko daya kuma bashida standard budurwa domin bai shirya aure yanzu ba sai auren ramuwar gayya.
[3/22, 4:25 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

1⃣9⃣

Na
UMMI A'ISHA


   Yau tunda yagama lecture yakoma gida yafara hada kayansa ya gama Mary dake kwance tana bacci yafara tashi dakyar ta tashi tana faman murtsuke ido tana tambayarsa har yadawo eh ya amsa mata sannan yace kitashi ki shirya kitafi sai next week zan dawo kinga yanzu ni nagama shiryawa kamar mai shirin yin kuka tace to sai munyi waya tashi yayi yadau jakarsa yatafi tareda bar mata sallahun idan tagama ta rufe gidan. Karfe 2 na rana  ya isa gida mummy yatarar zaune afalo yan biyunta sun zagayeta sai surutu suke mata ganinsa da sukayi yasa suka dan nutsu suna fadin oyoyo yaya harara yabisu da ita yace kunzo kun wani zagayeta kamar wasu kananan yara, ke hasna kin share min dakin dana saki? Dasauri tace yaya bani bace sai dai ko husna cikin sauri itama tace wlh bani bace banza yayi dasu domin dama haka suke masa irin wannan rainin hankalin idan yasa daya aiki to idan batayi ba sun rika cewa wance ce itama dayar tace ba ita bace ,mummy ya kalla yace mummy ina wuni cikin fara'a tace lfy babana kallonta ya sakeyi yace yakukayi da dady akan maganar nan? Dariya tayi tace kaifa kafiya zumudi ai mun gama maganar dashi ashema yar gidan Alh mukhtar magashi ce? Ai tuni dadynku yayi masa magana kuma yace bai mata miji ba dan haka yabaka ita yanzu saura aje ayanke rana, farin ciki ne ya cikashi ya mike ya nufi side dinshi.
[3/22, 4:27 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..

2⃣0⃣

Na
UMMI A'ISHA


    Zuciyarsa fes ya shiga dakinsa yasamu wuri ya zauna yana tunanin ta inda zai bullowa wannan yarinyar junada. Mukhtar wani malalacin murmushi yayi dalilin samo abinda zaiyi mata cikin haka yaji phone dinshi tana kara ahankali ya cirota daga cikin wandon jeans din dake jikinsa Angelina yagani a rubuce tsaki yayi ya ajiye wayar batare da ya daga ba daga karshema da yaga tana neman damunshi sai ya kashe wayar gaba daya. Ita kuwa junada kullum da tunanin lamin take kwana take tashi kafin ta ankara sonsa yagama cika zuciyarta, yau kamar kullum ta dawo daga school ta kwanta tayi bacci ta huta sannan tayi wanka ta fita zuwa falo amma bataga mahaifiyarta ba dan haka ta wuce dakinta adakin ta sameta tana zaune bakin gado tana waya kusada ita taje ta zauna tana sauraronta har tagama, gamawarta keda wuya ta juyo gareta tana cewa junada har kin tashi daga barcin? Dazu nashiga dakin naki naga kina bacci dama mahaifinki ne yabani sako nasanar dake yabada ke ga dan abokinsa ras junada taji gabanta yafadi kallon mahaifiyar tata tayi sannan tace a ina yake? Murmushi uwar tayi sannan tace dan gidan Alh kabir sulaiman yola ne mahaifinshi shine SSG na Adamawa state kuma yanada sarauta makaman Adamawa Turakin yola gashi kuma classmate din mahaifinki ne domin tare sukayi makaranta kedai kawai abinda nake so dake shine kiyi kokari kiyi biyayya insha Allahu zakiji dadi agaba don kin san mahaifinki bazai taba zaba miki mijin da ba nagari ba ita dai junada shiru tayi batace komai ba domin hankalinta yagama tashi amma duk da haka ta kuduri niyyar yiwa mahaifinta biyayya ahankali tace to umma naji abinda kikace Allah ya zaba min mafi alkhairi cikin jin dadi mahaiyarta tace amin Allah yayi miki albarka.
[3/22, 7:56 PM] Ummi A'isha: [3/22, 4:37 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

2⃣1⃣

Na
UMMI A'ISHA


   Tuni mahaifin lamin ya shirya shida yan tawagarsa yaje gidan su junada domin nemawa dansa aurenta batareda wani bata lokaciba mahaifinta ya amince tareda sanya ranar auren dai dai da ranar da za ayi na yayansa Abdulrahman sun rabu cike da farin ciki da girmama juna, ita dai junada bata cewa domin dama bata damu da tasan ko waye angon ba saboda tasan ba zabinta bane zabin iyaye ne (sunan wani littafi na hafsata bounzer) dan haka kawai hidimar gabanta takeyi. Abangaren lamin kuwa yafi kowa murna da sanya wannan rana, tuni ya koma kano yaje ya dora daga inda ya tsaya wannan karon Angelina da blessing ne suka je gidan nasa amma kullum cikin fada suke da zarar ya fita zasu fara dambe ganin haka yasa ya tattarasu yakora yayiwa Mary waya yace tazo.
[3/22, 4:39 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

2⃣2⃣

Na
UMMI A'ISHA


    Biki ya rage saura sati 2 lamin ya shirya shida yayansa sukaje bauchi domin gaisheda iyayen junada ita kuwa lokacin bama ta kasar sun tafi sudan itada kanwar mahaifiyarta mami inda za ayi mata gyaran jiki da sauran abubuwa na amare kuma bazasu dawo ba sai ana saura 3 days biki,cike da girmamawa da mutuntawa su lamin suka gaisa da kowa lfy sannan suka koma yola inda acanma shirye shiryen bikin ake tayi dan har an harhada lefe aranar aka kai na matar abdulrahman mai suna kausar yar gidan sarkin yola ce yayinda na junada akace sai washe gari. Hakan kuwa akayi washe gari yan kaiwa kaya suka nufi bauchi kayane na kece raini akwati 24 set daya brown daya set din kuma pink colour yan uwan junada sunyi mutukar murna hakan nema yasa suka bada tukwici na naira dubu dari biyu. Tunda biki ya rage saura kwana 8 gidansu lamin suka fara shirye shiryen komawa sabon gida domin acanne za a gudanar da bikin, wani tangamemen gida state government ta ginawa mahaifinsu akusada government house gidan unguwa gudane domin part guda 5 ne acikin gidan dan haka ananma su lamin din zasu zauna.
[3/22, 4:40 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..

2⃣3⃣

Na
UMMI A'ISHA


    Ana saura kwana 3 biki su junada suka dawo daga Sudan tasha gyara tayi tsananin kyau sai sheki da kyalli take tamkar wata tauraruwa, gaba daya ta yi wata kala ga uwar rama datayi saboda bata iya cin abinci. Shi kuwa lamin baima yi gayya ba domin acewarsa wannan ba biki zaiyi ba zaiyi bikinsa sai nan gaba yanzu bai isa aureba, ana igobe za afara shagalin biki suka koma sabon gidansu anan aka fara gudanar da biki washe gari akaje aka daura auren Abdulrahman da Kausar sannan aka wuce garin bauchi inda jama'a sukayi dafifi domin jiran daurin auren, ango yayi kyau cikin wata shudiyar shadda wadda tasha dinki mai tsadar gaske 12 dai dai aka daura auren junada mukhtar da angonta Lamin Kabir sulaiman akan sadaki dubu dari, ana daura auren lamin yayi tafiyarsa batare da ya nemi ganin amaryar ba. Ita kuwa dama ko sha'awar ganin fuskarsa batayi domin batasan waye ba kuma bata son tasanshi haka aka wuni ana kade kade da raye raye gamida bushe bushe yamma tanayi aka dauki amarya sai garin yola inda aka kaita dakinta.
[3/22, 4:42 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..

2⃣4⃣

Na
UMMI A'ISHA


    Wurin iyayen mijinta aka fara kaita sannan aka nufi sashenta da ita. Bayan kowa ya tafi ne husna da hasna suka shigo dakin nata idonta jajur kamar barkono tafara kallonsu dam taji gabanta yafadi domin sunyi mutukar yi mata kama da wannan copper din zama sukayi akusa da ita suka fara zuba mata surutu kallo ita dai take binsu dashi acikin ranta tana fadin waw identical twins dan hatta muryarsu iri dayace komai nasu iri daya babu ta inda suka banbanta, basu suka bar side dinta ba sai 10 nadare ita kuwa zaune tayi tana ta faman kuka shiru shiru babu ango babu dalilinsa har bacci ya dauketa. Karfe 6 ta tashi tashiga tayi wanka ta shirya cikin wata atamfa super purple colour dinkin bubu yayi mutukar amsarta, window din dakinta ta leka girman fadin tsakar gidan ne yaso tsoratata don babbane sosai part biyar tagani duk iri daya daga can gaba katon filin wasa ne an sassaka kayan motsa jiki ga wurin basketball da volleyball nan daga gaba kuma wurin table tannins ne komai dai na wasa an tanada awurin window din tasaki takoma na daya bangaren ta daga wani katon swimming poll ta hango gaba dashi kuma garden ne kawatacce.
[3/22, 4:44 PM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

2⃣5⃣

Na
UMMI A'ISHA


    Dakin nata tabi da kallo yasha furnitures masu tsada komai red da ratsin baki fitowa daga cikin dakin tayi wani dakin tagani yana kallon nata tsakiyarsu kuma dan karamin falo ne shima tunda ga kujerun zuwa labulayen duk red and black ne ga madaidaiciyar plasma tv manne ajikin bango, dakin dayake kallon nata ta bude tashiga shima babu laifi ya kawatu mutuka da kaya irin na zamani komai naciki red colour ne da toilet aciki fitowa daga ciki tayi ta murda kofar falon wani tangamemen falo tagani wanda ya sha luntsuma luntsuman kujeru har kala biyu daya ash colour dayan kuma pink colour ne dan haka labulayen ma sai suka kasance pink da ash colour ga wata jibgegiyar plasma manne abangon falon daga gaba kadan dining area ne taciki ga kitchen nan da store agefe, gefenta ta kalla shima dai wata kofar ce da alama shima irin dakunanta ne da dan falo aciki ma'ana dai sun saka tangamemen falon a tsakiya sukuma suna facing din juna dan haka shima ji tayi tana sha'awar ganin yanda aka tsarashi da karfin gwiwarta ta murda kofar tashiga dan karamin falo ne kamar nata da kujeru light green kanta ta daga tafara bin hotunan dake manne ajikin bangon falon da kallo cak! Taji numfashinta ya tsaya sakamakon ganinsa da tayi ajikin tangamemen hoton yana sanye da bakar riga ya gyara sumarsa yana murmushi.
[3/23, 9:51 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 9:21 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

2⃣6⃣

Na
UMMI A'ISHA

    Idanuwansa manya farare tatas kamar an diga zaiba aciki babu abinda yafi burgeta irin jajayen lips dinsa yayi bala'in yimata kyau sosai dadine ya kamata azuciyarta tafara fadin ya Allah kasa ba gizo wannan bawan naka yake min ba Allah kasa dagaske shine abokin rayuwata na har abada,sallamar da ta jiyo a babban falone yasata saurin fita daga cikin falon nasa hasna da husna tagani dauke da kayan breakfast sunsha ado sosai dasauri ta taresu tana fara'a a'a yan biyune sukazo sannunku da zuwa hasna ce tace sannu matar yaya ranta fari tas tazauna dasu suka fara hira har azahar tayi sannan suka bar side din nata suka koma nasu shiru shiru bata ga ango ba da haka har akayi kwana 5 da bikinsu sai dai kullum su hasna nazuwa su tayata hira wuni sukeyi awurinta wani lokacinma har dare suke kaiwa, yau tunda safe tafito babban falon ta zauna sallamar wata yar kyakkyawar mace taji ta amsa mata tashigo ciki bayan sun gaisa tace mata Kausar ce matar Abdul brother din lamin murmushi tayi tace sannu da zuwa yau kin fito kenan itama murmushin tayi tace eh yanzuma sallama nazo miki zamu tafi Uganda ne nida shi shiyasa nace baxan tafiba sai nashigo munga juna mikewa tayi tace yana waje yana jirana dan har mun fito itama mikewar tayi tabi bayanta tana cewa Allah ya saukeku lfy.



MACE GUDA DAYA👆TILO

2⃣7⃣

Na
UMMI A'ISHA


     Suna fita tsakar gida ta hangoshi gabanta yayi mummunar faduwa ahaka suka karasa inda suke tsaye suna jiransu sai da sukaje daf dasu sannan taga ashe ba mijinta bane sai dai suna mutukar kama sosai amma mijinta yafishi kyau nesa ba kusa ba kuma yafishi fari russunawa tayi ta gaida shi cikin sakin fuska ya amsa su husna ne suka runtumo suka zo suka rungumeta suna dariya itama dariyar tafara yi musu sallama sukayi dasu Kausar suka tafi ita kuma su hasna tabi side din mummy yaune karo na farko da ta fito tun zuwanta gidan side din mummy irin nata ne sak,adaki ta taradda ita ta sunkuya har kasa ta gaida ta amsa cikin kulawa sannan tace ai mijin naki yace gobe zai dawo daga kanon ko? Dam tayi sannan tace ehh dan bata son mummy ta fahinci har yau bata ganshi ba mummyn ce taci gaba da cewa jiya nake cewa aturo miki masu aiki guda uku da mai shara da wanke wanke da mai girki sai mai wanki shine lamin yace ai kince baki bukata zaki nayi duk da kanki kuma bakida ra'ayinsu shiyasa ma bakiyi magana ba kanta ta daga tace eh ninace kar akawo itadai mummy mamakine ya cikata saboda daga ganin wannan yarinyar kasan yar hutuce babu wahala atare da ita amma tunda ita tace bata ra'ayi shikenan mikewa tayi ta shiga dakin su husna nanfa suka fara hira babu laifi ta saba dasu dan haka ta sake dasu sosai fiyeda mummy domin tana dan jin nauyinta anan ta wuni har yamma sai da la'asar lis sannan suka dunguma suka koma bangarenta sai wurin goma sukayi mata sallama suka tafi.



MACE GUDA DAYA TILO

2⃣8⃣

Na
UMMI A'ISHA

   Yau a lissafinta kwanasu 10 da aure amma bata taba dora idonta akan mijinta ba kullum ita take yin aikinta shara wanke wanke girkine ake kawo mata daga wurin mummy kullum acan take wuni sai dare take dawowa side dinta. Wanka tayi taci kwalliya cikin wani material ja tafito da niyyar taje wurin mummy tana fitowa ta hango wata sabuwar mota blue kirar Mercedes 2015 new model tana shigowa tana karasowa ciki akaje akayi packing dinta a garage ya bude ya fito yana sanye cikin bakar riga an zana stars guda uku ajiki an rubuta just bring it ajiki yasa bakin wando yayi mutukar kyau fuska adaure ya karaso inda take yace ina zaki? Wata irin faduwa taji gabanta yayi yayin da zuciyarta ke dukan uku uku ba kakkautawa wurin mummy zani to muje ciki ina son magana dake yafada yana ta faman huci sim sim ta wuce yana biye da ita har cikin babban falon kujera ya samu ya zauna yayinda ita kuma ta zauna can nesa dashi kallo yabita dashi sannan yace ke! Karkiyi tunanin ko na aureki ne dan kin burgeni ko dan ina sonki no na aureki ne domin na wulakanta ki na nuna miki ke ba kowa bace face baiwa dan awurina baki da maraba da kuyanga zan maida ke tamkar baiwa wadda zata zama abin kwatance agari nine nan na hana mummy ta kawo miki yan aiki saboda wannan yana daya daga cikin horon da zanyi miki acikin gidan nan saina gama azabtar dake sannan zanyi miki saki uku kwarara yanda zaki dade kina jin bakin ciki arayuwarki, daga yau kece zaki nayin duk wani aiki nawa kama daga abinci wankin kayana gyaran dakina da sauran ayyuka kuma wlh koda wasa kika fadawa mummy saina raunata ki banza kawai ki kalleni da kyau ni ba class dinki bane wlh level dina ya wuce naki.
[3/23, 9:25 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

2⃣9⃣

Na
UMMI A'ISHA
   Tunda yafara bayaninsa binsa kawai take da ido batare da tayi koda motsi ba har ya diga aya wani mugun kallo ya watsa mata yace kalleta kamar mutuniyar kirki mai kamada aljana kawai sannan magana ta karshe duk abinda kika gani adakina kar ki kuskura ki taba mun ki bar min a mazauninsa idan kuma ba hakaba zaki yabawa aya zakinta dan sai jikinki ya gaya miki wlh yana kaiwa nan ya mike ya shige dakinsa ita kuwa ta kasa koda motsi dan fargabar irin zaman da zatayi dashi sai dai ita kuma har acikin ranta taji tana tsananin sonsa sannan kuma yana burgeta tun ranar farko data fara ganinsa ta dade azaune sannan ta tashi ta shiga kitchen ta dora abinci akaro na farko tun zuwanta gidan domin kullum mummy ce take bayarwa ake kawo mata shinkafa da miya ta dafa sa'arta daya ta iya girki domin ko agida wani lokacin itace take yiwa abbansu girki musamman ma idan zaiyi baki na kunya haka ta shirya abincinta mai rai da lafiya taje ta jera akan dining sannan ta wuce dakinta har yanzu bata jin zafin sa sai dai abu dayane ya tsaya mata arai auren ramuwar gayyar da yayi da ita shine har yanzu yake damunta tana daga cikin dakinta ta jiyoshi yana waya amma ba zata tantance da mace yakeyi ko da namiji ba abincin ya danci kadan sannan ya wuce side din mummy tundaga babban falo ya fara jiyo muryarsu husna suna cewa wlh mummy yaya lamin yafi yaya Abdul iya zabe matarsa tafi Anty Kausar kyau daya daga cikinsu yaji tana cewa to danma ba kiga gashinta ba ni jiya dana shiga dakinta lokacin ta fito daga wanka tsorata nayi gashinta fa har kugunta yanda kika san yar India murmushi momyn tayi tace ai dama daga ganinta zatayi gashi dai dai lokacin ya shiga cikin falon mummy suna ganinsa sukayi tsit sim sim suka fara kokarin fita suna cewa sannu da zuwa yaya lamin side din junada suka nufa suna fadin umm su anty junada yau honey ya dawo.



MACE GUDA DAYA TILO

3⃣0⃣

Na
UMMI A'ISHA


    Suna shiga suka sameta zaune acikin falonta tana kallon wani Nigerian film a tashar Nollywood zama sukayi suka fara tsokanarta yau anty junada ko nemanmu ba kyayi saboda yaya yadawo ko? Murmushi tayi tace ku kuka sani dai hasna ce tace wai anty junada ke yaya yana yimiki dariya husna ce tayi tsagal tace ba dolensa ba ita dai bata tanka musu ba haka suka karaci surutunsu nan suka zauna har magriba sai da sukaji shigowarsa sannan suka bar bangaren nata suka nufi nasu. Haka zamansu ya kasance Ita dashi kullum tana shiga tana gyara masa daki yauma kamar kullum tana jin fitarsa ta nufi dakinsa tashiga da toilet tafara sai da wankeshi tas sannan ta dawo cikin dakin tafara gyarawa ta shareshi tas ta goge tile din ta fito da kananan kayansa ta wankesu sannan ta fesa air freshener adakin drawer mudubinsa ta jawo tana shirya masa wasu takardu da tagani ya barbaza akan gado da alama test yayiwa dalibansa shine da yagama marking ya bazasu anan yatashi ya barsu awurin tana gama shiryasu kamar ance buda ta kasan ta jawo ta bude me zata gani wani kwali tagani yanata kyalli ta dauko tana budawa taga sun zubo tana duba jikin kwalin taga an rubuta condom gabanta ne yafara faduwa dasauri ta mayar masa inda yake ta ajiye ta rufe drawer ta koma dakinta innalillahi kawai take fada ba dai lamin neman mata yake yi ba? Tambayar da take ta yiwa kanta kenan innalillahi wa inna ilaihi raji'un zina? Kukane ya subuce mata nan ta zauna ta sha kukanta ta more wani kishine ya turnuke ta ganin kukan bashine mafita ba yasa ta tashi tashiga bathroom ta wanke fuskarta ta fito ta tsaya agaban mudubi ta gyara fuskarta fes ta fito ta nufi side din mummy tana shiga ta hango shi a babban falon yana kishingide yana karanta jarida ta gabanshi tabi ta wuce tashiga falon mummy ta samesu zaune ita dasu hasna suna ganinta suka fara murna oyoyo antynmu yanzu muke cewa bari mu tashi muzo tunda ke baki shigo ba har yanzu.
[3/23, 9:51 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 9:29 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

3⃣1⃣

Na
UMMI A'ISHA




    Murmushi tayi sannan tace ku dai kuyi shiru kawai tunda gashi na zo shikenan ta durkusa tana gaida mummy sannan suka dunguma zuwa dakinsu su husna anan suka zauna suka fara hira sai da rana tayi sannan tafito mummy ta hango tana kokarin shiga kitchen ta dora girki da sauri ta bita tace mummy me za adora? Cike da jin dadi tace jalop rice zan dafa to mummy barshi zan dafa cikin jin dadi mummyn tace to Allah yayi miki albarka ta juya ta fita daga cikin kitchen din cike da jin dadin yadda junada take darajata kuma take mutunta ta a falo ta zauna wurin lamin tanata yabon junada kafin kace me tuni junada tagama girkin ta yi farfesun hanta sannan ta hada salad ta zuzzuba su a flasks ta zo ta jera akan dining farin ciki ne ya mamaye zuciyar mummy, dakin su husna takoma ta zauna suka ci gaba da caftarsu ba ita ta tafiba sai dare tana zuwa dakinta ta sawa kofarta key ta kwanta nan da nan taji bakin ciki ya mamayeta sakamakon tunowa da abinda tagani adakin lamin wata zuciyar tace yanzu har ya isa neman mata? Eh ya isa mana tunda rayuwar waje yayi wata zuciyar ta bata amsa dakyar ta samu bacci ya dauketa. Ahaka suka zauna har ya gama weekend dinsa ya koma kano, kullum dakin su husna take wuni idan lokacin girki yayi ita zata shiga ta girka musu, suna jin dadin zama da ita sosai itama tana jin dadin zama dasu mutuka gashi kuma shi kanshi dadyn nasu yana ji da ita dan yauma foam ya kawo musu na federal university Yola yace su cike su ukun zasu fara zuwa makaranta tare. Su hasna psychology suka cike ita kuma micro Biology zata karanta,shi kuwa lamin yana can kano yana shagalinsa yama manta da wata junada tunda yatafi bai dawo ba saida yayi 2 weeks sannan yazo amma duk da haka junada bataji zafinsa ba asalima Allah Allah take yazo ta ganshi tana cikin dakinsa tana goge masa takalmansa ya shigo ko kallonta baiyi ba ya ajiye jakarsa ya shiga bathroom, murmushi tayi ta tashi tafita domin ta hada masa abinda zai ci.



MACE GUDA DAYA TILO

3⃣2⃣

Na
UMMI A'ISHA

  
    Taliya da macaroni ta dafa masa da miyar kwai ta kawo masa kan dining sannan ta fita zuwa bangaren mummy, yana fitowa daga wanka ya shirya cikin jar riga da wando baki yafesa turaren volish mai sanyin kamshi ya fito falo abincin data ajiye masa yaje ya buda kamshi ne ya bugeshi domin miyar tun a ido ta burgeshi tayi yellow tasha curry zama yayi ya zuba yaci ya koshi sannan ya fita wurin mummy acan ya samesu sunata zuba a babban falo amma suna ganinsa suka yi shiru bai kulasu ba ya shigewarsa dakin mummy. Sai dare yauma takoma side din ta lokacin data shiga yana zaune a babban falo yana daddana laptop dagowa yayi ya kalleta yace ke kawo min tea to ta amsa ta shiga kitchen ta hado masa tazo ta ajiye akan dan teburin dake gabansa ta wuce dakinta. Dasafe ta tashi ta gyara ko ina tsaf ta shiya breakfast sannan ta wuce dakinsa baya ciki da alama ya fita gyara dakin tayi sannan ta debo kayansa data wanke masa tun jiya tafara gogewa tana cikin gugar yashigo ya wuceta yashiga wanka bai dade sosai ba ya fito daga shi sai gajeren wando kallo daya tayi masa ta sunkuyar da kanta kasa ke ina kika ajiye min pants dina da kika wanke min? Mikewa tayi cikeda jin kunya ta dauko masa ta bashi warta yayi sannan ya wuce gaban drawer yafara shiryawa.
[3/23, 9:31 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

3⃣3⃣

Na
UMMI A'ISHA


    Kanta yana sunkuye har yagama shiryawa yafita daga cikin dakin gugar taci gaba dayi har ta goge kayan tas gaba daya ta fito ta shiga dakinta tayi wanka tana fitowa ta jiyo hayaniyar su hasna acikin falonta ta shirya ta fito wurinsu. Ranar Monday da sassafe ya fice ya nufi kano ita kuma ta tafi wurinsu mummy tana shiga suka fara yi mata albashir da sun samu admission har daddy yasa aje ayi musu registration dadi taji domin ko ba komai karatun zai dan debe mata kewa,aranar ummanta tazo mata murna kamar zatayi ihu haka suka koma side dinta ta cikata da kayan ciye ciye ita kuwa mahaifiyar tata kallon yartata takeyi tare da son jin irin zaman da sukeyi da mutanen gidan cikin fara'a tace wlh umma zamanmu lafiya dasu kowa yana kaffa kaffa dani harta shi kanshi daddy bakiga yadda yake kaunata ba kuma shi baima cika zama agida ba amma duk lokacin da yayo waya sai ya tambayi lafiyata dadi umman taji sannan tace to ya zamanku da mijin naki kuma? Murmushi nanma tayi tace shima lafiya lau muke zamanmu umma yau da sassafe ya tafi kano cikin fara'a tace ai mijinki yaron kirki ne last week ma yaje ya gaishe mu, amma ina masu aikin naki naga kamar babu kowa? Kanta ta daga eh wlh umma mummy ta samo min guda 3 to gaskiya banida ra'ayi ne tunda aikin nawa ba wani mai yawa bane kuma ni in banda kwanciya babu abinda nakeyi shiyasa nace gara kawai na rinka aikin mijina da kaina ko nafi samun lada murmushi umman tata tayi tace dakyau gaskiya kinyi kykkyawan tunani Allah yavada lada haka suka ci gaba da hirarsu batare da umman ta fahimci akwai matsala tsakaninta da mijin nata ba, wuni guda umman tata tayi amma ko kadan bata fahinci akwai matsala da mijin nata ba sai la'asar sannan sukayi mata rakiya zuwa airport ta hau jirgi ta tafi bauchi.
[3/23, 9:35 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

3⃣4⃣

Na
UMMI A'ISHA


   Acikin satin aka gama musu registration da komai na makaranta dama tuni anfara lectures dan haka daddy yace next week sai su fara zuwa da kansa ya dauko key din mota sabuwa Benz C230 ya bata yace saboda zuwa makaranta murna wurinsu ba acewa komai ita kanta junadan murna take domin ta daura aniyar karatun dagaske bada wasa ba,shi kuwa lamin ko weekend dinma bai zo ba saboda yana can tareda Mary a kano haka yayi zamansa bai waiwayi yola ba. Ranar Monday suka fara halarta makarantar su uku husna da hasna department dinsu daya ita kadai ce department dinta daban haka suka rinka zuwa wani lokacin har 2 suke kaiwa a makaranta babu laifi yanzu tana dan samun saukin tunanin da yaje addabarta. Sai karshen week din lamin yazo yola lokacin tana side din mummy suna kallon wani Indian film mai suna fashion kallo ya bisu dashi yace kullum Ku kenan a kallo kun shiga makarantar ma amma bazaku rage kallo ba maza dai yarinya ta samo carry over wlh saina tattakata sai a sannan junada ta daga kai ta kalleshi yana sanye da brown din riga da bakin wando fuskarsa sai sheki take tamkar wani tauraro bataso ya daina yi musu fadanba domin tana son amon muryarsa tana yimata dadi sosai dakin mummy ya shigewarsa husna kuwa taba baki tayi tace kaji shi ko ina ruwansa itama hasna bakin ta taba tace bar  masifaffe kawai ai kuwa nan da nan junada ta bata fuska tace bana son cin fuska gaskiya ya kuke zagin mijina agabana?  Murmushi sukayi sorry Anty harda hada baki hakan da sukayine ya bata dariya sosai. A haka sukaci gaba da zama har karatunsu yayi nisa alokacin shi kuma lamin ya gama service dinsa ya tafi Malaysia ya karbo result dinsa yana dawowa ya samu aiki a state university yola yafara lecturing tsakanunsa da matarsa kuwa sai dai kallo domin har yanzu yana nan akan bakansa neman mata kuwa yanzu ma yasa kafa.



Duniyar makaranta littattafan Hausa
Group Admin
       



MACE GUDA DAYA TILO

3⃣5⃣

Na
UMMI A'ISHA



   Haka suka ci gaba da zaman doya da manja tsakaninta dashi kullum side din mummy take wuni idan babu makaranta idan da akwai kuwa tana dawowa acan zasu yada zango ita dasu hasna sai dai kullum tana gyara masa dakinsa ta wanke masa toilet ta wanke masa kayansa ta dafa masa abinci ta ajiye masa amma bata taba burgeshi ba asalima shi a matsayin yar aikinsa ya ajiyeta. Semester tayi nisa domin har sun kai middle karatu sukeyi sosai kuma acikin wannan yanayin ne daddy da mummy suka samu visa zasu tafi kasar Spain inda daddy din zai halacci wani workshop na tsawon sati biyu daga nan kuma zasu wuce saudiyya domin gabatar da umara dan haka tuni suka fara shirye shiryen tafiya su kuma su husna sun gama hado kayansu sun dawo sashen junada,washe gari sukayi sallama dasu suka tafi suna tafiya suka dawo falon junada suka zauna suna hangowa yadda zasu kwashe da zaman gidan yaya lamin ai kuwa basu dade da zama ba sai gashi fuska babu annuri ya shigo ya ce ina take? Tana daki husna ta bashi amsa to kice ta kawo min abinci ya wuce dakinsa tashi husna tayi tashiga dakin lokacin ita kuma junada tagama shiryawa cikin wata atamfa yellow dinkin riga da skirt husna tayi murmushi kin gama adai dai anty domin yanzu yaya yadawo yace ki kai masa abinci to ta amsa tafita da sauri tashiga kitchen dambun shinkafa tayi da farfesun koda ta dauki juice mai sanyi ta nufi dakin nasa yana zaune bakin gado daga shi sai gajeren wando yana waya kanta a kasa ta isa gabansa ta ajiye farantin ta juya ta fice. Suna nan zaune a falon yafito cikin shiga mai kyau blue din jeans da pink din riga yayi kyau sosai sai kamshin turaren Phoenix ne ke tashi ajikinsa ko inda suke bai kalla ba yafice.
[3/23, 9:51 AM] Ummi A'isha: [3/23, 9:41 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO

3⃣6⃣

Na
UMMI A'ISHA


   Husna ce ta kalli hasna tace tofa ai mun shiga uku kuma tunda aka barmu awurin wannan mugun hasna tace ai dama wlh da yaya Abdul na nan agidansa zamu zauna harararsu junada tayi tace ai kuwa da baku isaba wlh suna cikin maganar sai gashi sun shigo shida wasu mata guda 2 kyawawa dakinsa suka wuce bako sannu dama yan matan ba musulmai bane Jim kadan sai gashi ya fito ya kallesu daya bayan daya yace wadannan abokan aiki nane zasu zauna anan dan haka wlh koda wasa naji yarinya ta fada idan su daddy suka dawo sai na illata ta kuna jina kai suka daga dan duk cikinsu babu wacce ta iya magana junada kuwa tafi kowa bakin ciki ranta ya gama baci sosai juyawa yayi ya koma dakin hasna ce ta mike ta shiga dakinsu wanda yake opposite din dakin junada husna itama tashi tayi tabi bayanta tana shiga tasameta ta rafka tagumi kusa da ita taje ta zauna tace hasna me kika fuskanta da wannan lamari? Cikin takaici hasna tace ai husna yaya lamin dan rainin wayone wai abokan aiki wadannan sunyi kama da lecturers? Kawai yan matansa ne wlh ni dama nadade da sanin yaya lamin yana neman mata cikin bacin rai husna tace ai shiyasa kullum nake tausayawa anty junada tana mutukar hakuri dashi kuma bata taba nuna mana laifinsa ba kullum cikin boye sirrinsa takeyi bata taba fada mana tsakaninsu ba Allah shiryeshi amin inji husna. Ita kuwa junada dakyar ta iya tashi saboda jirin da yake dibanta sai yau tasan tana tsananin kishin mijinta akan gadonta ta kwanta tafara wani irin kuka mai ban tausayi acikin zuciyarta kuwa addu'a take masa Allah ya shiryar dashi haka ta wuni tana kuka tuni kanta yafara ciwo amma haka ta fito ta shiga kitchen ta dafa musu abinci ta koma dakinta ranar haka dukansu su ukun suka wuni cikin takaici shi kuwa yana can yana holewarsa.



MACE GUDA DAYA TILO

3⃣7⃣

Na
UMMIA'ISHA


   Wasa wasa tun abin yana basu haushi har ya dawo ya daina basu domin yan matan nan sai da suka shafe kwana 9 acikin gidan sannan suka tafi shi kuwa ko ajikinsa su husna kuwa basu isa sun fadi laifinsa agaban junada ba dan yanzu zata bata rai taji haushinsu sai dai idan sun koma gefe suyita Allah wadai da halin yayan nasu ita kuwa junada addu'a kawai take yi Allah ya shirya mata shi ya karkato mata da hankalinsa kanta. Ranar Monday tunda wuri ta tashi ta shirya masa breakfast ta gyara masa dakin ta koma ta tashi su husna suka shirya suka tafi makaranta suna dawowa suka tarar yana fitowa shida wata farar budurwa Christian da sauri suka basu hanya suka fita sannan suka shiga falon,junada cikin ranta taji kamar taje ta shake wannan matar amma babu dama. Aranar da daddare yazo da wata daban shi kuma sassafe ya fice domin 8 to 10 yake yiwa wasu daliban lecture wasu kuma 1 to 2 ita kuwa junada saida tagama gyara ko ina sannan ta nufi dakin nasa da nufin gyarawa tana shiga ta ganta kwance kyakkyawa ce sosai ai nan da nan kishi ya cikata duka ta daka mata firgigit ta tashi tana mikewa ta kifa mata mari tace dan ubanki me ya hadaki da mijina tsorone ya kama arniyar tace kiyi hakuri bai cemin yana da mata ba, ni nafada miki kuma yau sai na kasheki wata kwalbar lemo ta dauka tace zaki kara kula mijina? Cikin tsoro tace a'a hakuri ta fara bata sosai saida ta Kara wanketa  da mari sannan ta hankadata waje ta cilla mata jakarta waje ai tuni tafice daga gidan aguje ranta babu dadi tagama gyara dakin tafice. Haka zaman nasu ya kasance har sati 3 tuni an kafe musu time table na exam anyi closing lectures din dan haka babu inda suke zuwa karatu kawai sukeyi agida.
[3/23, 9:47 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..

3⃣8⃣

Na
UMMI A'ISHA


    Yauma kamar kullum da sassafe junada ta tashi tagama gyare gyaren gidan su husna suna can suna aikin nasu wato bacci idan suka kwanta bacci daga asuba sai sun Kai 12 basu farka ba itace take tashi da wuri take ayyukanta duka. Wurin 11 tagama komai ta shiga dakinsa baya ciki da alama ya fita kananan kayansa ta tattara tashiga toilet ta wanwanke sannan ta wanke toilet din, tana gamawa tadawo cikin dakin tafara gyarashi tana gyaran gado suka shigo shida wata arniya siririya baka kyakkyawa ya dan saci kallon junadan yaga tayi kicicin kunya ya dan ji don baisan tana cikin dakin ba kallon yarinyar yayi yace Jen have a sit am coming ficewa yayi daga dakin Jim kadan sukaji karar tashin motar da alama fita yayi daga gidan juyowa junada tayi taga karuwar tasa tana gyara fuskarta ajikin mudubi fisgo ta tayi tafara wanka mata mari tas! Tas! Tas tace dan ubanki zaki kara biyo mijina? Cikin kuka tace no am sorry pls tace ba wani hakuri dan ubanki yau saina datse miki kafafu tuni Jen ta rude tafara bata hakuri fincikarta tayi ta hada da bango ta shaketa dai dai nan yashigo dasauri junada ta saketa ita kuwa tace kafa me naci ban baki ba sai gudu ko sauraronsa batayiba, cike da mamaki ya kalli junada yace me kikayi mata? Shiru tayi masa taci gaba da aikinta ransa ya baci sosai ficewa yayi daga dakin ya koma falon ya zauna ita kuwa aikinta tayi tana gamawa ta fito ta wuce dakinta.



MACE GUDA DAYA TILO...

3⃣9⃣

Na
UMMI A'ISHA



    Mamaki ne ya kamashi to me yakori jen? Wayarsa ya dauka yafara kiranta tana dauka tafara zaginsa tana cewa banza mayaudari dama ashe kanada mata shine ka daukeni ka kaini gidanka dan matarka ta kasheni ko? To daga yau babu ni babu kai macuci kawai ta kashe wayarta mamaki ne ya cikashi to me wannan yarinyar take nufi? Rannan ma da yadawo bai samu Grace ba bayan kuma yatafi ya barta adakin da yakirata awaya da kyar ta dauka ta zazzageshi wai ba ita bashi domin matarsa mahaukaciya ce kashe mutane take wato itace take korarsu kenan kodai sonsa take? Tashi yayi yabar falon ganin bashida amsar tambayar da yayiwa kansa. Ita kuwa ta daina ma saka abun aranta addu'a kawai takeyi Allah ya shirya shi, yau saura kwana 3 su mummy su dawo daga umara har sun fara shirye shiryen taryarsu tana dakinta akwance su husna kuma suna daya dakin ya shigo ki tashi ki dafa min indomie guda 4 da soyayyen kwai ki kawo min daki to tace ta mike ta shiga kitchen tana mamakin kanta wai yau itace ake juyawa haka duk irin gatan ta lallai ta yadda sarki agidan wani sarkin bawa ne da wannan tunanin ta gama dafawa ta soya kwai guda 6 ta dauki cokala guda biyu dan tasan shi kadai indomie Hudu tayi masa yawa dan bashida cin abincin sosai dakin nasa ta nufa ta kwankwasa shiru dan haka kawai sai ta tura kofar tana shiga ta hangoshi daga shi sai gajeren wando ita kuwa karuwar tasa zigidir take haihuwar uwarta sun shagala sai romancing juna suke tuni jikinta ya fara rawa ta saki farantin abincin ya zube filet din tangaram din ya fashe karar ce tadawo dasu cikin hankalinsu tuni ta ruga aguje tabar dakin shi kuwa jikinsa yaji yayi masifar sanyi rana ta farko da yaji kunyar junada ranar farko da yaji ya tsani zina arayuwarsa kuma yaji ta fita acikin ransa tashi yayi yace da Agnes ta shirya ta bar gidan tambayarsa abinda ya faru tafara wata tsawa ya daka mata yace ta fice kawai cikin sauri ta shirya ta dauki jakarta ta fita shi kuwa kamar wanda aka zarewa laka ajiki duk ya sukurkurce.


Duniyar makaranta littattafan Hausa Group Admin
        
Ummi A'isha




MACE GUDA DAYA TILO..


4⃣0⃣

Na
UMMI A'ISHA



  Tana isa dakinta ta kwanta akan gado jikinta sai faman rawa yake innalillahi kawai take ambata, hayaniyar su husna ta jiyo a falo amma bata fita ba tana nan kwance kamar marar lafiya, shi kuwa lamin dakyar ya iya tashi yasa kayansa ya fito daga falo tajiyo yana tambayar su hasna ina take? Tana cikin daki inji su kai tsaye dakin ya wuce ya ganta kwance ta kudundune kanta ke ki tashi kije ki gyara min dakina da kika bata ni fita zanyi yana fadin haka ya fita ita kuma tashi tayi tana mamakin shi kuwa lamin me yagani ajikin wannan arniyar? In banda kashi ita bata ga komai ajikinta ba amma dan jaraba irin ta maza shi burgeshi tayi ahaka mikewa tayi taje ta gyara dakin ta kunna turaren wuta sannan ta rufo kofar ta dawo wajen su hasna.  Washe gari da wuri ta fito saboda yunwar da takeji kanta tsaye kitchen ta wuce ta debo ruwan zafi tazo ta hada tea mai kauri ta dawo falo tafara sha da niyyar idan ta gama zata koma kitchen ta hadawa su hasna da lamin nasu, kamshin turarensa tafara jiyowa tuni kamshin nasa ya gama rudata ta ajiye kofin sakamakon ganinsa da tayi ya fito yana sanye cikin suit bakake yayi kyau sosai kallonta ya yi sannan yace bani breakfast dina fita office zanyi dasauri ta mike ta shiga kitchen ta soya masa manyan kwai guda 4 ta debo ruwan zafi a kofi sannan ta dauko masa bread ta dawo ta ajiye masa ta koma ta dauko butter da yar wukar da za ashafa butter din ta dawo ta ajiye ta nufi kitchen ke ni zan shafa butter din? Taji yace dawowa tayi tazo ta tsugunna ta dauka ta fara shafa masa shi kuma ya dauki kwan ya fara ci, yan yatsun hannunta ya zubawa ido farare sol dasu dogaye miko masa tayi yasa hannu ya karba yana mai ci gaba da kallon hannun nata tana gamawa ta mike ta koma kitchen.



Ummi A'isha
[3/23, 11:54 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 11:23 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO.....


4⃣1⃣


Na
UMMI A'ISHA


   Aiki tafara tanayi tana tunanin abin sonta lamin ita dai Allah ya dora mata sonsa tun ranar farko data fara ganinsa a makarantar su shigowarsa taji cikin kitchen din kamshin turarensa shine ya cika mata hanci tuni taji jikinta yayi la'asar ta bayanta ya tsaya ya ajiye kayan yabi bayanta da kallo sannan ya juya ya fita ajiyar zuciya ta saki sannan taci gaba da aikinta tana fadin Allah ya kara shirya min kai lamin, sai data gama dukkan ayyukan sannan ta nufi dakin sa domin gyarawa tana shiga taga wata arniya zaune a bakin gadonsa nan da nan kishi ya motsa saboda duk a tunaninta adakin ta kwana kallonta tayi tana sanye da wata yar ficiciyar riga iya cinya kanta taci gashin kanti fal dubanta tayi tace sannu amma ya zaki zauna tun safe acikin datti washe baki tayi tace no zuwana kenan yanzu shima bai san da zuwana ba nayi mishi surprise visit ne murmushin takaici tayi ta jawo wani karfe tace yau zan koya miki hankali jibga mata tayi zata kurma ihu ta toshe bakinta ta yar da karfen ta soma gaura mata mari tana cewa waya kawoki wurin mijina? Yau saina kasheki idanuwan tane suka firfito ita kuwa marinta taci gaba dayi saida ta kumbura mata fuska sannan ta kaita waje ta cilla mata handbag dinta ta dawo taci gaba da gyaran dakin aranta tana raya cewa har yanxu ina son mijina kuma zanci gaba da sonsa ya Allah ka ganar dashi gaskiya tana gama gyaran dakin yana dawowa alhalin kuma ba haka ya saba yiba idan ya fice wani lokacin sai dare gabanta taji yafara faduwa saboda ta tabbata karuwarsa ce ta fada masa dukan da tayi mata dan haka cikin sauri ta shige dakinta yana shigowa su hasna na fitowa falo tambayarsu yayi ina antynku? Tana daki suka bashi amsa cikin dakin ya nufa tana zaune bakin gado ki fito ki bani abinci yunwa nakeji.




MACE GUDA DAYA TILO...


4⃣2⃣


Na
UMMI A'ISHA



    Yunwa nakeji office zan koma ko sai kin bata min rai? Murna ce ta rufeta tafito ta nufi kitchen shikuwa mamaki yakeyi wai wannan yarinyar ce kiri kiri ta hanashi zama a office domin tunaninta daya addabeshi. Gari na wayewa su mummy suka dawo dama tayi musu shirye shiryen karbarsu tayi girke girke da yan soye soyen karbarsu. Da daddare daddy dakansa ya shigo bangaren mummy ya kirawo lamin sudai suna zaune suna sauraron abinda zai faru cikin fada daddy yafara cewa lamin baka kyauta mana ba yanzu ashe dama baka da mutunci? An tabbatar min da cewa kana kawo mata gidan nan da bama nan cikin sauri junada tace a'a daddy karya ake yi masa abokan aikinsa ne aka kawosu basu samu dakiba to shine ya kawo su nan kafin su samu daki kuma saida ya fada mana nida su husna cewa zasu zauna kafin a sama musu masauki sannan kuma daina shiga dakin yayi har sai da suka tafi cikin mamaki yabita da kallo su hasna kuwa shiru sukayi domin sun san wannan maganar ba gaskiya bace kawai ta fadi hakane danta kareshi amma ba wani abokan aiki girgiza kai daddy yayi yace shikenan Allah ya rufa asiri suka amsa da amin sannan dadyn yatashi ya koma sashensa shima sashensu ya tashi ya tafi sai faman cika yana batsewa yake.



MACE GUDA DAYA TILO...

4⃣3⃣


Na
UMMI A'ISHA


    Suna nan zaune a falon mummy, mummy ta fiddo musu da tsarabarsu ta basu kowa jaka guda ta ciko masa da kaya, nan suka baje kayan kowa yana ganin nasa sai murna sukeyi. Shi kuwa lamin yana can dakinsa yanata tunanin me junada ke nufi? Anya kuwa yarinyar nan bata fara sonsa ba? Xumbur ya mike ya nufi sashen mummy ya taradda su yanda ya barsu mummy dan Allah baku dawo da maganin ciwon kai ba? inajin akwai junada ya kalla ki kawo min ina daki, mummy ce ta shiga dakin da kanta ta debo mata maganin ta bata, mikewa tayi ta nufi sashensu ta dauki ruwa a kofi marar sanyi tana shiga dakin ta sameshi tsaye abinka ga lecturer ansaba tsaiwa mika masa ruwan tayi bai karba ba, yace kya iya zubarwa dan ba shine a gabana ba, agidan uban wa kika zama matata da zaki rinka korar min yanmata? Ai nafada miki ni ban daukeki a matsayin mata ba, a yar aiki na ajiyeki mamakine ya kamata lallai wani mutumin ba ayi masa gwaninta yaci gaba da cewa banda ke shasha ce kuma munafuka ina ruwanki da sha'anina? Cikin bacin rai ta kalleshi gaka nan babban munafuki mai sabawa Allah da manxonsa dan nace ni matarka ce shine ina nufin sonka nake? Allah ya sawwake me zanyi da mazinaci, kazami mai bin yayan arna? Nayi hakane dan na kareka daga masifar zina amma ba don ina sonka ba ko kana nufin ban san illar shaidar zir ba? Nasani amma nayi don na tseratar da kai daga fushin iyayenka dan na lura kana da karancin ilimin addini baka san hukuncin mazinaci ba taja wani dogon tsaki ta juya tafice dakinta taje ta kwanta tafara kuka sam bata so haka ta faruba taso ace yanda ta sauke duk wani girman kanta take binshi sau da kafa shima yayi hakuri ya karbeta a matsayin abokiyar rayuwa kuka takeyi sosai. Shi kuwa yana nan tsaye inda ta barshi kamar dashen ice ya kasa koda motsi maganganunta ne kawai ke masa yawo a kwakwalwarsa abu 3 ne yafi bata masa rai kalmar data kirashi da ita ta jahili da kuma kiransa da mazinaci da tayi sannan cewa me zatayi dashi yafi komai daga masa hankali da bata masa rai, dakyar ya iya daga kafarsa ya isa bakin gadonsa ya kwanta kansa sai zugi yake masa kamar zai rabe gida 2.
[3/23, 11:25 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

4⃣4⃣

Na
UMMI A'ISHA

    Kwana 2 yayi yana jinyar maganganunta kuma tun daga ranar bai Kara yadda sun hadu ba abinci ma idan ta ajiye masa baya ci yanda ta ajiye kayanta haka zata dauka bai ko buda ba abin duniya ya isheta, bayan ta gama ayyukanta tazo ta tsaya ajikin window ta daga labule lamin ta hango yana motsa jiki afilin wasa yasa farar riga irin ta yan ball da wandonta yasa farin takalmi combos yanata buga kwallo shi kadai nan ta tsaya tana ta kallonshi har yagama ya nufo cikin falon labulen ta saki ta nemi wuri ta zauna a bakin gado su husna ne suka shigo hasna tace ah anty junada wannan rigar fa? Hararsu tayi tace ba ason sa ido da sauri husna tace gaskiya rigar tayi kyau kamar shimi amma har gwiwa take shigowar lamin ce ta katse musu maganar yabi junada da kallo ita kuwa da sauri ta jawo hijab ta saka su hasna ya kalla yace yaran nan baku da kirki kwana biyu banida lafiya amma ko ku dubani cikin sauri sukace wlh yaya bamu sani ba eh amma wadda kuke tareda ita ai tasani juyawa ga junada sukayi suna cewa amma anty baki kyauta ba kallo tabishi dashi yayi kyau sosai yana sanye cikin riga t. Shirt brown da jeans blue yanata kamshin turaren Phoenix kallonta yayi yace zakizo ki bani abincin ko kuwa? Dasauri ta mike ta shiga kitchen ciki yabita yana tsaye yana kallonta tana zuzzuba masa abincin har tagama ta dauko zata fito hanya yabata amma yana tsaye a bakin kofar tsayawa tayi tace zan wuce to ki wuce mana ko na hanaki ne? Ahaka ta wuce amma dole saida ta dan bugeshi sannan ta iya wucewa bayanta yabi har suka isa dining area din.
[3/23, 11:40 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TIILO..

4⃣5⃣

Na
UMMI A'ISHA


     Kallo ya ringa binta dashi har ta gama zuzzuba masa ta ajiye masa ta wuce dakinta murmushi yayi yafara ci. Wasa wasa sai jinsa yayi ya wayi gari da matsanancin son junada kuma tun ranar data gaggaya masa maganganun nan yaji zina ta fita daga ransa baya sha'awar aikatata dan haka tuni yafara neman gafarar ubangiji ba dare ba rana. Gaba daya sonta yagama shigarsa ta ko ina bashi da buri illa kasancewa da ita dan haka ya daura aniyar nuna mata so afili tare da bin duk wata hanya domin yasamu ta shaku dashi, yau sai 5 yadawo domin meeting sukayi kansa tsaye ya wuce side dinsu amma ya tarar bata nan ya tabbata tana wurin mummy  dan haka ya nufi can din yana shiga ya tarar da mummy a babban falo tana waya ita kuma dama yaji motsinta a kitchen dan haka kitchen din ya bita ya taradda ita tana fere doya kamshin turarensa kawai taji tasan yashigo tsayawa tayi cak daga aikin da take bayanta ya karaso yazo ya tsaya ahankali tamkar mai yin rada yace wai ni meyasa duk abinda kikeyi daga kin ganni sai ki daina sai kace wani dodo? Saboda ina sonka tafada acikin zuciyarta amma a fili shiru tayi bata amsa masa ba, da rana me kuka dafa? Tuwon shinkafa ta bashi amsa yanzu kuma me zaki dafa? Soyayyiyar doya da miyar koda murmushi yayi to ni yanzu me zaki bani? Dan yunwa nakeji babu abinci amma akwai snacks to kawo min snacks din da juice tana jiyowa sukaci karo sorry ya fada tareda ja baya ya koma falo murmushi junada tayi tace Allah yakara shirya min kai lamin yana zuwa ya zauna kusa da mummy hayaniyar su husna ya ji a dayan falon ya kalli mummy me yaran nan sukeyi ne? Kallo mana mummy ta bashi amsa murya ya daga hasna kuzo nan suna zuwa ya fara masifa wato ku baku da aiki sai kallo ko? Kun bar junada ita Kadai da aiki kuna jira ta gama ta kawo muku kuci ko saboda ga baiwa? To wlh baku isaba kune zaku rinka girki ba matata ba ku tashi ku shiga kitchen ku karasa aikin da takeyi tashi mummy tayi tana fadin dakyau ka kyauta yara yan mata dasu amma ba su iya girki ba idan akayi aurensu ya zasu yi ta shigewarta dakinta su kuma su hasna suka shiga kitchen juyowa yayi ga junada wadda tun dazu take rike da kaya a hannu tana jiran ya karba.



MACE GUDA DAYA TILO..

4⃣6⃣

Na

UMMI A'ISHA


    Mika masa tayi ya karba yana cewa kar ki kara yi musu girki a marerece tace ai basu iya ba kallonta ya sakeyi yace karya suke sun iya ki rabu dasu dolensu suyi falon taga yayi gaje gaje kamar ba agyara ba dan haka tsayawa tayi tafara gyara falon ahankali yafara binta da kallo wannan yarinyar gaskiya kyakkyawa ce ta ajin karshe sai wanda yake kusa da ita ne ma zaifi tabbatar da hakan ta hadu ta ko ina da haka yagama cin snacks din yatashi ya fice ya nufi side dinsu ita kuwa dama duk a takure take yana fita ta tashi ta shiga kitchen wurinsu husna. Sai dare tabar side din mummy tare dasu hasna domin har yanzu basu dawo sashen mummy ba sanda suka shiga yana falo yana kallo sannu yaya su hasna suka fada suka shige kai kuzo nan ya fada jiyowa sukayi suka dawo junada ya kalla wannan yaran har yanzu anan suke kwana? Kai ta daga masa tace eh kallonsu yayi to wlh kun kusa komawa inda kuka fito dalla ku wuce ku bawa mutane waje da sauri suka wuce ya kalli junada kawo min ruwan zafi amma empty kar kisa milk to ta amsa masa ta shiga cikin kitchen ta hado masa ta kawo masa rissinawa tayi ta mika masa karba yayi yana kallon yan yatsunta wanda suke tsananin burgeshi tana bashi ta wuce dakinta. Washe gari da wuri ta tashi ta gama abubuwan da za tayi ta shirya domin ranar zasu fara exam tun 8:30 suka tafi lokacin ko tashi daga bacci baiyi ba lokacin data shiga dakinsa kwance ta ganshi daga shi sai gajeren wando ko riga babu ajikinsa,ya kure A. C baccinsa yake hankali kwance, kallonsa ta tsaya ta farayi fatarsa sai sheki take kamar ta mace da gani zatayi laushi ko ina najikinsa gashi ne ya kwanta luf luf wani irin kyau taga yayi mata sleeping beauty ta fada ahankali ta fice daga dakin. Shi kuwa lokacin da ya tashi ya shirya ya fito sai yaji falon tsit da alama sammako sukayi zuwa makaranta.



Ummi A'isha🏻
[3/23, 11:54 AM] Ummi A'isha🏻: [3/23, 11:45 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO
....

4⃣7⃣


Na
UMMI A'ISHA


   Falon ya fito yakarasa kan dining  yaga flasks a jere, yafara budewa soyayyen dankali da kwai yaga sai kamshi yake, ya bude dayan farfesun kaji ne shima kamshine kawai ke tashi duk abinda tasan yana bukata ta hada masa nan ya zauna ya cika tumbinsa sannan ya nufi cikin dakinta yana shiga yaji kamshin room freshener dana turaren wuta sun hadu sun doki hancinsa dakin nata yafara kallo komai tsaf tsaf babu datti ko daya gefen gadonta yaje ya kwanta aransa yana tunanin cewa ya kamata ya ajiye duk wani girman kansa ya rungumi matarsa ya nuna mata soyayya dan tabbas yar halak ce duk matsayinta da mukamin mahaifinta amma ta kaskantar da kanta take yi masa bauta har kayansa ta ke wankewa ga wulakancin datake fuskanta daga wurinshi amma duk ta jure wani irin juyi yayi akan gadon yace nayi alkawari sai nayiwa junada abinda zata soni, zata kaunace ni tashi yayi yakoma dakinsa domin duk ba yajin dadin jikinsa sakamakon rashin ganin junada dan haka yau bazashi aiki ba. Yana nan kwance ya saka fari ya saka baki har ya kwashe awanni bai ankara ba ya jiyo hayaniyarsu acikin dakin junada, tashi yayi ya nufi dakin nata lokacin hasna tana daya dakin tana wanka ita kuma husna tana tsaye tana sanye da wata doguwar shimi ta bawa kofar shigowa baya tana shirya lecture note dinta ita kuma junada dogon wando ne ajikinta da  bra tana zaune akan gado tana facing din kofa ta sunkuyar da kanta tana duba questions paper din su husna gaba daya hankalinta yana kan question paper din yana shiga ya ganta yasalam ya fada sadaf sadaf ya juya da niyyar ficewa amma sai aka samu akasi kafarsa ta bugi kofa dago kanta tayi tana dagowa suka hada ido wata kunya ce ta lullubeta shi kuwa cewa yayi sorry you are changing? Ya fice daga dakin hankalinsa a tashe acikin ransa yana cewa lallai ashe yarinyar nan lullube take da baiwa iri iri shiyasa take yanga? Lallai da yaso tafka babban kuskure a rayuwarsa, ita kuwa junada haka kawai ta kasa jin zafinsa amma taji wata azababbiyar kunyarsa ta kamata.





MACE GUDA DAYA TILO...

4⃣8⃣

Na
UMMI A'ISHA


    Tun daga lokacin ta daina yarda su hadu, wasan buya suka shiga tun bai gane ba har yagano kunyarsa take ji murmushi kawai yayi yace yaro yaro ne. Ahaka ahaka har suka kusa gama exam dama shi kawai kyaleta yayi tagama exam din lokacinne zai fito mata da manufarsa a fili, da daddare yashigo a babban falo ya iskesu suna cin abinci suna kallon wani Nigerian film mai suna i promise kowa rike da filet dinta a hannu gaba daya hankalinsu ya tattara akan film din ahankali yazo kusa da junada ya zauna batare da sunji motsin sa ba magana yayi yace sannunku sarakan kallo gaba dayansu babu wadda bata tsorata ba dan sam basuji shigowar sa ba kallo junada ta fara binsa dashi yayi kyau sosai rigar jikinsa maroon colour an zana tsintsaye guda uku ajiki an rubuta Angry Birds brown din jeans yasa kamshin turaren sa kamar kullum ya baibaye wurin,husna ce tayi dariya tace gaskiya yaya ka bamu tsoro wlh junada ya kalla wadda har yanzu itama shi din take kallo murmushi yayi yace ga babbar matsoraciya nan wadda take neman cinye ni da ido dariya suka sa ita kuwa murmushi tayi ta dauke kanta daga kallonsa abincin nata ya dauka yace matso muci nima yunwa nake ji kallonsa tayi tace ni na koshi kaci sai in karo maka tsareta yayi da ido tamkar mai yin rada yace wlh baki isa ba sai munci abincin nan tare kafada ta make ahankali ahankali yafara matsowa har yazo kusa da ita sosai ya kamo hannunta daga shi har ita wani bakon al'amari ne ya ziyarce su wani irin yarr taji ajikinta, su husna kuwa tsayawa sukayi suna ganin ikon Allah, ganin bazata ci ba yasashi kwanto da ita jikinsa ya debo yana shirin bata tamkar wata jaririya kunya ce ta kamata ganin su hasna na kallonsu shi kuwa yama manta dasu na wurin ganin taki ci yasa yajiyo asannan ne ya gansu korarsu yayi yace kai ku bar nan da sauri suka mike suka shige daki suna shigewa ya jiyo gareta yasa tattausan hannunsa ya kamo hannunta wanda ya dade yana burgeshi ahankali yafara murza yan yatsunta acikin hannunsa wani irin taushi da laushi yaji a hannun nata tuni ya shagala yama manta da batun abinci.
[3/23, 11:50 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...


4⃣9⃣

Na
UMMI A'ISHA


     Ahankali ta zare hannun nata daga cikin nasa ta kalleshi tace to kaci abincin kace yunwa kakeji kallonta shima yayi idanuwan shi sun canza launi yace ai nace miki tare zamuci tashi tayi taje cikin kitchen ta zubo abincin ta dawo wurin shi ta ajiye akan stool din gabansa kallonta yayi yace to muci kinga cokalin guda daya ne don haka sai muyi kama kama zama tayi a kusa dashi abincin ya fara ci ya miko mata cokalin karba tayi itama tafara diba tana ci shi kuwa gaba daya hankalinsa yana wajenta ahaka har suka gama cin abincin mikewa tayi da nufin zuwa ta dauko musu ruwa da sauri ya kamo hannunta yace barshi na dauko mana a'a ka barshi zan dauko no barshi kawai mikewa yayi yaje fridge ya dauko musu ruwan da kofi ya dawo wajenta yace zakisha da kanki ko na baki a baki? A'a zan sha da kaina tsiyayo mata yayi ya mika mata ta karba tasha sannan ta mika masa shima yasha, mikewa tayi tace zan shiga daki binta yayi yace to muje tana gaba yana biye da ita har cikin dakin a gefen  gadonta ya xauna ita ma zaman tayi domin a takure take gashi tana son tayi wanka amma bazata iya tashi tashiga a gabansa ba.




MACE GUDA DAYA TILO...


5⃣0⃣

Na
UMMI A'ISHA



      Tashi yayi yace to sai anjima Allah ya jima damu tafada a hankali fita yayi daga cikin dakin ya nufi dakinsa ita kuma wanka ta tashi ta shiga tana fitowa ta ganshi tsaye daga shi sai gajeren wando da farar best kallonta yafara yi sosai daga ita sai dan guntun towel, gashin kanta har kugunta sai faman kamshin mai dadi takeyi na sabulun da tayi wanka dashi yaya lamin me kake so? Ta fada cikin rawar murya kamar wanda yake koyon magana yace ruwan wanka zaki zo ki hada min to ina zuwa ta bashi amsa acikin zuciyarta kuwa cewa take aikin nawa ya karu kenan tunda yanzu har dasu zuba ruwan wanka, tsaye ya tsaya mata yaki fita jiyowa tayi tace ina zuwa shiryawa zanyi kallonta yayi sannan yace to shirya mana ko na hanaki ne? Ganin bashida niyyar fita yasa ta tattaro gashin kanta ta tufke tamkar gammo a kunyace ta dauki dogon hijab ta sa tazo zata wuce jawota yayi yace tsaya mana madam kisa kayanki mana a'a sai na dawo zan sa to shikenan muje wucewa tayi izuwa dakin nasa ta shiga bathroom ta hada masa ruwan wanka harda turaren wanka ta zuba masa ta fito lokacin yana waya sunan Jen taji ya ambata dan haka ba tayi wata wata ba ta fice daga dakin cikin sauri zuciyarta sai faman tafarfasa takeyi wato arnan nan ba zasu kyale mata lamin ba ko? Allah yasa yarinya tayi gangancin zuwa mata gida wlh sai ta raunata ta da wannan tunanin ta shitya cikin rigar baccin ta ja mai kyan gaske ta jawo hand out dinta ta soma karantawa domin tana da exam gobe dama guda 2 ne suka rage mata. Washe gari ta tashi ta hada breakfast ita dasu husna dankali da kwai ta soya musu shi kuma lamin plantain da kwai ta soya masa tayi masa farfesun kayan ciki ta zuba masa ruwan zafi a cikin flask tazo ta jera akan dining ta nufi dakin su husna taje ta taso su agurguje suka shirya suka fito amma sai da junada ta leka dakin lamin inda yake kwance yanata shakar baccinsa da sauri taja masa kofar ta fita cikin sauri suka shiga sashen mummy suka gaidata sannan suka wuce makaranta.





Ummi A'isha🏻
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha🏻: [3/24, 10:11 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..


5⃣1⃣

Na
UMMI A'ISHA

    Karfe 9 ya tashi yayi wanka yafito cikin bakaken suit wanda sukayi masa kyau sosai, kan dining yaje ya xauna yayi break yana gamawa ya shiga dakin junada yauma kamar kullum dakin a tsaftace yake sai kamshi ne yake tashi fitowa yayi ya nufi side din mummy ya gaisheta sannan yatafi office. Yau tun 1 suka fito daga paper da wuri suka dawo gida su hasna daki suka shige suna ramuwar bacci ita kuwa junada kitchen ta fada tafara kacaniyar hada abincin rana inji turawa sukace lunch, faten doya da danyen kifi tayi tana gamawa tashiga wanka yauma tana fitowa ta ganshi a tsaye kamar jiya sannu da zuwa tace dashi yawwa sannu ya amsa mata ganin kallon da yake mata yasa tayi saurin sunkuyar da kanta kizo kibani abinci amma bari nima naje nayi wanka kafin ki gama shiryawa ya juya yafita, agurguje ta shirya cikin wani bakin lace mai digon pink ajiki anyi masa zanen fulawa ajiki dinkin riga fitet da skirt, turaren urban woman shine turarenta ta feshe jikinta ta nufi falo tana fitowa shima yana fitowa yayi wanka ya canza shiga cikin wata riga purple colour anyi zanen heart kanana an rubuta cute style a tsakiya da wando brown, gayen nan akwai iya daukar wanka tafada acikin zuciyarta kujera yaja ya zauna ta zuba masa abincin ta koma falon ta zauna tana hango shi yana cin abincin shi kuwa mamaki yakeyi wai duk lokacin da yarinyar nan take kusa dashi sai ya tsinci kansa cikin farin ciki amma da zarar bata nan sai ya samu kansa cikin tashin hankali tab! Allah mai yadda yaso.





MACE GUDA DAYA TILO...

5⃣2⃣


Na
UMMI A'ISHA


    Ahankali ahankali yake cin abincin har ya gama, wayoyinsa ya tattara yataso daga dining area din cike da ladabi tace yaya lamin dama ina son yin magana dakai, kujerar dake kusa da ita yazo ya zauna yace ina sauraronki dama dan Allah idan nagama exam ina so kabarni naje bauchi kallonta yayi yace me akeyi? Babu abinda akeyi ta fada tana wasa da yan yatsun hannunta wani hamshakin murmushi yayi sannan yace to idan kin tafi ni kuma ki barni dawa? Kiyi hakuri zakije bauchi amma ba yanzu ba kinji? Kai ta daga tace to shikenan a falon tabarshi ta shiga dakinta, yana nan zaune har su hasna suka fito harara yafara aika musu da ita sannan yace wato baku ji abinda nace muku ba ko? Allah yabaku sa'a tashi yayi ya nufi side din mummy. Washe gari suka gama exam sun samu hutu harna 3 weeks dan haka yanzu sai zaman gida babu inda suke fita shima lamin hutun sukeyi dan haka kullum yana gida, gaba daya ya canza ya daina shan kunu da babbata rai yana bin duk wata hanya da zasu shaku da junada kuma yana kokarin kyautata mata a kowanne lokaci,yauma tana kitchen tana girka abincin dare yashigo su husna kadai yaga a falo suna aikin kallon wani American film mai suna prison break ko magana baiyi musu ba ya wuce kitchen din lokacin daya shiga tana tuka tuwon semo vita ahankali ya lallaba ya rufe mata ido tana jin hannunsa tasan shine domin komai nasa kamshi yake na turarensa, murmushi tayi tace yaya lamin murmushi shima yayi yadawo kusa da ita yace sannu da kokari yawwa sannu da zuwa tafada tana kwashe tuwon kawo na kwashe miki yafada yana kallon fuskarta a'a ai baka iya ba tafada waya gaya miki? Ki tambayi mummy kiji idan ban iya ba a'a ni basai na tambayi mummy ba su hasna zan tambaya to ai lokacin da nakeyi su husna basu da wayo a'a to duk yadda akayi baka iya ba na iya mana ko lokacin da nake Malaysia nine nake girki na ba girki kakeyi ba take away kake ci ai nasani a'afa kar kisa nayi fushi gobe kina tashi kiga nagama shirya breakfast hmmm da kuwa kaga nafi yarda da abinda ka fada uhm kinga zaki sa yau naki yin marking din papers din dalibai na tunda kince ban iya tuwo ba a'a wasa nake ka iya tuwo harda miya daidai lokacin tagama kwashe tuwon taje ta sauke miyar danyar kubewar data yi ta kalleshi to idan bakayi wa dalibanka marking ba yaya zakayi dasu? Kowa yasamu carry over yafada yana ficewa daga cikin kitchen din.
[3/24, 10:21 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..

Na
UMMI A'ISHA

5⃣3⃣


   Bayanshi tabi da kallo tana murmushi saida tagama shirya komai acikin flask sannan ta debo ta kawo kan dining ta jajjera ta karasa wajen su husna wanda suke zaune sun kurawa tv ido suna kallo, gefensu taje ta zauna itama ta fara kallon, lamin ne ya fito shima yazo gefenta ya zauna daga shi sai short nicker da farar riga body hug laptop dinsa ya ajiye akan Stoll din dake gabansa ya miko mata wata takarda ungo rinka fado min mark din ko wanne dalibi karba tayi tafara karanto masa kallonsa tayi yanzu fa muma da dalibanka ne tsaf zaka bamu carry over ko? Kwarai kuwa shi yafi komai sauki ma musamman ma wadannan yaran masu masifar kallon tsiya murmushi tayi ta kalleshi ya sunkuya ya dukufa yana daddana laptop din fuskarsa dauke da murmushi fado min mark din Khadija Aminu 25 a'a ban yarda dakeba sai dai 35 don yarinyar tanada kokari kusanma tafi duk matan ajin kokari ras taji gabanta yafadi to ko itama budurwarsa ce? Tafada acikin ranta kin san ku mata baku fiya karatu ba shiru tayi masa bata bashi amsa ba shi kuwa bai ma san Kalmar daya fada ya bata mata rai ba da haka suka gama fuskarta babu walwala shima saiya samu kansa cikin damuwa, kiran sallar magribar da suka jiyo ana kwallawa a masallacin gidan ne yasasu tashi gaba dayansu,nan yabar kayan aikin nasa yashiga dakin junada a bathroom dinta yayi alwala sannan yafito ya tafi masallaci, abinda yake Kara burge junada kenan domin sam lamin baya wasa da sallah, yana fitowa daga masallaci sashen daddy yawuce anan ya taradda mummy murmushi yayi yace mummy kema nan kika taho? Dariya tayi tace to ai babana kune kuka kwashe min abokan hirar tawa sai asannan daddy yayi magana yace to shi basai yana zuwa yana tayaki hirar ba zama yayi akusa da daddy yace to ai sai nazo indai mummy tace nazo din, ko cewa tayi nadawo gaba daya ma sai nadawo dariya sukayi gaba dayansu daddy yace ina matar taka take? Kwana 2 ban ganta ba amma ina ganin girkinta kullum murmushi mummy tayi tace ai gaskiya yayi dacen mata yarinyar nan karfi da yaji ta hanani yin girki kullum sai dai ta dafa ta kawo min ta dauke ni tamkar mahaifiyarta Allah yayi mata albarka shidai lamin shiru yayi amma har cikin ransa yaji dadyn yabon junada dasu daddy sukayi dama  yasan dole su mummy su sota domin ko acikin yayansu sunfi sonshi,son da suke yi masa nema ya shafi matarshi.





MACE GUDA DAYA TILO..

Na
UMMI A'ISHA

5⃣4⃣


    Anan ya zauna har saida aka kira sallar isha sannan suka tafi masallaci shida daddy, yana fitowa daga masallaci ya wuce side dinsu nan ya taradda su sun baje suna cin tuwo gaban junada ya je yasa hannu acikin kwanonta yafara cin tuwon sudai su husna mamakin yayan nasu sukeyi kwana biyu domin duk ya canza sai tattalin matarsa yake gamida tarairayarta murmushi yayi mata yace gaskiya miyar nan tayi dadi itama murmushin tayi tace ko? Eh mana ai tayi dadin da bazai misaltu ba gobe ma kiyi mana ita kin san ita kubewa tanada mutukar amfani ajikin dan adam likitoci sun tabbatar da haka dariya tayi tace to kai kuma yaushe kabar lecturing ka koma doctor? Ranar da kika bar daliba kika koma noman kubewa dariya tayi masa sosai sannan tace gaskiya ya kamata nasa maka waigi dan naga alama santi kake murmushi yayi ai tuwon naki ya kai matsayin da za ayi masa santin yanzu daddy ma nasan yana can yana santin wannan miyar kubewar hmmm kai dai tunda kayi shikenan yana koshi ya mike idan kin gama ki shigo min da laptop dina da sauran kayan cikin daki to ta amsa masa dakinsa ya wuce yaje ya kunna labarai a BBC yana kallo sai wurin 9 sannan tashiga dakin nasa da laptop din a hannunta ya baje akan gado yana kallo daga shi sai gajeren wando idonta ta sauke kasa batare data kalleshi ba tace ga kayan naka ajiye anan kishiga bathroom ki hada min ruwan wanka, wanka zanyi ajiyewa tayi ta shiga cikin bathroom din sai data dan wakeshi tafesa air freshener mai kamshi sannan ta hada masa ruwan wankan ta fito na zuba maka to ki jirani na fito sai mu karasa wannan aikin ko? Tom ta nemi wuri ta zauna agefen gadon bai dade sosai ba yafito ya sameta zaune inda ya barta.




MACE GUDA DAYA TILO...

Na
UMMI A'ISHA

5⃣5⃣


     Bakin gadon shima yaje ya zauna ya kamo hannunta ya rike cikin nasa junada ita dai shiru tayi tana ganin ikon Allah murmushi yayi ya dan kalleta yace junada kalleni kin kallonsa tayi magana ya sakeyi ki kalleni junada ni mijinki ne abokin rayuwarki, komai da kikaga yana da sanadi kuma akwai yadda yake zuwa yanzu ki tashi kishiga toilet ki dauro alwala kizo mu gabatar da sallar ma'aurata tunda kin korar mun yan mata kinga sai ke ki dauki dawainiya ta dam! Taji gabanta ya fadi me lamin yake nufi ta tambayi kanta dubansa tayi cike da mamaki ta fizge hannunta daya rike cikin nasa tace ma'aurata? A ina na zama matarka? Ta ina muka zama ma'aurata? Kamanta abubuwan daka fada a baya? Kai da bakinka kace ba ka daukeni a matsayin mata ba a yar aiki ka ajiyeni, dan haka ina son kabarni a matsayin yar aikin kamar yadda zuciyar ka ta kudurta tun farko kar ka canza min matsayi daga yar aiki kuma yanzu duk abinda zaka fada bazai yi tasiri agareni ba saboda nasan ba gaskiya bane kafada ne kawai saboda ka cimma wata manufa taka tana kaiwa nan ta tashi fuuuuu! Tafice ta bar dakin shi kuwa lamin yakasa koda motsi dama yasan dole sai haka ta faru tsakaninsu duba da yadda haduwarsu ta kasance tun farko,wani guntun tsaki yaja to ita wannan yarinyar me takeso tace? Nufinta ba sonta yake yiba kawai sha'awarta yake? Mts dama haka ita zatayi tunani gani zatayi kamar sha'awarta nake dan haka da zarar na cika burina zan daina kulata alhalin kuma ba haka bane alokacinne ma zanfi kulawa da ita zanfi nuna mata tsantsar soyayyar da nake yimata, zan nuna mata kauna wacce bata samu ba afarkon aurenmu yafada acikin zuciyarsa.




UmmiA'ishah
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha🏻: [3/24, 10:28 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...

Na
UMMI A'ISHA

5⃣6⃣



    Ji yayi zuciyarsa ta fara tafarfasa kamar ana hada mata wuta lallai ma yarinyar nan to itada ahaka zasuyita zama? Wannan ma ai shirme ne kuma ba mai yuyuwa bane tunda shi yanada bukata ita kuma ta tsare ta kasa ta hanashi kula ko wacce mace sai ita kadai MACE GUDA DAYA TILO tashi yayi yafara zagaye dakin nasa yayinda bacci kuma yayiwa idanuwansa kaura. Ita kuwa junada tana zuwa daki tafara godewa Allah domin ta san yafara amsar add'arta tunda gashi har lamin yafara nuna son kasancewa da ita ina sonka lamin tafada acikin zuciyarta wani murmushi tayi sannan tace zan mallaka maka kaina amma ba yanzu ba sai lokacin dana tabbatar da ka gama kamuwa da ciwon sona kagama yarda da cewa nikadai ce MACE GUDA DAYA TILO acikin zuciyarka da wannan tunanin ta tashi tayi shirin bacci tayi kwanciyarta ba tare da damuwar komai ba shi kuwa lamin yana can yana ta faman sintiri atsakar dakinsa kamar wani soja awannan daren dai sai bacci barawo shine yayi nasarar sace shi daf da asuba. Da misalin 8 ta fito ta shiga kitchen kamar kullum ta shirya lafiyayyen breakfast ta kawo kan dining ta jera tana gamawa ta shiga dakinta tayi wanka ta fito tashirya cikin wata body hug baka mai dan siririn hannu da wata bakar skirt ta matseta sosai ta gyara gashin kanta ya sauko har gadon bayanta ta feshe jikinta da turaren urban woman tasa wata bakar hula mai gashi ta nufi falo tana fitowa ta hangoshi akan dining a zaune ya zubawa abincin ido fuskar nan tasa tayi mutukar kyau yana sanye da orange colour din t. Shirt mai gajeren hannu da blue din jeans hannunsa daure da agogo golden colour gaba daya falon ya gauraye da kamshin turarensa manyan idanuwansa ya dago yafara kallonta fuskarta tasha make-up kayan da tasa sunyi bala'in matseta kuma sunyi mata kyau abunka da farar mace nan da nan yaji ya rude ya nemi nutsuwarsa ya rasa tuni hankalinsa ya soma neman tashi kallo kawai yake binta dashi dakyar ya iya furta pls zo ki hada min tea din, ayangance kamar mai tausayin kasa ta tako zuwa kan dining din ta dan russuna yaya ina kwana acan kasan makoshinsa yace lfy beauty





MACE GUDA DAYA TILO

Na
UMMI A'ISHA

5⃣7⃣



  Tea din ta fara hada masa sai wani shan kamshi take shi kuwa lamin yasaki baki sai binta da kallo yake sai kace wani soko tana gama hadawa ta kawo gabansa ta dire masa ta juya zata tafi hannunta taji ya ruko cikin nashi jawota yayi ya zaunar da ita akan cinyarshi yafara murza yan yatsunta cikin nashi ahankali kamar kullum yarr! Taji nan da nan ta tuno da yan matansa acikin zuciyarta tace yanzu suma haka yake yi musu ko? Wata zuciyar tace mata fin haka ma yayi kamar wadda aka tsikara tayi zumbur ta mike ta fincike hannunta kallon mamaki yabita dashi wai junada meye yake damunki ne?. Bata kalleshi ba ta wuce daga dining area din falo taje ta zauna ta kunna kallo tana nan zaune har ya gama yin break din ya taso ya dawo falon ya zauna yana zama ta tashi ta shige dakinta tayi zamanta abin duniya ya taru yayi masa yawa shima mikewar yayi ya nufi side din daddy anan ya iske mummy zama yayi suka fara hira babu laifi ya dan jin saukin damuwar da yake ciki. Anan ya kusan wuni sai da yamma yakoma side dinsu yana shiga ya tarar dasu husna suna zaune a falo ita kuma junada yajiyo motsinta a kitchen dakinsa yashiga yayi wanka yafito cikin ash colour din riga da bakin wando kansa tsaye ya shiga kitchen hangota yayi tana kaiwa da kawowa acikin kitchen din daga ita sai wata yar mitsitsiyar shimi ja da dogon wando masha Allah yafada acikin zuciyarsa ahankali ya karasa daf da ita ya tsaya tana jinsa taki jiyowa ta shareshi gyaran murya yayi sannan yace sannu da aiki beauty sunan taji har cikin ranta ita dai tana son muryarsa shiyasa take son taji yana mata magana koda kuwa fada ne jikinta ya matso ya ziro hannuwansa ta bayanta yace kawo in yanka miki salak din a'a kabarshi nagode ta fada cikin wata iriyar murya domin gaba daya ya gama rikitata lokaci daya saboda duk yabi ya dabaibaye ta ya hanata sakat kafa sakar min nauyinka nauyi kuma? Ni wanne nauyi gareni? Au kai bakasan kanada nauyi ba? Ni banida wani nauyi babu mamaki ma idan akace kin fini nauyi uhm anya kuwa zan fika nauyi? To ko za agwada ne? A'a ba sai mun gwada ba tafada tana girgiza kai hmmm yayi murmushi ke kin fiya raki dayawa.






MACE GUDA DAYA TILO


Na
UMMI A'ISHA

5⃣8⃣



      Kin fiya raki da yawa tun yanzu kin fara cewa inada nauyi anya kuwa zaki iya naukar nauyina? A'a bazan iyaba tayi masa gatse acikin zuciyarta kuwa cewa take wadan nan tsiga tsiga matan ma suka iya daukar ka balle ni? Hannuwan shi ya janye daga jikinta yace natafi masallaci ya juya yafita ita kuwa wata ajiyar zuciya ta sauke. Tunda ya fita salla bai dawo ba sai bayan sallar isha yau falon babu kowa mamaki ne ya kamashi to ina suka shiga? Dakinta ya nufa ya murda yajishi a kulle yadawo nasu hasna shi kuma a bude yake amma basa ciki duk yadda akayi suna side din mummy yafada acikin zuciyarsa can din ya nufa yasamesu sunata hira da mummy amma babu junada ganin haka yasa ko zama baiyi ba yafice sai yanzu ya gano wato daki ta shiga ta rufe kenan dan kar ya bukaci wani abu agurinta tsaki yaja yace ni kuwa zan baki mamaki junada in dai nacika lamin baxan sake nuna miki bukatata akanki ba kan dining yaje ya samu ta shirya komai faten dankali da hanta sai salad data hada masa domin tasan shi yana son salad zama yayi yaci ya koshi sannan ya shiga dakinsa wanka yayi abin mamaki hatta ruwan wankan ta hada masa murmushin mugunta yayi yace yarinya ina tausaya miki cike da damuwa yayi baccin wannan rana.
[3/24, 10:32 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO


Na
UMMI A'ISHA


5⃣9⃣


   Washe gari da safe ya tashi yayi wanka ya shirya ya fito yauma kamar jiya taci ado tamkar baturiya cikin wata doguwar Riga dark brown shara shara mai hannun shimi ta tufke gashin kanta wanda yake lodi guda ta kame akan kujera har cikin zuciyarsa yaji sonta ya ratsashi babu karya ta tafi da imaninsa ahankali ya jefeta da wani irin kallo wanda shi kadai yasan ma'anarsa falon yashiga ya zauna ina kwana yaya lamin tace dashi cike da murmushin da yake karawa fuskarsa kyau yace lfy lau kawo min tea kawai yau babu abinda nake sha'awar ci kallonsa tayi nayi maka farfesu fa a'a ki ajiye min anjima zanci yanzu fita zanyi tashi tayi taje ta hado masa ruwan zafin ta kawo masa kadan yasha sama sama yatashi ya kwashi wayoyinsa da key din motarsa ya fita lekensa ta farayi ta window ga mamakinta sai taga ko side din mummy bai kalla ba ya shiga motarsa yafita daga gidan to ina ya tafi?? Ta tambayi kanta karfa yakoma yawon bin matan da yasaba gabanta taji ya fadi ya Allah ka kare wannan bawa naka,ka kawar da idonsa daga kan matan banza Allah ka dawo min dashi lfy wani irin kishine taji yana taso mata agaskiya tana kishin lamin sosai domin tasan mijinta ya hadu ta kowanne bangare tamkar tauraro yake acikin taurari kana ganinsa kaga cikakken bafulatani yanayin da taganshi lokacin da yana bacci ne ya fado mata hmmm dole yan mata suna rububinsa domin kyansa ya isa.





MACE GUDA DAYA TILO


Na
UMMI A'ISHA

6⃣0⃣


    Haka ta zauna sukuku ko tea dinma ita takasa sha domin duk a tunaninta yawon neman mata ya tafi musamman ma yau da taga ko sha'awar taba hannunta bai yi ba, nan ta nemi wuri ta zauna tanata sakar zuci ta na nan zaune har su husna suka tashi daga barci suka fito sukazo suka isketa a falon suka fara kokarin yin break ita kuwa hirar da suke yimata sama sama take ji domin bata cikin nutsuwa hankalinta naga abin sonta lamin ni dai ummi A'isha yar kallo ce, tana nan zaune motsi kadan ta kalli agogo har 12 tayi ganin bai shigo ba yasa ta tashi tashiga kitchen tabar su husna suna kallon wani Indian film atashar zee aflam mai suna muhabbatien,aiki take amma sam babu walwala da sukuni a tattare da ita ahaka ta gama hada hadaddiyar fried rice dinta wadda tasha hanta da carrots ga cabbage yaji sai kamshi take tayi wara wara da ita gwanin sha'awa dan ko ni ummi A'isha saida naji yawuna ya tsinke, tana gama hada fried rice din ta soya naman zabbi tayi masa kykkyawar suya ta tattara komai ta zuzzuba a cikin food flask ta kawo kan dining tafara jajjerawa su husna dake falo suka fara tandar baki hasna ta taso tace Anty me kika girka mana ne? Hararta tayi tace mijina nayiwa girki ku jira idan yaci ya rage sai ku karashe sauran dariya hasna tayi ta koma falon tana fadin to bari mu zauna zaman jiransa husna dake zaune tana sauraronsu tace ai kema hasna nasha fada miki mu tattara mu koma sashen mummy amma kika ki gashi nan ai muna ganin wariyar launin fata awajensu dariya sukayi hasna tace ai Anty tana shagwaba yaya tafi sonsa ma akanmu murmushi junada tayi tace ai dole dama nafi sonsa tunda matsayinsa yafi naku dariya suka yi ita kuwa daki ta shiga tayi wanka ta shirya cikin atamfa super kalar ruwan kwai ta yiwa fuskarta kwalliya sosai ta kafa dauri kamar goggoro ta feshe jikinta da turarruka masu dadi tasa sarka fashion golden colour ta fito falo lokacin karfe 4 har tayi wuri ta nema ta zauna tana jiran gawon shanu, ni dai ummi A'isha ina daga gefe ni ma ina sauraron zuwan oga lamin.



Ummi A'isha
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha🏻: [3/24, 10:37 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO..


Na
UMMI A'ISHA

6⃣1⃣

   Tana nan zaune har 5 tayi tuni su hasna sun tafi sashen mummy ita kuwa junada ta cika tayi dam kiris ya rage ta fashe, sai 5:30 ya shigo gidan tana zaune a falo ya bude ya shigo hankalinsa kwance fuskarsa wasai ganin haka yasa junada taji ta dada tsarguwa da shi kallo bishi da shi babu alamun damuwa ko kadan a fuskarsa sallamarsa ce ta katse ta, ta amsa fuska babu annuri can nesa da ita yaje ya zauna tuni ta gasgata zarginta fuskarsa dauke da murmushin keta yace ina su hasna? Kamar ba zatayi magana ba tace suna side din mummy kallonta yayi kwalliyar tata tayi masifar yi masa kyau gamida jan hankalinsa amma bai nuna mata hakan ba shi kansa ya san junada first class ce asahun kyawawan mata kamar yadda yake first class a sahun kyawawan maza dagowa yayi yaga ta kafe shi da ido ko kiftawa batayi wai lfy kuwa? Ya tambayeta lafiyar ce ta kawo haka tafada tana mai ci gaba da kallonsa har sai da ta tabbatar da zarginta domin lips dinsa taga alamun jan baki ajiki a fusace ta mike yabita da kallo ya ce gobe ki shirya za muje bauchi banza tayi masa ta shige dakinta shi kuwa tashi yayi ya hau kan dining yafara kwasar girkin da ta tanadar masa. Ita kuwa junada tamkar zata mutu dan kunar rai, hankalinta duk yabi ya gama tashi ita kam ya zata yiwa lamin ya daina neman matan nan? Wata zuciyar tace duk laifinki ne meyasa alokacin da yazo miki da bukatarsa baki bashi hadin kai ba? Ai da kin amince dashi kin bashi kulawa to da babu macen da zata sha gabanki awurinsa saboda duk matan da zai yi mu'amula dasu awaje babu wacce zata nuna miki kyawun halitta, hakika nayi babban kuskure da ban amincewa lamin ba lokacin da ya bukaceni ta fadi hakan acikin zuciyarta mikewa tayi tace ya zama dole na tsaya na gyara kuskure na tunda wuri.






MACE GUDA DAYA TILO


Na
UMMI A'ISHA

6⃣2⃣


   Falon ta koma akan dining ta ganoshi yana cin abinci yana waya amma bata hango fuskarsa saboda ya bata baya hakane ya bata damar bude idonta sosai tafara kare masa kallo komai nashi mai kyaune ya hadu ta kowanne fanni tamkar shi yayi kansa tana nan zaune har ya gama cin abincin ya tashi ya shiga dakinsa Jim kadan sai gashi ya fito daga shi sai gajeren wando kallo 1 tayi masa ta sunkuyar da kanta kizo ki zuba min ruwan wanka tun kafin ya karasa ta mike a zuciyarta tana cewa ai dole kayi wanka dan kai kadai kasan me ka aikata bathroom din ta shiga ta hada masa ruwan sannan ta fito ba tareda ta kalleshi ba tace na zuba maka yawwa thank you taji yafada cikin tausasshiyar muryarsa fitowa tayi daga cikin dakin ta nufi nata ta fara shirya kayanta acikin babbar trolley sai dai acan kasan zuciyarta kuma tunanin tafiyar nan da zatayi take anya kuwa idan ta tafi bazai samu damar holewarsa yanda ya gadama ba? Mts tsaki taja tace nasan dai duk tsiyarsa bazai kawo mata gidan nan ba tunda su mummy suna nan sai dai yaje hotel da wadannan tunane tunanen tagama hada duk abinda tasan zata bukata. Washe gari da wurwuri ta tashi ta hada breakfast ta gyara gidan ta shiga tayi wanka ta fito taci kwalliya cikin wani leshi orange tasha kwalliya tayi kyau sosai ta fito kamshi ne kawai ke tashi daga jikinta tana fitowa ta hangoshi shima har ya shirya yafito yana zaune yana cin soyayyen dankalin da ta soya masa yayi kyau sosai cikin wani lallausan bakin yadi mai tsadar gaske yasa hula itama baka agogon hannunsa na azurfa ne sai kyalli da walwali yake kamar kullum kamshin turaren Phoenix ne ke tashi daga jikinsa kallonsa tayi acikin zuciyarta tace Kai dai ko wanne kaya kasa sai yayi maka kyau gaka da son kamshi kamar me, afili kuwa dan russunawa tayi tace ina kwana? Kin tashi lfy? Lfy lau kujera itama taja ta zauna ta hada tea tasha agurguje ta shiga side din mummy tayi mata sallama tafito lokacin suma su hasna sun tashi kayanta ta dauko tafito sukayi sallama ta nufi inda yake tsaye yana jiranta.





MACE GUDA DAYA TILO...


Na
UMMI A'ISHA


6⃣3⃣



   Wata sabuwar mota katuwa baka taga ya dauko yazo gabanta ya tsaya su husna ne suka bude mata motar ta shiga yaja suka fita daga gidan tana ta dagawa su hasna hannu, kira'ar sudais ya kunna cikin suratul Yusuf ya kure A. C din cikin motar lumshe idanuwanta tayi tana sauraron karatun tana bi acikin zuciyarta kamar a mafarki taji shima lamin yana bi ahankali mamaki ne ya cikata ashe dai shima mahaddacine sai tsabar shagala Allah ya kyauta tafada cikin ranta gudu yake sosai tun tana tsorata har ta daina dan ta fahimci yanayin tukinsa ne haka kafin kace me bacci yayi awon gaba da ita kallon fuskarta yayi yaga tana bacci wani kayataccen murmushi ya saki junada kenan junada zanyi mutukar baki mamaki yafada acikin zuciyarsa. Karfe 12 suka isa garin bauchi sai da suka shiga cikin gidan sannan ya tasheta cikeda mamaki tace har munzo? Eh ga zahiri kuwa kin gani fitowa sukayi daga cikin motar suka tasamma cikin gidan suna shiga falo ta hango ummanta ai da gudu taje ta fada kanta ta rungumeta shi dai lamin abinma dariya ya bashi sai yau ya yarda junada muguwar yarinya ce, dakyar ta daga umman tata suka gaisa da lamin nan da nan aka cikasu da kayan ciye ciye waya ummanta tayiwa abbansu tafada masa zuwansu, office din ya baro yazo suka gaisa da lamin, sai da lamin yayi sallar azahar sannan yayi musu sallama ya fito biyo shi junada tayi tace sai yaushe zan dawo sai kin ganni nadawo 2 weeks zakiyi, tace to Allah ya kaika lfy amma dan Allah ka rage gudu, har cikin ransa yaji dadin maganarta murmushi yayi mata yace insha Allah yashiga motar ya tafi.
[3/24, 10:40 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO


Na
UMMI A'ISHA

6⃣4⃣



   Tsayawa tayi har sai da taga fitarsa sannan ta shiga gida ta na mai addu'ar Allah ya kaishi gida lfy. Wuni sukayi suna hira ita da ummanta har Abbanta ya dawo daga office shima suka ci gaba dashi,sai bayan sallar isha sannan ta shiga dakinta wanda har yanzu yana nan a kintse babu abinda aka canja sai kace tana gidan. Wanka taje tayi tazo ta shirya cikin rigar baccinta ta haye gado, lamin ne ya fado mata Allah sarki ko yanzu me yake yi? Ko har yayi bacci? Ko kuma kallo yake? Wayarta ta jawo ta fara kiran husna ringing 3 ta daga tana fadin Allah yabar Antynmu dariya junada tayi sannan tace yagida? Gida lfy ya kika tarar da mutan gida? Duk lfy ina hasna? Hasna tana falo ni kuma na shigo daki, ok ina yayanku? Gashi can na hangoshi ta window yana fitowa daga side din daddy, wanne irin kaya ne ajikinsa? Body hug baka da boxer baki  ajiyar zuciya junada tayi sannan tace kije kice ina gaidashi da fatan ya isa gida lfy to Anty angama, mikewa husna tayi ta fita zuwa inda ta hangoshi yana zaune acikin wata yar karamar runfa wadda aka tanada domin hutawa da wasu yan kujeru aciki sai kace a turai sannu yaya yawwa sannu dama Anty junada ce tace ince tana gaisheka da fatan ka dawo gida lfy? Murmushi yayi sannan yace kice ina amsawa sannan kuma na dawo lfy da fatan zatayi bacci lfy to tafada ta juya tana cikin tafiya junada ta kirata ta daga tafada mata sakon murmushi junada tayi tace nagode kigaida su mummy ta kashe wayar ko ba komai hankalinta ya dan kwanta tunda taji halin da yake ciki amma kuma sai ta tsinci kanta da son ganinsa a wannan lokaci fatanta daya Allah yasa ba da wata manufa ya dawo da ita gida ba.





MACE GUDA DAYA TILO...


Na
UMMI A'ISHA

6⃣5⃣


  Juyi kawai takeyi amma bacci ya kauracewa idonta tunanin mijinta ne kawai ke addabarta da kyar ta samu bacci ya dauketa. Da safe da misalin karfe 10 ta kira husna ta tambayeta ina lamin? Murmushi husna tayi tace yana side dinku yana bacci inajin bai tashi ba cikeda damuwa junada tace dan Allah kije ki gano min shi tashi husna tayi ta fita tana ta faman mita ni kam ai na shiga uku kuma da haka takarasa sashen nasu ta lalleka dakunansa amma baya ciki dakin junada ta buda abin mamaki hangoshi tayi baje akan gadon junadan yanata sharar bacci rufe kofar tayi tajuya ta fita tafara kiran junada tana dagawa ta fara bata labarin lamin wani dadi junada taji ashe dai yafara damuwa da ita yanzu. Abin har ya zamewa husna jiki domin kullum junada sai ta kirata ta tambayi lamin hatta kalar kayan da yasa sai an fada mata kuma sai taji shin ya fita ko bai fita ba da haka har tayi sati 1 da zuwa aranar kuma ta tafi azare gidan kanwar mamanta mami da niyyar yi mata kwana 2 nan da nan mami ta fara yi mata dure dure da tsume tsume ita junada abin ma har isarta yayi aranta kuwa fadi take ai wanda aka yimin a sudan ma har yanzu yana nan ajikina kwananta 2 ta dawo gida cikeda kayan gyare gyaren da mami ta hado mata. Ranar da ta dawo aranar yayunta suka dawo daga makaranta Khalid da Amir harda cousin dinsu Mahmud wanda shima duk tare suke karatun a waje kar kaso kaga murna wurin junada  haka tashiga cikinsu suka baje ana ta hirar yaushe gamo kasancewar ko lokacin bikinta basu samu sun dawo gida ba.



Ummi A'isha
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha: [3/24, 10:45 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO


Na
UMMI A'ISHA


6⃣6⃣


    Yanzu tafi jin dadin zaman gidan saboda dawowar su Khalid kullum wuni suke suna hira amma fa tunanin lamin yana nan makale acikin zuciyarta, waya kuwa kullum sai ta kira husna taji labarin lamin amma hankalin ta yadan kwanta domin kullum yana gida baya fita koda wanne lokaci idan ta tambayi husna ya fita sai tace a'a yana wurin daddy ko kuma yana side din su. Ahaka har hutun nata ya kare husna ce takirata take ce mata Anty yaya yace ki shirya ranar Saturday zai zo ku tafi domin ranar Monday zamu koma sch murmushi tayi to husna kice masa zan shirya, nan da nan tafara harhada kayanta wuri guda. Hakan kuwa akayi ranar Saturday sai gashi wurin karfe 12:30 lokacin da ya shigo falon yayyun junada suna zaune hannu ya basu suka gaggaisa har umma tafito itama ya gaida ta dakin junadan ta leka ta ganta tana shiryawa tace to kifito yazo idan kukayi sallah kuka ci abinci sai ku tafi to umma ina zuwa inji junada tana gama shiryawa ta fito ta sameshi zaune a falo yasha waganbari milk colour da hula milk colour ya gyara sajensa fuskarsa tayi kyau hannunsa ya daura agogon fata milk colour gabansa ta karasa tana fadin yaya lamin sannu da zuwa amsawa yayi yana kallonta tayi kyau sosai cikin bakin material din data sa kallon da ya lura Mahmud yana yima ta ne yasashi fadin kije ki dauko mayafinki to tafada ta tashi tafita. Saida suka ci abinci sukayi sallah sannan suka fito da niyyar tafiya Khalid ne yayi dariya yace autar umma kin manta wayarki awurin mahmud kallon khalid din tayi tace wlh naso na manta kuwa hangowa mahmud din tayi shida amir suna tahowa tace yawwa gashi nan ma shida yaya amir shidai lamin yana tsaye baice komai ba har suka karaso wurinsu khalid ne yace mahmud ka bawa auta wayarta zasu tafi dariya Mahmud din yayi yace ai ba ita ta baniba warta nayi dan haka nima ba bata zanyi ba tunda lokacin danace ta aramin guduwa tayi.





MACE GUDA DAYA TILO...


Na
UMMI A'ISHA

6⃣7⃣


Guduwa tayi wurin mummy dan haka nima bazan bata ba kallon khalid tayi tace yaya Khalid dan Allah karbo min wayata, karbo mata yayi ya mika mata shi kuma mahmud yaci gaba da fadin ai wlh yarinya ba don kin gudu ba da sai na murde hannunki na kwace, kallonsa lamin yayi cikin kunar rai tuni zuciyarsa tafara tafasa motar ya bude yashiga itama shiga tayi ta zauna hannu suka fara daga musu amma lamin ko kallonsu bai yi ba saboda ransa ya gama baci ai nan take ya murtuke fuska idanuwansa suka rine sukayi ja acikin ransa fadi yake warta? Ya warci waya a hannunta? Yabita ta gudu wurin umma? Lallai ashe ma wasa sukayi tunda harda su guje guje yayi kyau yafada afili ita dai junada tuni ta gama tsurewa saboda bata san meya bata masa rai ba ko kadan ba ta zata maganganun mahmud sunada nasaba da bacin ransa ba shiyasa taja bakinta tayi gum ahaka har suka isa garin yola. Yamma lis suka shiga gidan amma har yanzu lamin akule yake da ita yana parking ko kallonta baiyi ba yafice ya shige side dinsu ita dai batasan me tayi masa ba, fitowa itama tayi ta kwashi kayanta ta shigar cikin falonta sannan tashiga wanka tayi salla ta nufi side din mummy tana shiga su husna suka taso suka rungumeta cike da zolaya husna tace yau nima zan huta da tambaye tambayen da ake min hasna tayi caraf ta cafe ai dan an san zaki iyane shiyasa aka saki ni da aka san bazan iyaba ai kinga ba asaka ni dariya suka saka mummy tace kun karata dai masu surutun tsiya karasawa junada tayi ta durkusa ta gaidata sannan ta tashi takoma side dinta yan rakiyarta suna biye da ita abaya.




MACE GUDA DAYA TILO...


Na
UMMI A'ISHA

6⃣8⃣


    Suna shiga ta fada kitchen ta dafa musu indomie da kifi ka kawo musu shi kuma lamin ta dora masa tasa akan dining, shiru shiru har dare yayi bai fito ba yana can acikin dakinsa ita kuma tsoron yi masa magana take, har suka gama hirarsu suka shiga daki bai fito ba, abin yayi mutukar damun junada domin bata son bacin ransa ita ba abun taje ta tambayeshi ba wata zuciyar tace mata ki bari sai ya huce tukunna sai ki tambayeshi inyaso alokacin sai ki bashi hakuri gaba kuma sai ki kiyaye da wannan shawarar tayi amanna. Washe gari ta tashi ta gyaggyara gidanta tayi komai amma girkin data ajiyewa lamin yana nan yadda yake bai ko buda ba ranta taji ya sosu to shi wannan me nayi masa ne? Ta tambayi kanta amma ganin bata da amsa yasa ta ci gaba da abinda take. Wasa wasa har tayi sati daya da dawowa lamin baici abincinta ba asalima ita tun daga ranar da suka dawo daga bauchi bata kara saka shi a idanunta ba kuma yana gidan, da haka suka koma makaranta kullum tana busy bata da lokacin kanta gashi tunanin halin da lamin yake ya gallabi ruhinta ahaka har sati 3 da dawowarta amma lamin ya daina cin abincinta ya daina kiranta ta hada masa ruwan wanka tama daina ganinsa kwata kwata dan haka sai ta tattara zamanta ta mayar side din mummy ita dasu hasna bacci ne kawai yake dawo dasu side din junada. Yau lecture tayi mata zafi ga test din unexpected da wani malami yayi musu ga lecture note da aka bayar akace kowa ya siya ga ta gaji dan haka sai kawai ta kira wani dan department din su wanda ta fahimci yanada hankali ta bashi sakon.
[3/24, 10:49 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...


Na
UMMI A'ISHA


6⃣9⃣


   Tabashi sakon tace dan Allah ya siya mata lecture note din ya kawo mata gida cikin girmamawa yace hajiya inane gidan naki, kasan gidan SSG? Eh tsohon gidansa nasani amma ban san sabon gidan da ya koma ba, bakasan new government house ba? Cikin sauri yace nasani hajiya, to kana zuwa government house daga gefen dama ba gefen hagu ba, gefen hagu gidan deputy governor ne nagefen dama shine namu, wani dan kati ta ciro ta mika masa ( visitors card) tace ungo wannan sai ka nunawa securities din gidan zasu barka ka shiga dan Allah ka kawo min ayau dan karatu nake son zanyi to hajiya zanzo insha Allahu ya juya yatafi yana ta faman murna domin ko ba komai yau zaije gidan SSG wanda ba kowane yake shiga ba sai mai kwalli a ido irinsu hawwa jabo da Adda Benaxir, ita kuwa junada juyawa tayi ta nufi motarta domin yunwa takeji sosai ga tagaji su husna kuwa tuni sun dade agida dan tun 12'suka gama lectures dinsu ganin bata gama ba yasa sukayi waya gida aka turo musu driver ya daukesu. Tana zuwa gida side din mummy ta wuce anan taci abinci tayi salla sannan ta wuce sashen ta,takwanta tayi bacci sai wurin 4 ta tashi tayi wanka taci kwalliya tayi sallar la'asar ta fito ta tafi wurinsu hasna tana fitowa ta hango wani daga cikin ma'aikatan gidan da kayan sojoji yana dosota yana zuwa ya dan rissina yace hajiya kina da visitor yana ina? Gashi can awurin second Gate,to ina zuwa ciki ta koma jim kadan ta fito ta nufi wurin,wannan dan department din nasu ta gani cikin sakin fuska tace sannu yawwa sannu hajiya gashi nayi miki guda biyar bayan kin taho aka bada sauran murmushi tayi tace amma nagode ta karba ta mika masa kudi yan dari dari nidai ummi Aisha ban san ko nawa bane yawan kudin, cikin girmamawa yace nagode nagode hajiya ah nice da godiya meye sunanka hajiya sunana lamin wani kayataccen murmushi tayi sunan maigida nane to hajiya nagode Allah yasaka da alkhairi sai anjima ya juya yatafi itama juyowar tayi da nufin tafiya side din mummy kawai sai hango lamin tayi yana tsaye yafito daga side din daddy yana sanye cikin wata body hug coffee colour an zana hannu ajiki an rubuta show time da wando jeans blue yayi mutukar kyau yana jingine ajikin motar daddy ya harde hannuwansa akan kirjinsa ashe duk wannan abun da yafaru akan idonsa ne.




MACE GUDA DAYA TILO...


Na
UMMI A'ISHA

7⃣0⃣


    Nufuto yayi fuskarsa a daure kamar bai taba dariya ba yaja hannun ta bai tsaya ako ina ba sai falonsu ya mayar da kofa ya kulle ya zare key din, ya kalleta yana ta faman huci waye wancan? Cikin tsawa yayi tambayar wadda tayi mutukar gigita junada badake nake magana ba? Nace waye wancan wanda yazo wurinki? Cikin dakewa tace dan ajinmu ne ya kawo min lecture notes, wato ke bakida hankali ko? Kula maza kikeyi baki san hakkin dake kanki ba ko? Bude idonta tayi cikin mamaki tafara kallonsa maza? Tafada acikin zuciyarta to ita wanne namiji ta kula awaje? Yaci gaba da yayyafin masifa ke na lura bakida hankali kamar yadda sauran mazan dake kulaki na fuskanci dakikai ne marassa ilmi, da aurenki zaki rinka biya wasu shashashu wai har kuna wasa saboda tsabar jahilci, cikin tashin hankali ta kalleshi tace wa na kula har mukayi wasa? Au tambayata ma kike? To wannan dakikin dan uwan naki mahmud da yake shi jahiline mai kwakwalwar kifi shine zai rinka kokawa dake alhalin da aurenki to wlh wannan yazama na karshe duk ranar da yasake kulaki sai na daure dan iska, sai yanzu junada ta gano ma'anar fushin da ya ketayi da ita to amma wannan ai fadan rashin gaskiya ne, muryarsa ce ta dawo da ita gareshi inma banda tsabar rashin tunani tayaya mutum zai tsaya yayi wasa da matar da ba tasa ba sai irinsu tsinannu gogaggun yan bariki nan da nan junada ranta yafara baci da zagin da yake yiwa dan uwanta ai wannan cin fuska ne kuma ayanda ta fuskanta zuwan wannan dan ajin nasu bai bata masa rai sosai ba kamar yadda maganar Mahmud ta bata masa rai, kallonsa tafara yi cike da takaici tace dan Allah dakata min kar ka kara zagar min dan uwa saboda kai xan iya canzaka amma shi bazan taba iya canzashi ba domin ahalinmu ne, kanata wani ikirarin ina kula maza ba gara ni ba kaifa? Tsawa ya daka mata wadda saida taji yan hanjin cikinta sun juya oh! Kin fara son maza ko? Nace kin fara son maza? Lallai ba laifin ki bane laifinane cikin bakin ciki tace eh nafara son mazan kai mata nawa ka kawo cikin gidan nan kayi fasikanci dasu? Ai ko falon nan da ace yanada baki ya isa bada shaida, ni kuwa duk kule kulen mazana ban taba kawowa gardi cikin gidan nan ba kallonta yafara yi sama da kasa haka kikace? Nace haka kikace? To yau za ayita ta kare akan wanccan shashan dan uwan naki kike gayamin bakar magana? Tabbas kin fara son maza dan haka yazame min dole ayanzu na dauki mataki.





Ummi A'isha
[3/24, 12:34 PM] Ummi A'isha🏻: [3/24, 11:00 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...


Na
UMMI A'ISHA


7⃣1⃣


   Yana fadin haka ya danko gashin kanta ya nufi cikin dakinta da ita suna shiga ya cillata kan gado ya rufe kofar ya zare key din ya jiyo yana ta huci ita kuwa junada duk da haka bakinta bai mutu ba fadi take wlh sai dai idan kasheni zakayi ka kasheni amma babu wanda ya isa ya rabani da dan uwana domin jinina ne murmushin takaici yayi yace ai kuwa yanzu zakiga jinin naki yarinya belt din jikinsa taga ya cire da sauri ta runtse idonta don duk zatonta dukanta zaiyi tana nan sankame taji shi ya zo kusa da ita ya jefa gado cikin sauri ta bude idonta ganinshi tayi dagashi sai gajeren wando ai tuni suka fara kokawa ganin bata da nasara yasa tafara kurma ihu amma sai dai kash! Babu wanda zai jiyota, hakuri tafara bashi dan Allah yaya lamin kayi hakuri wlh bazan kara magana da kowanne namiji ba murmushin mugunta yayi yace wlh yau idan kinga na kyaleki to numfashina ne ya yanke amma indai ina numfashi to sai na rabaki da abinda kike tunkaho dashi daga yau zaki daina kula wani da namiji a doron kasa, hannuwanta yahada duka ta baya ya rike kafin kace kwabo muryar ta har ta disashe tun tana iya ihu har ta dawo bata iyawa banda hawaye babu abinda ke zuba a idonta, shi kuwa lamin baima san a duniyar da yakeba ba saboda gaba daya junada ta gama rikitashi duk da dama yana yakinin zai sameta haka to amma sai yaga ya sameta fiye da tunaninsa. Sai bayan sallar isha'i sannan ya iya kyaleta lokacin ko motsi bata iyawa shi kansa saida ya tsorata saboda yanayin daya ganta gaba daya ta jigata marabar ta da matacce numfashi, sai alokacin yaji tausayinta ya darsu azuciyarsa shi kansa yasan baiyi mata ta dadin rai ba saboda lokacin ransa yagama baci afusace yake alhalin kuma bai kamata yabi da ita ta haka ba sam bai tausaya mata ba yanda yasaba bida yan matansa haka yabida ita alhalin kuma yasan akwai banbanci su da ita, ahankali ya rungumeta yafara hawaye acikin zuciyar sa yace Allah nagode maka da kabani kamilalliyar mace hakika nasan wannan rahama ce babba kayi min batare da ka duba halayyata ba, duk yadda na kasance ina saba maka amma sai ka dauko kamilalliyar mace kabani,baka bani mazinaciya Irina ba ya Allah nayi maka alkawari daga yau bazan kara aikata zina ba har nadawo gareka, zan tsaya a iya gonata daka albarkaceni da ita.





MACE GUDA DAYA TILO....



Na
UMMI A'ISHA

7⃣2⃣



   Hawaye ne yaci gaba da gudana akan kumatunsa na tausayin matarsa, shi kansa yasan ta wahala dayawa awa 4 ana abu 1 ummm tom ummi A'isha dai bata da ta cewa, ganin bacci ya dauketa yasa yatashi yashiga toilet dinta yayi wanka ya fito haka kawai ya samu kansa cikin wani nishadi ai rayuwar aure tayi yafada acikin ransa domin tunda yake yawon bin mata bai taba tsintar kansa acikin yanayin da ya samu kansa yau ba, dakinsa yaje ya saka jallabiya yayi sallar magrib da isha sannan yafito afalo ya tsinkayo wayoyinsa yana dubawa yaga miss called din daddy wurin 5 murmushi yayi yasan dan bai ganshi a masallaci bane shiyasa yakira yaji dalili to amma idan ya tambayeshi me zaice? Ai gaskiya da kunya dan haka sai kawai ya tura masa txt da cewa kanshi ne yake ciwo kuma shine da yasha magani bacci ya dauke shi sai yanzu ya tashi, dakin junada ya nufa lokacin ta farka tana tuno abinda ya faru tsakaninta da lamin dazu bude kofar ta ga anyi shine ya shigo daga shi sai gajeren wando runtse idonta tayi tafara fadin dan Allah yaya lamin kayi hakuri ka kyaleni wlh zan mutu ahankali yazo gefen gadon ya zauna yakamo hannunta ya rike cikin nashi yafara kama yan yatsunta daya bayan daya yana murzawa, junada! Taji ya ambaci sunanta saura kiris ta sume domin ji tayi duk duniya babu wanda ya iya fadar sunanta kamar shi, yaci gaba da cewa ki yafe min abinda nayi miki nasan na wahalar dake ban biki asannu ba amma dan Allah kiyi hakuri kinji hawaye taga yafara bin kumatunsa ahankali ta girgiza kanta alamun ya daina kuka hannunta ya saki ya tashi yashiga toilet ya hada mata ruwan wanka yadawo dakin yace tashi kije kiyi wanka, bazan iya tashi ba caraf ya dauketa ya kaita toilet din wanka yayi mata ya gyarata tsaf sannan yadawo da ita dakin ya saka mata doguwar riga sannan ya shimfida mata sallaya daga zaune tayi sallolin shi kuma ya cire bedsheet din ya shimfida mata wani tana idarwa ya cire mata doguwar rigar ya saka mata rigar bacci ya dauketa ya dora akan gado yazo kusa da ita ya zauna me zan dafa miki nasan kina jin yunwa ahankali tace tea kawai zansha ka duba kitchen akwai ruwan zafi acikin flask da sauri ya mike ya Shiga kitchen din ya hado mata tea mai kaurin gaske kamar koko ya kawo mata dakyar ta tashi zaune ya fara bata har ta shanye sannan ya kwantar da ita ya fita kafin yadawo har bacci yayi awon gaba da ita.






MACE GUDA DAYA TILO..


Na
UMMI A'ISHA


7⃣3⃣



       Yana shigowa yaga har bacci ya dauketa dan haka kusa da ita ya je yakwanta yashiga cikin jikinta, can cikin dare yaji zazzabi ya rufeta jikinta yayi zafi zau kamar wuta cikeda tausayawa yaja bargo ya rufesu sai dai shi baiyi wani baccin kirki ba motsi kadan zai tashi ya haskata yaga halin da take sannan zai kwanta ana jimawa zai kara tashi da haka har gari ya waye shi tun asuba yayi salla amma bai tasheta ba gudun kar ya katse mata baccinta sai wurin 6 sannan ta tashi yana kwance agefenta ta dan kalleshi sai taga idanuwansa arufe duk azatonta bacci yake dakyar ta iya tashi kamar mai koyon tafiya tafara takawa ahankali ya bude idonsa ya bita da kallo cikeda tausayawa ahaka yaga ta fito ta shimfida sallaya tasa dogon hijabinta har kasa zama tayi saboda ba zata iya tsaiwar ba kwalla ce yaji ta ciko masa ido yayi saurin gogewa ahaka ta idar da sallar ta dawo gadon ta kwanta, kanta ya dago ya kwantar akan kirjinsa yace sannu junada yaya kike jin jikin naki, zazzabi nakeji yana neman rufeni kuma kaina sai ciwo yake sannan jijiyoyin jikina jinsu nake kamar ana tsintsinka min su, cinyoyina kuma kamar ana sassara min gashi sunyi tsami kuma sunyi min nauyi,cikin tausayawa yace sannu bari naje na nemo miki magani, yana fitowa falo yaji ana kwankwasa kofar budewa yaje yayi husna da hasna yagani a tsaye yaya ina kwana lfy ya akayi? Gurin Anty mukazo, me zakuyi mata? Mun jita shiru tun jiyane shiyasa, lafiyar ta lau,Ku koma ku shirya mana breakfast zan zo na karba yana gama fadin haka ya maida kofar ya rufe yashiga dakinsa ya saka jallabiya da dogon wando yafito saida yasa key ya kulle kofar falon sannan yafita motarsa ya dauka ya tafi wani chemist ya siyo mata magunguna sannan ya dawo gidan, side din mummy ya shiga ya dauko kayan breakfast din yashiga side dinsu lokacin har ta tashi daga bacci tayi wanka da ruwan dumi ta gaggasa jikinta babu laifi ta danji dama dama tayi kwalliyar ta cikin wani brown din leshi tana zaune a falo ta kunna kallo, yana shigowa ta sukwi da kanta kasa bata yarda sun hada ido ba gabanta yazo ya ajiye abincin ya zuzzuba mata soyayyiyar doya da kwai da farfesun hanta, sauko da ita yayi ya dorata akan cinyarsa yafara bata abaki gaba daya idonta sunyi jawur fuskarta ta kumbura abinka da farar mace sai kace sweet choco kawata, ahaka har ta koshi ya bata maganin tasha sannan shima ya dan ci abincin ya tashi ya shiga dakinta ya gyara mata ya share ya kunna turaren wuta yadawo falonma ya gyara ya shiga kitchen ya wanke mata kwanuka ya share sannan ya dawo falon da take,kallo kawai take binsa dashi daga shi sai best da gajeren wando.
[3/24, 11:04 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO...


Na
UMMI A'ISHA


7⃣4⃣


   Falon yadawo ya feffesa air freshener yasaka turaren wuta bugun kofar da yaji ana yine yasashi tashi ya leka su hasna ne cikin shirin tafiya makaranta lekowa yayi yace ya akay? Yaya dama mun shirya ne shine muka biyowa Anty, kuyi tafiyarku ita yau bazata ba sai kun dawo kofar ya mayar ya rufe, wunin ranar dai bai huta ba dukkan ayyukan gidan shine yayi mata har tausayi yabata saboda yanda yaketa nan nan da ita gashi yanada lecture amma duk ya share yaki zuwa shi ta lafiyar matarsa yake. Haka ya rinka bata kulawa har na tsawon sati daya lokacin da ya fuskanci ta warware ne yafara fita kuma aranar ya kawo mata yan aiki guda 3 yace bai yadda tayi kowanne aiki ba in banda girki da gyaran dakinsa,wata soyayya mai wuyar fadi suke nunawa junansu, su husna kuwa tuni sun koma sashen mummy domin abin yafi karfinsu agabansu lamin yake kissing din junada ko ya rungumeta,yauma suna zaune acikin falo dukansu suna kallo ya dawo daga office ko kunyar su baiji ba yaje yashige cikin jikin junada ahankali ya lalubi bakinta yasaka cikin nashi hasna ce tace kinga husna zo mu tafi duk lokacin da suke da bukatarmu sa kiramu hakan kuwa akayi suka tashi suka tafi wurin mummy, ita kuwa junada dama tama manta da suna wurin domin ta dade tana kaunar jajayen lips din lamin dan suna mutukar burgeta. Ahaka rayuwarsu tayi ta tafiya cikin farin ciki alokacinne Kausar suka dawo daga kasar Uganda ita da Abdulrahman cikinta ya tsufa sosai, lokacin itama junada ta soma nata yan jinyace jinyacen da zazzabi ganin abin yayi yawa yasa lamin yakira mata likita har gida yana dubata ya ta tabbatar musu tana dauke da juna biyu na wata 2 tuni lamin yafara murna wai shine zai haifi dan kanshi, murmushi ya saki mai kayatarwa junada tace lfy? Kallonta yayi yace abin ne ya burgeni dalibata zata haifa min yara, murmushin itama tayi tace ai malamin ne akwai iya daukar fansa dariya yayi yajawota jikinsa ya rungumeta yace duk cikin friends dina fa ni kadai ne nayi auri gashi har zan haihu dariya itama tayi tace to ai kayi dabara nasan nice zan rigaka tsufa tunda kai namiji ne murmushi yayi ya kama hannunta yayi kissing dinsa sannan yace no ni yanzu inada 27 ke kinada 21 tare zamu tsufa, malami dai ya auri dalibarsa.





MACE GUDA DAYA TILO....


Na
UMMI A'ISHA

7⃣5⃣


  Ahaka ya shagaltar da ita da soyayyarsa mai wuyar fahimta. Washe gari kausar ta haifi yaronta santalele mai kamada lamin sak dan haka ranar suna ma sunan lamin din yayansa yasakawa yaron, yanzu rayuwa tayiwa junada dadi domin ta fahimci ita kadai ce MACE GUDA DAYA TILO acikin zuciyar mijinta yana bata dukkan kulawa kuma ahaka yayita tayata renon cikinta har ya isa haihuwa ranar da zata haihu lamin baya nan dan haka sai dawowa kawai yayi yaga ta haifi jariranta masu kama dashi sak, su husna kuwa tamkar zasu cinye su don so shi kanshi lamin yaran sun shiga ranshi dayawa haka akasha shagalin suna inda yaran sukaci sunan mahaifinsa da mahaifin junada ana kiransu sudais da shurem ansha buduri sosai washe garin suna mami kanwar umman junada ta tafi da ita bauchi tace sai bayan sunyi arba'in zasu dawo lamin kuwa bai so ba dan babu yadda zaiyi ne amma baiso sukayi nesa dashi ba, ita kuwa Mami tayi hakane domin ta samu damar gyara masa ita, duk karshen sati yake zuwa bauchi wurinsu da haka har suka cika arba'in saida suka dan zazzaga dangi sannan suka dawo yola lamin ne yaje dakansa ya daukosu yaci gayu cikin wani farin boyel mai shegen kyau da tsada idan kaganshi bazaka taba cewa yana da mata ba balle har kace ya ajiye yara biyu.
[3/24, 11:08 AM] Ummi A'isha🏻: MACE GUDA DAYA TILO.....

Na
UMMI A'ISHA


7⃣6⃣


    Haka ya debo su yana cike da doki domin shi kansa yasan yayi missing din junada, la'asar lis suka karaso gida cike da tsarabar bauchi su husna sai murna akeyi shi kuwa lamin alla alla yake su kebe shida matarsa domin ya tabbatar mata da cewa yayi rashinta. Ahaka suka ci gaba da rainon yaransu kuma alokacinne aka sanya ranar bikinsu husna zasu auri wasu twins yayan Governor din garin zamfara, dan haka suna gama karatunsu aka fara bikin junada itace uwar biki domin itace akan komai yan biyunta kuwa har sunyi wayo sun girma ba adade da bikinsu hasna ba ta yayesu lokacin sun cika 1 year. Haka suka ci gaba da rayuwarsu cikin farantawa juna tareda kyautatawa junansu ayanzu auren ramuwar gayya yazama auren soyayya. Yau an tashi da sanyi junada ta shirya cikin wani jeans da riga body hug ta dora katuwar riga sanyi asama ta nufi dakin lamin yana kwance yana bacci shida yaransu murmushi tayi ta juya tafice. Da yamma yafito cikin wata riga t. Shirt green da bakin wando ya isketa afalo tayi kyau tamkar wata budurwa ta bayanta yaje ya rungemata tattausan hannunta tasa ta shafo sumar kansa tace naga kayi kwalliya sai ina? Neman aure ai tuni tafara kwalla aure ? Dariya yayi yace dauko gyalenki ki rakani da gudunta ta dauko ta fita ta sameshi a mota shida yan biyu suna jiranta cikin garin yola suka shiga basu zame ko ina ba sai state university yola suna zuwa yafito yashiga cikin hall din inda dalibai sukayi dafifi suna jiransa, test ya rubuta musu yana cikin rubutunne yan biyu suka shigo cikin hall din dagudu sudais ne agaba shurem ya biyoshi cikin muryarsa ta yan yara yace daddy help me pls dagudu yazo ya rungume lamin cikin sauri lamin ya dagashi sama yana fadin wooh! Bai kamaka ba gaba daya yan ajin suka sa dariya wasu kuwa mamaki suke yanzu wannan malamin dama yana da aure? Sun ganshi dan yaro dashi ahaka yagama yi musu test din suka nufo gida akan hanyarsu ta dawowa ne yakalle junada yace yanzu idan akace miki zanyi aure sai ki yarda? Kallonsa tayi tace ehh mana murmushi yayi yace to ni babu auren da nake nema domin ke kadai kin isheni kuma ke kadaice MACE GUDA DAYA TILO acikin zuciyata, kwantar da kanta tayi ajikin kafadarsa tana cewa na gode mijina.

Alhamdulillah!

Anan nakawo karshen labarin MACE GUDA DAYA TILO, barayin fasaha kuji tsoron Allah ku daina yimana editing din littattafanmu batare da izininmu ba, duk wanda ya canza min wannan labarin ko ya cire sunana yasa nasa, ko yacire number na,ko yayi min editing Allah ya isa ban yafe ba.

Fatan Alkhairi gareki
Halamcy

Jinjina ga yan uwana marubuta

Fatima zarah ( d writer of xarah)

Kausar m Hassan ( d writer of tsaka mai wuya)

Serdeyeer ( d writer of miss Aysha)

Zainab Rogo ( d writer of auren gida)

Hafsat bounzer ( d writer of rabuwa da masoyi)

Aysha chuchu ( d writer of Duniyarmu)

Dorlin choco ( d writerof Aysha Noor)

Benaxir oumar ( d writer of kalma daya)

Hawwa jabo ( d writer of wacece ita)

Maman Khadija ( d writer of ni marainiya ce)

Maman Nana ( d writer of Mairo)

Cyama galadima ( d writer of Rayuwar rufaida)

Bebeelo ( d writer of kaddararmu)

Humaira ( d writer of samra)

   Uhm! Yau fa abin na marubuta ne, yan uwa makaranta kuyi hakuri sai mun hadu a labari nagaba mai suna..... Nice taku akoda yaushe sunan nawa bai canza ba UMMI AISHA
Duniyar Makaranta littattafan Hausa

3 comments:

  1. Allah ya Kara basira,in shaa Allah muna binku abaya

    ReplyDelete
  2. CONTACT:(wizardcyprushacker@gmail.com) We are best when it comes to hacking our services include: 1. School Grades Change 2. Drivers License 3. Hack email 4.
    Database hack 5. Facebook, Whatsapp 6. Hack Call Logs, 7. Retrieve messages, deleted data and recovery of messages, bitcoins hack and recovery lost funds
    on cell phone 8. Crediting , Money Transfer and other various activies 9. Sales of Dumps, Dead drops and fresh CC We
    also sell high grades techs and hacking chips and gadgets if you are interested in Spying on anyone. We sell software,
    apps for hacking service. Your security is 100% guarantee and we have testimonies all around the world.We get your job done without any disappointment.
    Interested parties can reach us at (wizardcyprushacker@gmail.com) whatsapp +1 (424) 209-7204

    ReplyDelete