Friday 6 January 2017

MARTABA TA 1-50

5, 7:16 PM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑


    Na
UMMI A'ISHA

Pg 1-5
 
DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN KAI!!




  A gaggauce take fitowa daga cikin bathroom din tana daure da towel wanda ya rufe iya gwiwarta, da sauri ta nufi room 4 dakinsu, tana shiga ta isa gaban mudubi ta fara shiryawa cikin sauri nikaina Ummi A'isha sai da nashiga mamaki saboda ganin tsaruwar dakin wanda sam baiyi kama da na yan makaranta ba, komai a jimulle yake acikin dakin tamkar dakin gida, bayan ta gama shiryawa ne ta isa gaban makeken akwatinta ta bude ta ciro wata hadaddiyar doguwar riga kalarta blue mai duwatsu tayi mutukar tsaruwa, da sauri ta saka doguwar rigar bayan ta feshe jikinta da daddadan turaren Mazda, dan siririn mayafi blue kalar rigarta ta yafa tayi rolling tare da daukar wayarta wadda ta kasance kalarta blue kirar galaxy s7, dogon takalmi ta sa baki ta jiyo da zummar ficewa daga cikin dakin, cubus suka yi da wasu yan mata guda biyu.

  Kallon kallon suka fara, cikeda fada daya daga cikin yanmatan ta kalleta "wai yau ma haka zaki fita ba kiyi mana girkin ba? To wallahi yau a dakin nan sai dai kowa ya zauna da yunwa dan wallahi nidai ba zanyi girkiba"

Kallonta budurwar tayi   "haba Sadiya kinga fa nakusa makara tun jimawa aka shiga lecture, dan Allah kuyi mana girkin ko taliya ce ku dafa mana" ta karashe maganar kamar zata fashe da kuka

"Tab wallahi yau kowa tashi ta fissheshi fati amma wallahi ba zanyi girki ba, ke kullum babu abinda zakiyi da zarar anyi magana sai kice lecture kamar ke kika fi kowa karatu"

Sai a lokacin daya budurwar tayi magana wadda tun lokacin da suka fara mahawarar take tsaye tana kallonsu "ya isa haka ku da kullum baku da aiki sai na fada, in dai girki ne ni zanyi, shikenan period magana ta kare"

Harararta Sadiya tayi "sai kiyita yi ai, dama ai dan kina yine shiyasa bata son yi"

"Eh din ina ruwanki sai tayi din" fati ta fada tana hararta, "ya isheki haka malama" Sadiya ta fada cikeda masifa

"Maza dai kar ki tafi har afito daga lecture din kin tsaya neman fadan da kika saba" A'isha ta fada lokacin da take shiga cikin dakin murmushi fati tayi tareda yiwa sadiya gwalo ta fice daga cikin dakin da sauri, tana fita A'isha ta kalli Sadiya tana dariya "Allah ya barni daku yaran nan kuna bani dariya wallahi"

Dariya Sadiya tayi "ai nasan zanyi missing din fati idan muka gama makarantar nan" dariya A'isha tayi ba tareda tace komai ba.

Koda fati ta fita a hankali take takunta har ta fita daga harabar hostel din, jin karar wayarta ne ya sata rage takun da take tare sakin wani murmushi "hello yayana yakake?" Tafada tana murmushi shima murmushin yake daga inda yake zaune akan luntsumemiyar kujerarsa ta office sai juyawa yake, office din nashi ya tsaru mutuka, farine bufulatani na asali,dogo marar kiba yana da dogon hanci mai tsini tareda manyan idanuwa farare kakal, sumarsa kawai zaka kalla kasan cewa ruwa biyune,yana sanye da blue din riga mai dogon hannu da bakin wando, wuyansa daure da necktie baki,a yanda na kiyasto muku shekarunsa ba zasu haura 34 ba,

"yanmata yakike?" Yafada yana murmushi mai kayatarwa

"Yaya Aadil kaga ka hana Sadiya, kullum kullum sai ta jani da fada" takarasa maganar cikeda shagwaba

Tsam ya mike daga kan kujerar da yake ya nufi window din office din, ahankali ya sauke glass din ya fara hango mutanen daketa kaiwa da komowa a kasan benen nasu wanda ya kasance hawa bakwai kuma shi office dinshi a last floor yake.

"How comes?" Ya fada yana dariya "common baby,haba yanmata yau ma sai da kuka yi fadan? Ke tsokana gareki ita kuma Sadiya saurin fushi, amma duk me ya kawo fadan? Fada min kinji sha lele" ya fada cikin sigar lallashi

Rausayar da kansa yayi tareda kurawa wani dan kayataccen lambu dake girke a can kasan office dinsu ido, "kin san bana son bacin ranki ki fada min menene"

Shiru tayi bata bashi amsa ba tana nazarinsa a hankali

"Kina so ki tayar min da hankali ko? Kina so hankalina ya tashi na kasa samun nutsuwa?"

Dan murmushi tayi hakan ya sake rudashi dan duk a zatonshi kuka take

"Kuka kike?,uhm?"

Sai a lokacin tayi murmushi "Kai yaya Aadil nifa ba kuka nake ba, kawai dai ina tunanin irin son da kake yimin ne, domin na kasa banbance tsakanin nida anty Salima wadda kafi so"

Murmushi ya saki mai kayatarwa ya saki dan zaren labulen dake hannunsa ya fara takawa a hankali ya nufi kayataccen falonsa.

Murmushi kawai yakeyi "kema kin san nafi sonki ai, shiyasa ma nabar Salima a gombe saboda ke idan na aureki nan zan kawoki kusa dani yanda zan samu damar kulawa dake"

"Hmmm yaya aadil kenan to kuma idan anty salima taki fa?"

Fridge ya bude ya dauko madara mai sanyi ya zauna ya fara kurba kafin ya fara bata amsa

"Ai itama antyn naki tasan irin son da nake miki saboda kin san ance amarya bata laifi"

Bata rai tayi kamar yana ganinta "ni baka sona dayawa, idan kana sona kayi min waka"

Dariya ya fara harda kwarewa "waka kadai kike so yanmata?"

"Ehh" tafada cikeda shagwaba

"To zanyi miki kar kiyi kuka pls, karkade kunnenki kiji zan fara"

"Ina jinka" ta fada a hankali

"Fatima, fatima yar auta, fatima tauraruwar mata
Dafari da farko, fatima gunki nataso da kidan jita fatima daure leko
Yau ga mai sonki fatima dauke da sako
Nidai fatana fatima kice dani miko,
Ki amince min fatima nayo roko zan sa kuka in bakya sona yanmata"!

Dariya fatima tafara kyalkyalawa "ayya yaya aadil basai kayi kuka ba, ina sonka kar kayi kuka"

Dariyar shima yayi  "to tunda kin hanani shikenan bazan yi ba amma da baki hanani ba da kuka zanyi"

Murmushi tayi "wakar tayi dadi yaya aadil, dama ka iya waka shine baka taba yimin ba? Tunda ka iya yanzu kullum sai kayi min".

Murmushi ya saki mai hadeda farin ciki dan bashida buri illa yaga fatinsa tana cikin fara'a da annashuwa

"Zan rinka yi miki, amma yanzu me kike?"

"Lecture zan je"
"Kinyi laifi, dama lecture zakije shine baki fada min ba, kika biyeni na rike ki da hira? Idan nazo gombe sai nayi punishing dinki"

"Am sorry yayana"

"Na hakura amma kiyi sauri ki shiga lecture"
"Yes sir" tafada tana dariya tareda saurin zare wayar daga kunnenta dan tasan bazai kara cewa wani abuba tunda tace mishi lecture zatayi.

Sai alokacin da ta gama wayar sannan ta fara daga kafarta da niyyar taje ta iske lecture din amma sai me? Tana bullowa ta wurin hall din ta hangoshi tsaye jikin motarsa kirar BMW ash colour, shikuma yana sanye cikin dark red din t shirt da black din trouser, sumar kansa tamkar ta larabawa domin a kanannade take akalla shekarunsa ba zasu wuce 30 ba a duniya, yana da kyau mai mutukar daukar hankali, nidai Ummi A'isha nakasa tantance tsakanin saurayin farko da wannan na biyu wanda yafi wani kyau da aji.

Take ta murtuke fuska domin a rayuwarta idan da wanda ta tsana to JAWAD ne, nan fa ta fara harare harare marassa dalili, a hankali ya taso yazo yasha gabanta,

"Fatima Xarah" ya fada yana kallon fuskarta

Dauke kanta tayi tamkar bata san da mutum a Gabanta ba,

Ahankali ya fara yi mata magana tamkar wani me yin rada,cikin hausarsa marar fita me kamada ta yan koyo ya soma yi mata magana amma abisa dukkan alamu hausar bata samu gurbin zama ba a bakinsa saboda fillanci da turanci su yafi iyawa sai wasu lokatan yakan dan hada da larabci domin asali ma shi hausa wahala take bashi saboda bai iyata ba shiyasa bai fiya yawaita yinta ba, ganin zai wahala da yawa yasa ya fara yi mata magana cikin harshen turanci,

"Queen why all this hateness? Meyasa kika tsaneni yanzu?"

Wata harara ta wurga masa kafin tayi magana cikeda gatsali

"Kaga Malam ni dama can ban sanka ba, balle har na soka, so stay away from..."

Cikin sauri ya katseta idonsa har ya sauya launi daga fari zuwa ja

"Karya kike fatima kin sanni, kuma kin soni, kuma har yanzu kina sona, kuma wallahi dole kici gaba da sona har abada"!

Wani dan malalacin murmushi ta saki kafin ta kalleshi fuskarta cikeda masifa

"Kai zan so? Hmm har abada bazan taba sonka ba, kasa a ranka fatima makiyiyarka ce ta har abada, dan haka ina mai shawartar ka da ka cire Fati daga sahun masoyanka domin bata kaunarka ko kadan"

Kallonta yayi ido cikin ido

"Karya kike, ke masoyiya ce agareni ba makiyiya ba, kuma sunanki da matsayinki bazai taba gogewa daga masoyiya ba, zanci gaba da tattalin sonki acikin zuciyata kamar yadda kema nasan kullum da sona kike kwana kike tashi"

Sausauta muryarsa yayi tareda ci gaba

"Queen ki sausautawa ranki, ki taimakawa zuciyata da taki mu ci ribar soyayyar da mukewa junanmu"

"Dawa zaka rayu?" Ta tambayeshi cikeda bacin rai

"Kar ka kuskura kayi gangancin rayuwa dani, domin tsanar da nayi maka tana iya sawa na kasheka"

Cikin bacin rai ya kalleta idanuwansa sunyi jajur

"Sai na rayu dake in yaso ki kashenin domin na shiryawa mutuwata in dai ta sanadinki ne, amma ki sani da sonki zan koma ga mahalicci na"

Yana kaiwa nan ya juya ya nufi motarsa cikeda bacin rai kafin wani lokaci har ya bar cikin makarantar cikin wani mahaukacin tuki, itama fatin cikeda damuwa hadeda bacin rai ta ta juya tabar wurin, lecture din da bata shiga ba kenan.













Ummi A'isha🏻
[5/5, 7:16 PM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑

    Na
UMMI A'ISHA

Pg 6-10



~~~Cike da bacin rai pherty ta juya tabar wurin ta nufi hanyar hostel tana tafe zucyarta na yi mata tukuiki kamar wuta,

A daidai wata baranda ta zauna ta fara kuka "nikam me zan yiwa jawad ya kyale rayuwata na huta? Na tsaneka jawad bana sonka bana kaunarka, bana kaunar duk wani me kaunarka, i hate u!"

Haka take ta furtawa tamkar wata zautacciya.

Ta dade a zaune tana faman kuka sannan ta tashi taja kafarta dakyar ta nufi hostel fuskarta cikeda damuwa,

Tana zuwa daki ta samu Sadiya tana yiwa A'isha kitso, ko kallonsu bata yi ba tafada kan gadonta ta fara wani sabon kukan, dukkaninsu tsayawa suka yi suna kallonta domin a yan kwanakin nan kusan kullum sai tayi kuka wanda su basu san dalilinsa ba.

Cikin damuwa A'isha tayi magana "pherty menene? Me ya ke damunki?" Shiru bata bata amsa ba kafin ta sake wata maganar tuni wayar phetyn ta soma ruri, cikin kuka ta daga wayar "yayana" tafada tana share hawayen fuskarta, "yanmata na me yake faruwa?" Cikin kuka tace"yunwa nake ji kuma ina jin ba suyi mana girki ba" da sauri ya katseta "suna ina?" "Gasu nan" tafada tana kuka "oya bani A'isha"

Mikawa A'isha wayar tayi takoma ta kwanta

"Hello yaya aadil" cikin sauri yace "haba A'isha ya zaki bar pherty na da yunwa har tana kuka?"

Cikin murmushi A'isha tace "yaya aadil wallahi girkinta ne yau kuma bata yi ba nikuma nace zanyi to yanzu kitso Sadiya take yimin shine nake son da zarar ta gama min sai na dora mana girkin, muma wallahi bamu ci komai ba, amma ga cornflakes nan tasha kafin ayi girkin"

Murmushi yayi "naji wannan to amma me ya hadasu fada da Sadiya dazu kafin ta tafi lecture?"

"Yaya aadil fati bata son aiki duk ranar girkinta sai sunyi fada da Sadiya saboda batayi ita kuma Sadiya itama sai tace bazata dafa ba"

"To shikenan daga yau ku daina girki ku rinka zuwa captaria kuna cin abincin in yaso duk end of month zan rinka biyan abincin, shikenan?

Girgiza kai A'isha tayi "a'a yaya aadil kabari kawai ni nayi maka alkawarin kullum zan rinka yin girkin in yaso fati sai ta rinka wanke wanke ko cefane"

"Phertyn nawace yar wanke wanke? No gaskiya ki sake mata duty"

Murmushi Aisha tayi "to yaya aadil zan sake mata, sai anjima"

Mikawa Sadiya wayar tayi "ungo yaya aadil zakuyi magana"

Karbar wayar tayi tana dariya "yaya aadil ina wuni?" "Bazan amsa ba saboda kin yi mana laifi nida pherty na"

"Tuba nake yayanmu"

Murmushi ya saki a hankali "to na yafe miki amma kar na sake ji" "baza a sake ba"

"To sai anjima"
Mikawa pherty wayar tayi tana yi mata dariya,cikin haushi pherty ta fusgi wayar tareda karata a kunnenta

"Hello yayana" tafada a hankali

"Yanmata kiyi hakuri komai ya wuce kinji? Ki daina kuka kinji pherty na, ina nan zuwa ganinki"

Cikin doki tace "dagaske? Yaushe zaka zo?"

"Sai kin daina kuka sannan zan fada miki", "nadaina yayana fada min" murmushi yayi mai dan sauti "to yi dariya naji" dariya ta fara harda kyakyacewa ahankali yace "zanzo upper week, me kike so na taho miki dashi?" Cikin farin ciki tace "ni kai kadai nake son gani"

"Ki fadi abunda kike so pherty na", "wallahi bana bukatar komai yayana" murmushin jin dadi yayi "to shikenan yanzu ki zauna ki huta sannan anjima zan turo miki 20 thousands ta account dinki, saboda nasan akwai abubuwan da budurwa irinki take da bukatarsu amma kunya ba zai barki ki tambayeni ba"

"Yaya aadil inada kudi fa, kabarshi kawai"

"Nidai anjima zan turo miki"

"Tom, nagode Allah ya saka da alkairi, Allah ya kara budi, Allah ya...!"

Katseta yayi ta hanyar dora dan yatsanshi akan lebenshi "shiiiiiii godiyan ya isa haka pherty na, nasha fada miki duk abunda nayi miki cancantar kice ta sani yi miki, nidai kawai addu'ar da zaki yimin kwaya daya ce, cewar Allah ya bani ke"

Cikin murmushi tace "amin"

"Bari na kyaleki zan kira antynki bata jin dadi tana fama da mura, kema ki kirata kiyi mata sannu kinji, and expect my call later"

"Zan kirata, sai najika yayana, bye bye" tafada tareda zare wayar daga kunnenta, cikin sauri ta danna number Salima ta fara kiranta, ringing uku ta daga,

"Hello kanwata" aka fada daga can bangaren

"Anty yajiki? Yanzu yayana yake fada min bakida lafiya"

Murmushi Salima tayi

"Ai yayan nan naki ya cika surutu, bafa wani ciwo bane mai yawa ba, just mura ce fa, kuma naji sauki ma"

"Ayya, Allah ya baki lafiya, gasu Sadiya da A'isha zasu gaisheki"

Wayar ta mika musu kowaccensu ta gaisheta sannan suka yi sallama,

A'isha ce ta mike ta janyo risho ta kunna ta fara kokarin dora musu girki, kallon pherty tayi, "oh da haka mata suke da an zauna lafiya aduniya, wallahi nikam anty saliman nan tayi min, tana burgeni babu ruwanta"

Sadiya ce ta karbi zancen ta hanyar cewa "ai shiyasa shi kansa yaya aadil din yake darajata saboda bata nuna irin wannan kishin haukan ba, domin daga lokacin da mace ta zubar da kimarta wai dan mijinta yana neman aure to wallahi daga ranar ta rasata har abada"

Baki A'isha ta tabe "ai kuwa yawancin matan yanzu haka suke, basu san Kansu suke ragewa daraja ba,wata ma dan tsabar rashin aji har budurwar take yiwa waya ta zaga dan tsabar bada kai"


Sai a lokacin pherty tayi magana "ni wallahi dan mijina yana neman aure banda time din kiran budurwar, aure ai hajace tazo kowa ya baje tasa mai rabo sai ya siyar"

"Banda matan yanzu, matan yanzu mugunta da son kai sunyi musu yawa kowa sai tace ita kadai zata zauna a gidanta, alhalin kuma tana da kanne, idan kannenta ne tana son su auri mijin wata amma ita bata son a auri mijinta" A'isha tafada lokacin da take dora tukunya akan rishon data kunna

"Allah dai ya rabamu da sharrin zuciya" inji Sadiya

"Amin" suka amsa dukansu, pherty kuwa hoton aadil ta kurawa ido, yana tsaye yasha bakaken suit wanda suka yi tsananin yi masa kyau, yanata murmushi ya dafa wani karfe a bakin wani tafkeken kogi da alama hotonma a kasar waje yayi shi, murmushi ta fara yi ita kadai saboda tunowa da tayi yace zai zo nan da sati biyu masu zuwa.


**********************

A bangaren jawad kuwa koda ya fita daga makarantar su pherty gidansu ya nufa cikeda kunar zuciya saboda kiyayyar da pherty take nuna masa yanzu tayi yawa alhalin shi kuma yanzu a duniya idan da wacce yake so to itace.

Cikin tsananin gudu ya isa gidan nasu yana zuwa bai jiraba ya kutsa kan motarsa zuwa harabar gidan wanda yake katoton gaske, a fusace ya kashe motar ya zare key din ya nufi side dinsa,yana shiga bedroom dinsa ya shige yaje ya fada kan gado take zuciyarsa ta fara tafarfasa, idanuwansa kuwa tamkar gauta dan ja,

Zaraf ya tashi zaune kamar wanda aka tsikara "Xarah, Xarah wallahi sai na aureki, mutukar ina numfashi bakida mijin da ya fini, nine mijinki ko kinki ko kin so, wallahi babu mai aurenki sai ni, haba Xarah!" Ya fada tamkar wani zautacce,

"Kai jawad kai da waye?" Wata mata fara tamkar balarabiya ta fada cikin harshen fillanci kana kallonta zakaga tsananin kamarsu da dan nata jawad, kamar kara aka tsaga, shekarunta zasu kai 45 a duniya,

Cikin damuwa ya jiyo ya kalleta "Ummi babu komai" yabata amsa cikin harshen fillanci shima,

"Kowa ya kalli fuskarka yasan kana cikin damuwa jawad, ka fada min abunda yake damunka",

Tamkar zaiyi kuka yace "Ummi wata budurwa ce bata sona, ta tsaneni nikuma ita nake so ummi, wallahi bazan iya rayuwa da wata mace ba idan ba itaba, she's the part and parcels of my life, i can't do without her, my life without her is just like a car without fuel, i can't survive without her"

Ya karashe maganar cikin rawar murya

Cikeda tausayawa mahaifiyar tashi ta karaso gabansa ta zauna kusa dashi tareda dafa kafadarsa, kayi hakuri jawad hakika kai ba kayi kamada irin mazan da mata suke tsana ba domin ka mallaki komai, wannan kar ya daga hankalinka zaka aureta zata soka fiye da yanda kake sonta".







Ummi A'isha🏻
[5/5, 7:16 PM] Ummi A'isha: [4/25, 6:23 PM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑

  Na
UMMI A'ISHA

Pg 11-15


~~~Fuskarsa da damuwa ya kalli ummin tasa yace

"Ummi Xarah daban take acikin mata, sannan kuma duk abunda ta aikata a gareni daidai ne saboda....!" Kasa karasa maganar yayi, yai shiru da bakinsa,

"Saboda me jawad?" Mahaifiyar tasa ta bukata, "jawad anya kuwa babu wani abu wanda kake boye min?"

Kallonta yayi da jajayen idanuwansa

"Ummi babu abinda nake boye miki, nidai ki tayani da addu'a kan Allah ya saukaka min al'amura na musamman ma dangane da pherty saboda idan har ban aureta ba to bazan taba gafartawa kaina ba"

"Saboda me?" Ta tambayeshi tana kallonsa

"Ummi saboda zuciyata tana sonta"

Hannunsa ta kama "ka tashi kazo muje kaci abinci, dan uwanka ma yana nan zuwa nan da wani dan takaitaccen lokaci",

Sai da gabansa ya fadi jin an anbaci cewar dan uwansa zai zo, shidai a halin yanzu idan da wanda yake jin haushi a rayuwarsa ta duniya to bai wuce dan uwan nasa ba domin ya fahimci yana yi masa shisshigi a gonarsa,

"Katashi muje jawad"

Muryar Mahaifiyar tasa ta dawo dashi cikin hayyacinsa, dan haka dole ya mike ya bita ba dan yaso ba.


Part din mahaifiyarsa suka shiga an kawata komai akan table, abinci ne iri iri daban daban na alfarma, sai kamshin kanumfari da tafarnuwa ne ke tashi, idan da sabo to ya saba domin ko farar shinkafa aka dafa a gidan sai an sa mata kanumfari wannan yana daya daga cikin al'adar mahaifiyar tasu kasancewarta balarabiya usul,

Kadan ya zuba abincin ya fara ci yana ci yana tunanin hanyar da zai magance matsalar da ta kunno kai gareshi, daga karshe ya yanke shawarar ci gaba da farautar zuciyar pherty har Allah yasa ya dace.

****************

Yau ta kama ranar weekend dan haka gaba daya hostel din cike yake da hayaniya, pherty da A'isha kowacce tana kan gadonta a kwance, Sadiya ce ta shigo cikin dakin

"To yan hutu sai ku tashi aje ayi wanki"

Juyi A'isha tayi tareda dago kanta ta kalli Sadiya

"Dan Allah ki bari ajima sai ayi"

Harararsu tayi su duka

"Wallahi ko ku tashi ko kuma na debi iya kayan da nasa na wanke na bar muku naku"

Juyi pherty tayi sannan ta tashi zaune

"Meye" ta fada tana hararar Sadiya

"Ba asani ba" Sadiya ta fada tana hararar ta itama,

"Wanki za ayi wai yanzu da sanyin safiyar nan" A'isha ta fada tana kallon pherty

"Tab babu wankin da zanyi wallahi, daga tashina ko muryar yayana banji ba", wayarta ta dauka ta fara kokarin kiran yayan nata,

"Kun san halina ai, kowaccenku tayi duk abinda take so yanzu" Sadiya ta fada lokacin da take kokarin ficewa daga cikin dakin,

"Yayana ko baka tashi ba?" Pherty ta fada a hankali, ita kam A'isha kwanciya tayi tafara sauraron hirar pherty da aadil, ita dai a duniya bata taba ganin masoyan da suke burgeta ba kamar pherty da Aadil,

Yana daga kwance akan makeken gadonsa yayi murmushi tareda yin juyi "natashi tun dazu antynki ce ta tasheni ma, badon haka ba sai 11 zan tashi"

Murmushi tayi "ai kuwa dai ta kyauta dan da bata tasheka ba da bazan ji muryarka ba yau sai nan da 11?"

"Eh mana" ya fada yana kokarin bude laptop dinshi wacce ke ajiye a kan bed side drawer dinshi,

Yana budewa hoton pherty ne ya mamaye kan screen din, hoton ya tsaya yana kallo,

"Kinyi kyau pherty na" ya fada lokacin da yake shafa hoton,

"Kaima ai kullum kana yin kyau yayana"

"To yaushe kika tashi?"

"Yanzun nan Sadiya ta tada mu wai zamu yi wanki, nikuma wallahi yaya na tsani wanki bata min rai yake yi"

"Shine baki taba fada min ba? Ina sadiyan?"

"Tafita"

"A'isha fa?"

"Gata"

"To bani ita"

A'isha ta mikawa wayar, "ungo yayana zai yi magana dake" karbar wayar A'isha tayi ta kara a kunnenta

"Hello yaya aadil"

"A'isha daga yau na soke yin wanki, babu ku babu wanki, ku rinka kaiwa shago ana wanke muku kinji? Wadanda zaku iya wankewa kawai na yarda Ku wanke"

"To yaya aadil zamu kiyaye" A'isha ta fada tana kallon pherty tareda mika mata wayar

Karba tayi ta juya suka ci gaba da hirarsu da aadil har Sadiya ta shigo ta fara aika musu da harara,

"Albishirinki?" Inji A'isha

"Goro" Sadiya ta mayar mata da amsa

"To yayan pherty ya hanamu wanki yace sai dai muna kaiwa shago inners wears kawai ya yarda mu wanke, zama Sadiya tayi "ai yaya aadil dinnan yana shagwaba yarinyar nan ina jin idan sunyi aure babu abinda zata rinka yi"

Dariya A'isha tayi "ai kuwa ya kyauta danni wallahi hakan burgeni yake"

Mikewa Sadiya tayi ta nufi risho tana fadin "eh ai keda ita duk halinku daya na rashin son yin aiki".

   Ranar Monday da wuri dukkaninsu suka shirya domin zuwa lecture kowaccensu taci kwalliya ajin karshe, atare suka fito suka nufi area classes, a ta gaban wani babban hall pherty ta hangoshi zaune acikin motarsa kirar KIA kalarta ja yana sanye da bakin face a fuskarsa,

"Jawad ko kai maye ne sai haka" tafada acikin zuciyarta, yana hangosu ya fito ya nufo inda suke, kasancewar basu sanshi ba sai suka tsaya kallon gun wacce zai zo,

Agaban pherty ya tsaya yana mayaudarin murmushinsa dake sace zuciya wanda pherty ke ganinsa tamkar hayaki dan baki, "morning my queen" ya fada a hankali,

Kanta ta juyar, yayinda A'isha taja hannun Sadiya dan su dan basu waje, suna matsawa ya dubi fuskarta wadda tasha kunu murtuk a hankali ya furta "ki saki fuskarki, wannan bata ran da kikayi bai kamaci kyakkyawar fuskarki ba pherty na"

Dam,dam gabanta ya fadi, saboda wannan sunan yayanta ne kadai ke kiranta dashi,

Gabanta ya dan sake matsowa "don't break d heart that love you pherty, love can neva being hate, and you know..!"

Hannu ta daga masa, "kai jawad, kai macuci ne, kai azzalumi ne, kai marar imani ne, wai me na tare maka a rayuwar duniya da kaketa burin sai ka ga bayana? Jawad har yau ina tareda bakin cikin da kunsa min koda wannan ka barni kayi wa MARTABA TA babbar illa, kayi hakuri ka kyaleni ka barni da abinda nake ji, kai maha'inci ne nasan duk maganganunka na yaudara ne, yanzu nasamu mai kare MARTABA TA dan haka kayi nesa dani"

"Impossible" ya fada cikin daga murya

"Ni jawad nine mutumin da zan dawo miki da MARTABAR KI nine zan aureki zan nuna miki soyayya sannan na kare miki MARTABAR ki, wallahi kinji na rantse mutukar ina rayuwa to sai na aureki pherty, indai kika ga ban aureki ba to mutuwa nayi" yana kaiwa nan ya juya ya nufi motarsa, sai a lokacin tabi bayanshi da kallo yana sanye cikin dark blue din jeans da yellow din t shirt mai gajeren hannu.


Kamar ta fashe da kuka take ji saboda ta rasa yadda za tayi da jawad ya fita daga cikin rayuwarta,

Su A'isha da Sadiya ne suka karaso inda take "yau yaya aadil ya samu abokin takara kenan" A'isha ta fada tana dariya,

"Kuma fa kinga shima ya hadu" Sadiya ta bata amsa, ai pherty na jin haka hawaye ya fara sulalowa daga cikin idonta dama kamar jira take,

Cikin mamaki dukkaninsu suka fara magana

"Allah ya baki hakuri daga wasa?" Wasu hawayen ne suka gangaro mata ba tareda ta basu amsa ba,

"Kiyi hakuri pherty mun san yaya aadil kike so, to amma shi masoyi bai taba zama makiyi ba dan haka shima wannan din ki lallabashi ku rabu lafiya" Sadiya ta fada tana kallonta, jan hannunta A'isha tayi "muje mu shiga lecture pherty zamu tattauna daga baya" inji A'isha.

Koda suka fito daga lecture ma bata sauya zani ba in banda kuka babu abunda pherty take yi lallashin duniya suka yi mata amma taki yin shiru ganin haka yasa Sadiya Kiran aadil a waya ta sanar dashi, cikin rudu yace

"Bani ita" bata wayar Sadiya tayi "ga yayanki zaku yi magana"

Karbar wayar tayi cikin kuka ta fara magana.



Ummi A'isha🏻
[5/5, 7:16 PM] Ummi A'isha🏻: [4/27, 6:12 PM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑

   Na
UMMI A'ISHA

Pg 16-25


*** Cikin kuka hadeda shagwaba pherty ta fara magana

"Yayana"

Arude ya amsa mata

"Pherty na me ya sameki? Ki fada min pls"

Hawayen fuskarta ta goge

"Yaya Aadil kaina ke ciwo amma yanzu ya daina"

"Um um fa phertyma ki fadi gaskiya"

Murmushi tayi itama

"Wai yaya Aadil baka kunyar fadin sunana bayan kuma sunan umminka ne"

Yar dariya yayi mai dan sauti

"To ai ba sunan Ummi na fada ba sunan matata na fada kuma sunan first born dina"

"Anty saliman mace zata haifa?" Ta tambayeshi cikeda zolaya

"Ke dai, kece zaki haifi mai sunanki insha Allah"

Shiru tayi, can kuma tayi zakal tace

"To ai babba shine ya kamata ya fara haihuwa,in dai ba tsari ake yi ba"

"Babu wani tsari ita kanta antyn naki tana son haihuwa nima kuma ina mutukar kokarina kawai dai Allah ne bai kawo ba"

"Wanne kokari kake? Babu wani kokari"

"Haka kikace? To bari muyi aure zaki ga rashin kokarin nawa"

"Allah ya baka hakuri wasa nake ai nasan kai mai kokari ne ako ina"

Murmushi yayi "matsoraciya, har kin tsorata? To albishirinki?"

Cikin doki da murna tace "goro"

"Nafasa zuwa next week, this week zanzo naganki, so ki daina kuka kinji?"

Cikin murna tace "ranar yaushe?"

"Ranar juma'a zaki ganni domin wurinki ma zan fara zuwa"

"Woooh" ta fada cikeda murna "yeeeeh" ta sake sakin yar kara "zanga yayana"

Dariya ya soma yi mata daga karshe yace "tunda naga kinata murna to bari na barki anjima zan kiraki"

"To yayana, bye"

Tsalle ta daka ta dale jikin Sadiya da A'isha "yaya Aadil zaizo this Friday, me zan dafa masa? Yeeeh fried rice zanyi in hada masa coconut juice"

Sadiya da A'isha dai kawai dariya suke suna kallonta kamar ba itace take kuka dazu ba amma yanzu gashi tanata dariya, haka suka rankaya suka nufi hostel.

   Tun daga ranar pherty kullum cikin lissafi take na zuwan yayan nata, yau ta kama ranar laraba a lissafinta saura kwana biyu yayanta yazo, ko kwalliya ta daina yi sai ranar da zai zo zatayi.

Shiryawa tayi ita da A'isha suka nufi class yayinda suka bar Sadiya kwance tana bacci saboda ita bata da lecture, yau ma kamar kullum yana tsaye inda ya saba tsayawa, wani kululun bakin ciki taji ya tokare makogaronta amma yau tayi niyyar yi masa abinda indai yana da zuciya ba zai sake zuwa gareta ba.

  Kanta ta dauke tareda kama hannun A'isha suka wuce,shima bai yi kasa a gwiwa ba ya bi bayansu yana kiran pherty,

Juyowa tayi ta dubeshi fuskarta a daure ga dalibai fal kowa yana harkar gabansa,

"Tsaya ki saurareni queen"

"Me zan saurara? Karya ko yaudara? Aciki wanne kake son na saurara? Jawad ka fita daga harkata rayuwar data faru can abaya tsakanina da kai ka barshi a matsayin mummunar kaddara kuma jarrabawa a gareni"

Kallonta yayi a raunane, "tayaya zan barki bayan zuciyata tana sonki?" Ya fada cikin harshen turanci

Dan murmushin takaici tayi "sanin kanka ne bazan taba aurenka ba har abada"

Cikin daga murya ya mayar mata da amsa "dole sai kin aureni kuwa, kuma wallahi bazan hakura dake ba"

Hankulan jama'a tuni suka daddawo Kansu saboda yanda jawad yayi maganar da karfi,

"You kid your self jawad, pherty will not marry you,idan mafarki kake to ka farka, dan bazan aureka ba ko ka zata na manta waye jawad? To har yau ina sane da kai, kai macuci ne, mayaudari, maha'inci sannan babban mazinaci"

Da sauri A'isha ta jiyo ta kalleta, yayinda daliban wurin suka shiga mamakin wannan wulakanci da ake yiwa wannan kyakkyawan saurayi dan ya hadu tako wanne bangare,

Shi kuwa jawad wata kunya yaji ta rufeshi a wurin saboda yanda mata da maza suke turarreniyar kallonsa, wani bacin rai yaji ya ziyarci zuciyarsa,

"Marar tsoron Allah mai raba "yayan mutane da MARTABAR su..!"

  Bata karasa maganar ba sakamakon janyeta da A'isha tayi suka nufi bayan wani hall shima jawad juyawa yayi ya shige motarsa ya fizgeta da karfi yabar wurin,

  "Haba pherty wannan wulakancin da kike yiwa gayen nan yayi yawa,idan wani abu yayi miki ai ya kamata ace kin yafe masa, idan kuma ramawa kike son yi to bai kamata ki rama ta wannan hanyar ba domin kin ci mutuncinsa mutuka"

Cikin masifa pherty ta kalleta,"naci mituncin nasa idan yanada zuciya daga yau kar ya sake zuwa wurina" tana gama fadin haka ta juya ta nufi hostel ba tareda ta jira Aishan ba.

Bin bayanta A'isha tayi tana yi mata magana "ai so baya zama ki, wulakanci bai kamata ba" juyowa pherty tayi "sai kiyi tayi kuma"

Haka dai suka ci gaba da tafiya suna fada har sukaje hostel, suna shiga daki suka samu Sadiya zaune tana shirya musu kayan sawarsu cikin akwatinansu

Nan suka ci gaba da fada har Sadiya tasa baki "indai gayen nan na rannan kika yiwa rashin mutunci gaskiya baki kyauta ba" nan pherty ta sake harzuka,kawai sai ganinta suka yi tasa kuka, harararta Sadiya tayi "ace mutum bashida wani aiki sai na kuka?"

"Um ai kin san gaskiya wuya ne da ita" A'isha ta fada lokacin da take kokarin tashi domin rage kayan jikinta, jin maganganunsu yaki karewa yasa pherty ta tashi tabar musu dakin ta tafi wani dakin.

Tun daga lokacin ta fita harkarsu har ana igobe zuwan yayanta, shi kansa bata fada masa ba, ganin tanata fushi yasa A'isha da Sadiya lallashinta har ta sauko suka koma harkokinsu kamar da amma basu sake tayar mata da batun jawad ba.

******

A bangaren jawad kuwa yaji bakin cikin wulakancin da pherty tayi masa acikin mutane domin har kwalla ya zubar amma yayi alqawarin jure duk wani wulakancinta har sai ya cika burinsa na mallakarsa a matsayin mata, daren ranar bai iya bacci ba saboda bacin rai.

Yau itace ranar da Aadil zaizo daga Abuja, tunda sassafe su pherty suka je kasuwa suka iyo cefanen da zasu yiwa Aadil kayan sauka,

Fried rice da hanta suka yi masa wadda tasha cabbage da su carrots da sauran tarkacen kayan lambu, ga lemon kwakwa da aka hada masa.

Karfe 12 daidai ya iso cikin makarantar, pherty ansha kwalliya cikin brown din doguwar riga mai tsananin kyau ga make up data tsarawa fuskarta tasha turarruka kala kala, kallonta suka yi kawayen nata "kinyi kyau yanmata" murmushi tayi "nagode, bari naje in yaso kwa kawo abincin ko?" Dariya Sadiya tayi "irin wannan kwalliyar kam bai kamata ki dauki kwanukan abinci ba" dariya suka yi su duka ita dai pherty juyawa tayi ta fita yayinda su kuma suka fara kokarin shisshiryawa.

  A karkashin wata bishiya ta hangoshi ya shimfida katuwar darduma yana zaune cikin manyan kaya farar shadda goggagiya mai tsada yasha hula mai adon fari da baki hannunsa daure da agogon azurfa yana yin waya da alama da matarsa yake wayar,

Da murmushi a fuskarta ta karasa, shima murmushin yake yi, a hankali ta zauna can dan nesa dashi kadan tana jiran ya gama wayar, "yau ko zaki ganni sai dare dan daga nanma gidan Ummi zanje" haka taji ya fada lokacin da yake ajiye wayar.

Yana ajiyewa ya juyo ya fara aika mata da tsadadden murmushi, "pherty na" ya fada yana murmushi

"Yaya na sannu da zuwa, ya hanya? Yaka sauka?"

"Alhamdulillah pherty na, antynki tana gaisheki tace kuma karki cika mun cikina da daddadan abincinta gudun kar nakasa cin nata abincin idan nakoma gida"

Murmushi tayi ta kalleshi "ai kuwa sai dai tayi hakuri dan yau cikinka iya abincina zai dauka, gobe sai ya dau nata"

Kallonta yayi cikin farin ciki "kinyi kyau pherty na" hannunta tasa ta rufe fuskarta tana murmushi

"Haka ma agida zaki rinka yimin wannan kunyar?"

Dakyar ta iya kallonsa, "ya aiki? Ina fata yanmatan abuja basa kallon yayana?"

"Yayanki nakine keda antynki kawai, ki kwantar da hankalinki"

"A'a ka fada ne fa kawai" tafada kamar zatayi kuka

"Haba pherty na, yau bakya son wakar?"

"Ina so" tafada tana dariya

Daidai lokacin Sadiya da A'isha suka karaso dauke da kwanukan abinci a hannunsu

"Sannu da zuwa yaya Aadil" suka fada dukkaninsu atare tareda ajiye abincin a gabansa, bayan sun gaisa suka juya suka tafi,

Abincin ta zuzzuba masa ta tura masa gabansa,kallonta yayi "duk wannan abincin a cikina zan sa?"

"Eh mana yayana"

Murmushi yayi "pherty na kenan"

Kallonsa ta tsaya lokacin da yake cin abincin ita dai bata taba tunanin zata auri namiji mai mata ba sai gashi ashe mai mata ne mijinta, taso ta more rayuwarta da saurayi ashe da bazawari zata yi,

"Ya akayi ne kika tsaya kinata kallona"

Murmushi tayi babu komai kawai kayi min kyau ne shiyasa"

"Fadi gaskiya dai"

Hira suka yita yi har ya gama cin abinci yayi alwala ya tafi sallar juma'a ita kuma ta koma hostel ta sake wani sabon wankan ta sake shiga cikin wata atamfa kalar ruwan kwai tasha dauri su A'isha da Sadiya sai tsokanarta suke, gurin Aadil ta sake komawa bayan ya dawo daga masallaci,

"Yau dai zaki barni natafi kuwa?" Ya fada yana kallonta "naga sai kyau kiketa zubawa"

"Yaya banda zolaya dai"

"Babu wani zolaya" ya fada yana yi mata murmushi.

Har yamma suna tare sai wurin 5 sannan ya tafi bayan ya firfito mata da shopping din da ya siyo musu, kaya kamar a shago kama tun daga kayan makulashe har zuwa turarruka da hadaddun mayuka, yana fita daga school dinsu pherty gidansu ya wuce wato gidan iyayensa.

Lokacin da ya shiga gidan nasu mahaifiyarsa da kaninsa suna zaune a tsararren falon ummin tasu, cikeda fara'a ummin ta fara yi masa sannu da zuwa amma shi dan uwan nasa kau da kai yayi tamkar bai ganshi ba,

Kusa da ummin yaje ya zauna "sannu da hutawa Ummi". "Yawwa Aadil barka da sauka" da sauri ta tashi ta nufi kitchen domin hado masa kayan motsa baki,tashi yayi ya nufi inda kanin nasa yake ya mika masa hannu "Assalamu Alaikum ya Aki"  "wassalam" jawad ya fada tareda dauke kansa ya tashi ya fice daga cikin falon ba tareda ya bashi hannu sunyi musabaha ba, bin bayansa da kallo Aadil yayi wannan wacce irin kaddara ce take kokarin kutso kai tsakaninsa da dan uwansa, yana nan zaune Ummi ta dawo dauke da faranti wanda ta doro kayan motsa baki a kai, akan dan table din gabansa ta ajiye, nan ta zauna ta fara hira da dan nata har tsawon wani lokaci daga bisani yayi sallama da ita ya nufi sashen mahaifin nasa.

Lokacin da yafito ya shiga part din abbunsu a lokacin shi kuma jawad yana kokarin fitowa, wata harara jawad ya aika masa da ita ya dauke kansa ya wuce, wucewa ciki Aadil yayi yanata jajanta wannan lamarin acikin zuciyarsa, a babban falon mahaifin nasa yayi ya tarar dashi yana kishingide yana wuridi da casbaha a hannunsa,

Da sauri yaje ya duka a gaban mahaifin nasa bayan sun gaisa ne yake sanar masa da cewa yana so zai kara aure,kallonsa mahaifin nasa yayi "aure Aadil? Lafiya zaka kara aure?" "Lfy lau abbu, kawai dai akwai dalili ne, ina son taimakon yarinyar ne abbu, domin inada halin iya rike mata hudu tunda Allah ya bani arzikin da zan iya yin haka shiyasa nake son yin amfani da wannan damar wurin taimakon yarinyar" kada kai mahaifin nashi yayi "Allah ya saka maka da alkairi, Allah ya albarkaci rayuwarka, dama nayi tunanin ko dan saboda matarka bata haihu bane shiyasa zaka kara aure to amma tunda ba haka bane to Allah ya tabbatar da alkairi"

"Amin abbu"

"Nan da yaushe zaka kara auren?"

"Abbu nan da watanni hudu"

"To Allah ya kaimu"
"Amin abbu,a huta lfy"

Tashi yayi ya fita ya koma yayiwa mahaifiyarsa sallama ya fito ya nufi gidansa inda matarsa ke zaman jiransa.

Koda yaje ya samu Salima cikin kyakkyawar shiga tasha kwalliya tayi kyau sosai, nan ta tarbeshi cikeda kisisina, wanka ta kaishi yayi ta shiryashi cikin kayan shan iska.

Bayan wani dogon lokacine Aadil ya shafo gashin kanta yace "Salima kiyi hakuri da abinda zakiji daga gareni"

Dam gabanta taji ya fadi amma sai ta daure tace ina jinka

"Salima bikina da phertyma nan da watanni hudu masu zuwa za ayishi, dazun nan muka gama maganar da abbu"

Duk da hankalinta ya tashi amma sai ta dake tayi murmushi ta riko hannunsa "Allah ya nuna mana lokacin, Allah ya baka ikon yin adalci a tsakaninmu"

Hannunta ya damke "amin baby, hakika ina jin dadin yanda kuke mu'amula keda pherty tun kafin tashigo gidan"

"Babu komai dear ita kishiya ai yar uwace"

"Allah yayi miki albarka, nikuma nayi alaawarin kulawa dake har karshen rayuwata".

  Washe gari da misalin karfe  3 yaje wurin pherty bayan sunsha hirane yake sanar mata da batun bikinsu nan taji jikinta yayi sanyi amma ta nuna masa farin cikinta a fili, koda ya tafi ta shiga hostel nan ta fadawa su Sadiya da A'isha sai kuma ta fara kuka, nan suka shiga tsokanarta wai kukan farin ciki take.


***

Jawad yana zaune a falo daga shi sai three quarter da yar body hug yana tv game ajikin computer kamar wani yaro, Ummi tana zaune tana waya kamar daga sama ya jiyo ta tana cewa "bikin Aadil ne ya taso nan da 4 months zai auri wata yarinya phertyma shine nake son ki hado min kayan lefe....!"

Zunbur ya mike kamar an tsikareshi, da sauri ya wuce side dinshi ya dauko key din motarsa ya nufi gidan yayan nasa Aadil, lokacin da ya shiga gidan iya Aadil ne zaune a falo yana kallo yayinda Salima take kitchen tana aiki,

A can ciki yayi sallama,shi dinma Aadil din a dakile ya amsa domin ba don ta zama wajibi ba ma to da bazai amsa ba,

Kallonsa jawad yayi idonsa kamar gauta dan ja, "nazo ne nayi maka kashedi, pherty ba taka bace tawace, ta sanadiyyata ka ganta har ka kamu da sonta saboda tsabar abin kunya"

Kallonsa Aadil yayi "Kai wanne irin shasha ne? Kana tsammanin pherty zata aureka ne? To idan mafarki kake gara ka farka, bayan ka gama rusa mata MARTABAR TA shine yanzu zaka dawo kace wai kana sonta? To babu abinda pherty zata yi dakai gara ma ka daina batawa kanka lokaci"

"Ba batawa kaina lokaci nake ba kuma kai kanka zaka tabbatar da haka domin indai ina rayuwa to nine mijin pherty, kuma nine zan dawo mata da MARTABAR TA"

"Ahakan? You are very stupid, idiot"

Har ya juya zai tafi ya sake dawowa, "kar ka kuskura ka sake zagina dan zan iya daukar mataki"

"An zageka din, idiot ko zaka rama ne?"

Idonsa jawur ya kalleshi "kai kanka kasan a doke ba iya duka na zakayi ba dan ko fafatawa muka yi ba zakayi nasara ba akaina so be very careful" ya nunashi da yatsa sannan ya juya ya fice daga falon yabar Aadil a tsaye.




Ummi A'isha🏻
[5/5, 7:16 PM] Ummi A'isha🏻: [4/28, 8:49 PM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑


   Na
UMMI A'ISHA

26-30


~~~ Jawad yana fita Aadil ya dunkule hannunsa ya naushi iska "oh! My God", ya fada da karfi tareda fadawa kan kujera dabas ya zauna daidai lokacin Salima ta fito daga cikin kitchen ta zauna kusa dashi,

"Sahibi meke faruwa ne?"

Cikin kunar rai yace

"Babu komai"

"Da kuma sai naji kamar muryar jawad"

Shiru yayi bai bata amsa ba sakamakon tafarfasar da zuciyarsa keyi, aransa fadi yake "yaron nan jawad na fuskanci ya gama rainani amma zanyi maganinsa dan ni ba sa'ansa bane, a haifi yaron akan idona amma yazo yana kawo min raini?"

Dafashi Salima tayi tareda fara rarrashinsa tamkar karamin yaro duk kuwa da cewar bata da masaniyar abunda ya faru amma dai taga ransa a bace don haka ta fara kokarin mantar dashi bacin ran dake tare dashi.


******

Lokacin da jawad yabar gidan Aadil gudu kawai yake shekawa ya nufi sch din su Xarah wato state university gombe, yana zuwa babu jira ya shiga cikin makarantar a gaban auditorium yayi parking yana daga cikin motarsa a zaune, wani irin zugi yaji zuciyarsa nayi masa tabbas ko shakka babu yasan yana daf da kamuwa da ciwon zuciya.

Yana nan zaune cikin motar tasa kamar daga sama ya hangosu itada Sadiya sun fito karatu, da sauri ya bude motar ya fita ya nufesu, sai da gaban pherty yayi mummunar faduwa lokacin data ganshi, cikin dashewar murya yace da ita

"Zo ina son magana dake"

Yana gama fadin haka ya juya ya yi gaba, kamar wacce take tsoronsa ta kalli Sadiya tace "ina zuwa, bari nadawo"

Binsa tayi har wurin motarsa ta tsaya ta waje tana kallonsa cikeda alamun tsoro karara akan fuskarta,

"Gani" ta fada tana kallon wani wuri,

"Pherty"

Yakira sunanta cikin damuwa,

"Kina son ki hadani da dan uwana ko? Kina son hada yaki acikin familynmu ko? Aadil is my brother and i love him more than how you are think, so kar ki jawo abun da zaisa na tsani dan uwana, kar kisa nafara gaba dashi, tabbas idan kika auri Aadil kin gama da rayuwa ta kuma babu abinda yayi saura acikin rayuwata"

Kallonsa ta danyi ta gefen ido ga mamakinta sai taga yar kwalla acan lungun idonsa,idanuwansa sun kada sunyi jajur,

"Sai dai kayi hakuri jawad amma a gaskiya ni ahalin yanzu banida miji in ba yaya Aadil ba...!"

Cikin sauri ya balle murfin motar ya fito wata damka ya kai mata "ke me kike takama dashine? Am asking you dame kike ji? You are not serious pherty, ke kin isa ki auri wani namijin da ba niba? Kinyi kadan wallahi ni zaki aura"

Yana kaiwa nan ya sassauta rikon da yayi mata "pherty kar kiyiwa rayuwata haka, bai kamata ki rama abinda nayi miki ba ta hanyar auren dan uwana, haba pherty so kike ki kasheni ne? Wallahi indai baki aureni ba mutuwa zanyi i will die if you didn't marry me, pls save my life, pls pherty,pls, pls" kansa ya kifa akan kafadarta kwalla tana kokarin zubowa daga idonsa, ita kanta phertyn hawaye ne yake kwaranya daga idonta domin tasan tana son jawad so nagaskiya to amma bazata taba iya aurensa ba, dole ta auri aadil saboda wani dalili mai karfi,

Yakai mintuna biyu ajikinta yana shakar kamshin jikinta sannan ya dago kansa yana kallonta, "idan har na mutu ko kuma na fada cikin wani hali to ki zargi kanki"

Yana kaiwa nan ya matsa daga kusa da ita ya shiga motarsa yaja ya fita yana driving yana hawaye Wanda shi kansa bai san ko na menene ba, yana isa gidansu part dinsa ya shiga ya kwanta akan tangamemen gadonsa ya fara tunani "hakika pherty nasan na cutar dake, amma ki yafe min ki bani dama domin gyara kuskurena,pls and pls pherty" haka ya fada a hankali,

Juyi kawai yake ga wani irin ciwo da yaji kansa yana yi masa gashi yayi nauyi kamar an dora masa katoton dutse akan nasa, daren wannan rana yayishi ne cikin bakin ciki da tashin hankali.

  A bangaren aadil ma haka abun yake domin shima hankalinsa a tashe yake kwata kwata bashida walwala sai sakar zuci yake, dan haka koda Salima tayi bacci falo ya koma ya zauna yayi tagumi, yayinda bacci yayi kaura daga idonsa.


  Wannan dare darene mai cikeda fargaba, kunci, takaici, bacin rai ga mutane guda uku wato jawad, aadil da pherty, domin itama tun lokacin da jawad ya tafi ya barta take kuka dakyar su Sadiya suka sata tayi shiru, amma idonta kyamas babu alamun bacci.

  Washe gari da safe bayan aadil yayi wanka yayi breakfast ya shirya domin fita zaije yaga pherty sannan yaje gidansu, lokacin da yaje makarantar yana ganin pherty yasan akwai matsala saboda fuskarta duk ta kunkunbura alamun tayi kuka ta more amma tambayar duniya yayi mata taki fada masa gaskiya,

Kallonta yayi cikeda damuwa "pherty na ban sanki da haka ba, ada bakya boye min komai amma yau kin canza daga yanda nasanki"

Murmushi ta dan kakaro "yayana yau ma ba canjawa nayi ba, gaskiya na fada maka babu abinda ke damuna"

Kallo kawai ya bita dashi amma bai yarda da abunda ta fada ba sam,
daga karshe dole ya hakura ya tafi.

  Yana zuwa gidansu yayi parking din motarsa a gurinda aka tanada ya tasamma cikin gidan yana shiga ya hango jawad akan dinning yana yin breakfast shida Ummi, kamar kazar da kwai ya fashewa aciki haka ya karasa inda suke, durkusawa yayi ya gaida Ummi sannan ya mike yana kallon jawad wanda yayi kicin kicin ya hade rai, shi dinma aadil din ta ciki na ciki yake kallon jawad cikeda jin haushi, falo ya koma ya zauna yana jiran Ummi tagama tazo, shi kam jawad sai hararar aadil yake kasa kasa gudun kar Ummi ta ganesu.


******

Tun tafiyar Aadil pherty take faman kuka kamar ranta zai fita, cikeda damuwa pherty da Sadiya suka sakata a tsakiya,

"Pherty dan Allah kiyi hakuri, shifa auren nan ba mutuwa bace" A'isha tafada tana dafa kafadarta,

"Ni nafasa ma auren, shima yaya aadil din nafasa aurensa tunda abin hakane" tafada cikin kuka,

"Kinada hankali kuwa?" Sadiya tafada cikin razani,

"Wallahi da hankalina Sadiya, da hankalina,idan na auri yaya aadil zan haifar masa da matsala tsakaninsa da dan uwansa, zan jawo rikici a tsakaninsu wanda har sai duniya tayi ala wadai dani, haka auren jawad ma bazai haifar min da kwanciyar hankali ba domin idan na aureshi banyi wa yaya aadil halacci ba sannan nazama butulu wadda take mance alkairi hakan zaisa nan gaba mutane suji tsoron yiwa wani taimako domin idan sunji labarina zasu dauka kowa mai irin halina ne"

Cikeda mamaki dukkaninsu suka kalleta

"Bamu ganeba kin bamu abu a dunkule" Aisha tafada,

"Dan Allah ki daure ki warware mana ko mafi fuskantarki" Sadiya ta fada tana kallonta,

"Tabbas nasan zamanmu daku ban taba sanar daku labarina da matsayin yaya aadil agareni ba, to amma yau ya zama dole nasanar daku labarina wanda babu komai acikinsa face, gargadi, bacin rai, tausayi, ban mamaki hadeda ban haushi, labarina cike yake da sarkakiya da abun mamaki nagaske, ina so ku nutsu ku saurareni domin jin wannan labari nawa domin ina so ya zamo izina ga yanmata da iyayenmu mata"


Nutsuwa suka yi cikin mamaki sukace "muna sauraronki, amma kafin ki fara meye alakar aadil da jawad?"

"Aadil yayan jawad ne uwa daya uba daya, zaku fahinci hakan idan kuka biyo labarina"

"Muna sauraronki" suka fada a tare.


Masu karatu kun shirya jin labarin pherty?? Nidai Ummi Shatu na shirya, dani daku mubi pherty Xarah dan jin labarinta, gaisuwa gareku masoya masu bibiyar labarin.





Ummi A'isha🏻
[5/5, 7:16 PM] Ummi A'isha🏻: [5/1, 7:32 AM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑


     Na
UMMI A'ISHA

31-35


~~~ Kowaccensu gyara zama tayi ta nutsu ta fara sauraron labarin pherty wacce ta fara da cewa

"phertyma maitama Umar shine cikakken sunana asalin mahaifina dan gombe ne acikin wata local government da ake kira da kumo, muna zaune acikin unguwar tudun wada, mahaifina Malam Umar sunyi aure da mahaifiyata tun auren saurayi da budurwa kuma suna zaune lfy basuda wata matsala sai ta rashin haihuwa, duk zamansu shekara da shekaru basu samu haihuwa ba amma hakan bai Sa mahaifina kara aure ba,

Mahaifiyata malama Adama yar asalin gombe ce acikin karamar hukumar funakaye,sana'ar mahaifina itace kasuwanci kuma a unguwa shine na'ibin limamin unguwarmu kasancewar mahaifina mutum ne mai addini,

  Tun lokacin da aka haifeni na taso cikin gata da kulawa domin rayuwar gidanmu rayuwace ta babu yabo babu fallasa iyayena suna gudanar da rayuwarsu cikin godiyar ubangiji.

  Nayi karatuna na primary har nakai ga secondary gashi babu laifi nayi karatun addini daidai gwargwado.

   Tun daga makaranta har gida banida kawaye, kawata kwaya daya ce hawwa wacce muka taso tare sannan hatta makaranta tare muke zuwa. Lokacin da nashiga aji hudu a makarantar secondary a lokacin ne samari suka fara yimin caa gashi dai ba wani girma gareni ba sai dai kyawuna wanda ya fara bayyana a lokacin domin nafara zama cikakkiyar budurwa.

  A zahirin gaskiya nikaina nasan inada kyau daidai misali kuma inada kirar jiki mai daukar hankali wannan dalilinne ma yasa samarin fara bayyana min soyayyar su adai dai wannan lokaci.

Kamar kullum yau ma nadawo daga makarantar boko jikina sanye da uniform riga da wando jajaye da farin dankwali da farin hijabi, kafata sanye da takalmi sandal in banda yunwa babu abinda ke damuna domin da safe banyi kyakkyawan breakfast ba natafi kasancewar na makara,

  A gaggauce nashige gida duk kuwa da cewar naga wani saurayi sai bina yake amma ban saurare shi ba domin nagama gajiya, ko sallama ban iya yiba nashige cikin gidan "phertyma ya ko sallama babu" muryar mama najiyo daga cikin kitchen

"Mama nagaji ne ga yunwa wlhi"

"To ai maganinki kenan tunda kullum bacci kikeyi bakya tashi da wuri kinga kuwa ai dole ki rinka makara"

Daki nashige naje na tube uniform dina na dauro zani kawai na fito na nufi kitchen wurin mama, Ina zuwa na tarar ta tana jifan dan wake, "sannu mama" nafada ina kokarin jawo filet

"Sannu phertyma, an dawo, amma kin shanyo rana" mama tafada cikeda tausayina

"Wallahi mama yau ana kwalla rana ga zafi"

Dan waken na zuba na saka mai da yaji nan na zauna nafara durashi acikina,ina ci muna hira da mama acikin hirar tamu har korafin samarin dake yawan damuna nayi mata, amma sai tace babu komai Allah ya zaba min abinda yafi Alheri agareni, daf da zan gama cin abincin naji sallamar hawwa kawata,

  Dan waken na zuba mata muka shige daki muka kule "hawy nikam ina fama da jarabar samari, kema suna damunki haka?"

Murmushi tayi tafara gauraya dan waken dake gabanta tace "pherty ai kin san dama su samari haka suke da zarar sunga ka kusa gama makaranta sai subi su addabeka"

Baki na tabe na dubeta

"Hawy nidai gaskiya ko zanyi aure to sai nagama university saboda ni kinga ni kadaice a gidan nan banida yaya banida kani dole nice mai taimakawa su mama, gara ke kinada yayyu"

"A'a pherty nima fa ina son yin karatu saboda gaskiya karatu yanzu shine babban gata"

"Yawwa to kin gani, dan haka kuwa in dai zamuyi karatu to dole mu share samarin nan na zamani"

Yar dariya hawy tayi tace

"Ai dama hakan shine mafita"

Hirarmu muka ci gaba dayi har tsawon wani lokacin kafin hawy tayi min sallama ta tafi gida, gun mama nakoma na zauna muka fara hira.

  Haka rayuwata taci gaba da tafiya cikin farin ciki da kwanciyar hankali domin banida wata damuwa da haka muka shiga s s 2 komanmu nida hawy muke yi, ajinmu daya bencinmu daya, kuma koda yaushe agida muna tare.

  Lokacin da bazan taba mantawa ba shine lokacin da muka shiga s s2 second term har a wannan lokacin banida saurayi kuma ban taba son wani saurayi ba,bayan mun taso daga makaranta nake cewa hawy zata rakani kasuwa da yamma sai tace itama dama tana son zuwa akwai abunda zata siyowa mamansu, bayan nadawo gida nayi wanka naci abinci na huta wurin misalin karfe 3 na yamma na biyawa hawy gidansu anan nasamu yayanta nan ya fara tsokanata

"Kaga phertyn mama me kukan kitso"

Dariya nayi nace "kukan kitso sai kace hawwa"

"Ke me kike nufi, nice me kukan kitson?" Hawy ta fada daidai lokacin da take saka hijabinta

"Oho miki" nafada ina dariya, fitowa tayi muka kama hanyar kasuwa, cefane na iyowa mama sannan na siyo mana kayan amfanin gida, ganin kayan sun yimana yawa yasa na ce wa hawy mu ajiyesu in yaso idan mun karasa siyayyar sai muzo mu dauka mu tafi gida, wata sabuwar plaza muka je a bakin kasuwa, kuma da alama ma ko fara amfani da shagunan ba ayiba, "kinga mu bayar ajiyar anan" hawy ta fada tana nuna min plaza din,wurin mai gadin dake zaune awurin muka je muka bashi ajiyar sai yace mu saka daga dan ciki gudun kar tashi ya kamashi ga kayan awurin, daga ciki din muka saka muka koma cikin kasuwa.

   Bayan mun kammala siyayyarmu ne na dubi Hawwa nace "gaskiya sai dai mu nemi keke napep saboda kayan nan namu da yawa"

"Nima haka zan fada kika rigani phertyn mama" tabani amsa cikeda zolaya

"Kya karata dai hawwan mama" nafada ina dariya amma dariyata sai ta tsaya saboda ganin kayanmu a warwatse agaban wannan plaza din, wani matashin saurayi muka gani tsaye sai yatsina fuska yake yanata nuni da hannunsa sai kace wani bebe, sai alokacin na iya daga kaina na duba sunan plaza din JAWAD PLAZA haka aka rubuta da manyan harrufa,

"Kut, kan bala'i" nafada cikin jin haushi

"Wannan rashin mutuncin fa" Hawy ta fada itama cikin bacin rai,

"Kuyi hakuri kunji me wurinne yazo, kuyi hakuri yayana" mai gadin wurin ya fada yana kallonmu

Nanfa naji na kulu saboda hango always din da nasiyo ayashe ana gani, "waye me wurin? Shi ba acin arzikinsa?" Na tambayi mai gadin

"Kuyi hakuri kawai yara"

Bakin cikine ya rufe mu dukkanmu nida hawy saboda tsakanin nida ita babu mai iya zuwa ya dauki always dinnan dan kunya, "wallahi bazan hakura ba na fada cikeda masifa"

Wannan saurayin na gani ya nufo inda muke sai a lokacin na yi masa kallon kurulla farine jawur kamar kana taba fatarsa jini zai fito, yana sanye da doguwar riga jallabiya baka da wando jeans aciki, da hannu yake tambayar mu wai me ya faru yaga muna fada, "rainin hankali" nafada da karfi

"Ba yajin hausane yanmata daga turanci sai larabci, eh ai balarabe ne kuma bature" mai gadin ya fada yana washe baki

"Kar yaji din" nafada da karfi

"Yana ma ji, wulakancine kawai tsaba" inji hawy

Ganin munki kulashi yasa ya fara tambayar me gadin wai me ya faru nan yayi masa nuni da kayanmu da ya zubar mana, hannuwansa ya hada guda biyu ya dan risina a gabanmu alamun muyi hakuri, kayan yaje ya fara tattara mana, sai da yazo kan pad din sai ya jiyo yana kallonmu,dauke kaina nayi acikin raina ina cewa "dan iska kawai meye zaka wani kallemu" ina juyowa sai naganshi tsaye a gabana yana miko min ledar pad din "take, and am sorry queen" fuska na hade na bata rai na karbi ledar naja hannun hawy muka je muka deddebi kayan muka karasa bakin titi muna zuwa muka yi sa'a muka samu mai keke napep muka hau,har lokacin wannan saurayin yana tsaye yana kallonmu har sai da ya daina hangomu.

   Hannuna hawy ta dafa "yauma da alama kinyi sabon saurayi"

"Tab, wannan ya zama saurayina ai fada zamu rinka yi saboda naga kamar ya fiya iyayi"

"Irinsu ai sunfi, sune first class" tafada cikin zolaya, haka muka rinka hirarsa har muka isa gida.

  Tun daga wannan lokacin ba mu sake zuwa kasuwa ba har wurin sati biyu sai acikin sati na ukune sannan muka shirya muka tafi, kamar yadda muka saba kowacce tasha hijabinta dogo har kasa "phertyn mama wai mu meyasa ba zamu rinka irin wannan kwalliyar ba kullum mu kenan acikin hijabai" hawwa ta tambayeni daidai lokacin da zamu tsallaka titi,

"Kin San dai ko ana bidi'a bai kamata a yita agidan na'ibin liman ba ko?" Nafada ina murmushi caraf muka hada ido da wannan saurayin na rannan yana zaune akan farar kujera a bakin plaza dinnan,

"Kinga gayen nan na rannan amma karki kalleshi sosai kar ya gane maganarsa muke yi" na radawa hawy a hankali,

  Ganinsa kawai muka yi tsaye a gabanmu yana murmushi, "barkanku da fitowa yanmata" ya fada cikin harshen turanci,

Mamaki nafara araina wai dagaske wannan bai iya hausa ba? Na tambayi kaina, lallai kam dan gashinan dan gayu dashi nafada acikin zuciyata,

  "Yau idan kun yi siyayyar ku kawo na ajiye muku kunji?" Ya sake magana da turanci,

"Mun gode kuma zamu kawo" Hawy ta bashi amsa, fuuuu najata muka shige cikin kasuwa muna tafe muna fada sai faman masifa nake mata na kulashi da tayi, daga nan nace mata

"Wallahi idan dan yankan kaine babu ruwana iyakaci idan ya yanke kanki na kaiwa su mama labari"

Dariya ta fara shekawa sannan ta bani amsa

"Dadinta ma dai bani yake so ba balle har ya yanke kaina"

"Eh sai kifadi wanda yace yana so"

  Muna siyayya muna fada nida ita har muka gama dama fada sabon mu ne amma da yake kowa yasan kowa shiyasa baya zama na gaske da zarar munyi fadanmu kuma zamu ci gaba da hira,

  "Dan Allah hawwan mama ko ya sake tasowa karki kulashi" nafada ina rikeda hannunta

"Haba ta mama, wulakanci fa babu kyau, gayen nan wallahi sonki yake"

  Ban bata amsa ba saboda ganinsa da nayi ya taho inda muke

"Kun gama ne?"

Ya tambayemu yana kallona, nikam dauke kaina nayi, yayinda Hawy ta bashi amsa da "ehh"

"Nazo na kaiku gida?"

Nanma bashi amsa tayi da "ehh"

Yana tafiya dauko motarsa na harareta amma banyi magana ba ita kuma ta mayar min martani da murmushi

  Wata mota hadaddiya new end of discussion ya dauko baka mai kyau, gidan baya nabude zan shiga, hawy ta rikeni "karki bada mu mana, ki shiga gaba pls"

"Ke meya hanaki shiga gaban" nafada cikeda masifa nashigewata gidan baya, itama bayan ta shigo, muna tafiya suna hirarsu da hawy ni bana saka musu baki da haka har muka karasa unguwar mu, kasancewar ga gida ga gida tsakanin gidanmu da nasu hawwa yasa muka sauka a kofar gidansu ban tsaya jiranta ba na dauki kayan na shige gida, nan nabarta suna magana dashi.

  Ta dade awaje kafin ta shigo tana dariya "yau dai kin samu matsala a kwakwalwarki ko?" Na fada ina hararta "wlhi ras nake kawai keda saurayinki ne kuke bani dariya" ta fada lokacin da take zama kusa dani

"Saurayinki dai malama" na fada ina kallonta

  Zama tayi kusa dani ta fara yimin bayanin maganganun da suka yi dashi wai yana sona kuma zai zo gobe,

"Ke nifa na fada miki ba yanzu zanyi aure ba"

"Eh nasani phertyn mama to amma at least dai ace kanada wanda zaka aura a hannu ai da dadi, saboda kinga yanzu idan kika rike wannan kuna soyayya har ki gama karatunki, lokacin da kika gama sai ayi maganar biki kinga lokacin kun gama sanin halin juna basai an tsaya binciken halayen juna ba"

   "Eh maganarki gaskiya ce ta mama amma nifa kin san natsani fita zance gaskiya"

"Duk wannan mai sauki ne ku zaku tsara kayanku"

  "Shikenan tunda kince haka sai dai naga kamar baya jin hausa fa"

  "Eh ai daidai kenan" tafada tana dariya nan muka shantake har bayan magrib sannan ta rakani gida.


******

Washe gari bayan na dawo daga sch da yamma sai ga hawy ta shigo, adaki ta sameni ina kwalliya, "ke bakonki fa har yazo"

"Dan jaraba ko dan me?" Nafada ina dariya

"Dan Allah yi sauri muje"

"Sai kiyi kuma"

  Kaya natashi nasa wani material ash colour nasa farin hijab, muna fita hawy tace gani nan ta kawoni bari ta shiga gida, tana tafiya naji na takura kasancewar wannan shine karo na farko da na fito zance

  "Pherty my queen" ya fada cikin daddadar muryarsa
  Kallonsa nayi ta gefen ido yana sanye da bakar t shirt da bakin wando na jeans, gaskiya ya hadu ba kadan ba, hira yayi tamin duk kuwa da cewar maganar tasa a hankali yake yinta dan da alama bashida yawan surutu kuma bai da hayaniya,

  Ya dan jima sannan ya tafi, yana tafiya nashiga gidansu Hawy nafara bata labarin hirar da salim yayi min domin yace min sunansa salim dariya kawai take yi har nagama bata labarin

"Bana son wulakanci fa" 

  "Allah ya baki hakuri" ta fada tana dariya.


Tun daga lokacin soyayya mai karfi ta kullu tsakanina da salim, yanzu yana zuwa wurina duk bayan kwana biyu sai dai wani abu da yake daure min kai dashi shine yawan son taba jikina da yake yi,

Yauma kamar yadda ya saba zuwa yazo bayan sallar magrib, hijabi nasa nafita na sameshi zaune cikin motarsa, gaban motar na shiga na zauna,

  "Queen" ya fada yana kashe min ido

Dan murmushi nasaki

"King" nafada nima ina kallonsa

Hannu ya miko zai shafi fuskata amma sai na dauke kaina,

"Wai queen bakya sona ne? Kullum idan muna hira sai ki rinka kyamata"

  "Ni ban kyamaceka ba salim, lokacine dai bai yiba wanda zaka rinka taba min jiki"

"Yaushe ne lokacin?"

"Idan munyi aure"

"To ai kafin aure ma akwai taste before marriage"

  Kallonsa nayi cikeda kuruciya a tare dani

"To ai ni ban saniba"

Hannunsa yasa wanda yake baibaye da gashi ya kamo nawa hannun

"Ki kwantar da hankalinki queen bazan taba cutar dake ba, aurenki zanyi"

Hannun yakai kan fuskarsa ya fara shafar fuskarsa dashi in banda shock babu abinda jikina keyi wurin kamar mintuna biyar nace mishi zan shiga gida saboda abbana ya kusa dawowa daga masallaci kuma idan yazo ya sameni anan fada zai yi.

  Yana tafiya nashiga gidansu hawy na sameta, hannunta na janyo muka fito waje "hawy mutumin nan fa gaskiya dan iska ne" nafada ina kallonta

"Meya cemiki, maganar iskanci yayi miki?"

"Hawy nidai gaskiya zance ya daina zuwa saboda kullum fa sai ya rinka wani shasshafa ni yana kokarin sai ya rike hannuna ko ya taba jikina"

  Kallo na tayi kafin tayi magana muka hango abbana yana tahowa ganin haka yasa kowacce shigewa gida batare da mun karasa maganar ba.



Ummi A'isha
[5/5, 7:16 PM] Ummi A'isha🏻: [5/3, 5:52 PM] Ummi A'isha🏻: 👑MARTABA TA👑

   Na
UMMI A'ISHA

36-40


~~~ Koda nashiga gida naci abinci nayi sallah shirin kwanciya nayi amma koda na kwanta sai nafara tunani acikin raina shin me salim yake nufi dani? Nafarko dai ni agaskiya nafara tsorata dashi saboda yadda yake shafata idan muna hira gashi kullum bashida zance sai na ni kyakkyawa ce yasan yanda nake da kyau awaje aciki ma haka nake, abunku da kuruciya sai dai nayi murmushi nace nagode, da yake yarinta na damuna tuni na watsar da zancen nayi baccina.

   Da safe kamar kullum nayi shirin tafiya sch, ta gidansu Hawy na biya lokacin tana kokarin shiryawa, bayan mun gaisa da mamansu ne nafara yiwa Hawy masifa "kullum ke kike makarar damu, gaskiya sai kin taho" nafada lokacin da nake kokarin fita daga cikin dakin, "yi hakuri phertyn mama"

Juyowa nayi na kalleta "wannan sunan bazai fita daga mouth dinki ba ko?"

  Murmushi tayi "ai sunanne ya shiga bakina sosai"

Dariya nayi saboda tun ina karama aka lakaba min wannan sunan yan unguwa ko kwatance za ayi da gidanmu sai dai ace gidansu phertyn mama,

  Bayan ta gama shiryawa ne tafito muka dauki hanyar makaranta muna tafe muna hira,

"Yawwa phertyn mama maganar jiya tsakaninki da salim meke faruwa ne?"

"Um hawyn mama ai salim dinnan dai dan iska ne, abubuwan da yake min sun fara yawa gaskiya"

  "Meya ce miki?"

"Ai ba wani abu yake cemin ba ni kawai taba min jikin da yake ne bana so"

"To idan ya sake kokarin tabaki ki hade rai ki bata fuska kice ke bakya son haka"

"Na fada masa fa amma dai zanyi hakan"

  "Yawwa kiyi masa haka, kin san su irinsu sunada jarabar son taba mace gashi dai yace a mecca yayi rayuwarsa, amma baya tsoron Allah"

"Wallahi kam, Allah dai ya kyauta"

  Haka muka karasa makaranta muna tafe muna hirar salim.

  Yau ma da daddare salim yazo dan haka na shirya na fita, acikin motarsa yake zaune sai kamshi turare ne ke tashi yayi kyau sosai cikin farar t shirt da red din wando ya gyara sumarsa da sajensa, ahankali na shiga na zauna kaina akasa na gaida shi,

   Wani mayaudarin murmushi yayi min sannan ya fara kokarin matsowa jikina da sauri na dakatar dashi raina abace "salim meye wannan?" Nafada cikin fada,

"Sorry my queen wannan ai itace soyayyar kece baki sani ba"

  "Nidai ka bari gaskiya bana so"  nafada kamar zanyi kuka

  "Ashe bakya sona?" Yafada cikin fillanci

  "Ina sonka mana" nafada ahankali

"To tunda kina sona ai dan na tabaki babu damuwa, wannan abunfa shine son"

  Shiru nayi bance komai ba,hannuna ya kama na kwace,

  "Nidai ka daina gaskiya"

"Allah ya baki hakuri phertyma, amma daga yau bazan sake dawowa gidanku ba tunda abun hakane"

Hankalina naji ya tashi domin gaskiya ina son salim sosai,

"Kayi hakuri, wallahi ina sonka sannan kasan babu kyau mutum ya rinka taba mace in dai ba aure suka yi ba"

  Dan murmushi yayi "sai yanzu nagane abunda kike nufi, wato gani kikeyi kamar ba aurenki zanyi ba ko, tunda hakane ina komawa gida yau maganarki zan yiwa dad dina za azo a nema min aurenki a kawo komai gidanku in yaso kina gama karatu sai ayi bikinmu"

  Wani dadi naji ya shigeni yanzu kam nasan da gaske salim yana kaunata,

"Yawwa kaga haka yafi" nafada cikeda jin kunya, yan yatsuna naji ya kama

"Jarababbe ai bazai hakura ba" nafada cikin zuciyata.

  Sai da yagama mammatsa min yan yatsuna sannan ya tafi amma ni duk sai ban kawo komai ba araina tunda aure za muyi.

  Lokacin da nashiga gida abba na yana biye dani a baya yana shiga falonsa naji yana kwalla min kira, da sauri na tafi wurinsa,

"Waye wanda naga yanzu?" Tambayar da abba ya jefo min kenan

"Abba sunansa salim" nabashi amsa

"Meye alakarki dashi?"

Shiru nayi banyi magana ba,

"To daga yau kar nasake ganinsa a kofar gidana idan ya sake zuwa ki fada masa kar nakara ganinsa, idan aurenki zaiyi ya bari idan kika gama karatu sai ya fara zuwa, idan kuma bazai iya jiranki ba to Allah ya hada kowa da rabonsa"

  "Haba Malam ya za ai kace haka? Yaron nan dan arziki ne be kamata ka hanashi zuwa ba, kabarshi yaci gaba da zuwa har lokacin da zata kammala karatunta in yaso sai ayi bikinsu" mama ta fada tana tsaye a kofar daki

  "To me amfanin tarayyarsu tunda ba yanzu za ayi bikin ba? Akan me zai rinka zuwa wurinta mutukar ba yanzu za ayi bikin ba?"

  "Malam dan Allah ka kyale maganar nan haka" inji mama

  "To tunda yanzu na fuskanci kin fasa yin karatun idan ya dawo kice masa ya turo magabatansa muyi magana dasu in yaso kina kammala secondary sai ayi miki auren tunda haka kike so"

  "Sai tayi karatu zata yi aure amma dai ya turo manyan nasa" inji mama

"Dama yace yau zai fada agidansu kan azo a nemar masa aurena" nafada cikin tsoro kamar wata marar gaskiya,

  "Tashi kije" abba ya fada amma da alamu ransa ya baci.

   Tunda nafito nake jiyo musayar yawu tsakanin abba da mama abunda ya zame min sabon al'amari domin ban taba jin sunyi musu ba sai yau akaina, shi abba yana cewa yaron nan yadaina zuwa gurina har sai na kammala karatu ita kuma mama tana cewa a'a yaci gaba da zuwa, nidai kawai sai taintar kaina nayi cikin hawaye saboda sai naji hankalina ya tashi.

Bayan faruwar haka da kwana biyu sai ga yan gidansu salim da akwatuna guda uku masu kyau da tsada da kudi dubu dari biyu wai kayan angani ana so da kudin aure,mama ba karamin murna tayiba, yan unguwa sai shisshigowa suke suna kallon kayan, nikuwa ina can gidansu Hawy muna hira da ita, "phertyn mama kin fasa karatu kenan sai aure?" Ta tambayeni

"Waya fada miki? Zan yi karatu na mana"

"Tayaya?" Tasake tambaya ta

"Ta yanda zakiyi" na mayar mata da amsa

"To Allah ya kaimu lokacin"

"Amin"na amsa mata

  Tun daga lokacin da salim ya kawo wadannan kayan gidanmu tun daga nan salon zancenmu ya sauya ada idan ya nemi taba min jiki idan nace babu kyau yana yarda amma yanzu ko nace masa babu kyau sai yace ai yanzu ni matarsa ce aure za muyi, dan haka in kyaleshi, kullum sai munyi fada dashi akan wannan, yauma tunda yazo muke fada akan wai lallai dole sai nayi masa kiss nikuma naki,

  "Hmm wlhi yarinyar nan bakya sona kuma nagode"

  "Meya faru" nafada ina kallonshi

"Wlhi indai baki yimin kiss dinnan ba na hakura bazan sake zuwa ba"

  Shiru nayi nafara tunani, "yanzu pherty ashe ba zaki rinka yimin abinda zuciyata keso ba?"

  "Kayi hakuri"

"Indai kina so in hakura to kiyi min ko ki barni nayi"

  Ban bashi amsa ba nayi shiru ganin haka yasashi matsowa jikina, ban ankaraba naji lebensa kan nawa, ahankali ya fara kissing dina, akaron farko, abunku da abun shaidan sai naji na samu kaina cikin nishadi nan ya fara yi min wasu abubuwa wanda ban taba sanin su ba, mun jima sosai cikin wannan halin sannan ya matsa daga jikina yakoma kujerarsa ya zauna idanuwansa sun sauya launi, kafin mu rabu sai da ya gargadeni cewar kar na kuskura na fadawa hawwa kawata domin wannan sirrin mune wato sirrin mata da miji, nikuma a lokacin ina fama da kuruciya kawai sai na rinka yarda da abubuwan da yake fada min koda wasa ban taba fadawa hawwa abunda yake faruwa ba.

  Haka muka ci gaba da gudanar da soyayyarmu nida salim cikin wannan yanayi na tasting dan yace duk wadandan abubuwan acikin taste suke wai, da haka muka kwashe lokaci mai tsawo yanzu har takai nagama sabawa da salim bana jin komai dan ya taba jikina,a lokacin ya fara nuna kwadayinsa na son kebewa dani anan ne nikuma nayi turjiya nace sam bazan yarda, lallashi na ya fara yi wai ni kadaice fa gatanshi ni kuwa nace ga iyayenshi nan haka tun yana nacin har ya hakura.


Wata rana da yamma kwatsam sai ga salim wai yana son muje na gaida umminsu, da dafarko nace ba zanje ba amma koda ya yi min dadin baki sai na yarda naje nafadawa mama cewar za muje na gaida ummin salim, mama bata kiba tace amma kar na dade gudun kar abbana ya dawo bai sameni agida ba.


  Ko Hawy ban fadawa ba dan salim yace kar na fada mata baya son mu tafi da ita kuma ma wai ai ba komai zan rinka fada mata ba, haka na shirya naci kwalliya nasha shadda ja mai kyau dinkin doguwar riga nayi kyau das dani sai dai kallo daya zaka yimin kaga kuruciya karara akan fuskata.

  Komai ja nasa, haka kawai sai na samu kaina cikin faduwar gaba ga wani irin sanyi da naji jikina yayi, haka na fito daga gida nashiga motar salim mai mutukar kyau, shima yayi kyau sosai cikin ash colour din riga da jan wando jeans sai kamshin turaren midnight ne ke tashi daga jikinsa, wata faduwar gaba naji lokacin da muka hada ido dashi.




Ummi A'isha🏻
[5/5, 7:16 PM] Ummi A'isha🏻: [5/4, 3:41 PM] Ummi A'isha🏻: 👑 MARTABA TA👑

  Na
UMMI A'ISHA

41-45


~~~   Wata faduwar gaba naji lokacin da muka hada ido dashi, gashi zuciyata sai harbawa take da sauri da sauri haka na daure na kakaro murmushin dole na aika masa,

"My Queen ki saki jikinki naga kamar a tsorace kike" maganar da ya fada min kenan lokacin da ya fara driving, daidai lokacin da muka hau titi ya kamo hannuna ya rike ya fara driving da hannu daya,

"Ina sonki sosai queen, saboda kina da kyau, nadade banga Hausa/Fulani kyakkyawa kamarki ba"

Murmushin jin dadi nayi saboda yabona da naji salim yana yi,

"Kefa kina sona?" Ya tambayeni lokacin da yake kallon gefensa zai karya kwana,

"Uhm" nafada cikeda jin kunya

Hannuna yasake damkewa ya matsa tafin hannuna

"Banga alamun hakan ba atare dake, amma idan dagaske kike zan gani"

Shiru nayi bance komai ba,sai da muka danyi tafiya mai nisa sannan muka shiga cikin garin gombe kasancewar ban san cikin gombe sosai ba bazan iya tantance unguwar ba amma dai shiru unguwar take sai hadaddun gina gine masu kyau daga ganin unguwar ta masu hannu da shuni ce.

  Wani dankararren gida muka dosa, da kansa ya fita ya bude get din gidan sannan muka shiga gidan bayan yayi packing ne ya koma ya rufe gidan yazo ya kama hannuna zuwa cikin gidan.

  Da farko wani babban falo muka shiga hannuna rike cikin nashi, bamu tsaya anan ba yaja ni zuwa wani hadadden bedroom wanda yaji kaya na alfarma komai ja, abakin gado ya zaunar dani shima ya zauna,

"Ina ummin?" Na tambayeshi cikin tsoro

"Meyasa baki yarda dani ne wai? Nifa mijinki ne, wlhi queen nakasa daurewa har sai munyi aure, pls aid me"

Cikin tsoro da rashin fahintar inda zancensa ya nufa nace "salim meya faru?"

"Queen pls help me just one pls and pls"

Kallonsa nayi idonsa tuni har ya zama ja kamar wanda yasha abin maye

"Salim me zanyi maka?" Nafada a tsorace

"Pls pherty"

  Hannuna ya kama yajani zuwa jikinsa take jikina ya fara rawa, "karki tsorata queen u are my wife, don't reject my..." Bai iya karasawa ba saboda yadda ya shide,nan ya fara shinshinata tamkar wani zararre, nayi iya kokarina ganin na hanashi amma nakasa, ina ji ina gani ya rabani da kayan dake jikina amma har lokacin jikina rawa yake tamkar mazari.

  Idanuwana na kulle saboda ganin salim yana tube kayan jikinsa, ban taba ganin namiji babba ahaka ba sai lokacin, "innalillahi" itace kalmar da bakina yake fada lokacin da naji salim ya fara yimin wani salo yana juya ni son ransa.

  Tun ina daurewa har nafara kuka saboda zafin dake shigata,

"Daure queen" haka salim yake ta fada har ya samu ya cimma burinsa, shafata ya fara yana yimin kalamai masu mutukar dadi tareda kwantar da hankali.

"Queen wannan abun da yafaru tsakaninmu ina so kibarshi a matsayin sirri don't tell to any body, tsakanina dake ne kin gane, kiyi hakuri sannan har yanzu ina nan akan burina na sai na aureki"

Cikin kuka na daga kaina na kalleshi "yanzu nasan shikenan ka daina sona salim"

Dasauri ya rufe min bakina da nashi ya fara kissing din lips dina sannan a hankali ya rada min "wannan abun kara min sonki yayi, yanzu nema nasan ina sonki, ashe da ba so nake miki ba"

  Shasshafa min jikina ya ci gaba dayi har ya sake samun damar yin maimaici,

"Haba salim kaji tausayi na mana, da wahala fa" nafada ina hawaye

"Sorry nadaina"

Tashi yayi ya nufi toilet bai jima ba ya fito daure da towel ajikinsa, "queen muje nayi miki wanka"

"Kabarshi zanyi" nafada a hankali, daukata yayi ya kaini toilet, sai da ya fita sannan nasamu nayi wanka, duk jikina sai ciwo yake yimin hatta tafiyata ta sauya ganin haka kawai sai na fashe da kuka, da sauri ya shigo cikin toilet din,

"Queen what happened?" Yafada arude,

"Salim wlh idan abbana ya gane ina jin kasheni zaiyi, kaga fa tafiyata ma duk ta sauya"

"Sorry zakisha magani yanzu, sannan ki daure ki shiga cikin ruwan zafi, bari na taimaka miki"

  Karasa shigowa ciki yayi ya tayani nashiga ruwan zafi na fito, daukata yayi ya maida ni cikin daki nashirya nasa kayana, juice ya dauko min da magani yace indai nasha zanji dadi, karba nayi nasha nan take naji dan dama dama, agogon dakin na kalla karfe 6 daidai, kallon salim nayi

"Katashi muje wurin ummin sai ka mayar dani gida"

"Basai munje wurin ummiba saboda kinga dare ya fara yi kar abba yazo ya tarar bakya nan yayi fada tunda bai san mun fito tare ba"

Kai nadaga "to shikenan"

Tashi nayi nafara tafiya a hankali yana biye dani har muka karasa motarsa.

  Bayan mun fita daga cikin gidan ne ya kama hannuna yana yimin murmushi "Queen yau kin gama biyana, yanzu abinda ya rage kawai kina gama karatu sai ayi bikinmu"

Dadi naji ban ce komai ba, kasuwa muka shiga yayi min siyayyar kayan make up masu kyau da tsada sannan ya sai min waya mai kyau kirar Samsung yace gashi nan na boyeta kar nabari mama tagani ko Hawy zamu rinka yin waya a boye, kayan kuma nacewa mama Ummi ce tabani.

   Ana kokarin yin sallar isha'i muka isa gidanmu muna zuwa ya kalleni cikeda so yace "zanyi traveling amma dai za muyi waya, ki boyeta kinji?"

"To shikenan sai ka dawo" nafada tareda dibar kayan nayi cikin gida ina tafiya ahankali.

  Lokacin da nashiga Ummi tana salla dan haka na ajiye kayan a falo nashige daki naje nayi alwala sannan na boye wayar da yabani acikin akwatina nadawo falo nayi salla.

Bayan na idar ne na fara nunawa mama kayan, murna mama tafara 'ta karbeki hannu bibbiyu kuwa?". "Eh mama, ta karbeni sosai ma"

Dariya mama tayi "to ai gashi nan ta hadoki da kayan kwalliya yadda zaki tayiwa danta kwalliya" dariya nayi bance da mama komai ba muna nan zaune abba ya dawo, nan mama ta nuna masa kayan amma abba baiyi murna ba sai fada ma da yayi wai danme zan bi salim gidansu shi baya son wannan sakarcin kar nasake zuwa nan gaba koda wasa saboda wasu samarin suna amfani da wannan damar suna bata yara, ajiyar zuciya nayi jikina yayi sanyi sai a lokacin hankalina ya tashi. Ina komawa daki nafara kuka nadade ina kuka sannan nayi shiru na dauko wayar da salim ya bani na kunnata, massages dinsa ne suka yita shigowa rututu na kalaman soyayya daga karshe ya kirani mu kayi hira ya kwantar min da hankali cewar maganar aurenmu fa ta na nan kar na daga hankalina.

Tun daga wannan lokaci muke waya da shi a boye tuni har na warke daga abinda yayi min, kuma ko Hawwa kawata ban bari ta saniba. Bayan wasu lokuta masu tsawo kamar watanni biyu har lokacin salim bai sake zuwa gidanmu ba a cewarsa tafiyar da yayi har yanzu bai dawo ba mama ma tasha tambayarsa sai nace mata yayi tafiya ne.

  Kiba na danyi sannan sai nake jin kasala ga kwadayi da nake fama dashi, shinkafa kuwa a duniya ji nayi na tsaneta daga na ganta sai naji hankalina ya tashi. Yau da safe bayan nayi shirin sch mama tace min ga tea nan da wainar kwai, "mama bana son wainar kwan nan, idan naje sch zan siyi awara naci"

"Yau bakya son wainar kwan? To Allah ya kiyaye hanya sai kin dawo"

Fita nayi nabiyawa hawy muka tafi makaranta muna tafiya ina fada mata yau awara nake sha'awa gashi yanzu bana son ganin shinkafa, daga ni har ita bamu zargi komai ba da haka muka karasa sch.

   After first period second period na shiga malamin mathematics dinmu ya shigo, ina jin kamshin turarensa take naji cikina ya fara juyawa numfashina ya fara yin sama, da gudu na fita gaban class na fara sheka amai kamar wacce zata amayar da hanjin cikinta, hawy ce ta biyoni ta rikeni, sai kwara amai nake kafin nagama har na fita hayyacina hakan yasa hawy ta kira yan bencinmu suka taimaka mata suka kaini clinic din makarantar, nan aka kwantar dani aka fara kara min ruwa.

  Nadade ina bacci kafin nafarka duk bakina babu dadi, hawy tana zaune kusa dani lokacin an kusa tashi daga makaranta, antyn clinic dince ta shigo ta kalleni "sannu kin tashi? Kinada aure ne?" Ta bambayeni

"A'a" nabata amsa

"Yaushe rabonki da al'ada?" Ta sake tambayata

Tunani nafara yi rabona da period tun kafin salim yayi min wannan abun dan lokacin ma kwanana biyu da gamawa hakan ta faru

"Za akai 2 months" nafada ina kallonta

Kallona tayi sosai "akwai matsala kenan" tafada tareda juyawa har takai bakin kofa tasake juyowa tace "zaku iya tafiya tunda kinji sauki"

Tashi muka yi nida hawy muka fita lokacin an fito second break nan na hango mai wainar fulawa da sauri na kalli Hawy "Hawwa dauko min kudin break dina a aljihun jakata, ga mai wainar fulawa can, yunwa nakeji"

Tafiya tayi ta dauko nikuma nakara wurin mai wainar fulawar ina zuwa nafara ci ban jira hawy ba,sai da naci ta naira dari.

  Bayan an tashi daga sch ne nafara yiwa Hawy korafin rashin zuwan salim, kallona tayi "idan bai dawoba Allah ya kawo miki wanda yafishi"

Cikin razani na kalleta "hawy anya zan iya rayuwa da wani namiji idan ba salim ba? Ya rigada ya dandana min zumarsa a bakina hawy"

Hawaye nafara na dafa hawy

"Hawy ina son salim kuma bana fatan rabuwa dashi domin muddin idan na rabu dashi to kamar na rabuda MARTABA TA ne"

"Ban ganeba" ta fada cikin razani

Hannunta naja muka nufi karkashin wata bishiya nafara bata labarin abinda salim yayi min saboda bazan iya boye mata ba nakare labarin da cewa "da yana yimin waya akai akai amma yanzu sai dai ni na kirashi kuma kwata kwata yanzu ma wayar tasa ta daina shiga"


Kuka hawy ta yi sosai sannan tafara magana cikin hawaye "pherty meyasa kika yarda da zancen salim, meyasa baki fada min ba, meyasa kika bari ya cimma mummunan kudirinsa akanki, meyasa kika yarda yayi nasarar rabaki da MARTABAR KI?"

Ta jero min wadannan tambayoyin tana kuka,

"Hawy kidaina kuka aikin gama ya gama"

"Tashi muje gida da yamma sai muje wannan plaza din tasu ta kasuwa ko zamu sameshi acan" tafada tareda jan hannuna muka tafi amma har lokacin bata daina kuka ba.

  Da yamma hawy tazo tacewa mama mamansu ta aiketa kasuwa shine tazo na rakata, mama bata hanaba tabari muka tafi, muna tafiya take yimin magana "samarin nan fa basuda tabbas pherty"

"Hakane hawy amma lokacin da abun ya faru baki ga yadda ya rinka makalkale mun ba yana min wasu surutai ni banma san ko wanne irin yare yake yiba daga karshe yace zancen aurenmu yana nan bai fasaba"

"Ai mayaudari ne yasan yana son naki meyasa bazai bari har sai kunyi aure sannan zai karbi wannan abun ba, Allah yasa ma ba guduwa yayi ba" gabana ne naji yanata faduwa.

Lokacin da muka je plaza din babu kowa sai wannan mai gadin da muka taba bashi ajiyar kaya, bayan mun gaisa ne  sai hawy ta tambaye ina salim

"Wanne salim fa?" Ya tambayeta itama

"Wanda ya yi mana watsi da kaya"

"Auho jawad zakice ai, jawad ya dade bai zo nan ba dan akalla zai kai watanni biyu rabonsa da nan kuma yana kasar dan ko jiya da naje gidan nasu na ganshi"

Kallona hawy tayi muka hada ido tace "um baba inane gidan nasu?"

"Gidansu yana nan a new g.r.a acikin gombe"

"Amma baba ai ance yakusa aure ko?" Tasake tambayarsa

"Anya kuwa? Shi jawad bana zaton zaiyi aure nan da shekaru 4 ma saboda naga shi bature ne"

"Baba ko zamu iya sanin waye jawad?"

"Me zai hana yayan nan" zama ya gyara ya fara da cewa.


"Alhaji Habibu mai goro shine mahaifinsu, sana'ar mahaifinsu itace sayar da goro tun yana sayarwa acikin kasar nan har takai yana fita kasashen larabawa yana sayarwa acikin yawonsa ne ya auro mahaifiyarsu a kasar saudiyya, babarsu balarabiya ce, su biyune awurin mahaifan nasa daga shi sai yayansa Aadil mahaifinsu dan asalin cikin garin gombe ne, Allah ya bashi arziki mai tarin yawa ta sanadiyyar sayar da goro, tun lokacin da aka haifi jawad aka yayeshi ya tafi saudiyya acan yayi rayuwarsa baya zuwa sai lokaci lokaci, nikuwa nadade ina tare da mahaifinsu tun da kuruciyata muke tare, amma maganar gaskiya jawad bashida niyyar yin aure yanzu"

Hankalina ne naji ya tashi mutuka, tabbas salim mayaudarine kuma marar gaskiya tunda gashi harda boye sunansa na gaskiya,

"Mun gode baba" Hawy ta fada tareda jan hannuna muka fara tafiya, "kinji dai da kunnenki sunansa jawad ba salim ba,muje gida kafin musan abin yi gobe" nidai kasa magana nayi binta kawai nake har muka je gida, gidansu ta shiga bayan tayi min gargadin na kwantar da hankalina gudun kar mama ta gane.

  Ina shiga gida na iske wani tashin hankalin domin ashe bayan tafiyarmu kasuwa principal din sch dinmu yazo ya samu abba ya sanar dashi cewa ina dauke da juna biyu na wata biyu dan haka sun dakatar dani zuwa makaranta.

   A falo nasamu mama tayi jugum fuskarta sharkaf da hawaye abba kuwa sai fada yake ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba,

"Dama ni tunda naga yaron nan naji ban yarda dashi ba, gashi nan kin zuba musu ido yaje yayi mata cikin shege, to wallahi bari kiji, ni bazan zama mutumin banza ba, bazai yiyu ina na'ibin limami aga wannan danyen aiki agida ba, dan haka dole ne phertyma tabar min gidana ayau, kuma wallahi ban yarda taje gidan wani nawa ba, ke ko wurin wanda nasani taje ya taimaketa Allah ya isa ban yafeba"

Kalaman dake fita daga bakin abba kenan, da sauri na juya na nufi dakina na dauko wayar da jawad ya bani nafice daga gidan, tashar mota na nufa ko gidansu Hawy ban shiga ba, lokacin da na shiga tasha karfe 8 na dare, ina zuwa nabayar da wayar aka bani dubu uku alhalin kudinta yafi haka kawai dan sunga a matse nake ne amma ni nasan mai tsada ce, dakyar na samu motar da zata je gombe saboda babu passenger da yawa, saboda tsabar tashin hankali ko kukan ma yaki zuwa.

  Karfe Tara da wani abu lokacin da muka je cikin gombe ana saukemu nasamu mai keke napep nace ya kaini sabuwar g.r.a koda naje unguwar shiru take baka jin motsin kowa, sauka nayi na biya mai keke napep kudinsa sannan nafara tunanin yadda zan lalubo gidansu jawad, a karkashin wasu fulawoyi dake shuke akofar wani gida na makale, sai a lokacin naji kuka ya subuce min take nafara kukan bakin ciki.

Kwana nayi ina kuka har gari ya waye lokacin mutane suna wucewa jifa jifa masu zuwa office da masu kai yara makaranta dakyar nasamu ruwa nayi alwala nayi sallar asuba sai lokacin na tuna da cewar ko sallar magrib da isha jiya ban yiba,tashi nayi na fara neman gidansu jawad,sai wurin karfe 10 sannan na samu gidan, gidane mai mutukar girma da tsari kwankwasa gate din na fara yi ahankali mai gadin yazo ya bude min,

"Nan ne gidansu jawad ko?" Na tambayi mai gadin

"Eh nanne" hanya ya bani na wuce ciki, bin gidan kawai nake da kallo saboda tsaruwarsa ta isa, wani babban falo na shiga, ina bude kofar na hango jawad zaune daga shi sai three quarter baki da farar body hug yana yin tv game, daga can kuma wata matace tamkar balarabiya zaune tasha jan kunshi taci ado cikin koren lace tasha dauri tana lallatsa wata fankaceciyar waya,

"Assalamu alaikum"

Nafada lokacin da nake karasawa cikin falon

"Wa alaikis salam"

Matar ta amsa min, wacce kallo daya nayi mata na fahinci itace mahaifiyar jawad domin babu ta inda jawad ya barta, kamar su daya,

Ina shiga nasamu wuri na zauna, gaba ne yayi masifar faduwa saboda ganin irin kallon da jawad ya jiyo ya watso min, kallone mai nuna alamun ban sanki ba, ban taba ganinki ba sai yau,

Ahankali na gaishe da matar cikin sanyin jiki, na dan kalli jawad ta gefen ido wanda yafi mayar da hankalinsa akan game din da yake yi, nan na fayyacewa matar komai duk abinda ya faru tsakanina da jawad sai da na fada mata har kayan auren da ya kaimin da zancen cikin jikina,

"Jawad kasan wannan?" Ta jefa masa tambaya

"Ummi ni ban taba ganin wannan yarinyar ba sai yanzu" ya fada hankalinsa yana kan tv

"To kinji bai sanki ba, kila wanda ya kwatanta miki gidan bai kwatanta miki daidai ba, idan kuma wani ne ya turo ki dan ki bata mana suna agari to ki koma ki fada masa yakoma yabi wata hanyar"


Wasu zafafan hawaye masu dumi naji sun fara zarya akan kumatuna kamar an bude fanfo

"Jawad kaji tsoron Allah, ka tuna zaka mutu ka tarar da Allah, abinda kayi min nabarka da Allah shi kadai ne zai yi min sakayya"

  Kofa aka bude aka shigo, wani matashi nagani mai kamada jawad amma daga gani ya girmi jawad din,

Cigaba nayi da fadin "jawad ka cuceni ka rabani da MARTABA TA, ka rabani da iyayena ka rabani da mahaifata, to insha Allahu sai Allah ya saka min...!"

"Ke maza tashi ki fice min daga cikin gidana, ya zaki zo har gidana kina yiwa dana mummunan baki?"

Murmushi takaici nayi nace "danki ya aikata fin haka shi yasan duk abinda nafada babu karya aciki amma ki binciki danki saboda Allah ne kadai yasan yawan yanmatan da ya yaudara yayiwa ciki"

Kallon jawad din nasake yi bayan na mike "jawad zan shiga duniya da cikinka ajikina kuma zan haifeshi zan reneshi har sai yayi girman da zai nemoka ya kasheka" ina kaiwa nan najuya na fita ina zubar da hawaye zuciyata tana tafarfasa, shi dai wannan yayan jawad din yana tsaye cikin mamaki yana kallonmu, ina fita nabi lungun gidan nafara tafiya ga azababbiyar yunwar da nake ji, ko kadan bana ganin abinda ke gabana, ban ankara ba sai ji nayi na fada kan wani dutse take dutsin ya bugi gefen marata ta dama, wani azababben zafi nafara ji yayinda marata da cikina suka gauraye suka fara ciwo babu kakkautawa, wata kara nasaka daidai lokacin da naji marata ta murda jini ya fara bin jikina.




Ummi A'isha🏻
[5/5, 7:16 PM] Ummi A'isha🏻: [5/5, 5:36 PM] Ummi A'isha🏻: 👑 MARTABA TA👑

   Na
UMMI A'ISHA

46-50


~~~Wata kara nasaka daidai lokacin da naji marata ta murda jini ya fara bin jikina, juyowa tayi ta kalli Sadiya da A'isha wadda ko wacce acikinsu hawayene kawai ke bin kumatunta sun rafka uban tagumi,

"Kun san meya faru?" Ta tambayesu tana murmushin takaici

"Tayaya zamu sani alhalin baki fada mana ba" suka fada atare

"Amma meya biyo baya? Ni na kagu naji karshen labarin" Sadiya ta fada tana goge hawayen fuskarta,

"Zakuji ai amma ba yanzu ba saboda ko sallar azahar ba muyi ba gashi har lokacin la'asar yayi,kuma ni yunwa ma nake ji"

"Ai ni yau labarinki ya kosar dani dan ko yunwar ma bana ji" A'isha ta fada a hankali

"Hmmm duniya kenan kaji abubuwa iri iri, ku tashi kuyi salla ni tunda bayi zanyi ba sai na dafa mana indomie" Sadiya ta fada daidai lokacin da take tashi daga kan gadon, wurin da suke girki ta nufa domin dora musu abinci yayinda A'isha da pherty suka fita yin alwala.

  Bayan sun idar da sallar ne suka fara cin abinci, wayar pherty ce ta fara ringing tana neman agaji, dauka tayi ta duba, yaya aadil ne da kamar ba zata dauka ba sai kuma ta daga tafara magana a hankali

"Yayana"

"Pherty na yau shine bakya nema na?"

"Ayya yaya aadil bana son shiga hakkin anty nane shiyasa"

Murmushi ya danyi sannan yace da ita "kinaji da antyn nan naki kila ma idan kikazo gidan hade min kai zakuyi"

"A'a yaya" tafada tana dariya,"kaga zaka sani in kware gashi abinci nake ci"

"Zaki ci dani?"

"Why not?"

"To aci dadi lafiya" yafada yana murmushi.

Kashe wayar tayi tana dariya "kuji yaya aadil da tsokana ko a ina dadin yake, shi dan makaranta ai baya wani samun dadi"

"Mudai kici gaba da bamu labari kawai malama" Sadiya ta fada

"Gaskiya kam" A'isha ta sake fada,

"Hmmm to,tunda kun matsa bari nakarasa yanzu, tunda na fadi ban sake sanin a inda nake ba sai bayan wani lokaci sannan na dawo hayyacina, ahankali na bude idona,acikin wani daki naganni wanda abisa dukkan alamu dakin asibiti ne, gefena na kalla wannan saurayin nagani yana zaune yana jiran farkawa ta, koda muka hada ido dashi sai naji nafara hawaye, da sauri ya karaso gaban gadon da nake kwance "sannu pherty, kin tashi?" Ya fada da sauri, ban bashi amsa ba illa kukan da yaki tsayawa wanda nake yi ganin haka yasa shi juyawa ya fita da sauri.

  Jim kadan sai gashi shida wani doctor sun shigo tare, da sauri doctor din ya karaso inda nake "sannu, inane yake miki ciwo?" Muryata a dashe nace "gefen marata ne yake min ciwo sosai gashi ina ji kamar an anjiye min wani katon dutsi a wurin"

Kallon yayan jawad likitan yayi ya girgiza kai, "Aadil am sorry to say gaskiya yarinyar nan ta samu matsala sosai a mararta wanda ina tunanin idan ba wani iko na Allah ba bazata kara iya daukar ciki ba balle har ta haihu, ina jin gaba daya wurin yayi damage dan ko lokacin da na dauki hoton wurin naga yadda buguwar da tayi ya haddasa mata matsalar zubewar cikin jikinta, gashi kaga she's still bleeding, jini take fitarwa kamar zata karar da jinin jikinta"

"Pls doctor help me, pls and pls try your best pls..!" Wanda aka kira da suna aadil ya fada a rude

"Aadil am so sorry because i hv trying my best but abunne yafi karfina, duk wanda yace maka yarinyar nan zata sake iya daukar ciki to ya yaudareka ne kawai, saboda gefen mararta gaba daya ya tashi daga aiki, kai harta rayuwar aure ma dakyar idan zata iya saboda za arinka fama mata wannan ciwon da take tare dashine, but ga shawara guda daya ka fitar da ita kasar India kawai, ina jin idan Allah ya taimaka zata iya samun lafiya but is under probability" yana kaiwa nan ya juya ya fita daga cikin dakin,

Juyowa aadil yayi ya nufo inda nake kwance ina kuka mai tsuma zuciyata "yanzu shikenan ni ba mace bace?" Tambayar da naketa yiwa kaina kenan acikin zuciyata,

"Pherty" ya fada idonsa cikeda hawaye

"Kiyi hakuri kinji, nayi miki alqawarin zan taimaki rayuwarki har sai inda karfina ya tsaya, sannan ina son ki manta da duk wani abu wanda ya faru dake a baya, ki fuskanci rayuwar da zata zo miki nan gaba, kuma ki yarda da qaddarar data hau kanki, ki dauka hakan wata jarrabawa ce daga Allah subhanahu wata ala"

  Daga kaina nayi na kalleshi abin mamaki sai na ganshi yana kuka, hawaye suna bin kumatunsa,

"Nagode yaya Aadil amma karka wahalar da kanka wurin taimako na saboda mutuwa zanyi, ni yanzu ba mace bace, babu namijin da zai yi sha'awar aurena, jawad ya cuceni ya rabani da MARTABA TA, mutuwa yanzu itace tafi dacewa dani"

"Karki sake fadin haka pherty domin zakiyi sabo, babu kyau bawa yana nemarwa kansa mutuwa, kidaina yiwa kanki fatan mutuwa kinji, ki dauki kaddarar da Allah ya aiko miki da ita, nikuma da taimakon Allah zan yi duk iya bakin kokarina na ganin kin samu lafiya sannan zan dawo miki da martabar ki"


Idanuwa na narufe naci gaba da hawaye yayinda shi kuma ya fice daga cikin dakin da sauri, hannu nasa na shafo marata wadda ke radadi da zugi ga wani bleeding da naji ina yi kamar an bude fanfo.

   Ban sake ganin yaya Aadil ba sai dare, yana shigowa ya hada min tea ya taimaka min nasha, doctor yazo ya bani magani nasha ba tareda bata lokaciba bacci ya dauke ni. Kwanana uku a asibitin ina fama da ciwo kullum babu sauki, a kwana na hudu ne yaya aadil yazo da driver suka daukeni muka tafi airport lokacin ko tafiya bana iyawa, acikin jirgi ma ajikinsa ya jinginani nayi barci har muka je kasar India. Wani hadadden hospital aka kaini aka kwantarni nan manyan doctors suka taru akaina suna yimin aiki.


Nasha wahala mutuka domin bayan sun gama min aiki harda wankin ciki suka yimin da wasu karafa, bayan an gama aikin ne yaya aadil ya shigo cikin dakin nake, sannu yayi tayi min nan ya samo min abinci naci nasha magani, duk wata kulawa wacce marar lafiya yake bukata to ina samunta wurin yaya aadil shine ya rinka kulawa dani har na tsawon sati biyu amma har a lokacin zan iya cemuku har yanzun nan da nake baku labarin ina jin wannan ciwon a marata domin ba karamar buguwa nayi ba.

  Satinmu uku acan aka sallame mu babu laifi sunyi kokari domin nadan ji sauki da taimakon Allah amma sun bawa yaya aadil tabbacin cewa kila idan anci sa'a zan iya daukar ciki idan kuma aka yi rashin sa'a to ko rayuwar auratayyar ma bazan iya ba, haka dai muka tarkato muka nufo Nigeria tunda na dan ji sauki domin bleeding din da nake yi yanzu ya tsaya sannan ciwon marar ya dan lafa sai dai yana dan damuna daga lokaci zuwa lokaci.

Kafin mu baro kasar sai da yaya aadil yayi min siyayya mai tarin yawa sannan muka taho, tun acikin jirgi yake jana da hira yana son jin meya faru tsakanina da kaninsa jawad, dakyar na iya fada masa duk abinda ya faru daga farko har karshe,

"Kiyi hakuri phertyma, jawad bai kyauta ba sannan kuma wallahi agida ba asan cewar ya na neman aurenki ba, wannan kawai wani salon yaudara ne ya bullo dashi yaje ya nemo wasu suka kai kaya gidanku, amma kiyi hakuri insha Allah hakan zai zame miki alkairi"

"Allah yasa yaya aadil" nafada ina share kwallar data cika min ido

"Bana son ki rinka kukan nan kinji?"

Kaina na daga ba tare da nace komai ba.

Wurin karfe 3 na yamma muka sauka nan driver yazo ya dauke mu ya nufi unguwar riyal damu, wani madaidaicin gida muka shiga yafito yace mushiga ciki, wata yar dattijuwa muka samu zaune a falo tana kallo, "dada kin ganmu sai yanzu" ya fada yana murmushi,

"Ayya sannunku da zuwa, lale lale" tafada cikeda fara'a, wuri nasamu na zauna aka kawo mana abinci muka ci sai hirarsu suke da wannan matar, bayan yayi sallar la'sar ne yayiwa Dada sallama yace zai tafi nikuma ya kirani nabi bayanshi,

Adaidai bakin gate din gidan ya tsaya yana kallona "pherty zanje gida ke anan zaki zauna wurin dada amma insha Allah kullum zan rinka zuwa ganinki kafin nakoma abuja wurin aikina, yanzu zan tafi saboda naga antynki sai damuna take da waya kamar wanda na bata"


Kallonsa nayi "kanada mata ne?"

"Yes, shekarata biyu da aure haihuwa ce dai ban samu ba har yanzu, may be uwar yayan nawa ta kusa zuwa"

"Ayya Allah ya baka masu albarka yaya aadil, Allah yabaka masu jin kanka"

"Amin pherty na, nagode"

  Sai da naga tafiyarsa sannan nakoma wurin dada, haka zamana ya ci gaba da tafiya a wannan gida, kullum yaya aadil na zuwa safe da yamma hakanne ma yasa nayi mutukar sabo dashi muka shaku mutuka, bayan kamar dawowar mu da sati biyu ranar da yamma sai gashi yazo yana sanye da t shirt ja da bakin wando yasha turare, ina zaune a falo ina kallon wani Indian film a tashar zee aflam ya shigo film din ya tafi dani sosai musammam ma saurayin cikin film din (Luv story 2015) shine sunan film din,

"Sannu mai kallo" haka ya fada yana dariya,

"Lah yaya aadil sannu da zuwa" nafada nima ina dariya"

Zama yayi a kan kujerar dake kusa dani "ina dadan?"

"Tana kitchen tana yimana tuwo" nabashi amsa, sai ga dadanma ta shigo bayan sun gaisa ne ta koma kitchen,kallona yayi

"Dada fa kanwar babar dady ce uwa daya uba daya dan haka ki saki jikinki da ita kinji?"

Kai nadaga wlhi dama nagama sakin jiki da ita saboda bata da matsala ko kadan

"Yawwa to ni sallama nazo muyi saboda gobe abuja zan tafi, amma ya jikinki babu wata matsala ko? Kin daina bleeding din ko kinayi?"

Shiru nayi ban bashi amsa ba saima rufe fuskata da nayi da dan kwalina,

"Bazaki bani amsa ba? Shikenan Allah ya sawwake"

  Haka muka fara hira tsilla tsilla har magrib tayi lokacinne yayi mana sallama ya tafi.


  Washe gari kawai sai nasamu kaina cikin damuwa saboda rashin ganin yaya aadil sai kawai nafara kuka, dada tayi rarrashin duniya naki daina kuka, da haka har yayi sati daya da tafiya kullum cikin kuka nake ganin haka yasa dada yi masa waya ta fada masa, aranar sai gashi da yamma.

   Ina daki bayan naci kuka na koshi ko ruwa bansha ba bare abinci ya shigo ya sameni "haba pherty na"

Haka ya fada lokacin da yake shigowa cikin dakin,

Tashi zaune nayi nafara murmushi "sannu da zuwa yaya"

"Bazan amsa ba, tashi ki shirya nakaiki gurin antynki yau kuga juna"

Zumbur na mike na shiga wanka shi kuma ya koma falo, kwalliya nayi sosai nafito na sameshi shida dada zaune a falo, "ja'ira mai kuka kawai" dada ta fada tana dariya, muma dariyar muka yi yayi mata sallama muka tafi.

   A unguwar Federal low cost gidan yaya aadil yake, gidane tsararre wanda kana ganinsa kasan naira tayi kuka, lokacin da muka shiga cikin tamfatsetsen falon nasu daidai lokacin wata kyakkyawar mata ta fito daga cikin wani daki,

"Ko kanwar tawa ce yau tazo?" Matar ta fada tana fara'a

"Kamar kuwa kin sani itace, yau zakiga pherty na"

Murmushi tayi tazo ta kama hannuna shikuma yaya aadil ya shige dakinsa, zaunar ni tayi ta cikani da kayan cima kala kala,

"Kinga amaryarki yau ko?" Yaya aadil ya fada daidai lokacin da yake fitowa daga cikin dakin,

"Naganta kuma gaskiya ka iya zabe, she's very beautiful, cute, pretty and amazing" ta fada tana dariya, filitanci ya fara yi mata, itama tana mayar masa suna dariya har naji na tsargu,

"Ko zaki zauna da ita Gida daya pherty na? Nace ke abuja zan tafi dake tace wai a'a tafi son ku zauna tare"

Murmushi nayi a zuciyata nace au dama filatancin da kayi mata ce mata kake dani zakaje abuja,

"Ai muna nan tare da ita sai dai kai ka nemi ta tafiya abujanka" ta fada tana dariya,

"Ai kuwa wasa kike dan kafata kafar pherty na"

Abunsu gwanin sha'awa har dare nakai a gidan sai wurin 8 sannan yaya aadil ya daukeni muka koma wurin dada, washe gari sai gashi da kaya niki niki ya kawo min ciki harda wayar hannu mai tsada wai gashi nan sai mu rinka yin waya idan baya nan basai nayi kuka ba, haka yayi kwana biyu ya tafi tunda ya tafi na sake shiga damuwa danma dai muna waya.

Haka naci gaba da zama da dada duk karshen sati yaya aadil yana zuwa ganina, da haka yaci gaba da yi min hidima acikin rayuwata har yayi min cuku cukun karatu ya sama min admission a wannan university din bayan nasake paper, idan baku mantaba, ranar farko da nafara zuwa makarantar nan yaya aadil ne ya kawo ni karewa ma shine ya hadani daku lokacin da kuka fito daga hostel, yaya aadil yayi min komai na rayuwa yanzu kuma daidai lokacin da zai aureni sai ga jawad kaninsa kwatsam ya dawo da soyayyata wai shi zai aureni saboda shine first love dina"

Hmm tayi murmushin takaici ta dubi Sadiya da A'isha tace "yanzu ya dace naki aurar yaya aadil na auri kaninsa jawad? Ko kuwa ya dace na auri aadil nabar jawad fitina ta kunno kai cikin zuri'arsu? Ni pherty naga wani abu wai shi rayuwa"

Ajiyar zuciya Sadiya da A'isha suka yi atare "ina labarin gida,ina su mama da hawy kawarki?" Sadiya ta tambayeta

"Tun lokacin da na baro gida har yanzun nan da nake yi muku magana ban sake jin labarin gida ba"

"Hakane amma ni ina ganin auren jawad agareki shine alkairi" A'isha ta fada tana kallonsu

"Hmm A'isha kenan, Allah dai ya bamu mafita" pherty ta fada a hankali.


Masu karatu a naku ra'ayin waye yafi dacewa da ya auri pherty???


3 comments:

  1. Kawai ta aure jawad,tnk sis more grease to ur elbow

    ReplyDelete
  2. Thanks for sharing these amazing works. I'll make sure to read them through.
    hausa novel

    ReplyDelete