Thursday 5 January 2017

SANADIN GATA 1-End

ONLINE HAUSA WRITERS

SANADIN GATA


            Na
UMMI A'ISHA

JAN KUNNE-Duk wanda ya canja wannan labarin ko sunan taurarin ciki ko na marubuciyar Allah ya isa ban yafe ba.

Pg 1-10

~~Kanta dauke yake da farantin talla wanda aka kasa mata dafaffen rogo da gyada kulli kulli, taci damara sai kace wadda za tayi dambe tana tafe tana rera wakar ta"iye nanaye ayye yaraye nanaye carmama, ina tafiya ta jirgin goro zaya kade ni, jirgin goro kar ka kadeni, jirgin goro zan maka sako, sakon goro ko na turare in kaje kace da uwata, in kaje kace da ubana jirgi yai bari, jirgi yai bari da madaurin aurena, iye nanaye ayye ya raye nanaye carmama, da inna da baba an kawo kudin toshina cacas cas suna kirgawa, sun ganni suna boyewa in kun so kubar boyewa, auren fari sai na zaba sai na zabi wanda na ke so koda soja ko dan sanda, koda kuku koda boyi, koda jinjiri sha mama sai yaci tuwon kwanona sai yasha ruwan kwanona sai na kai ruwa sai nakai ruwa ban daki yai wanka, iye nanaye ayye yaraye nanaye carma....kuluwa, kuluwa kawo rogon, muryar wasu maza masu sai da ruwa ne ya hana kuluwa karasa baitin wakar da take rerawa, cikin sauri ta nufi wurin da suke, tana zuwa ta sauke farantin da ke kanta ta fara kukkulla musu kamar yadda suka saba siya, nan da nan aka warwashe ta dauki farantin ta cikin hanzari bayan ta kirga kudinta ta hada Kansu naira dari biyu cif cif, sauri take sosai dan tasan yanzu iyatu tana nan tana jiran zuwanta.

Tafiya take gudu gudu sauri sauri kamar zata bar garin har ta karasa gidan nasu wanda yake ginin kasa ne wato jar kasa, ciki ta karasa can ta hango iyatu kwance a tsakar dakin ta kamar yadda ta saba a kullum. Ta maza tayi ta tunkari cikin dakin ta shiga bakinta dauke da sallama agwasale iyatu ta amsa sallamar tata ta kara gyara kwanciyarta kafin ta wurga mata harara, tsugunnawa kuluwa tayi tace gashi iyatu na sayar na dawo, baki iyatun ta taba sannan tace miko min kudin na gani, mika mata kuluwa tayi ta karba ta kirga kudi sun cika cif cif ko kwandala bata bata ba, ungo wannan ki tashi ki tafi kasuwa kije ki iyo cefanen tuwon dare da zakiyi saura kuma ki tsaya a yawon da kika saba ki ga yanda zan rugurguje ki a gidan nan, yar masu da bakar zuciyar tsiya, tashi kuluwa tayi ta fita daga cikin gidan ta nufi kasuwa inda za ta iyo cefanen.

Wata azababbiyar yunwa take ji saboda rabonta da taci abinci ta koshi har ta manta yunwa take ji sosai, haka ta samu ta shiga kasuwar ta yi cefanen ta nufo gida, akan hanyarta na dawowa ne taci karo da mairo kawarta, kallon mairo tayi cike da sha'awa saboda sanye take cikin uniform din makarantar islamiya duk da cewa ita ma mairon tana talle to amma ita tana zuwa makarantar boko da islamiya sabanin ita da babu abinda take yi sai talle, daga talle sai aike sai aikin tsakar gida komai na gidan ita ke yinsa ita iyatu bata da abin yi sai kwanciya sai ko idan tayi wani abun na laifi ta jibgeta, cikeda tausayawa mairo tace kuluwa daga ina haka? Hmm mairo kenan ai kema kin san daga inda nake domin daga talle sai aika sune ayyukana ina son makarantar boko da arabi amma iyatu ta hanani karfi da yaji, gashi iyatu bata tausaya min ko kadan hatta baba bata daga masa kafa, dafa kafadar ta mairo tayi kiyi hakuri kuluwa kuma dan Allah kici gaba da hakuri da halayen iyatu saboda wata rana sai labari komai na duniya da kika ganshi mai wucewa ne, daga kai kuluwa tayi idonta duk ya cicciko da kwalla naira goma mairo ta mika mata gashi inji shamsu yace idan na ganki na baki, karba tayi tace nagode nagode mairo hakika shamsu ya cika masoyi cikakke saboda komai runtsi yana tare dani, murmushi mairo tayi hakane sai dai Allah yasa soyayyar taku takai ga aure, murmushi kuluwa tayi tare da juyawa ta fara tafiya tana murmushi wa ya ganni nida shamsu a matsayin ma'aurata? Ni kaina nasan za a zuba love ba dan kadan ba.

Gida ta tunkara tana shiga tun daga cikin soro ta fara jiyo hargowar iyatu wannan shegiyar yarinya tana kona min rai, wannan yarinyar kwai marar albarka, tun da dadewa na aike ta amma saboda bata ganina da mutunci shine taje tayi zamanta to wlhi bara ta dawo yau mai rabani da ita sai Allah, jikin kuluwa ne ya fara rawa saboda jin kalaman iyatu saboda tasan bata iya duka ba duk abinda ta samu kwada mata za tayi, da makyarkyata ta shiga cikin gidan bakinta yana rawa tayi sallama, ai iyatu na ganinta ta fara ruwan bala'i sai yanzu kika dawo? Nace sai yanzu kika dawo min? Saboda ke shashasha ce mai bakin hali shine kika je kika yi zamanki ko? Cikin in ina kuluwa tace wlh iyatu babu a inda na tsaya, zaki fada min a inda kika je kika zauna yanzu yanzun nan iyatu ta fada tare da daukar wani faskare ta nufe ta tana cewa kar ki kuskura ki gudu idan kika fita daga gidan nan sai na lahanta ki, kuka kuluwa ta fara yi ita kuwa iyatu ta nufeta gadan gadan, da gudu mahifinta ya fito daga cikin turakar sa yazo ya rike faskaren hannun iyatu yana cewa haba tsahare me yasa kike haka ne? Yarinyar nan kina gallaza mata, kina cutar da ita ki kiyayi ranar da sakayya za tazo wlh kiji tsoron Allah tsahare domin yawancin yaron da ka cutar shine yake zama wani abu a rayuwa,kuma irin su Allah yake daukaka wa, rufe min baki tsohon banza tsohon wofi, kai in banda ma hudubar shaidan ta yaya zaka zauna kana yabon wannan yarinyar har kana tunanin zata zama wata nan gaba, to ai ba irin wadannan Allah yake daukakawa ba saboda yarinyar nan ba yar arziki bace yar tsiya ce kuma wlhi in dai ta iyo cikin shege babu ruwa na sannan sai dai ta nemi wani gidan amma ba dai wannan ba, in sha Allahu hawwa'u ba zata yi cikin shege ba saboda ni nasan irin tarbiyar da na bawa yata, dakyau malam muhammadu, nace da kyau Malam muhammdu lallai yayi maka kyau wato saboda ban taba haihuwa ba shiyasa zaka yi min gorin haihuwa? Yayi maka dai dai babu shakka kanka ya fito daga kuttu kuma ka samu lafiya, nagode da ka daurewa yarka kugu tayi min rashin kunya a gidan nan sannan kuma ka nuna mata ban isa da ita ba dan bani ce na haifeta ba,to wlhi sai na dau mataki a kanku, ba dai da ni kake magana ba, yayi maka kyau, juyowa ga kuluwa tayi ke kuma idan kin ga dama kije ki dauko ruwa kizo ki dora abincin idan kuma baki ga dama ba ki barshi shashasha mai mugun yancin tsiya, bokiti kuluwa ta dauka ta fita daga cikin gidan ta tafi tuka tukar dake girke a filin gidan sarki, nan taje ta saka bokitin ta akan layi ta koma gefe ta zauna ta fara tunanin rayuwarta.

Ita kadai ce a wurin mahaifin ta, bayan ita bai sake haihuwa ba, Allah ya karbi ran mahaifiyar ta tun lokacin da ta haifeta domin a wurin haihuwar ta ta rasa rayuwar ta, tun lokacin da mahaifiyar ta ta rasu babanta ya auro iyatu domin ta riketa amma sai abin ya canja salo domin iyatu babu abinda take mata sai zalunci sam ba ta kaunar ta ko kadan asalima duk wanda ya nuna yana kaunar kuluwa to sai ta dau karan tsana ta dora masa, ayanda mahaifin ta ya bata labari mahaifiyar ta salaha ce mutuniyar kirki mai son jama'a sam duniya bata dame ta ba gata da rikon addini she is pious, religious, gata kamila tunda ta samu cikin kuluwa take fatan Allah yasa ta haifi yarinya Mace domin ta rada mata suna hawwa'u amma sai Allah bai yi zata zauna da yar tata ba. Iya babanta da iyatu kawai ta sani saboda bayan su ba tasan dangin mahaifiyar ta ba balle na mahaifin ta sai dai ako da yaushe mahaifin ta yana bata labarin cewar yana da yan uwa guda 2 a birni daya mace daya namiji, namijin yayan sa ne yayin da macen ita ce take binsa sunanta Salma amma ita bata taba ganin yan uwan nasa sun zo ba kuma yasha fada mata cewar yasan iyatu ce tayi surkullen ta irin nasu na mata ta raba shi da yan uwansa, wasu zafafan hawaye ne suka zubo daga idanuwan ta suka gangaro kan kumatunta saboda tausayin mahaifin ta da taji ya mamaye ta a hakikanin gaskiya mutum ne mai hakuri baya son fitina amma iyatu ta sako shi gaba da masifa har kuka ta ke sashi shiyasa itama taji iyatun ta fita daga ranta saboda tsanar da take nuna mata ga mugun bakin da take binta dashi kullum tsine mata take tana yi mata fatan cikin shege ga zagin mahaifiyar ta da take yawan yi alhalin ko zama ba su yi ba tare tunda sai da mahaifiyar ta ta rasu sannan aka auro iyatun.


Ummi A'isha©OHW


🔸SANADIN GATA🔸

       Na
UMMI A'ISHA

Pg 11-20

~~Ganin layi yazo kanta ne ya sata katse tunanin da ta keyi ta tafi bakin tuka tukar ta tara bokitin ta,ta debi ruwan ta kama hanyar gida tana zuwa ta tsinkayo iyatu tana  ta kai komo a tsakar gida sai yi take da bakinta me za ayi da dan riko? Ai dan riko jaraba ne kuma masifa ne saboda idan ka zuba masa ido ya lalace laifinka za a gani ace ka bar da ya lalace, idan kuma ka na yi masa fada nan ma baka tsira ba sai ace dan ba kai ka haife shi ba shiyasa kake takura masa, ai sharrin dan riko yawa ne dashi, sai dai kawai fatan samun sauki a wurin Allah, ni dai duk wanda yasa duniya ta zageni bazan yafe masa ba, karasawa ciki kuluwa tayi ta sauke ruwan ta fara hada wuta a murhu domin ta dora tuwon sayarwa yayin da ita kuma iyatu har yanzu ba ta bar bakinta ya huta ba sai masifa take ta yi, yo dama waye zai rungumi dan kishiya ai sai wawa shashasha saboda dan ma ko ka rike shi ba fita za kayi ba wani dan ma in mai bakin hali ne Allah Allah yake ya samu duniya domin ya wulakanta ka, sallamar maryama ce ta katse iyatu daga babatun da ta ke yi ita dai kuluwa iyatu har mamaki take bata saboda kwata kwata bata gajiya da surutu ga masifa idan aka yi mata abu ta kama mita wuni za tayi tana abu daya. Inda kuluwa take maryama ta karaso tana cewa kuluwa kinga har mun taso daga makarantar a hanya na hadu da shamsu yace nazo na kiraki, wa zaki Kira? Iyatu ta fada cike da fada to wlh daga yau babu ke babu gidan nan munafuka, dama ashe kece kike hure mata kunne ko? To maza zo ki fice kije ki ce masa ba zata zo ba kuma maza yaje ya nemi matar auran sa amma ba wannan marar asalin ba ehe, kallonta maryama tayi iyatu ni kuma me nayi miki? Daga shigowa ta zaki fada ni da fada kuma naga ai ni ba wani abu na cewa kuluwan ba da zaki ce ina zuga ta, ke maryama ni kike fadawa haka? Saboda tsabar baki da kunya ko, to tun kafin ranki ya baci ki bar min gida idan ba haka ba duk abinda ya biyo baya ke kika jawa kanki, juyawa maryama tayi zan bar miki gida amma ina so ki sani duk abinda mutum ya shuka shi zai girba tana gama fadin haka ta juya tabar gidan, take iyatu ta hayayyako ta fara bala'i tare da jan zaninta tana fadin bari naje na jawa uwar taki kunne kar na kara ganin kafarki a gidan nan tunda abin babu mutunci, nagaji da wannan cin kashin da ake min idan da saninta gwara naji, dagowa da kanta kuluwa tayi tabi bayan iyatu da kallo daidai lokacin da take fita daga soron gidan tasan halin iyatu sarai dama dan ta raba su da maryama da shamsu ne yasa ta takalar fadan, saboda ita dai duk wanda zai kaunaci kuluwa to ita kuma shine abokin gabarta,figar mayafin tayi ta fita tana ta ruwan bala'i ita kam kuluwa ko ba a fada mata ba tasan gidan su maryama ta tafi kai togaciya, haka taci gaba da hada wutar har ta kama ta dora tuwon sayarwar, mahaifinta ne ya fito daga cikin daki ya karaso in da take sannu kuluwa kiyi ta hakuri kinji, komai na duniya yana da iyakar sa shiyasa zaki ji kullum bani da magana sai kiyi hakuri domin shi hakuri baya baci kuma komai yayi farko zai yi karshe ni kaina kin ga hakuri nake da ita amma duk da haka bata barni ba, share kwallar idon ta tayi tace babu komai baba insha Allahu zan ci gaba da hakuri kamar yadda ka bukata, yawwa hawwa'u Allah yayi miki albarka ya baki kyakkyawan rabo duniya da lahira, amin baba tafada tana hawaye, to me ya naji kana sa mata albarka ni kuma sai ka tsine min ai, muryar iyatu suka jiyo daga soro tana magana cikin fushi, in banda munafurci meye zaka wani zo ka saka yarinya a gaba kana zagina a wurinta ko dan ka iya ha'inci sai nayi magana kuma ace ni masifaffiya ce to wlh na fara gajiya ehe, shi dai baban kuluwa sa kai yayi ya fice daga cikin gidan ya bar iyatu tana ta masifa wanda hakan ya zame mata jiki domin kullum wuni za tayi tana babatu a unguwar duk makota suna jinta sai kace ita kadai ce mata, juyowa ga kuluwa tayi tafara yi mata fada duk abinki dai ba zaki auri shamsu ba ke da aure sai dai kiga a nayi amma ba dai ke kiyi ba ita dai kuluwa bata ce komai ba taci gaba da girkin da take yi.

Mangarubar fari ta gama tuwon ta zuba a fanteka ta dauka ta nufi dandali inda a ka'ida can take kaiwa kullum da daddare, tana zuwa tuwon ya kare, kudin da shamsu ya bawa mairo ta bata ta dauka ta siyi abinci taci tayi kat, tana shirin harhada kwanukan ta ne mairo tazo inda take cike da damuwa akan fuskarta, kuluwa kinji abinda iyatu taje ta fada a gidanmu dazu? Girgiza kai kuluwa tayi me tace? Wlh kuluwa iyatu tayi duk wani rashin mutunci da kika sani tare da gargadin shamsu wai babu shi babu ke kuma baki ji zagin da tayiwa iyayen mu ba to shine mahaifin mu yace da shamsu kar ya kara kulaki, wasu hawaye ne suka gangaro akan kumatun kuluwa lallai iyatu ta gama nuna mata kiyayya saboda tunda ta rabata da shamsu ta gama da rayuwar ta,share mata hawayen mairo tayi tace kiyi hakuri kuluwa Allah yasa haka shine mafi alkairi, amin mairo nagode kuluwa ta fada tare da kinkimar kayanta ta nufi gida tana hawaye.

      A haka rayuwar kuluwa taci gaba da guduna cikin ukuba da matsati gashi kaf garin babu saurayin da yake zuwa wurinta saboda kowa tsoron masifar iyatu yake domin dama iya shamsu ne ya jajurce to shima iyatu ta raba su kullum kuluwa cikin kuka take mahaifin ta kuwa hakuri kawai yake bata acikin wannan halin ne aka sanya ranar bikin mairo wadda sai alokacin kuluwa taji hankalinta ya tashi saboda ita da mairo ne kawai suka rage gashi mairon ma zata tafi ta barta nan tabi ta rarrame har mahaifinta ya fahimta ya kirata yayi mata nasiha da cewa tayi hakuri in Allah ya yarda za tayi aure wanda za tayi alfahari da mijin, nasihar mahaifin ta tadauka ta dangana yayinda iyatu ita kuma ta samu nayi kullum habaici wai kuluwa tayi bakin jini bata da saurayi gashi shekarunta 19,kuluwa tun abin yana damunta har ta hakura. Yau da gobe babu wahala har lokacin bikin mairo yazo haka aka sha hidimar biki aka kaita dakin mijinta, bayan bikin da kwana 2 ne kuluwa ta dawo daga talla ta ratsa ta gidan mairo, tsayawa tayi tana kallon dakin mairo wanda yasha kwanukan silba da su dan cana ga gadonta mai runfa na karfe, Allah ya sanya alheri mairo kuluwa tafada kamar za tayi kuka dan tausayin kanta saboda ita tasan babu wanda zai yi mata wannan kayan domin babanta ba shi da hali, zaunar ta mairo tayi ta fara bata labarin irin bakar wuyar da tasha a daren farkonta nan da nan kuluwa tsoro ya shigeta take taji ta fara tsoron maza saboda wannan labarin da mairo ta bata saboda tace mata akwai wuya, yan kayayyakin ta ta dauka ta nufi gida tana tafe tana cewa lallai maza ashe abin tsoro ne, tana zuwa kofar gida ta ga wata dalleliyar mota mai kyau sabuwa dal, gidan ta shiga tana shiga taga iyatu a tsakar gida hankalin ta ashe kamar wadda yan sanda suka kama, jin sallamar ta ya sanya mahaifin ta fitowa daga cikin turakar sa ga wata mata kyakkyawa yar gayu a biye dashi, kallon kulawa matar tayi tace wannan ce hawwan? Lallai hawwa ta girma, amma nayi mamaki ace yarinya kamar wannan bata zuwa makaranta, babu komai Salma ai mun gama magana dake kuje kawai nagode Allah ya bar zumunci, kallon kuluwa yayi yace hawwa ga yar uwata Salma nan da nake baki labari yau tazo zata tafi dake birni zakije kiyi karatu Salma kanwata ce uwa daya uba daya dan Allah ki riketa a matsayin uwa, to abba kuluwa ta fada cikin farin ciki saboda zata bar masifar iyatu, cizon yatsa iyatu ta fara yanzu ina ji ina gani zata tafi da yarinyar nan ta zama irin ta? Inama na barta ta auri shamsun ta kare rayuwar ta a wahala ta fada acikin zuciyar ta, maza shiga ki dauko kayanki inji mahaifin ta, no basai ta dauki komai ba yar gayun ta fada tana murmushi, kama hannun kuluwa tayi tace to zo mu tafi hawwa nan fa iyatu ta biyo su kamar zata kurma ihu tana ji tana gani kuluwa ta shige mota ta dare luntsumemiyar kujera.

Ku biyoni masu karatu dan jin ci gaban labarin, hakika nasan za kuyi alfahari da wannan labarin na Ummi A'isha. [1/29, 10:19 PM] Ummi A'isha: 🔸SANADIN GATA🔸
             Na
UMMI A'ISHA

2⃣1⃣

~~~Wani bakin ciki ne ya turnuke iyatu take ta fara masifa tamkar wata zautacciya munafuki dama nasan wata kulalliyar ka kulla saboda yarinyar tana yi min talla tana dan samo min kwabo shine kake bakin ciki, to ai gani nayi dai hawwa yata ce ba taki ba ko? Kuma bake ce kika haifa min ita ba dan haka baki isa kiyi min iko da ita ba yana gama fadin haka ya shige cikin gida nan fa ta bishi tana cewa eh dama ai ka saba yi min gorin haihuwa dan yanzu kayi ba zan ji ciwo ba, shi dai baban kuluwa bai sake tanka mata ba saboda yau burinsa ya cika ya raba kuluwa da wahalar iyatu.

       *************
Gudu anty salma take shararawa a motar ta kamar ba mace ba saboda yadda take tuki babu tsoro a take da ita, sai da suka dan yi nisa sannan ta jiyo ta dubi kuluwa tace hawwa yanzu za kije Inda zaki samu sauyin rayuwa kuma insha Allah zan cikawa yaya burinsa na son yaga kin samu kyakkyawar rayuwa.



🔸SANADIN GATA🔸
             Na
UMMI A'ISHA

2⃣2⃣


Dadi ne ya ratsa zuciyar kuluwa saboda idan da abinda take so to karatu ne ita dai a rayuwar ta tana so ta ganta a makaranta tana daukar darasi, maganar anty salma ce ta katse mata tunanin ta, yaya ya fada min komai game da irin rayuwar da kike yi a hannun iyatu da duk irin tsangwamar da tayi miki, na rasa me yasa iyatu bata da halin kwarai ta dauki duniya ta riketa kamar ba zata barta ba, amma yanzu gashi ai kin tafi kin barta sai muga wanda zata takurawa, shiru kuluwa tayi aranta tace Allah sarki babana yanzu kuma shine zai jure jarabar iyatu tunda ni bana nan.

    Misalin karfe 3 na yamma su kuluwa suka isa garin kanon dabo tumbin giwa wanda masu iya salon magana su kance ko da me kazo an fika, kai tsaye unguwar sharada phase 2 suka wuce, kuluwa zare ido tayi ta fara kalle kallen abubuwan ban mamakin da suke cikin birnin saboda ko motocin dake wucewa abin kallo ne gashi dan adam kamar ba a mutuwa,


suna shiga unguwar kuluwa ta cika da mamaki saboda ganin irin gine ginen dake girke a unguwar kowanne gida ya hadu iya haduwa ga shuke shuke ta ko ina.
[1/29, 10:19 PM] Ummi A'isha: 🔸SANADIN GATA🔸
             Na
UMMI A'ISHA

2⃣3⃣


Manyan gidaje ne iya ganinka saboda unguwa ce ta masu hannu da shuni, kuma unguwar shiru take babu hayaniya gata tsit kamar babu mutane,


wani babban gida mai bene suka isa anan anty salma tayi hon cikin dan kankanin lokaci wani mai gadi yazo ya bude musu kofar gate din, kutsa kan motar tayi ciki taje tayi packing dinta a inda aka tanada, cikin gidan suka hara wanda yake katoton gaske gashi yasha ginin zamani sai kyalli yake, tana gama kuluwa na biye da ita a baya har cikin wawakeken wani falo wanda ya tsaru iya tsaruwa, kujera anty salma ta nuna mata tace zauna ina zuwa, nan kuluwa ta zauna in banda kalle kalle babu abinda take yi komai na falon bakone a wurin ta shiyasa ta tsaya take ta kallon fallon har anty salma ta fito ta kawo mata abinci ta bata. 

Abincin ta fara afkawa har ta koshi sannan ta samu nutsuwa, kallonta anty salma tayi hawwa kin san Ummi? Girgiza kai tayi, Ummi yata ce ita ma ba zaki fita a haife ba, tare zaku zauna a gidan nan saboda dama ni ba anan nake da zama ba, zuwa nake yi lokaci lokaci, yanzu ki taso muje ku gaisa da kishiya ta kafin ummin tazo.
[1/29, 10:19 PM] Ummi A'isha: 🔸SANADIN GATA🔸
               Na
UMMI A'ISHA

2⃣4⃣


Bin bayan anty salma tayi har zuwa wani hadadden sashe mai mutukar kyau da tsaruwa komai na ciki mai tsada ne,

wata farar mata kyakkyawa ta gani zaune a falo tana ganinsu ta fara fara'a da alama suna zaman lafiya da anty salman, zama kuluwa tayi ta gaida ta ta amsa fuska a sake kamar dama ta santa, maman ummi ga yar tawa wadda zasu zauna da ummi dan Allah idan anga tayi ba daidai ba a tsawatar mata, babu komai anty ai shi da na kowa ne, tashi anty salma tayi tace to zo mu tafi hawwa, binta kuluwa tayi suka fita daga bangaren Maman Ummi suka koma nata suna zuwa suka tarar da har Ummi ta dawo nan kuluwa ta saki baki tana kallon ummi wadda take yar gayu kamar yar India gata dai bata fita a haife ba amma ta iya tsara gayu, zaunar su anty salma tayi ta gabatar wa da kowacce  yar uwarta tare da dorawa ta hanyar cewa hawwa zan samo miki teacher wanda zai rinka yi miki lesson kafin ki fara zuwa makaranta murmushi kuluwa tayi nagode anty salma Allah ya saka da alkairi dama wlh ina son makaranta sosai, kiyi hakuri hawwa zaki yi kinji, to anty na gode. Kwana 2 da zuwan kuluwa ta dan goge tayi fes saboda yanzu bata aikin wahala komai yi musu ake yi sai dai kawai suci su sha su kwanta nan fa kuluwa ta fara hada kiba saboda samun jin dadin da take,

tuni anty salma ta nemo mata lesson teacher wanda zai rinka koyar da ita turanci da sauran subjects din da za tayi a makaranta, ita kuma ummi kullum tana zuwa school safe da yamma a halin yanzu tana ss2 zata shiga ss 3.
[1/29, 10:19 PM] Ummi A'isha: 🔸SANADIN GATA🔸
            Na
UMMI A'ISHA

2⃣5⃣


  Lokaci ne yaci gaba da tafiya da dafarko kuluwa ta dan fuskanci matsala wajen koyon harshen turanci amma koda ta dage ta maida hankali dandanan ta fara fuskanta kan Ummi A'isha ta ankare tuni kuluwa ta zama baturiya domin ita da ummi yanzu basa hausa komai nasu da turanci suke yi, ganin haka yasa anty salma zuwa tayi mata registration a wata private school mai suna sharada standard boys and girls school, ss 2 suka bata saboda tayi girma ta wuce asata a junior section, sai dai ba makarantar su daya da Ummi ba kowa tasa daban ita ummi inda take zuwa da nisa ita kuma kuluwa babu nisa domin acikin unguwar ne.


Tuni kuluwa ta fara zuwa makaranta uniform dinta riga da skirt ne maroon da hijab fari head tied dinma fari ne tun farkon zuwan ta tasaba da mutane tayi kawaye saboda yadda take da farin jini sai dai kuma wani lokacin ta kan shiga damuwa na rashin babanta a kusa da ita. Yau ma kamar kullum bayan sun gama breakfast dinsu da ummi kuluwa ta tashi zata shiga wanka, kallon ta ummi tayi hawwa yau ba zaki school bane? Zanje mana wanka kawai zanyi saboda bana son naje ina tsami a rainani, um to sai kin fito ni kam na tafi, uniform ummi tasa ta dauki school bag dinta ta tafi ita kuma kuluwa wanka ta shiga ta silla ta fito ta shirya tasha turare tasa wankakken uniform dinta kuma gogagge ta sabi school bag tayi hanyar makaranta tasha safa fara da farin combos  ga school bag dinta baka,

daidai kwanar da zata sada ta da makarantar su ta hango wata bakar mota hadaddiya mai black din glasses kirar KIA Rio, in banda tashin sautin music babu abinda kake ji yana fita daga cikin motar kai kace speakers aka doddora ma motar, motar tana zuwa saitin kuluwa ta shiga cikin wani ruwa wanda ke kwance a tsakiyar hanyar ya hadu da jar kasa yayi jawur, fatsalllll ruwan ya fantsama ajikin kuluwa gaba daya farin hijabinta ya wanke da ruwan kwatar ita kanta fuskar ta sai da ruwan ya jikata, tsayawa kuluwa tayi tana son ganin wanda yayi mata wannan aikin, kamar motar ba zata tsaya ba sai kuma taja ta tsaya a sannu aka bude bangaren mai zaman banza wani dan kyakkyawan sauri ya fito, baiwar Allah kiyi hakuri wlh muna sauri ne ya fada yana kallonta, haba malam wannan wanne irin abune kawai kuna driving without...  Rufe kofar motar yayi ya tako inda take kiyi hakuri dan Allah tsaki kuluwa taja amma gaskiya ba kusan mutuncin dan adam ba domin kun cuceni sai da na gama shirina tsaf har na kusa zuwa school zaku batani da kwata? Hon mai karfi aka matsa daga cikin motar da alama wanda ke cikine ya gaji da jiran na wajen, hakuri yaketa bata amma kuluwa ta rufe idonta taci gaba da yaba masa magana, shi kuma na cikin motar sai hon yake,yayi hon sunfi talatin ganin na wajen yaki zuwa su tafi yasa shi bude kofar motar a fusace ya fito, hmmm ni dai ummi A'isha guy din yayi mugun tafiya da hankali na, dogo ne dan madaidaici fatarsa chocolate colour ce tamkar dan kasar Ethiopia yanada dogon hanci gashi da manyan idanuwa kamar kwai idonsa yake saboda round eyes gare shi, gashin girarsa kamar na mace dan sunada yawa, lebensa jajaye ne sosai ga dan madaidaicin bakinsa, yana da dan saje a fuskarsa,kumatunsa na dama kuma dauke yake da beautiful point, ya tara suma him akansa kamar wanda za a kitsa, kunnensa guda daya yasaka earring fari, haka wuyansa ma yasa sarka fara yar sirirya, yana sanye da bakar riga mai gajeren hannu da shorts trouser iya gwiwar sa,

kamar wani wanda yaga kashi ya fara magana kamar me yin rada, bobo meye haka? Kazo mu tafi kawai kana bata min lokaci, wanda aka kira da suna bobo ne ya kalle shi sorry baka ga abinda muka yi bane? And so what? Me zaka yi mata? Zaka wanke mata ne ko kuwa? Ya fada yana yiwa kuluwa kallon banza,ganin haka yasa kuluwa fashewa da kuka, wlh ban yafe muku ba mamugunta kawai yanzu idan naje makaranta a haka dukana za ayi a wurin assembly sai dai na koma gida, kiyi hakuri yanmata bobo ya fada ba wani hakuri da zanyi wlh ban yafe muku ba,

shi dai classic guy dinnan na jikin motar tsayawa yayi kawai yana kallon ta wannan wacce irin shagwababbiyar yarinya ce? Dan kuka bashi da wuya kawai daga haka sai kuka? Maganar bobo ce ta katse shi JUNIOR ka bata hakuri tunda kaine ka bata ta, wannan ne kuma bata isa ba junior ya fada yana komawa cikin motarsa.

Masu karatu ku biyo ni dan jin waye junior. [1/29, 10:19 PM] Ummi A'isha: 🔸SANADIN GATA🔸
       Na
UMMI A'ISHA

2⃣6⃣


  Kara rushewa da kuka kuluwa tayi tace wlhi sai Allah ya saka min mugaye kawai, sake fitowa daga cikin motar junior yayi yace kai bobo wlhi idan ba ka bar wannan village girl din ba zan iya tafiya na barka ka tsaya sai wasting din time dina kake a banza, tahowa bobo yayi yana cewa double sorry my friend, juyawa kuluwa tayi ta kama hanyar komawa tana tafe tana kuka sai kace wata karamar yarinya, bobo yana shiga motar Junior ya fusge ta aguje kamar zai tashi sama yana driving yana bin wakar omalele, dan kallonsa bobo yayi yarinyar nan ta bani tausayi fa, sai kayi kuma junior yafada lokacin da yake kara gudun motar,kai tsaye unguwar jan bulo kubuga suka shiga dai dai first gate suka karasa wani hamshakin gida ginin dutse da dutse gida ne tangameme kuma katoton gaske very massive, tun daga kofar gidan ga wasu mopol nan da sojoji zaune suna ganin mai shiga da mai fita, kan motar junior ya kutsa cikin gidan,yana shiga yaje yayi packing dinta acikin jerin gwanon yan uwanta, ya fito shima bobo fitowa yayi yana cewa ya bahbah na jira ka ne ko naje kawai? Jeka kawai bobo i will call you letter, ok sai na jika, cikin mai falon gidan junior ya wuce yana tafe yana fito gamida wakar oh my Darling i love you! Da wannan wakar ya karasa cikin falon wanda yake unguwa guda mai karatu duk abinda ka sani na jin dadin rayuwa to an tanade shi acikin wannan falon,


mom dinshi ya hango zaune tana waya da wata fankaceciyar wayar ta tasha ado kamar bata manyanta ba, wani dandatsetsen leshi ruwan kwai tasa a jikin ta takafa dauri kunnenta da wuyanta yasha gold mai girman gaske ga zobuna data zubawa yan yatsunta da takalmi hill a kafarta golden colour, inda take ya karasa yana zuwa ya zauna kusa da ita gamida dora kansa akan cinyar ta, kansa ta fara shafawa kamar wani karamin yaro,muryar ta naji tana cewa hajiya yabi ki siyo min setin gold dan saudia guda daya amma ki hado da komai nasa ajiki ina nufin tun daga kan dan kunnensa, zobensa, awarwaron sa da sarkarsa amma bana son mai araha kuma dan Allah ki zabo na yanmata saboda wata girlfriend din junior ce za tayi birthday shine zai bata a matsayin gift, ok sai kin dawo, daidai lokacin ta kashe wayar ta ajiye ta akusa da ita ta fara lailaya sumar kan junior, junior whats happen? Nothing mom, ok har ka dawo daga wurin exercise din?


Mom na dawo amma zan kara yin wani now now yana gama fadin haka ya tashi ya nufi wani injin motsa jiki wanda ke girke acikin falon, hawa yayi ya fara motsa jikinsa har na tsawon mintuna 20 mom dinshi tana zaune tana kallonsa har ya gama.
[1/29, 10:19 PM] Ummi A'isha: 🔸SANADIN GATA🔸
            Na
UMMI A'ISHA

2⃣7⃣


   Sai da ya gama ya sauko daga kan gym din kai tsaye dakinsa ya wuce, junior ba kayi breakfast ba fa, zanyi mom kin san ban iya yin break da sassafe sai nan da 11 yanzu bacci nake ji saboda am too tired,to je ka huta maza aje ayi bacci, murmushi yayi ya shige dakinsa wanda yake kayace da kayan alatun more rayuwa, toilet ya fara shiga yayi wanka ya fito yazo ya kunna ac din dakin ya fada kan tafkeken gadonsa wanda ya isa mutum 15 su kwanta ba tare da takura ba domin gadon royal bed ne dan gaske, remote ya dauka ya kamo tashar wakokin turanci a tauraron dan adam ta cikin jibgegiyar plasma tv din dake kafe a bangon dakin nasa, kallo ya fara yi sama sama na wakokin da ake sakawa marassa kyan gani domin wata wakar ma mata ne tsirara suke rawa, yana cikin kallonne bacci ya dauke shi nan ya bararraje ya fara sharar baccinsa.


Ya dan jima yana bacci kafin ya tashi ya shiga toilet yayi brush ya fito, falo ya nufa yana zuwa yaga mom dinsa zaune ita da jawaheer  da gudu jawaheer ta taso tayi hugging dinsa tana sanye da riga da skirt matsattsu, rungume ta yayi tareda bata kiss a kumatu hy jawa yakike? Yaushe kika zo? Naje ai na ganka kana bacci, oh yeah ya fada tareda sakalo hannunta cikin nasa ya nufi wurin mom wadda ke zaune tana kallon su sai faman murmushi take, hannun jawa cikin na junior suka zauna kan kujera,bani labarin boyfriend dinki, ya sunanshi, kafadar sa ta dan doka, kasan ni ai ban fara soyayya ba amma kai bani labarin girlfriend dinka, ni? Ni ban da budurwa amma ina da girlfriends da yawa more than 100, dariya jawa tayi tace ai nasanka da farin jinin yanmata sai alokacin mom tayi magana ai junior kam girlfriends domin akwai ma wadda zata yi birthday next week kinga har gida tazo tayi inviting dinsa, dariya jawa ta fara wa yaga na mamajo, duka junior ya kai mata ta rike hannunsa ni dai ummi A'isha yau mamaki ya gama cika ni, kallon junior mom tayi junior baka yi breakfast bafa, mom ki barshi kawai na yi lunch anjima, what? Baka isa ba junior yanzu zan yi maka dura kamar yadda muka saba, wai mom har yanzu junior bai cin abinci sai kin dura masa? Ai haka yake jawa har yanzu, maza dauko min flask din farfesun nan na dura masa da sauri jawa ta mike zata tashi Junior ya jawota ta fado jikinsa, riketa yayi wlh babu inda zaki je yarinya.
[1/29, 10:19 PM] Ummi A'isha: 🔸SANADIN GATA🔸
           Na
UMMI A'ISHA

2⃣8⃣


~~~ Mom da kanta taje ta dauko abincin tazo inda yake ta tashi jawa ita kuma ta zauna ai tuni Junior ya bata fuska sai kace wani karamin yaro dan yaye mom ki barni Allah anjima zan ci da yawa, a'a my boy ka daure ka danci ko babu yawa kaji, pls junior yawwa maza bude bakin, naman ta yanko wanda yaji tumatur da albasa da tafarnuwa dakyar junior ya bude dan karamin bakinsa mom ta saka masa naman amma yana hadiyewa yaji zuciyarsa na tashi saboda shi baya son garlic kwata kwata, jin cikinsa yayi ya fara murdawa abunku da shagwababbe tuni ya fara langwabewa mom barshi haka my stomach... Mom karki kara min pls, cikin rudu mom ta kalleshi junior menene? Mom cikina ciwo yake duk yadda aka yi ansa garlic ni kuma bana sonta, a fusace mom ta danna inter come kamar zata tsaga gidan dan kara, aguje ma'aikatan gidan suka shigo cikin tsawa tace ina kukun da yayi girkin nan? Da sauri wani mai green din Kaya yace hajiya bata nan taje gida ta dawo, to yana dawowa ku turo min shi, juyowa tayi ga junior ta rikeshi ta kwantar dashi a jikinta tafara shafa bayansa tana jijjiga shi kamar wani yaron goye, sannu Junior jawa ta fada tare da matsowa kusa dashi, kamo hannun jawa yayi yace zaki iya yin driving ki kai mu country mall? Zan iya mana me zaka yi acan? Zanje ne naci abinci na siyo wasu abubuwan da nake bukata, ok tashi muje, to kije dakina ki dauko key din motar mana suna nan akan bedside drawer dina duk wadda yayi miki ki dauko, tashi jawa tayi ta nufi bedroom dinsa ita kuma mom taci gaba da yi masa sannu tana cewa junior zaka iya zuwa kuwa? Ko dai na aika a siyo maka, mom zan iya zuwa ai cikin nawa ya daina ciwon zanje ne kawai na siyo shawarma da dan fish gasasshe, to junior sai kun dawo, tashi yayi lokacin da jawa ta fito suka fita tare yana rike da hannunta domin shi junior ba wani abu bane ya rike hannun mace ko ya rungume ta harma yayi mata kiss duk wannan is nothing a wurinshi dan har ya saba duk lokacin da ya hadu da friends dinshi mata to hugging da kissing din gaisuwar su, suna fita wayar mom ta fara kara, a hankali ta daga tana cewa hello dadyn junior, yes maman junior ya kuke? Lfy lau, ina junior?
Junior yanzu ya fita zaije country mall shida jawa,
Yaci abinci kuwa?
Wlh dad junior yau baici komai ba,
Haba maman junior why ke ba zaki bashi ba tunda kin san shi ba ci zai yi ba,
Am sorry dad junior wlh na fara bashi sai cikinsa ya kama ciwo ashe abincin akwai garlic aciki shi kuma kasan ba ya sonta,
What? Yanzu yana ina?
Yaji relief har ya fita cin shawarma
Ok wanne kukun ne ya dafa abincin? Ki tabbatar kin sallame shi yabar gidan kafin na dawo,


To shikenan sai ka dawo, katse wayar yayi ya ajiyeta cikin fushi domin a duniya ya tsani abinda zai taba lafiyar junior, zai iya yi masa komai a SANADIN GATAN da yake nuna masa.
[1/29, 10:19 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

2⃣9⃣

Na
  UMMI A'ISHA

Su junior suna fita county mall suka nufa shi da jawa, ga wani kida da yake tashi tamkar a cinema ko kuma wurin wani kwarya kwaryar party suna tafe suna bin wakar har suka karasa, parking din motar jawa tayi tareda fitowa, hannun junior ta kama suka shiga ciki mutane sai binsu da ido suke duk inda suka wulga idone kawai yake binsu sai dai da yawa daga cikin mutanen wurin kama tun daga ma'aikatan su har masu siyayyar ba suyi mamaki ba kasancewar sun San ko waye junior, kallonsa jawa tayi junior what's all this eyes for? What's the meaning of this all looking?? Gaskiya yan garin nan naku akwai gyara har yanzu baku waye ba you are still villagers wlh, dan murmushi junior yayi, that's why I hate 9ja komai nasu abun kallo ne, yanzu dan na rikeki meye abin kallo?? Tsaki jawa tayi forget about them kawai, zagayawa suka ci gaba dayi har suka tsini abinda suke so suka koma wurin shan ice cream.

     *************

A bangaren kuluwa kuwa tana komawa gida ta kwanta taci gaba da kuka, kullum dama tana kewar mahaifin ta, amma yau sai taji tafi tunashi musamman wannan wulakancin da gayen dazun yayi mata, kuka tayi sosai sannan taji zuciyar ta ta dan nutsu yanzu ta danjita ta dama dama, to amma shi wannan guy din waye shi?? Dan gidan waye?? Hakan halinshi ne ko ita kadai yayiwa?? Dan rainin wayo,tsaki tayi tareda yin juyi, Allah sarki babana yanzu ko wanne hali yake ciki gameda masifar iyatu? Allah sarki kauyen mu, ko ina mairo da shamsu? Kila yanzu shamsu yayi sabuwar budurwa but still i love him,

da wadannan maganganun bacci ya saceta ba ita ta tashi ba har sai da Ummi ta dawo daga makaranta ta sameta tana bacci gashi wurin 2 ko salla bata yi ba, tashinta ummi ta fara, wake up jidda, zumbur ta tashi tana kallon ummi, har kin dawo ummi? Ni yau wani banzan gaye ne yayi min sanadin zuwa sch wlhi, shiyasa duk naji na tsaneshi tun lokacin dana fara ganinshi, zaro ido Ummi tayi hmm jidda ba ason a zurfafa a kiyayya kuma ba ason a zurfafa a soyayya domin duk wanda kaji ka tsana to at the end shi zakaji kana tsananin so, God forbid kuluwa ta fada lokacin da take sauka daga kan gadonsu, to shikenan tunda ba zaki yarda da abinda na fada miki ba, toilet kuluwa ta shige ba tareda tace komai ba
[1/29, 10:19 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA
            

Na
UMMI A'ISHA

3⃣0⃣

    Zama su junior suka yi shida jawa suna shan ice cream har suka koshi sannan suka tashi suka dauko hanyar dawowa gida amma duk da haka kamar tv haka mutane ke rakasu da ido saboda abun nasu sam babu tsari, shi junior daga shi sai wando iya gwiwa da wata body hug dinshi ga sarka a wuyansa,kunnensa na hagu kuma da dan kunne sannan ga wata suma kaya guda ita kuma jawa tasha wata atamfa super mai tsadar amma kuma dinkin fited gown ne wanda ya matsata tsam sannan ga wani dan ziririn mayafinta data dan yafa a iya kanta amma dashi da babu duk daya, hannun junior ta rike suna tafe suna hira tana dan kai masa duka ko kuma shi ya daki kafadar ta da haka suka karasa inda suka ajiye motarsu suka shiga suka fita suka nufi Gida, lokacin da suka isa gida mom bata cikin falon tana dakinta ta sake wanka da shiri cikin wani kyakkyawan leshi, kai tsaye dakinta junior ya shiga yana zuwa ya zauna ajikinta mom wai sai yaushe dad zai dawo?? Sorry junior ya kusa dawowa nan da gobe zai dawo kaji, gashin kansa ta shafa junior kaci shawarman? Mom naci amma yanzu zanje na dan buga kwallo afilin wasa na, tashi yayi kamar an tsikareshi ya nufi dakinsa jawa tana biye dashi kamar jela, yana shiga ya fara cire kayansa jawa tana tsaye tana jiransa babu ruwanshi da wai jawa tana tsaye tana kallonsa kawai wurin saka wandon ball dinshi ne yaji dan kunya yace jawa close you eyes pls, kaima ka cika problem tafada tareda fita daga dakin, wasu fararen kaya yasa wadanda suke gasu nan lodi lodi sababbi fil, riga da wando da abun hannu da wani dan faffadan hankicif wanda yake daurawa akansa, farin combos yasa da safa fara ya fito a bayan rigar tasa an rubuta junior da manyan baki, number rigar number 1 tun daga nan ummi A'isha ta gane junior dan kwallo ne naji da gani, kansa tsaye ya nufi tsakar gidansu acan ya nufi wani babban fili wanda aka tanadi wurin buga kwallo kala kala kama tun daga, handball, volleyball, football, table tennis, racket ball, basketball da sauransu, wasa ya fara bugawa shi kadai, handball ya fara daga bisani ya fara buga football har bobo abokinsa yazo ya sameshi suka ci gaba da bugawa tare. Washe gari da safe junior yana kwance yana bacci da misalin karfe 11 yaji alamun yar hayaniya agidan, ba dan yaso ba yatashi ya shiga toilet ya fito, kai bari anjima nayi sallar kawai ya fada acikin zuciyarsa tareda fita, dad dinsa ne ya dawo dan haka part din dad din ya nufa yana zuwa ya shiga dakinsa, suna tsaye shida mom tana cire masa babbar rigar sa, welcome dad, yawwa junior, zuwa yayi ya rungume dad din nasa, dad i miss you yafada cikeda shagwaba, kayi hakuri junior, dan murmushi junior yayi dad tunda kadawo ina son zanje abuja yau saboda tun jimawa akwai wata girlfriend dina da na jima ina yimata alqawari cewar zanje nayi mata weekend amma ban samu naje ba, no problem my boy ai sai kaje babu damuwa, dad ya fada cikeda rashin damuwa, dariya mom tayi kuma how many days zakayi junior?? Mom ranar Sunday zan dawo saboda ranar Tuesday zanje kd birthday din teemah, ok to amma junior banda sakaci da cin abinci pls, mom ta fada tana murmushi, dan murmushi junior yayi zan kula mom, juyawa yayi yafita ya koma part din mom yaje ya hau kan gym ya fara motsa jikinsa saboda shi dan ball ne koda yaushe cikin motsa jikinsa yake, sai da ya dan jima sannan yashiga dakinsa yayi wanka yafito ya dauki wata jar t shirt mai gajeren hannu yasa, ya dauki black din trouser ya sa, ya taje sumar kansa ya dauki chain yasa ya makalawa kunnensa earring,wani hadadden agogo samfarin bc yadauka ya daura a hannunsa sannan yaja wani takalmi mai mutukar kyau ja yasa a kafarsa. [1/30, 7:27 PM] Ummi A'isha: ®OHW


SANADIN GATA

Na UMMI A'ISHA

3⃣1⃣


Turaren imfact ya fesa ya fito hannunsa rikeda wayoyi manya guda hudu, daya wayar ya kara a kunnensa ya fara magana, hello bobo zo mutafi mana nifa na shirya, ok kana gidan? Ok, fita yayi ya nufi wurin bobo wanda ke zaman jiransa acikin gidan. Karfe 2 suka isa abuja kai tsaye unguwar mai tama suka nufa gidansu Lana girlfriend dinsa wadda ita ba musulma bace kuma iyayenta ma Christian ne sannan itama babanta mai kudine gata da kyau kamar ita tayi kanta, lokacin da su junior suka shiga gidan da gudu Lana tazo ta rungume junior ta fara kissing dinsa, riketa sosai junior yayi yana mai wani dan malalacin murmushi, Lana yakike ya fada yana kanne mata ido daya, hannunsa taja zo muje ciki junior, har cikin falon gidansu ta kaisu anan aka cikasu da cima iri iri harda su burkutu sai dai shi junior baya sha, abincin ma sama sama yaci, hannunsa Lana ta kama zuwa wani shiryayyen daki wanda ya tsaru iya tsaruwa, zauna ka huta junior nasan ka gaji, lumshe idonsa yayi ya zube akan gadon yes of course am tired Lana, zama tayi akusa dashi nasani ai saboda nasan halinka junior, sai dai har yanzu baka sauya ba daga tsautsauran ra'ayinka?? Haba junior kaifa big guy ne you are rich,young, handsome, famous,popularly and adorable guy, ka tsaya ka mori kuruciyar ka, agaskiya am very astonished da naji wai baka making love da kowacce mace, kallonta junior yayi tana sanye da wata yar karamar bakar rigarta iya cinya ko hannu rigar bata dashi, hannunsa yasa ya jawota jikinsa, Lana you are very beautiful and attractive, kamar jira Lana take ta fara shafashi, rigar jikinta ta zame da sauri junior ya rufe idonsa, pls Lana stop it, stop it Lana, don't remove it, Lana ba tareda ta saurareshi ba ta cire rigar ta cillarta can gefe ta makalkale junior,nan ta fara sarrafa shi kasancewar ta ba sabin shiga bace, amma shi junior sabin shigane don duk rashin jinsa da iskancinsa baya neman mata barshi dai da rungumarsu da kiss da rike hannunsu amma baya nemansu sai dai su ne suke nemansa, sai ko yan syrup da yake dan kurbawa saboda tsaro shi dinma ba koda yaushe ba sai dai in yaji ransa ya baci, kafin ya ankara har Lana ta gama tubeshi, tuni tafara nuna masa zulamarta a fili, abunku da sharrin shaidan nan junior yaji ya nemi tunaninsa ya rasa haka ya biyewa Lana suka aikata tabargazar su iya son ransu har na tsawon lukuta masu yawa,

    Kumatunsa Lana ta shafa, junior kace baka iya ba, gashi kuma you make me soo happy, murmushi junior yayi batare da yace mata komai ba, Lana gobe zan koma gida saboda akwai wani wasa da zan buga, cikeda damuwa Lana tace shikenan babu damuwa ni duk lokacin dana bukaceka zan zo, ko parents dinka zasu yi fada?? No, Lana mufa wayayyu ne hakama parent dina basuda matsala, wai dan kin kawo min ziyara ai is nothing, dadi Lana taji saboda dama ta dade tana muradin kasancewar ta da junior.

  Wayewar garin junior yabar abuja shida bobo suka dawo kano, aranar da suka dawo ya taradda dad dinsa ya siyo masa babban doki, nan fa junior ya hau dokin ya fara zaga unguwa, kowanne lungu na unguwar sai da yabi, bobo na biye dashi acikin mota ya kure sauti, haka suka wuni suna abu daya duk sun addabi mutane da tseren doki da mota, ga kidan da yaki karewa.
[1/30, 7:30 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA


3⃣2⃣


   Sai da yamma lis tayi sannan junior ya iya hakura ya koma gida yaje ya daure dokinsa daga nan direct dakinsa ya wuce yaje ya fada akan makeken gadonsa, ko takalmin kafarsa bai cire ba haka ya kwanta ya fara bacci. Mom ce ta nufo dakin domin dubashi tana shiga ta ganshi kwance yana bacci inda yake kwance ta karasa ta cire masa takalman dake kafarsa taja blanket ta rufe shi ta juya ta fita tana murmushi domin babu abinda take so irin taga junior cikin farin ciki da nishadi, tana zuwa falo taci karo da kawarta hajiya yabi, barka da zuwa mutanen jidda, mom ta fada tana murmushi, yawwa barkanki dai hajiya Fati, wuri suka samu suka zazzauna, momyn junior ga sakon naki ya iso sarkar da na siyo miki agaskiya mai tsada ce kuma ba ta kananan mutane bace, karbar sarkar mom tayi ta fara duddubata yar siririya amma da gani mai tsada ce, yawwa hajiya yabi dadina dake kin iya zabe, dama junior ne zai bawa wata girlfriend dinshi a matsayin gift saboda zata yi birthday ne next week, mom ta fada cikeda farin ciki, kallonta hajiya yabi ta danyi, ni kuwa hajiya fati sai nake ganin kamar abinda kike yi kuskure ne saboda su yara tasu kyau take bata karko domin duk yadda ka dorasu haka suke tashi, shi junior yanzu bai san rayuwa ba saboda baku koyar dashi ba, abin takaici ne ace wai kina goya masa baya akan yayi abota da wata ya mace wadda baki san ko wacece ba alhalin shi kuma yana baligi, hajiya Fati bafa ya mace bace kadai ke dauko abin magana ba wlh da namiji ma yana daukowa kuma ya kamata ki rinka bincikar abokansa saboda bada kowa zaki barshi yayi abota tunda har yanzu junior yarone karami bana tunanin ya wuce 27, take fuskar mom ta sauya bacin rai karara ya bayyana akan fuskar ta, hajiya yabi dama abinda ya kawoki kenan? Kinzo ne kici min fuska ki zage dana tatas? Daidai lokacin junior ya fito daga daki daga shi sai dan karamin blue din wando da rigarsa yar karama irin na yan ball, tsayawa yayi ba tareda ya kalli ko inda hajiya yabi take ba yace mom wai dan Allah wacce talkative din kika samune haka? Haba wannan matar ta cika surutu tun ina bacci take damuna har sai da ta tasheni, gaskiya ni ban son irin wannan mom, adaina tashina da surutu, cikin kwantar da hankali mom tace yi hakuri yarona, koma ka sake kwanciya kaji, mom ai kun riga da kun tasheni kawai, ni yanzu filin ball zanje.

   Yana gama fadin haka ya juya ya fita yana hararar hajiya yabi saboda duk maganganun data fada acikin kunnensa ne, duk ya jisu, yana fita mom tace hajiya yabi naji maganarki kuma nagode amma dan Allah idan babu damuwa daga yau kar ki kara zuwa gidana, yanzu bari na kawo miki kudin sarkarki, rike baki hajiya yabi tayi hajiya fati daga fadar gaskiya? Allah ya huci zuciyarki,ba tareda mom tace komai ba ta mike ta nufi dakinta mintuna kadan sai gata rikeda kudi rafa rafa sababbi fil, mikawa hajiya yabi tayi, gashi hajiya nagode, tashi hajiya yabi tayi shikenan hajiya fati ubangiji Allah ya sada mu da alkairi, amin mom ta fada lokacin da take barin falon
[1/30, 7:33 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

3⃣3⃣

    Junior yana fita ya dauki bicycle dinsa ja domin dama wani lokacin akan keke yake yawo, filin kwallon unguwarsu bobo ya nufa wato sharada, yana tafe yana jin kidan da ya kure acikin wayarsa ya cuccusa earphone acikin kunnensa, daf da wata kwana ya hango kuluwa, kunu yasha itama tana hangoshi tasha kunu ta bata rai, wucewa yayi ba tareda ya kalletaba, itama bata kalleshi ba ta wuce dama lokacin islamiyya zataje Kuma ita kadai take zuwa domin ummi ita tayi sauka tuntuni, filin kwallon kusa da gidansu bobo junior ya karasa yana zuwa aka fara ihu, saboda ganinsa, sauka yayi daga keken ya shiga filin wasan, take aka fara wasa mai zafi sai daf da magrib sannan suka bar ball din shi kuwa dama junior salla ba wani damunsa tayi ba saboda bai ma cika yinta ba, mota bobo ya dauka yake biye dashi shikuma yana kan keke yana kuma buga kwallo da kafarsa, dai dai kwanar dazu da yaga kuluwa yanzu ma nan ya ganota, da saninsa ya daki ball din da karfi taje ta doki keyar kuluwa da sauri ta juyo, ganin junior ya sata daure fuska, bobo ne ya bude motarsa ya fito, yauma an samu akasi matar junior, da sauri junior ya kalleshi what? God forbid me zanyi da bakar fata, wata harara kuluwa ta aika masa sannan tace ai ko Senior ne bashida wannan matsayin balle wani Junior, God forbid me zanyi da jan lebe? Tsaki junior yaja dalla bobo muje kar kasa wannan village girl din ta bata min rai a banza, gaka nan dan kauye tafada tana murguda baki.

    Kallo junior ya bita dashi, kiyi hakuri matar junior bobo ya fada yana dariya, kallonsa bobo yayi Allah kiyaye na auri yar kauye, ni ma babu abinda zanyi dakai, kudai yi hakuri domin ba asan inda rana zata fadi ba, a yamma saboda acan ta saba faduwa kuluwa ta fada tareda daukar hanyar gida, tana zuwa gida ta fara bawa ummi labari, ummi ina dan rainin hankalin nan na rannan dana fada miki? To yauma mun sake haduwa munyi fada, dariya ummi tayi your fighting partner?? Mijinki zaki cemin ai sai nafi ganewa, sai kiyi kuma, nama fasa baki labarin, kuluwa ta fada tana hararar ummi.

   Shi kam junior kekensa ya murza ya tafi ba tareda ya cewa bobo komai ba yana tafe yana jin wakar p square if do me i do you man......! Bobo kuma yana binsa har suka karasa gidansu junior anan suka rabuda bobo shi ya shiga gida bobo kuma ya juya.
[1/30, 7:40 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

3⃣4⃣

Junior yana shiga cikin gidan ya wuce falon mom Wanda yake tafkeken gaske, kan dining ya hau ya fara kokarin duba abinda zai ci, shinkafa ya diba yar kadan wanda ba zata fi cokali biyar ba ya fara ci ahankali, fuskar kuluwa ya hango lokacin da take musu masifa shida bobo "yi hakuri matar junior" maganar da bobo ya fada ta dawo masa cikin kunnensa," ni me zanyi da jan lebe" amsar da ta bawa bobo itace ta sake dawo masa, murmushi yayi shi kadai lallai wannan yarinyar itama tana ji da kanta, fitowar mom ce ta katse masa tunaninsa, junior whats it? Naga kanata murmushi kai Kadai, babu komai mom amma dai kawai yau babu abinda ke damuna shiyasa naji inata annashuwa, murmushi mom tayi to ga sarkar nan can an kawo maka wadda zaka bawa teemah gift din birthday dinta, tnx mom amma matar nan ta dazu ta bata min rai, meyasa mutane suke da munafurci ne mom? Nifa abinda ake min a garin nan ya fara damuna, wlhi matar nan ta dazu taci darajarki mom da sai na zageta, kayi hakuri junior, mutane sun sako min kai a gaba, na rasa me ka tare musu, tsaki junior ya danyi tareda tashi ya nufi dakinsa yana zuwa ya haye gadonsa ya dauki remote ya kamo tashar music ya fara kalla.

   Koda dare yayi kuluwa bata iya runtsawa ba, tunanin junior kawai take yi, kuma shi take ta hangowa a idonta, zaune ta tashi tabi ummi da kallo wadda ke ta sharar baccinta, junior dinnan fa daga gani ba shiryayye bane kuma ba nagari bane saboda yadda yake sa sarka da dan kunne kai idan ba sani ma kayi ba bazaka taba tsammanin musulmi bane saboda yadda  yake dabi'unsa da halayyar sa, kuma da gani bayaji sannan kuma gagararre ne, to ni yanzu meye nawa na tunaninsa? Ta fada acikin ranta, komawa tayi ta kwanta duk kuwa da cewar ba iya baccin zatayi ba, babu shakka junior ya hadu iya haduwa to amma anya zai so mace kamata wadda ta fito daga kauye?? Tambayar da tayi ta yiwa kanta kenan amma kuma bata da amsa.

  Abangaren junior shima hakan take domin koda ya kwanta domin yin bacci kasawa yayi, tunanin kuluwa ne ya addabi ruhinsa, hakika yasan ya kamu da sonta to amma taya zai furta mata? Shifa yanmata hadaddu ma sune ke cewa suna sonsa ba shine yake cewa yana sonsu ba, ruf da ciki ya juya yayi, yafara shafa keyarsa, tab wannan shine gamo ya fada ahankali, daren ranar da kyar ya samu bacci ya dauke shi,washe gari kuwa sai da yakai 11 akwance yana ta bacci, bayan ya tashi ne yayi wanka ya shirya cikin bakin boxer da jar t shirt mai hoton yan yatsu ajiki, tulin sumarsa ya fara tajewa da cumb bayan ya makala dan karamin dan kunnensa ajikin kunnensa na hagu sannan yasa katuwar sarkarsa wadda tsayinta yazo har kan kirjinsa, cumb din ya dauka ya nufi falo yana tafe yana taje sumarsa yana wakar if u see this baby o.oh she was chop my money, because i don't care, don't care, falon dad dinsa ya nufa yana mai ci gaba da tajar sumarsa, afalo ya tarar dasu dad and mom dinsa suna kan dining suna yin breakfast, good morning dad, mom good morning ya fada lokacin da yake Jan kujerar da zai zauna, morning junior, dad ya fada yana dafa kafadar junior tareda dan murmushi, har an tashi?? Dad na tashi dakyar saboda ina son naje na koyawa dokina tsere, bana son na barshi haka, yana da kyau ai hakan, dad ya fada, junior me zaka ci? Mom ta tambaye shi, mom ki barni yanzu babu abinda zan iya ci saboda koko kawai nake son sha, koko junior?? To ni yanzu ina zan samo maka koko junior?? Mom ki barshi bari naje na dawo, tashi yayi yafita zuwa inda dokinsa yake a daure, kunce shi yayi ya hau ya fito daga cikin gidan, yana fitowa yaci karo da bobo, nan bobo yabi shi a baya sukayi bayan layi, tseren mota da doki suka fara take suka hargitsa unguwar da hayaniya dan suna farawa yara suka taru suka cika da samari suna kallo, wasu yaran ma uniform ne ajikinsu suka ki tafiya makarantar suka tsaya kallo,ganin haka yasa malam ladan wato babban ladanin masallacin unguwar yazo wurin, tunda yaga su junior ne ke yin wasan yaji jikinsa yayi sanyi amma duk da haka dai sai da yayi musu magana, kallon hadarin kaji junior yayi masa kafin yace, malam ladan ai lokacin raba zakkar bai yi ba bare kazo min ko? Haba junior yanzu abinda kake yi a unguwar nan ya kamata? Kai Malam ladan wlhi ba don darajar tsufa ba da sai na zageka, junior ya fada yana masa kallon uku saura kwata, juyawa malam ladan yayi ya nufi gidansu junior domin sanar da mahaifansa, yana tafiya junior ya kalli bobo yace, bobo nifa koko nake sha'awa, wanne irin koko? Koko dai da kasani amma ba wanda ake damawa ba, to wanne irin koko? Kai banza ne wlhi baka ganewa, koko damun Allah, oh to ai yanzu na gane, to ba gobe zamu tafi kd wurin teemah ba ai sai ka sha acan, dan murmushi junior yayi hakane fa kuma kasan teemah big girl ce wlh, amma bari gobe tayi.
[1/30, 7:45 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

3⃣5⃣

  Malam ladan na zuwa gidansu junior ya sanarwa da jami'an tsaron ko shi wanene dan haka basu hanashi shiga ba suka bashi hanya ya wuce, har falon saukar baki aka kaishi, nan ya zauna ya jira har dad ya fito, bayan sun gaisa ne malam ladan ya fara magana kamar haka" Alhaji dama ba wani abune yake tafe dani ba illa wani abu da yake faruwa a unguwar nan game da junior, wani abun yayi? Abba ya tambaya, eh to agaskiya dabi'un junior duk ba masu kyau bane, kullum cika unguwar nan yake da kide kide da wake wake, sannan kuma ga tseren mota da na doki da yanzu yake yi mana acikin unguwar nan saboda ya raina kowa babu wanda zai yi masa magana yaji, dan haka Alhaji a kula da yadda junior yake gudanar da rayuwar sa domin acikin hadisi ingantacce manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace kowannen mu mai kiwo ne kuma za a tambaye shi akan kiwon da aka bashi, shugaba mai kiwone, magidanci mai kiwo ne zai yi bayanin yadda ya gudanar da dukkanin harkar iyalansa da tarbiyar yayansa, wannan ya hadar da yadda ya ciyar dasu ya tufatar dasu, yadda ya sauke nauyin dake kansa nasu, irin tarbiyar da ya basu da kulawar da ya basu, Alhaji sufa "ya"ya amana ce kuma wlhi kowa sai yayiwa Allah bayanin yadda ya tafiyar da tasa amanar wacce Allah ya bashi, yana da kyau iyaye su kula da tarbiyar "yayansu, su kula da irin abokan da yaransu ke abota dasu domin shi aboki yana taka muhimmiyar rawa awurin gurbata rayuwar yara saboda aboki yana da wani tasiri na musamman" tunda malam ladan ya fara bayanansa dad jinsa kawai yake domin shi a duniya ya tsani azo ace masa ga laifin junior,malam ladan nagode da wannan bayanin naka kuma daga yau kar ka kuskura ka kara shigo min gidana, tunda duk kokarin da nake muku bakwa gani, Allah ya baka hakuri Alhaji amma ni aganina gyara kayanka ba ya taba zama sauke mu raba, kuma malam bahaushe yace ka so naka duniya taki shi ka ki shi duniya ta soshi, will you get out from here ko sai na kirawo securities sun fitar dakai? Dad ya fada cikin tsawa, jiki yana rawa malam ladan ya juya ya tafi.

   Cikin Gida dad ya koma yana faman fada haba jama'a wai junior me ya tarewa mutane ne, kowa a unguwar nan idan ya budi baki junior zai ce kowa junior sai kace shi kadai ne d'a to agaskiya nagaji daga yau duk wanda ya kara kawo min maganar junior sai na daureshi, daidai lokacin mom ta fito dadyn junior what's wrong?? Wannan mutumin ne wai wai malam ladan yazo min da wata magana wai junior bashida da'a bashida halayya mai kyau, ni narasa me yasa junior mutane suka sa masa ido, ka kyalesu dadyn junior babu abinda zai faru da danmu duk bakin cikinsu, kama daina kulawa dasu. Ba ajima ba sai ga junior ya shigo, kallonsa dad yayi junior daga yau duk wanda ya kara tarar ka da wata magana ka zazzage shi komai girmansa ni nasaka, dad ai ni ina dawowa ma daga bufday din teemah zan bar kasar zan koma sch saboda nagaji da yan sa idon nan, gara ma ka tafi yafi sauki, mom ta fada tana kallonsu.

   Washe gari da safe su junior suka tafi Kaduna birthday din teemah, awani shahararren hotel Kings palace aka shirya birthday din wanda manyan yarane kawai suka halatta, yanmata gasu nan burjik cikin shiga ta alfarma riga da wando ko riga da skirt wasu kuma doguwar riga, shi kam junior sanye yake cikin wata t shirt black & yellow mai tsada ga wata top da ya dora asama, black din trouser yasa, ga dan kunne ga sarka, yasha face baki sai shan kamshi yake, bobo yana kusa dashi, bayan an zazzauna ne sai ga teemah wadda ta sha kwalliya cikin wata hadaddiyar gown ja mai hannu daya, daga saitin cibiyarta an dan yanke wurin Wanda kana iya hango cibiyar ta, haka ta gaba an tsaga rigar duk cinyarta awaje take, ga kanta babu ko dankwali sai wani gashinta ta yankoshi ta gaba, tana shigowa aka saka tafi tareda sakin kida, kanta tsaye ta wuce kujerar da junior yake zaune ta kamo hannunsa ya taso suka fito tsakiyar fili, tuni aka sakar musu kidan oya shake body. [1/30, 7:53 PM] Ummi A'isha: ©ONLINE HAUSA WRITERS

SANADIN GATA

Na UMMI A'ISHA

3⃣6⃣

     Kowa acikin hall din sai da su junior suka burgeshi especially ma shi junior ya tafi da hankalin yanmata da yawa saboda ya hadu iya haduwa, yayi tako ina kyawunsa ya bayyana afili, sai da suka dan chashe sannan aka je wurin yanka cake, hannun teemah junior ya kama suka yanka cake din ya saka mata a baki, yankowa itama tayi ta mika masa, cikeda yanga ya dan bude bakinsa tasa masa, nan aka fara tafi raf raf raf, wani kidan aka saki wanda yanzu kowa da kowa ne ya shigo filin aka fara dancing, tuni filin ya rincabe gashi dama har duhun magrib ya bayyana sai da aka sha rawa iya rawa sannan wutar wurin tayi dif! Numfashi kawai kake ji yana fita sai ko motsin mutane.

  Acikin duhun junior ya kamo kugun teemah zuwa jikinsa, a hankali ya fara magana, baby ina son koko ne fa, cikin wata irin murya yayi maganar, ita teemah bata iya bashi amsa ba saboda jin da tayi yana shafar kirjinta, mannata ajikinsa yayi, ya fara kokarin fitar dasu daga cikin hall din, mutane suka rinka ketarawa suna wucewa har suka fita suka nufi bedroom din da junior yayi masauki acikin hotel din, suna shiga ya dan kalleta, kamar wacce tasha giya sai layi take yi a tsakar dakin, kan gado taje ta fada, takalmin kafarta junior ya cire sannan ya matsa kusa da ita, baby ya za ayi?? Lumshe idonta tayi, kawai kazo kasha kokon ka, ka manta da batun condom ai nasan kai ba kowacce mace ce zata samu kayi making love da ita ba, rungumeta junior yayi tareda zame rigar jikinta, baby bakida abubuwa fa why ba zaki shiga kanti ba? A ghana ana sayar da breast enlargement cream in dai nakoma i will buy it for you, ita dai teemah bata bashi amsa ba saboda ta gama zurfafa, nan fa junior ya fara sarrafa ta babu ji babu gani.

Tsawon lokacin suna abu daya kafin su dawo hayyacinsu, kallon teemah junior yayi ganin tana bacci ya sashi tashi daga shi sai gajeren wando yasa riga ya fice daga dakin, dakin bobo yaje ya fara bugawa, Jim kadan bobo ya bude ya baabah ya akayi ne?? Bobo zai yiyu mu koma kano a yau?? Meya faru? Bobo ya tambaya cikeda mamaki, bobo nifa na fada maka koko nake so kuma wlhi har yanzu ban ji na koshi ba, to ina teemah take yanzu?? Gata can adaki mana, to ka bari gobe da safe sai mu tafi yanzu kaje ka kula da teemah, ok, junior ya fada tare da juyawa ya koma dakin da teemah take.

    Lokacin da gari ya waye sai lokacin teemah ta tashi ta kalli junior yana ta bacci, kiss ta mannawa lebensa tare da sake rungume shi, murmushi ya saki idonsa arufe ya fara shafar na shanunta, teemah zan koma Kn yau saboda sch zan tafi acikin week dinnan kuma akwai wasan da nake son bugawa da zarar na koma ghana, daga kai teemah tayi babu damuwa zanzo sch din naku ai, dagaske?? Dagaske mana,ok ki bari kawai ni zanzo sch dinku weekend kinji, kai ta daga, dakyar suka iya rabuwa teema ta tafi shima ya shirya ya fito domin tafiya kn, akan hanyarsu ya fara bawa bobo labari, bobo har mom fa sai da na fadawa ina sha'awar koko amma mom ba ta gane abinda nake nufi ba, dariya bobo yayi shege baabah da ta dago fa? Da sai tamin aure kwana kusa, amma har yanzu banji ni daidai ba, saboda teemah tana da yan matsaloli ajikinta, bata hada komai ba dan har Lana tafita cikar halitta.
[1/30, 7:55 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na UMMI A'ISHA

3⃣7⃣

   Murmushi bobo yayi junior ka zama dan bariki fa, rikakke ma kuwa, junior ya fada yana kallonsa, wlhi bobo a matse nake ne to amma ita teemah ba zata iya dani ba, shiyasa na ke son na koma ghana kwana kusa, haka suka ci gaba da hirarsu har suka isa kanon dabo, suna zuwa gidansu junior suka yiwa tsinke, lokacin da suka shiga mom na zaune tasha ado cikin wani leshi blue mai tsada kai da ganinsa kasan naira tayi kuka, ga wata sarkar gold katuwa da tasaka, kusa da ita junior yaje ya zauna tareda kwantar da kansa akan cinyar mom, sannu da zuwa yarona, mom tafada tana shafa kansa a hankali, yawwa mom ina dad? Dad dinka yaje kasar Singapore amma ba jimawa zai yi ba, mom so nake nakoma sch acikin satin nan, junior zaka tafi ka barni, ta fada cikin alhinin rabuwa da danta, mom 1 month kawai zanyi fa nadawo, to yarona Allah ya kaimu, tashi yayi yakarasa cikin dakinsa sai a lokacin tunanin kuluwa ya dawo cikin kwakwalwar sa, zama yayi a gefen gadonsa ya lumshe kyawawan idanuwansa yana tuno kuluwa da shagwabar ta, shi dai yana son yarinya shagwababbiya kuma macen data iya shagwaba tana burge shi sosai, kayansa ya fara hadawa cikin babbar jaka.

    Tun karfe 7 na safe ya shirya driver ya kaishi airport ya tafi kasar ghana. Awanni kadan suka sauka, tunda ya sauka ya hango dayo abokinsa wanda suke karatu tare, gefensa kuma wata hadaddiyar budurwa ce wadda ta tsuke cikin riga da wando, da sauri dayo yazo ya tareshi suka gaisa suka nufi motar da dayo yazo da ita, gidan da suke haya suka tasamma, tun akan hanya junior yake kallon wannan budurwar yana murmushi saboda ta tafi dashi over. Suna zuwa gidansu yayi mata sign da idonshi daya take ta gane abinda yake nufi, murmushi tayi ta fita daga motar shi kuma junior ya fara diban kayanshi ya shigar cikin dakinsa.

  Karfe 6 na yamma Patricia ta shiryo ta nufi dakin junior dama lokacin ya shirya tsaf ita yake jira, Patricia yar asalin kasar Nigeria ce sai dai yaroba ce amma kuma kyakkyawa ce sosai, tana yin knocking ya dan leko ganin itace ya sashi bude kofar a hankali, shiga Patricia tayi tare da fara dan idanuwanta ta lumshe su, tsayawa tayi ta rike kugunta tana kallon junior wanda ya rikice yana kallonta, a hankali taje ta tsaya agabansa, hy! Tafada tana dan jujjuya jikinta, hy! Junior ya daga mata hannu, jikinsa ta matsa sosai takai hannunta kan fuskarsa tana shafa gashin girarsa wanda yake baki wuluk kuma yalwatacce, kana da kyau! Ta fada a hankali, lumshe idonsa junior yayi domin yasha jin wannan Kalmar abakin yan mata da yawa, zip din gaban rigarta ta ja tafara zugewa, nan ta rikita junior suka fara bawa junansu feeling.

Sai da komai ya kammala sannan junior yaji kuluwa ta fado masa arai duk kuwa da cewa bai san sunanta ba kuma sau 2 kacal ya taba ganinta a rayuwarsa to amma duk da haka yana jinta acikin ransa sai dai bai san me yake ji gameda ita ba.
[1/30, 8:01 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

3⃣8⃣

  Kansa ya fara shafawa saboda tunowa da kuluwa da yayi domin ya rasa me yasa tun ranar da ya fara ganinta yaji ta burgeshi kuma shagwabar da tayi ba karamin tsaya masa arai tayi ba. Zare jikinsa yayi daga jikin Patricia domin acewar sa yau yasha koko ya koshi, wayarsa ya dauka ya fita falo ya fara kiran bobo abokinsa, bobo yana dauka yace kaga masoyin koko, dariya junior yayi kamar kuwa kasan yanzu shi na gama sha, kuma yanzu haka fita zanyi, zanje stadium inda zamu buga wasa, good Allah ya baku nasara, amin bobo sai munyi waya, yana katse wayar kiran mom dinshi ya shigo, hello mom, junior ka sauka lfy, lfy lau mom ya gida, junior gida babu dadi saboda baka nan, mom ai bazan jima ba zan dawo, to junior a tsaya dai ayi karatu kaji, tom mom akula min da horse dina pls, karka damu my boy zan kula maka dashi fiyeda yadda zaka kula dashi, thank you so much mom, bye bye, ok bye, da sauri ya tashi ya nufi akwatinsa da yake ajiyar kudi, kudi mai yawa ya dauko ya ajiyewa Patricia a kusa da ita, toilet ya shiga yayi wanka ya fito dama salla ba dadashi da kasa tayi ba dan haka kayansa kawai yasa ya fito ya nufi stadium acikin taxi, yana sauka yashiga rest room dinsu inda anan kowanne dan wasa yake shiryawa, ana ganinsa aka fara murna welcome junior, cikin sauri ya shirya cikin fararen kayansa na ball, riga da wando da safa da combus duk farare da abin hannu, lambar rigarsa lamba 1 ajiki an rubuta JUNIOR da manyan harrufa, filin wasa suka shiga inda zasu buga da Accra Golden stars, su kuma kungiyar su Super Eagles, bayan an fara wasan da kamar minti goma sha biyar junior ya zira kwallaye har guda biyu acikin raga, tuni wuri ya gauraye da hayaniyar magoya baya,junior kam daman wannan abun shine yafi komai burgeshi a harkar kwallo domin yana son yadda mutane suke sonsa sosai, gashi ko ina yaje an ringa nunashi kenan kuma sai abin yazo daidai saboda he's handsome & good looking guy, shi kansa akaran kansa yasan ya hadu shiyasa baya missing target.

Bayan an kammala wasan ne ya koma gida lokacin Patricia ta tafi amma tabar masa wasika cewar zata rinka kawo masa ziyara akai akai domin ta yaba dashi, murmushi yayi tareda dunkule hannunsa, yanmata kuna son junior i don't know why, amma shi kuma junior yanada yarinyar da yake so ya fada a hankali, kwanciya yayi saboda ya gama gajiya take bacci ya dauke shi.

Washe gari sai 11 ya shiga makaranta bayan ya dauki dressing kai idan ka ganshi zaka rantse ba musulmi bane saboda yadda yayi dressing din,bashi da maraba da mawakan kasar turai, su kansu daliban da yawa ba su san musulmi bane domin ko sunansa basu saniba, sudai sunji kawai ana kiransa da junior, to masu karatu ma dai basu san sunan junior na asali ba, yakamata muji waye junior

      ***************

Abdulrahman Kabir Madaki shine cikakken sunan junior, mahaifinsa Alh Kabir madaki shahararren dan siyasa ne domin shine chairman party na kasa a jam'iyar LLP kuma dan kasuwa wanda yayi suna akasashen duniya, matarsa daya hajiya Fati, basu taba haihuwa ba sai akan junior wannan dalilin ne yasa suke sonsa fiyeda kima, tunda junior ya taso baya jin magana bashida girmama na gaba dashi domin bai taso cikin tarbiyar da ta dace ba, ko a makaranta ba a dukansa domin bai san wani abu wai shi discipline ba domin mahaifinsa ya hana adakeshi ko wanne irin laifi yayi, junior ya tashi cikin gata da kulawar iyayensa kuma tun yana dan karami yake abota da mata sam shi bashi da aboki namiji sai bobo, ko lokacin da yana karami idan jawahir tazo gidansu to tare suke kwana mom bata hanawa babu ruwanta da cewar ba gender dinsu daya ba, ga junior da rashin jin tsiya, he's naughty, unruly, rude, and cheeky boy, amma kuma duk da haka he's brilliant, gifted and talent domin baya wuce na first position.
Duk makarantun sa na kudi yake yi tun daga primary sch har zuwa high institution gashi da son kwallo tun yana yaro, ya iya kwallo sosai kusan kowanne lokacin kaje gidansu zaka sameshi yana buga ball, wannan dalilin ne yasa dad dinshi gina masa katafaren filin kwallo inda zai rinka bugawa hankali kwance, asalin mom dinshi shuwa arab ce kuma mahaifinta sarkin borno ne, wannan na nufin junior jikan sarki ne, shi kuma mahaifinsa dan asalin jihar jigawa ne a wata karamar hukuma da ake kira da birnin kudu cikin wani kauye wai shi chiyako.

A lokacin da junior ya dan tasa ya zama saurayi to alokacinne mom dinshi da dad dinshi suka sakar masa ragama dama dad dinshi he's lenient, permissive person, mutum ne da bashida matsawa yaro musamman ma junior domin ko tsawa bai taba yi masa ba balle har ta kaisu ga duka, ko salla junior baya yi  ga kula yanmata kamar me, har gida yanmata ke biyoshi amma babu ruwan iyayenshi basu taba tsawatar masa ba akan haka, lallai wannan shi ake kira da SANADIN GATA, a sanadiyyar gatan da yake samu daga iyayensa yasa yake kallon komai a banza.
[1/30, 8:07 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

3⃣9⃣

  Lokacin da junior ya girma yakai matsayin saurayi har lokacin bai daina kwanciya jikin mom dinshi ba kai har yanzun nan junior yana dora kansa akan cinyar mom, dad kuwa kamar wani abokinshi haka ya zama,sai dai tun lokacin da ya zama saurayi dad ke yawan bashi labarin yan uwansa to amma har yau bai taba ganin dangin dad dinshi ba amma mom dinshi yasan familyn su.

   CIGABAN LABARI

Kansa tsaye Barack Obama Hall ya nufa inda ake gudanar musu da lecture, wata farar malama ce wadda shekarunta zasu kai 35 kuma da alama sabuwar malama ce, wucewa junior yayi da niyyar zama hee! Tafada get out, you naughty boy, kallonta yayi ya dan harare ta yajuyo zai fita, zo nan ta sake fada, dawowa yayi ya tsaya, meye sunanka, Abdulrahman Kabir, meye registration number ka? 002 yafada yana lasar lebensa na kasa ok fita anjima ka sameni a office dina, fita junior yayi yanufi wurin da dalibai ke hutawa idan sun fito daga lecture, anan ya zauna har Mrs funke tagama lecture dinta tafita yana ganin fitarta yabi bayanta, har office dinta, tana zama ya shiga, kallonsa ta fara kai meye ma sunanka? Junior ya fada yana lumshe mata ido, kai baka da kunya ko? Kallonta yayi ta gefen ido tasha t shirt da jeans mai tsada, sorry ma ya fada agankali, rubutu tafara yi, tunda akayi resuming ba kadawo sch ba sai yanzu why? Bai bata amsa ba, biron aljihunsa ya zaro ya faketa yayi rubutu ajikin wani file dake kan table dinta I LOVE YOU MA, ya rubutu ba tareda ganiba, tana dago kanta tajawo file din nan taga rubutun da Junior yayi daga kai tayi ta kalleshi, shi kuma yana ganin haka ya dauke kansa ya basar, you naughty,kai wayasa kayi min rubutu anan?? Unrespectfull boy,Am sorry ma ya fada yana kallon fuskarta, do i look like your playing pertner? tafi sai anjima tafada lokacin da take ci gaba da rubutun da takeyi ajikin file din.

Tun daga lokacin wannan malamar ta zama budurwar junior amma shidai ba sonta yake ba kawai iskancine irin nasa, amma ita dagaske sonsa take shi kam bata yi masa ba dan ta girme masa nesa ba kusa ba, tun lokacin da yadawo sai ya gadama zai je makaranta idan bai gadama ba kuma sai yayi kwanciyar sa adaki yayi baccin sa da haka har semester tayi nisa alokacin ya shirya yazo ganin gida, ranar da zai dawo mom ji tayi kamar tayi tsuntsunwa taje ta daukoshi, girki kuwa ya sha su kala kala, karfe 3 ya sauka afilin saukar jirage na malam Aminu kano, yana isowa gida mom ta rungumeshi, yasha suit ash colour yayi fresh dashi, har yau gashi nan makale da dankunne da sarka katuwa awuyansa, ga wani sajensa da ya gyara shi yayi kyau, sumarsa kamar yayi mata shamfo dan baki, kansa ya kwantar akan cinyar mom, momyna nayi missing dinki, nima nayi kewarka junior, momy ta fada tana mai shafa sumar kansa, yanzu ka kwanta ka huta kafin na baka abinci kaci, to mom bari naje dakina, dakinsa ya shiga wanda aka sake masa sababbin furniture sai kace wani dakin amarya, kayan jikinsa ya cire ya kwanta, shi dai yana son bacci bashida aiki kusan kullum sai bacci.

Kwanansa hudu da dawowa budurwar sa Lana takawo masa ziyara, mom da murna ta karbeta nan junior ya kai mata kayanta cikin dakinsa amma mom babu ruwanta don lokacin da ta shigo ma junior na kwance akan kujera ya tasa kai da cinyar mom daga shi sai dan gajeren wando da riga yar body hug, yana jin sallamar Lana yaje ya rungumota ya shigo da ita cikin dakin, kalubale gareku iyaye wannan Sam ba wayewa bace ya kamata mu farka daga dogon baccin da muke, hannun Lana yaja zuwa cikin bedroom dinsa, Lana you have surprising me, how comes? I never expect you this time, wow! Junior don't talk like this again, ai na fada maka dama i will give you a surprise visit, yanzu kazo muje ka nuna min garinku, tashi Junior yayi yanzu kuwa Lana, yanda yake haka ya dauki key din motarsa ya ja hannun Lana suka fito, mom bari na kaita gari mu dawo, to junior adawo lfy mom ta fada tana murmushi.

Wata dalleliyar mota mai kyau kirar Lexus junior ya dauka suka fita shida Lana, tunda suka fita suke zagaya gari har yamma tayi, bayan ya nunnuna mata wurarene ya kaisu 11 stars hotel anan ya kama musu daki, suna shiga Lana ta kalleshi junior meyasa baka kara dawowa gidanmu ba?? Karki damu Lana yanzu dai ki barni nasha koko tukunna sai muyi magana idan na koshi, mursmushi Lana tayi oh junior case, bakinta yakama da nashi ya fara kokarin nuna mata matsuwarsa, sai dare suka baro hotel din suka koma gidansu junior
[1/30, 8:10 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

4⃣0⃣

  Kwanan Lana hudu agidan su junior, kullum sai sun fita sunje hotel sun shakata da haka har tayi musu sallama ta tafi, kayan goma ta arziki mom ta hada mata yayinda shima dad ya yi mata kyautar kudi mai tarin yawa, haka junior ya gama hutunsa yakoma sai dai har ya koma bai sake haduwa da kuluwa ba amma duk da haka yasha alwashin nemota a duk inda take.

     ****************

   Kuluwa ce zaune ita da ummi sai shirya kayansu suke yi cikin trolley babba wacce, zasuyi tafiya da ita,kallon kuluwa ummi tayi hawwa nikuwa ina saurayin nan naki? Waye saurayina?? Abokin fadanki, sai da gaban kuluwa ya fadi, oh ni tun lokacin nan ban sake ganinsa ba ta fada tana ninke rigar hannunta, tunani ta tsunduma ko yanzu yana ina? Saboda na jima ban ganshi ba amma gayen nan ya hadu matsalarshi daya ya lalace SANADIN GATAN da iyayenshi ke nuna masa amma ni nayi alqawarin zan gyarashi ya dawo cikakken mutum mai cikakkiyar kamala kuma zan aureshi, zan rayu dashi rayuwa mai dadi, duk wadannan zantuttukan da kuluwa take yi acikin ranta take yinsu, da haka suka karasa shirya kayansu suka tarkata suka tafi abuja wurin anty salma kasancewar yanzu sun gama karatu har sun fara neman admission a jami'a, ita ummi tana nema a north west, ita kuma kuluwa tana neman b.u.k, lokacin da suka je abuja ita dai kuluwa hankalinta na kano domin tasan ta bar junior a kano ita kuma shi take nema ruwa a jallo, yanzu ita da ummi basuda wani aiki sai kallo sai kuma yawon ganin wuraren shakatawa.

  Misalin karfe 7 na dare kuluwa tazo ta zauna gaban tv ta kunna, channel din ta canja zuwa wata har zata wuce saboda ganin ball ake yi sai taga wani kamar junior barin tashar tayi tana mamakin to me yakai junior kasar ghana? Saboda taga ball din da ghana da brazil ake bugawa, bayansa aka hasko, JUNIOR tagani arubuce, lah ashe shine, wlhi shine ta fada tana sake kallon tv din, Wasa ake gadan gadan cikin mintuna kadan junior ya zura kwallaye har guda uku acikin raga, da lokacin aka tafi half time wato hutun rabin lokacin. Ku sakarkaru ne kun bar wancan yaron sai kwallo yake zurawa to wlhi idan aka koma ku tabbatar ku karya kafarsa yadda zai fita gaba daya, wannan maganar coach din yan brazil kenan wato mai horar da yan wasa, kadawa aka yi alamar lokacin ya cika, take akoma aka ci gaba da gudanar da wasa, wani dogone ya fara bin junior a baya, duk inda junior yayi yana biye dashi, da zarar an jehowa junior ball zai kwarfe shi ya fadi ya dauke ball din, sunyi haka yafi sau biyu akaro na karshe ne junior ya dau ball din ya nufi raga aguje, binsa wannan dogon yayi yana zuwa ya daki kafarsa da karfe, take junior ya fadi tareda rike kafar tasa, da gudu rafarin yazo ya dagawa dogon jan kati alamar an koreshi daga cikin filin, sukuma likitoci masu kula da yan wasa suka rugo aguje zuwa wurin da junior yake kwance yana rike da kafarsa, kuka kuluwa ta fara, shikenan ya karya shi, wlhi ya karya min shi, Allah ya isanshi, macuci, ya karya masa kafa, ummi ce ta shigo falon ta tsaya tana kallon kuluwa wadda hawaye ya wankewa fuska, daukar junior akayi aka fita dashi ko taka kafar baya iya, waye ya mutu hawwa?? Inji ummi, kallonta kuluwa tayi amma bata furta komai ba ganin haka yasa ummi shigewa cikin daki, kuka kuluwa tafashe dashi saboda ganin an sako wani nadaban wanda zai maye gurbin junior, kuka take sosai kamar wani mijinta, acan gidansu junior ma haka abin yake domin mom ta rasa inda zata tsoma ranta tun lokacin da taga an fita da junior daga cikin filin, hankalinta bai sake tashi ba sai lokacin da taga anyi replacing dinshi da wani, take ta nemi nutsuwarta ta rasa, shikenan sun karya min yaro, daga yau junior yadaina buga kwallo mom ta fada tana kwalla.

Kuka kuluwa taci gaba da rusawa har na tsawon wani lokacin, minti 5 ya rage a tashi daga wasan sai aka fitar da wani, junior ne ya taho yana dan dingisawa take filin ya rude, yes! Kuluwa ta fada tana dariya, junior da karfin hali ahaka ya zira kwallo guda biyu kafin a tashi daga wasan, ana tashi mutane suka taho da gudu suka lullube shi, wani dadine ya ratsa zuciyar ta, um nasan shi har ya manta dani, amma ni ban manta dakai ba junior ta fada lokacin da take kokarin kashe tv din.

   Watansu kuluwa 2 a abuja suka dawo kano saboda sun sami admission a university sai dai kowacce makarantar ta daban, bayan sun dawo ne suka yi registration suka fara halattar makaranta, yanzu kuluwa ta zama yanmata tayi fes da ita kuma tayi kyau ta gyaru sosai, zuwanta b.u.k tayi sababbin friends yan department dinsu da sauran da suke haduwa wurin cin abinci ko wurin salla, medicine shine abinda take karantawa ita kuma ummi tana karantar pol science a north west,amma har yanzu kuluwa bataje kauyen su ba tun lokacin data baroshi rabonta da kauyen su shiyasa wani lokacin take jin kewar mahaifin ta ya kamata.

   A bangaren junior kuwa abin nasa babu sauki sai ma sake gaba da yayi, sai dai yanzu haka ya dawo hutu gida daga kasar ghana, misalin karfe 11:30 bobo yazo gidansu, dakyar junior ya tashi ya fito yana sanye da dark brown din wando iya gwiwa yasa yar body hug baka ajiki an rubuta why always me??,kunnensa kamar kullum da dankunne ajiki, wuyansa kuma yasa sarka, ko wayarsa bai dauka ba ya nufi inda bobo yake motarsa ya dauka kirar optima kalarta ruwan toka, tare acikin motarsa suka fita shida bobo, kallon bobo yayi ina son shiga b.u.k domin naga yadda su nasu yanmatan suke, dariya bobo yayi muje nima akwai wanda zanga aciki, suna tafe junior yana bawa bobo labarin budurwarsa malamarsu wadda ta mace akansa, suna shiga suka fara cin karo da dalibai iri iri, a admin block suka yi packing bobo ne ya fita ya nufi wani office shi kuma junior yana cikin motar yana sauraren wakar d'banj, yana jin wakar yana bi, kamar a mafarki ya hango kuluwa su biyu sun fito daga cikin wani office, ta jikin motarsa suka zo zasu wuje burum ya bude kofar motar ya fito yasha gabansu, dukansu sai da suka tsorata saboda yadda yasha gabansun kamar wanda suka yi masa laifi, kallo daya kuluwa tayi masa ta ganeshi amma ita abokiyar tafiyar tata bata san kowaye ba saboda ba saninsa tayi ba. [1/31, 8:05 PM] Ummi A'isha: ®OHW


🔺SANADIN GATA🔻

Na
UMMI A'ISHA

4⃣1⃣

   Kallon kuluwa yayi ta danyi kiba kuma ta sake zama budurwa cikakkiya, tana sanye da leshi blue da farin hijabi mai hannu, takalminta ma fari ne, so yanzu kin zama budurwa babu maganar saka uniform ko?? Ya fada yana kallonta, kallonsa tayi ta basar malam lfy? Ido ya dan kashe mata tareda duban kawar tata, baiwar Allah dan bamu wuri zamu yi magana, tafiya maimuna s alkali tayi ta barsu a tsaye, baki gane ni ba?? Dan Allah kibani number wayarki zamuyi magana, nifa banida waya kuma dan Allah kar ka sake kulani saboda mutane suna ganina da mutumci yanzu kuma idan suka ganni da mai dankunne a tsaye zasu yi min fassara kuma mutuncina zai ragu a idonsu, ras yaji gabansa ya fadi, anya kuwa wannan yarinyar zata soshi? Ya tambayi kansa, oh dan nasa earring da chain shine mutumcinki zai zube? Basu kadai ba har wannan kayan jikin naka duk Suna iya janyo min zubewar mutunci, ok to yanzu dai ki bari muyi magana, da wa? Dake mana, a'a kabari duk lokacin da kayi shiga irin ta mutanen kirki sai kazo muyi magana, tana gama fadar haka ta wuceshi tayi tafiyar ta,

gosh! Ya fada tareda dunkule hannunsa ya naushi iska, cikin mota ya koma duk jin zaman yake ya isheshi, wato kenan idan nacire chain dinnan da dan kunnen nan zata tsaya ta saurare ni? It seems kamar wannan shigar da nayi ne bata so, zancen zuci yayi tayi har bobo yazo ya sameshi, jikinsa a sanyaye yaja motar suka fita suka nufi gida, yana zuwa gida ya fada akan kujera a falo lokacin mom bata ciki tana side din dad, nan ya zauna har tazo ta sameshi kamar marar lafiya ya zama, junior lafiya? Mom ta tambayeshi cikeda rudu, lafiya lau mom, dad yadawo? Eh ya dawo dazu, mom dan Allah manyan kaya nake so tun daga shaddodi har yadika, to junior nima dama na dade ina son naganka da irin kayan da yayan manya suke sakawa amma tunda yanzu da kanka kana so shikenan bari ina zuwa, daki mom ta shiga ta dauki wayarta takira tailor din dake yi mata dinki yana dauka tace dashi yaje kasuwa ya siyowa junior shaddodi masu tsada da hadaddun yadika adinka masa idan angama an kawo zata biya kudin, murna ta fara yi oh junior an fara girma da hankali da alama yanzu nutsuwa ta soma shigarsa, falo ta koma inda yake.

Tana komawa ta sameshi yana waya da teemah big girl, zama tayi akusa dashi, kansa ya dora akan cinyar mom, mom yanzu idan nasamu mata zaku yimin aure?? Me zai hana junior na, ai zanso naga matarka da yayanka, uhm amma mom nifa ba yaro daya zan haifa ba ni dayawa nake so, shafa kansa mom tayi Allah ya amsa junior dama yanda kake kai daya agidan nan Allah yasa yara dayawa zaka haifa, amin mom, farin cikine ya shiga ransa domin sai yanzu yaji yana son yin aure kuma yaji yana sha'awar ya fara saka manyan kaya.

Kwana biyu junior yana gida babu inda yake zuwa har sai da aka kawo masa kayansa,aranar ya yi wanka ya shirya cikin shadda sky blue mai tsada, baisa dankunne da sarka ba, sai da yasha turare sannan yayiwa mom sallama ya fita kallonsa mom tayi to kodai junior ya fara neman auren ne?? Motarsa ya dauka mai kyau kirar corotoure ya nufi b.u.k ko takan bobo bai bi ba, a admin block yau ma yayi packing yana nan zaune yana tunanin abinyi kamar daga sama sai ya hango su kuluwa su uku wadda suka fito daga wani office,

sai raba ido takai ta inda zata ga junior domin tunda abin ya faru kullum idan tazo sch bata samun nutsuwa duk tunaninta junior fushi yayi, ranar kasa bacci tayi saboda tana gudun kar ya subuce mata, yana ganinsu ya fito daga cikin motar, ganinsa kawai tayi a gabansu amma tuni ta gane shi, kallon juna suka fara daga ita har shi, yayi kyau sosai yayi wani irin kwarjini, Gashi da kalar yan gayu domin kana ganinsa kasan dan gayune, barka da fitowa ya fada cikin muryarsa mai tsananin dadi da zaki, kallon kawayenta tayi kuyi gaba sai na taho ina zuwa, suna wucewa ya kalleta pls mu shiga cikin mota because am not comfortable for this hustle and bustle, wurin naku yayi hayaniya da yawa ni kuma bana sonta, kamar ba zata shiga ba sai kuma dai taga rashin dacewar haka, gidan baya ta shiga shi kuma yana gaba a mazaunin driver,

malama har yau fa ban san sunanki ba, sunana hawwa ta fada a hankali kai kuma ya sunanka? Sunana Abdulrahman, sunanka junior dai tafada tana kallonsa, eh wannan sunan da mom dina take kirana dashi ne.
[1/31, 8:14 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

4⃣2⃣

Kallonsa kuluwa tayi da alama dai yana ji da mom dinnan nashi sannan kuma tana gatale shi abisa dukkanin alamu, maijidda me yasa kika ki saurarata rannan?? Sai da ta danyi Jim sannan tace masa, kaga nan ai wurin mutane ne dayawa kai kuma ranar a yadda ki fito gaskiya bai dace ba amma yau dressing dinka yayi daidai dana mutanen kirki amma idan kaji haushi kayi hakuri, no ba haushi naji ba wlh dadi naji yadda kika fadamin gaskiyarki kuma naji kin burgeni shiyasa nake son ki zama friend dina idan har ba zan takura miki ba, dan murmushi tayi bana yin abota da maza amma kai bazan ki ba, saboda me? Saboda wani dalili, to nagode da wannan alfarmar da kika yimin, kibani phone number dinki, ai na fada maka banida waya, ok idan na siyo miki zaki karba? No ai agida ne har yanzu ba za abarmu mu rike wayar ba, to ba damuwa zan iya zuwa gidanku? A'a ba za abarni na fito ba, to zan rinka zuwa nan din, babu damuwa sai kazo, to yanzu zanje natafi sai na dawo, ok babu damuwa, nagode, fita tayi ta nufi wurin da kawayenta suke shi kuma junior sai da ya dade a zaune kafin ya tafi, tafiya kuluwa kawai take amma tunanin junior ne yake ratsata koda taje wurin kawayenta ma tambayar ta suka fara yi wai ina tasamo wannan mai kyan? Murmushi kawai tayi mijina ne tafada ba tareda ta sani ba, mijinki? Sai asannan tasan maganar ta fito, acikin ranta tace Allah ya amsa domin abokinsa da matar junior ya kirani bazan taba mantawa ba, ummi ma dana bata labarinsa cemin tayi mijina ne, duk acikin zuciyarta take wadannan bayanan.

Abangaren junior kuwa wurin bobo ya nufa bayan yabar wurin kuluwa, labarin kuluwa ya fara bawa bobo, bobo in banda dariya babu abinda yake yi.


Tun daga wannan ranar junior ya ke zuwa wurin kuluwa a makarantar su yanzu sunyi mutukar sabo da junansu kuma sun shaku kowa yana tsananin son dan uwansa amma har yau babu wanda ya furta, ita kuluwa tana ganin a matsayinta na mace ai bai kamata tace tana sonsa ba, shi kuma junior yana ganin shi duk wadda yayi mata itace take cewa tana sonsa amma shi baya furtawa mace kalmar so sai dai idan bada gaske yake ba sai ya fada amma shi baya cewa mace yana sonta,yau ma tsaye suke ajikin motarsa yana sanye cikin farin boyel yasha kyau har ya gaji duk wanda zai wuce sai ya kallesu amma mafi akasari junior suke kallo ba kuluwan ba domin junior ya hadu iya haduwa komai nasa ya tsaru, kallon hannunsa kuluwa tayi, junior ya kamata ka yanke farcenka fa kaga yadda yayi zako zako, oh yah zan je na yanke sai nakoma gida mom dina zata yanke min, yanken farcen ma mom ce take yi maka?


Eh nifa komai mom dina ce ke yimin, ke barima kiji ni ko abinci mom dina ce ke bani wlh,babu abinda nake yi, yanken farce, abinci da sauran wadannan small small things din duk mom ce ke yimin, to kuma idan ka koma ghana waye ke yi maka?? Farce Patricia ce ke yanke min, take kuluwa ta hade rai ta bata fuska, wacece haka? Junior wai meyasa kai baka jin tsoron mace ta tabaka? Babu kyau fa wlh akwai wani hadisi dana taba karantawa da mutum ya taba matar da ba tasa ba... To ke wai wa ya ce miki tabata nayi? To in ba tabata kayiba me kayi? Allah ya baki hakuri, yabaka hakuri dai, amma dan Allah kasamu islamiyya ka rinka zuwa kana jin hadisai da fassarar littafi mai tsarki, nagode da wannan shawara, zan barki haka zanje gida kin san jibi zanje ghana, gabanta taji ya fadi saboda sai duk taji hankalinta ya tashi da zai tafi, ina sonka junior ta fada aranta, meyasa zaka barni? Takara fada acikin ranta, sai nazo sallama gobe, ok babu damuwa, sallama suka yi yatafi.

Tunda yaje gida ya zauna yayi tagumi domin ya rasa yadda zaiyi da son kuluwa dake azalzalarsa gashi shikuma yarasa dalilin da yasa yake nauyin bakin sanar mata da sirrin ranshi, washe gari haka ya shirya yana cikeda damuwa ya nufi b.u.k amma kananan kaya yasa yayi kyau sosai amma sumar sa tana nan tuli guda yakasa askewa domin yana son sumar nan bayajin zai iya asketa, inda suka saba zama yauma anan suka zauna kowannensu zuciyar sa cikeda kuncin rabuwa da junansu da za suyi, kamar marassa lafiya suka dan taba hira,

kallonta junior yayi kinga gobe zan koma ghana, eh nasani Allah yakaika lafiya sannan kuma akoda yaushe ka rinka tuna hakkin Allah akanka, ka tsare hakkokin Allah da suke kanka, insha Allah ya fada yana kallonta da idanuwansa wadanda suka danyi ja, ita kanta kuluwa ji take kamar ta fashe da kuka, sanin idan yaci gaba da ganin kuluwa zai iya yin kuka agabanta yasa shi yi mata sallama ya tafi.
[1/31, 8:18 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

4⃣3⃣

Hawaye ne suka sauko akan kumatunta duk yadda taso dannewa hakan abin yaci tura dole sai da junior yaga kukanta, meye abin kuka ya fada cikin dauriya da yake shi namiji ne shiyasa shi bai yi kukan ba amma yana yin nazuci, i don't know why am cry, tafada tana share hawayenta, karki damu jidda zan dawo nanda 3 months ya fada yana dan murmushin dauriya, motar yaja yatafi, yana tafiya kuluwa ta dauki shirginta ta nufi gida tana shiga dakinsu ta fara kuka dama lokacin ummi bata nan hakan yabata damar yin kuka son ranta, gashi duk irin son da takewa junior takasa sanar da ko ummi saboda tsabar zurfin ciki, shi ma junior yana zuwa gida ya shige dakinsa ya zauna wani irin kunci yake jin ya lullubeshi amma bai san abinyi ba, yana nan zaune har mom tashigo ta sameshi, zama tayi kusa dashi taja shi jikinta ta rungume shi, hawaye ya fara yi, dasauri mom ta kalleshi junior meya saka kuka? Mom ina jin haushin rabuwa daku ne, ayya junior kar ka damu kaji haka mom tayita lallabashi kamar wani jinjiri.

Washe gari junior yabar Nigeria ya sauka a ghana ranar kuluwa ko makaranta bata shiga ba saboda tasan idan tashiga damuwace zata addabeta domin zata rinka ganin kamar zata ga junior yazo wurinta alhalin shi kuma baya nan, sai yanzu tayi da tasanin rashin karbar phone number dinshi, dan da ta karba da ko aron  waya sai tayi ta kirashi.

Shima junior tunda ya sauka a ghana yake tunanin kuluwa, wai meyasa ban sanar da ita son da nake mata ba? Kar fa kafin nakoma ta hadu da wani ya sace min zuciyarta, Kalmar da yayita furtawa kenan, wayarsa ya dauka ya kira bobo ya fara bashi amanar jiddansa har da cewa bobo kullum yaje b.u.k yaga halin da jidda take ciki, amsa masa bobo yayi sannan sukayi sallama.

Tun bayan tafiyar junior kuluwa ta shiga damuwa gashi tun lokacin da yatafi bata sake jin muryar sa ba, amma abokinsa bobo kullum yana zuwa wurinta suna gaisawa kullum idan yazo sai tayi niyyar tace masa ya kira mata junior su gaisa sai ta kasa fada da haka har suka fara exam, lokacin kanta ya dauki zafi sosai. Junior kuwa lokacin da ya koma ghana ya fara kokarin canja dabi'unsa sai dai amma yakasa musamman da Patricia ta sakoshi a gaba da ziyarar dole, dolensa yake making love da ita ba don yaso ba.

Bayan su kuluwa sun kammala exams ne anty salma ta shirya musu tafiya kauye ita da ummi musamman ma da taga kuluwa tayi yar rama to sai tayi tunanin ko damuwar gidace ta sata shiga damuwar dan haka lokacin da suka gama exams sai tace su shirya su tafi kauye suje can suyi hutunsu acan.
[1/31, 8:25 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

4⃣4⃣

Shiri sukayi sosai na tafiya domin kuluwa tunda ta baro kauyen nan bata taba zuwa ba sai wannan lokacin, duk abinda suka san zasu bukata sun dauka, aranar asabar da yamma suka sauka a kauyen chiyako wanda a yan shekarun da kuluwa tayi ba tajeba taga an samu ci gaba sosai, anyi titi ankai wutar lantarki ga gine gine da aka yiyyi, ga burtsatsen diban ruwa sun wadata da rijiyoyo.

Har kofar gidansu driver dinsu ya kaisu babu abinda ya canja na gidan tunda ga ginin har cikin gidan, da sallama suka shiga, iyatu ana zaune ana iza wuta ta dan tsufa gefenta kuma mahaifin kuluwa ne, zumbur iyatu ta tashi, kuluwa sannu da zuwa kulu, fara'a mahaifinta ya fara sannu da zuwa hawwa, yanzu kuke tafe, jakarsu iyatu ta kinkima takai daki ita dai kuluwa duk abin ya daure mata kai ganin yadda iyatu ta sauya.

Tabarma iyatu ta shimfida musu suka zazzauna aka fara gaggaisawa ido iyatu ta zubawa kuluwa ganin yadda ta goge tayi kyau tayi kal kal da ita gashi ta zama katuwa sosai, tacika ta zama cikakkiyar budurwa, mahaifinta kuwa bakinsa yaki rufuwa dan farin ciki domin yaji dadin ganin kuluwa yadda ta sauya tayi kalau da ita, da alama burinsa zai cika. Sannu kulu ina maman naku? Iyatu ta tambaya duk ta zama abun tausayi dama haka rayuwa take, abunda ya baka tsoro watarana shi zai baka tausayi.

Daren ranar har 12 suka kai suna shan hira gaba dayansu sai wurin 1sannan suka shiga daki ananma kuluwa da ummi wani babin hirar suka bude har 2 tayi sannan suka kwanta akan gadon karfen iyatu. Washe gari da safe suka shirya suka nufi gidan Mairo kawar kuluwa, suna tafe suna kallon canje canjen da aka samu agarin, gidan mairo suka shiga tana zaune da yaranta guda 2 duk maza, sallamar su kuluwa ta sata juyowa tana ganin kuluwa ta tashi da gudu ta rungumo ta, nan suka zauna aka fara hirar yaushe gamo. Kuluwa baki tambayi shamsu ba? Hmm yana ina to? Yayi aure ai bada jimawa ba, ayya Allah ya basu zaman lafiya, amin kuluwa saura naki bikin.

Kallon Mairo kuluwa tayi yanzu Mairo har kinyi yara biyu? Har natuno lokacin danazo kina amarya kike bani labarin daren farkonki, dariya Mairo tayi ehh ai gashi yawuce saura naki, dan nasan kema zaki dandana, dariya kuluwa tayi aranta tace har na hangoni nida junior acikin wannan yanayin ranar nasan zansha lasa kuma shima zai sha lasa ko ta ina.
[1/31, 8:35 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

4⃣5⃣

 
Shiru tayi taci gaba da sassaka abun aranta domin ita duk lokacin da take hangota da wani namiji to junior ne, dariya ummi tayi wannan uwar tsoron ai mijinta ya banu dan wlhi ranar sai ta kashe masa dodon kunne, dariya kuluwa tayi wlh indai gayen da nake sone sai dai ma na kara masa karfin gwiwa amma idan ba shi bane sai ahankali, ai kuwa zakisha wuya dan da wahala inji Mairo, to ai Mairo tun zuwan da nayi kika bani labari tun daga lokacin naji tsoron maza ya shigeni, ke fa na dare dayane, Mairo tafada tana dariya, duk da haka dai, haka suka sha hirarsu sannan suka yiwa Mairo sallama.

Suna zuwa gida suka san anyi baki saboda ga wata jibgegiyar jeep nan akofar gidan, haka suka shiga suna cikeda mamakin ko waye yazo? Suna shiga gidan suka tarar da baki mace da namiji ga body guard dinsu a tsaye, cikin girmamawa suka duka suka gaishesu, kuluwa ga dan uwana Alh Kabir Wanda yake birni, wannan kuluwa ce ga ummi kuma yar gidan Salma, ah sune wadannan? Eh sune ai awurin salman ma suke acan birni, masha Allah kyakkyawar matar tafada,ya karatu lfy lau su kuluwa suka amsa tareda tashi suka shige daki, kallon burgewa matar tabisu dashi, suna shiga daki ummi tace kuluwa wannan shine dan uwansu anty? Eh dama kin san su ukune, kinga ikon Allah yau gashi yazo dan uwan nasu.

Kallon mahaifin kuluwa dan uwan nasa yayi,ahamadu nidai ina tunanin yarinyar nan hawwa ahadata da yaron wajena kaga shikenan zumunci ya kara kulluwa, murmushi Baban kuluwa yayi to ai yarka ce dama Kaine zaka aurar da ita tunda kayi mata miji shikenan, ko yanzu kace ayi sai a daura, a'a ahmadu abari sai sati na sama zanzo adaura auren, murmushi matar tayi wannan abu yayi daidai Allah ya sanya albarkarsa aciki amin dai iyatu ta fada dan yanzu ta saduda, sai yamma dan uwan Baban kuluwa ya tafi shida matarsa.

Su dai su kuluwa basu san abinda ake yi ba kullum sai dai suyi wanka su nufi gidan Mairo can zasu jima suna hirar aure, ai aure akwai dadi Allah ya Baku mazaje nagari dan ku debi romon dake cikin aure, baki kuluwa ta tabe amin dai dan ni wlh ina tsoron maza namiji dayane bana jin tsoronsa, shima zaki ji tsoronsa sai ranar, ni kin ganni har yau ban daina tsoron abban kalifa ba saboda bai bani dadi ba wuya yabani ranar, dariya kuluwa tayi wai ni nashiga uku, dan nasan ranar dogon suma zanyi dariya su ummi da Mairo suka fara yi mata.

Sai da suka gama shan hirarsu suka taho gida suna zuwa suka tarar da baban kuluwa a tsakar gida zaune, kiransu yayi yafara sanar musu da batun auren kuluwa wanda za a daura gobe, jikin kuluwa ne yafara rawa amma bata musa ba saboda tasan mahaifin ta bazai yi mata zabin banza ba amma tasan da ciwon son junior zata bar duniya.


Mazewa kuluwa tayi ko kwalla bata yi ba, amma ranar bacci baiga idonta,washe gari dan uwan mahaifinta yazo da jama'arsa aka daura auren kuluwa da angonta Abdulrahman, bayan an daura aure ne su anty salma suka zo suka dauke ta ita da ummi sai birni ita dai kuluwa ganin abun take kamar a mafarki, wai yau ita aka daurawa aure babu ko shiri, yadda taci burin aurenta amma sai gashi yayi mata zuwan bazata, wani gawurtarccen gida aka kaita a unguwar jan bulo da zummar washe gari za a kaita gidanta.

      *************
A bangaren junior kuwa yana can ghana yana fama da ciwon son kuluwa, ana cikin haka dad dinsa yayi masa waya yace yana son ganinsa nan da sati biyu, cikin rudewa yace dad lafiya kuwa? Saboda duk a tunaninsa wani abun ne ya faru a gidan


Lafiya lau junior kasan dai nadade ina nuna maka gata ko? To SANADIN GATAN da nake yi makane yasa na daura maka aure da yar dan uwana hawwa'u, ajiyar zuciya junior ya saki to dad babu komai Allah ya kaimu zanzo amma duk da haka dad zan sake aure nan da shekaru 2 lokacin budurwar da nake so ta kammala sch, to junior Allah yayi maka albarka, amin dad agaida mom kafin nazo, kashe wayar junior yayi ya lumshe idonsa ya fara hango suffar jiddansa, bakace ba can ba amma yafita haske bata da tsayi sosai sai dai tsayinta daidai misali yake gata da dan jiki madaidaici sai dai yanzu tazama yar lukuta, tanada abubuwan da yake so ajikin mace, fuskarta zagayayyiya ce mai dauke da dan tsukakken baki da hanci dogo da fararen idanuwa, duk da yasan yafita kyau to amma ta burgeshi.



Ummi A'isha®OHW

SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

4⃣6⃣

Shirin tafiya gida ya fara, dakyar ya lallaba Patricia ta yarda ta kyaleshi sukayi bankwana.


A bangaren su kuluwa kuwa kayayyaki sosai mahaifiyar mijinta ta siya mata tun anan tasan dan nasu dan gatane kuma suna ji dashi,  ga manyan mata da mom din angon ta gaggayoto aka zo aka gudanar da wani hadadden lunching wanda aranar aka shirya kuluwa cikin leshi pink mai tsadar gaske, ba karamin kyau kuluwa ba, kwansu 3 agidan aka rakata gidanta wanda yake girke a unguwar shagari quarters, uwar mijinta da kanta takaita gidan wanda aka gyarashi yasha kayan alatun more rayuwa, dan zamanta agidan su mijin nata taga abubuwan ban mamaki kala kala domin uwar mijin nata itace ta zage ta gyarata tsaf tayi mata gyara na musamman ta tsumu gaskiya wannan matar tana ji da dan nata. Tunda aka kaita ummi tatafi tabarta amma har lokacin kuluwa ko hawaye batayi ba sai dai tasan tana son junior kuma gashi ta rasashi, washe gari sai ga anty salma da ummi sun dawo, kayane cikin viva na mata anty salma ta kawo mata tareda yi mata bayninsu dalla dalla, wlh idan baki sha ba nadawo sai naci mutuncinki, to anty tafada tana kallon kayan, bayan su anty salma sun tafi ne tafita gidan nata ta fara zazzagawa, gidane katon gaske wanda ya amsa sunansa gida, ga ma'aikata masu tarin yawa komai yi mata za ayi.

Ranar litinin da daddare junior ya sauka akasar Nigeria, gidansu yaje nan mom ta rungumeshi da murna tareda yi masa albishir na auren da sukayi masa, wanka yayi yaci abinci ya shirya ya nufi gidan nasa lokacin karfe 10 na dare, lokacin da ya shiga gidan jin jikinsa yayi yai sanyi ahaka ya karasa amma bai shiga sashen amarya ba sashensa ya wuce ya kwanta saboda agajiye yake sosai.

   Kamar kowanne dare yauma kuluwa tayi shirinta na bacci jin alamun shigowar mota gidan yasata kudundunewa tareda kankame jikinta wuri daya tana addu'ar Allah yasa ba angon bane yadawo, tunanin junior ta fara Allah sarki junior narasaka har abada duk irin son da nake yi maka ashe bazan sameka ba, idonta ta rufe ta fara hango rabuwar su, junior akwai kyau saboda duk budurwar da ta ganshi sai ta fada mata tace mata wannan saurayin naki kyakkyawa ne,shiyasa wani lokacin take kishin zuwansa b.u.k dinma.
[1/31, 8:45 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

4⃣7⃣

  Hawayene suka fara sauka akan kumatunta, juyawa tayi ta rungume filo, duk rayuwarta ta tsarata ne kan zata yita da junior kuma taga alamun nasara domin yana jin maganar ta kuma yana daukar shawarar da duk ta bashi, gashi kanta tsaye take fada masa maganar da ranta ke so wacce ya kamata ace yayi fushi amma sai kaga bai yi fushin ba da alama dai ba mai saurin fushi bane kuma bashida zazzafar zuciya.

  Tunanin wani lokaci da yaje b.u.k tafara, suna tsaye suna yar hirarsu ta duniya dan ba za ace ta soyayya ba domin duk cikinsu har yau babu wanda ya taba tona asirin zuciyar sa, wayarsa ce tayi yar kara ya daga, hello teemah, kin samu sakona? Yayi miki kuwa? Ya suka zama? Sun kara girma? No dan Allah kiyi using da wannan abun ke naki sun cika kanana da yawa, kallonsa kawai kuluwa ta tsaya yi ya wani saka hularsa agefe shi yadda ake saka hular ma ba haka yake saka tashi ba amma yadda yasaka tasan sai ta bada wani style na musamman kuma tayi masa kyau sosai, kashe wayar yayi yana dariya, amma ita kuluwa ta cika fam tayi dam sai tattare girar sama da ta kasa take yi tasha dogon hijabi har kasa babu abinda ake gani ajikinta daga fuskarta shikenan dan ko hannunta ba a gani,


shi kansa Junior duk da bai taba ganin surar jikinta ba amma yasan ta mallaki komai na ya mace gata yar lukuta kamar ummi A'isha, harararsa tayi meye haka? Wlh kaji kunyar duniya data lahira, me nayi?? Kawai dan kinji ina yin waya sai kice haka? Oho maka amma wlh ka rage sabon Allah domin kaima zaka haifa shiyasa nake tausayawa matarka domin bata yi sa'ar miji ba, nikuma kinga nayi sa'ar mata saboda matata wlh mahaddaciya ce mai son addini, she's pious lady, baki kuluwa ta tabe, Allah wadaran naka ya lalace tana gama fadin haka ta juya tayi tafiyar ta,


murmushi junior yayi yakoma cikin motarsa ya zauna, a tunanin kuluwa daga ranar ba zai sake dawowa ba amma sai gashi ya dawo, maimakon ita tabashi hakuri shine ya fara bata hakuri akan abunda ya faru jiya, kuma tun daga lokacin da ta hanashi saka sarka da dan kunne ba sake ganinsa dasu ba, suma ce dai yakasa askewa
[1/31, 8:53 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

4⃣8⃣

   Tun daga lokacin ya daina yawo da boxer da yar t shirt sai dai agida, amma komawar sa ghana bai daina yawo da sarka da dan kunne ba, tunanin junior tayi ta tayi barkatai har bacci ya dauke ta.

A dakin junior kuwa kwance yake cikin bargo gashi ana dan yin sanyi a garin,tunanin jiddan sa ya fara, bashida niyyar yin jayayya da auren da su dad dinsa suka yi masa domin yasan dan suna sonsa ne asalima SANADIN GATAN da suke yi masa ne yasasu aura masa matar da suka aura masa ahalin yanzu, sai dai fatansa Allah yasa jidda ta yarda tazo a second wife dan yaga kamar tana da kishi, kudundunewa yayi sosai kamar wani karamin yaro saboda shi ko agida alokacin sanyi mom ta rinka kai komo kenan akansa saboda tasan akwai shi da jin sanyi shiyasa a dakinsa na gida harda heater sannan blanket dinsa ma mai heater ne yanda idan yaji babu sauki zai jona shi ajikin socket yasha duminsa, amma gashi anan babu ko daya.

Baccine yayi awon gaba dashi sai dai sanyi yakasa barinsa ya sake har gari ya waye bai yi wani baccin kirki ba, sai 11 yatashi alokacin yayi wanka yayi sallar safe ya fito zuwa falo, yana tafiya da cumb a hannunsa yana taje sumar kansa,

ita kuwa kuluwa tun asuba ta tashi tayi salla ta koma ta kwanta domin babu abinda take yi komai akwai masu yi mata hatta girki kuku ne ke yi mata shi, sai 9 ta tashi tayi wanka tasa atamfarta rigada skirt tasa hijab ta fito zuwa kitchen daidai lokacin junior ya fito,yana ta fito da bakinsa kamar yadda al'adar sa take saboda bashida abunyi kullum daga waka sai fito, buruntun da yaji anayi acikin kitchen ne yasa shi shiga kitchen din, bayanta ya hango tana hada tea hello! Ya fada ahankali, juyowa tayi caraf suka hada ido, me yakawo ka gidana da sassafe? Tafada tana kallonsa, shigowa cikin kitchen din yayi daga shi sai boxer baki da shirt fara, ke zan cewa me ya kawoki gidana da sassafe ko kin san matar tawa ne? Oh kenan kaine angon? Kenan kece amaryar? That's great, juyawa kuluwa tayi cikeda farin ciki amma duk farin cikin da take ciki junior ya fita domin shi ji yayi tamkar ya zuba ruwa akasa yasha dan murna, haba shiyasa ko sau daya bai ji ya tsani auren ba ashe jiddanshi ce matar, ajikin bango ya jingina bayan ya harde hannuwan shi a kirjinsa kai Allah shine abun godiya ya fada acikin zuciyarshi, juyowa kuluwa tayi da cup guda biyu rike a hannunta, muje falo ta fada lokacin data wuce gaba, bin bayanta yayi har cikin falo,ga tea ta mika masa, kai ya girgiza ni bazan sha tea ba, to me zaka sha?? Ni koko zan sha ya fada yana lasar lebenshi kamar wani maye,kaji ai, ni yanzu ina zan samo wani koko, ka karbi tea din kasha, kwanciya yayi akan kujerar nafada miki ni koko zan sha, tom kayi hakuri na sa kuku ya dafa maka wani abun, ke nifa agida komai mom ce ke bani har abinci, da safe ni bana shan tea,to me kake ci? Dankali da miya zaki min kuma ki bani koko, nifa na fada maka banida koko ko gasara bani da ita, acikin ransa yayi magana ke kuwa kike da ita kuma nasan kokonki ba irin na sauran bane saboda ke naki fresh one ne, tashi yayi ya kalleta ina zuwa zanje gidan mom yanzu, gidan mom da safen nan junior? Eh ai dole naje saboda akwai kayan kwallona da kayan motsa jikina acan, to kuma ahaka zaka fita?? Dakinsa ya koma ya sako dogon jeans yazo ya wuceta a falo ya tafi gidan mom.
[1/31, 9:02 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

4⃣9⃣

  Yana fita ta rakashi da murmushi oh junior manya wai junior da mata, kuma matar ma ni, tab! Zansha aiki da shagwabar junior ga tsirfa iri iri, ga shi shagwababbe komai mom komai mom yanzu kuwa tunda babu mom ai nice zan karbi aikin mom dolena, tashi tayi tashiga dakinta sai yanzu ta ciro kayan da anty salma ta kawo mata ganin junior ne mijin ya sata fara amfani da kayan, tana sha aranta tana cewa wannan shagwababben ma me zai iya, ai inajin ko irin kukan nan da ake cewa anayi a first night ni bazan yi ba saboda junior ai yarone karami ko isa auren ma bai yi ba amma SANADIN GATA yasa aka yi masa yanzu, kayan ta duddura acikinta sannan ta tashi ta shiga kitchen, hmm nidai ummi A'isha ban raina junior ba ehe.

Gidan mom junior ya shiga cikeda farin ciki yana zuwa ya tarar da ita zaune akan dining taci kwalliya sosai tana yin breakfast, good morning mom ya fada yana murmushi, morning my boy, karasawa inda mom take yayi yai mata kiss a kumatu, mom bari naje filin kwallona nadawo, ho junior ba za dai ka hakura da kwallo ba ko? Murmushi yayi mom ko nadawo nan gidan ne naga dad baya nan mun barki ke daya, a'a junior ni ai haka yafi min dadi ganin kaima da gidanka sai dai kazo min yawo, ya amaryar taka? Lfy lau mom,fita yayi zuwa filin kwallonsa ya fara wasannin motsa jiki.

A bangaren kuluwa kuwa yau jinta take wasai wasai, kitchen ta shiga ta soyawa junior dankali da kwai kuma tayi masa miyar tunanin inda za asamu koko tafara gashi rana tayi anya za asamu koko kuwa? Daya daga cikin ma'aikatan gidan ta aika ko  za asamu, cikin sa'a aka samo agurin wata inyamura, fari tas dashi gashi yayi kauri, yawwa nasan junior yau zai yi murna ganin na samo masa koko, wanka taje ta dauka tafito ta shirya cikin leshi mai kyau tana zama junior ya shigo, sannu da zuwa, dadi yaji wai yanzu shi ake yiwa sannu da zuwa, wai shine da mata kuma nan da kankanin lokacin zai zama baba, yawwa sannunki, sai dai ba kayi sallama ba, oh sorry mantawa nayi, komawa yayi da baya ya sake shigowa Assalamu alaikum, wa alaikumus salam warahamatullah ta fada tana murmushi, ga breakfast din naka, to bari nayi wanka, dakinsa ya wuce yayi wanka ya fito sanye da gajeren wando da yar shirt, kan kujera ya zauna ya jawo abincin ya fara lakuta ita dai kuluwa tana zaune tana kallon ikon Allah,gashi ganinsa da gajeren wando sai duk taji kunya ta kamashi domin ko cinyarsa wandon bai rufe ba,


ga fa kokon nan nasa an siyo maka, kallonta yayi sai kuma ya fara dariya, abin yabata mamaki ganin junior yana ta dariya, wai kokon aka siyo min? Eh tabashi amsa, a ina aka siyo? Acan unguwar ne,to ki dauke kayanki dan ba sha zanyi ba, kaifa kace kana son shan koko, eh ni nace amma ba wannan ba, daukar flask din kokon tayi tafita zuwa kitchen bin bayanta yayi da kallo yana murmushi, lallai jiddana baki fahimci kokon da nake nufi ba amma hakan ya burgeni da alama nine zan sanar dake kokon yadda yake, abincin ya rufe ya dau wayarsa ya fara chaten da bobo da teemah anan yake sanar mata yayi aure, yana nan zaune har 1 tayi ita kuma kuluwa tana cikin kitchen tana yi masa girkin rana, lokacin data gama ta fito yana kwance yana bacci gashi anata kiran sallar azahar, kusa dashi taje ta fara tashinsa, junior, junior, junior, ko motsi bai yi ba, hannunta yana rawa tafara dan dukan kafadar sa junior ka tashi, uhm yayi juyo sannan ya tashi, bakayi salati ba junior, salatin yayi yana murmushi, katashi kaje masallaci karka makara, tashi yayi ya nufi dakinsa yaje yayi alwala ya fito tana tsaye afalon sai nadawo, to kayi addu'ar tafiya masallaci fa kasan akwai zikirin da akeyi lokacin da ake tafiya masallaci sannan idan za ashiga masallacin ma akwai addu'ar da ake yi, kuma da kafar dama ake shiga, meye dama left? No right ta fada tana murmushi ok tnx nagane, fita yayi akaro na farko don zuwa masallaci saboda shi sallar ma ba yinta yake ba balle har yasan wasu dokokin zuwa masallaci, lallai duk jahilcin miji indai matarsa mai ilimi ce to ya tsira saboda ko babu komai yaransa zasu tashi cikin tarbiya shiyasa fiyayyen halitta yayi umarni da a auri mai addinin domin tafi lasting kar aduba kyal kyalin fuska.

Bayan ya dawo daga sallar ne kuluwa ta gabatar masa da abincin rana, nifa kinga bana son tafarnuwa kuma bana son gishiri da yawa sannan bana son yaji, indai akwai daya daga cikin wadannan a abinci to bana iya ci, kallonsa kuluwa ta fara yi, junior ba dai iyayi ba, komai nasa a kididdige yake, to yanzu dai kaci kaji, bani aron wayarka zan kira anty salma, a ina anty salman take? A sharada to bari nagama sai muje gidan nata kodai kinfi son kuyi wayar? A'a muje din idan ka gama ta fada cikeda murna.
[1/31, 9:10 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

5⃣0⃣

Cikeda murna ta shige dakinta tafara shiryawa ta sake kwalliya ta fesa turare ta fito, lokacin ya gama cakular abincin sa, tashi yayi suka fita, acikin motarsa Lexus suka fita suka nufi sharada, itace ta rinka nuna masa hanyar har suka shiga kwanar gidan, kin tuna nan wurin lokacin da na watsa miki kwata, dariya kuluwa tayi tayaya zan manta wannan wurin, murmushi yayi aransa yace ina sonki Jidda sosai amma kin kasa ganewa, gidan suka karasa suka shiga ummi na zaune a falo tana karatu, ganinsu yasata tashi ta rungume kuluwa hawwa har kin fara fita, daidai lokacin anty salma ta fito a'a yau amare ne agidan, ita dai ummi kuluwa taja zuwa dakinsu na da, suka bar anty da junior a falo, suna shiga ummi tace hawwa wannan fine guy dinne mijin dama? Eh shine fighting partner dinnan nawa fa? Tafawa suka yi da ummi, to ya ake ciki? Komai ya faru ko?? Dariya kuluwa tayi babu abinda ya faru ummi saboda kin ga bai ma wani jima da dawowa ba fa, kuma still he's young, kut ai young din sunfi bada wahala banza, tab duk ranar da wannan gayen ya kamaki ina tausaya miki dan bazai kyaleki ba sai ya fasaki wlhi, hararar ummi kuluwa tayi dalla malama bari yimin fatan tsiya, ni yanzu ma kayan nan nake son akaro min dan wlhi wadancan sunyi min kadan, haba? Ummi ta tambayeta, Allah kuwa kifadawa anty akaro min wasu, anya kuwa hawwa junior bai fasaki ba? Ke sai kiyi kuma inma abinda yafi fasani yayi ai matarsa ce, eh ni dama bance ba tasa bace,amma junior yafi karfinki, wlhi kinji na rantse miki wancan gayen sai ya saki kuka duk ranar da kuka hadu, kin manta ihu zai sani ba kuka ba, eh ihunma ai zakiyi, hmm hawwa matan aure naga alamar junior bai baki feeling ba har yanzu, anty salma ce ta shigo hawwa to ki fito ku tafi ni ko gaisawa ba muyi ba sai da dan nawa muka gaisa, fitowa sukayi kuluwa tana cewa anty yi hakuri wannan ummin ce duk ta hanani sukuni, yawwa anty wai akara mata wadannan kayan, to kya kai mata shidai Junior yana jinsu amma bai gane wadanne kayan bane.

Har bakin kofa inda motarsu take su anty salma suka rakosu daga nan jan bulo ya kaisu gidan mom dinsa, suna zuwa taga yaje ya rungume mom hadida kwanciya ajikinta, murnar ganin kuluwa mom ta fara, hawwa sannu da zuwa nan da nan aka cikasu da kayan cima iri iri, lallaba junior mom ta fara ta bashi fruits ya dan ci dakyar ita dai kuluwa duk abin ya zame mata Sabo lalle junior dan gatan mom ne, tashi yayi yashige dakinsa ya kwanta, ita kuma kuluwa da mom suna yar hira lokaci lokaci.

Sai bayan sallar isha sannan suka koma gidansu, lokacin da suka shiga kowa dakinsa ya wuce, wanka kuluwa tayi tasaka rigar bacci ta dora rigar sanyi asama saboda sanyin da akeyi ta kwanta bayan jikinta ya karbi turarruka masu kamshi. Shima junior kwanciyar yayi sai dai sanyi ya hanashi sakat shi kwata kwata basa shiri da sanyi, kaje gurin matarka kasha dumi kawai zuciyarsa ta bashi shawara, tashi yayi yafita a hankali ya tasamma dakin kuluwa wadda ita tuni lokacin ta dan fara bacci, a nutse ya bude kofar ya shiga tana tukunkune da alama itama sanyin yana shigarta kuma ya ratsata, bargon ya yaye ya hau kan gadon daukartar yayi cancak ya dorata a samansa yaja bargon ya rufesu tun shigowarsa kuluwa ta farka amma sai taki bude idonta, wata irin runguma yayi mata wadda ta kusa sakata shidewa domin gaba daya kankameta yayi jin dumin baya shigarsa yadda yake so yasashi cire rigar sanyin da tasaka yabarta daga ita sai yar sleeping dress wadda da ita gara babu amma da yake duhu ne baya ganin jikin nata, lamo kuluwa tayi ajikinsa tana shakar daddadan kamshin turarensa na special man, shi duk a tunaninsa bacci take, bakinsa yasa yayi kissing din gashinta, goshinta, da kumatunta, sai jujjuyata yake akansa kamshin turarensa da nata turaren sun hadu sun bada wani kamshi na musamman, hannunsa yasa ya zagaye kugunta yana sake motsata ajikinsa yadda zai kejin dukiyar fulaninta akan kirjinsa, hannuwanta ta dora akan kirjinsa ta sake cusa kanta cikin kirjinsa sosai tana shakar kamshinsa ji take kamar ta kama bakinsa ta tsota amma kuma tana jin kunya, kamar yasan abinda take so, ji tayi ya dago kanta ya hada bakinsa da nata ya fara tsotsarsa a hankali kamar ta tayashi amma sai ta fasa sai shi kadai ke kidanshi yake rawarshi, alhalin itama tana so, sai dai abinda ya tayar mata da hankali shine tana off, tun jiya tafara fashin salla kar kuma ko junior ya shirya yin harka a wannan daren bayan ita kuma akwai matsala, wani irin numfashi taji yana fitarwa wanda ke sauka akan hancinta, murginata yayi ta koma kasa ya haye samanta, abin mamaki sai bataji nauyinsa ba ko kadan, bakinshi ya sake mannewa da nata tareda zame rigar baccinta ya rungume ta sosai, ahaka bacci ya daukeshi yana kankame da ita bakinshi cikin nata domin anashi tunanin har yanzu ita bacci take bata san abinda ake yi ba, ita kam kuluwa tafishi morewa saboda wani ni'imtaccen dumi taji yana ratsata, duk wannan sanyin da ake zurawa ta nemeshi ta rasa sai dumi mai dadi da yake shigarta dumin jikin junior ga bakinsa kuma hade da nata, saboda jin yanayin da bata saba shiga ba yasata kasa yin bacci sai junior ne keta sharar baccinsa, can cikin baccinsa yakai hannu ya dafe na fulaninta guda daya, wani zimmm taji kamar an saka mata wayar nepa dan shock din da taji, baccinsa yayi mai ni'ima har asuba tayi,karar agogon da kuluwa ta saita ne ya tasheshi, bakinsa ya cire daga cikin nata ya dauke hannunsa daga kan na shanunta sannan ya kai bakinsa kai ya goga harshensa ya tashi ya mayar mata rigar tata ya zira mata ta sanyi ya lullubeta ya fita, duk kuluwa najin sa, wani lafiyayyen sanyi taji ya fara kunno kai cikin dakin kun san sanyin asuba yanda yake, bargon ta nunka gida biyu ta rufa amma duk da haka a banza jikin junior yafi komai bata dumi, shima junior duk da sanyin da yake ji haka ya daure yayi alwala da ruwan zafi yafito acikin sanyin ya nufi masallaci.



Ummi A'isha[2/4, 5:48 PM] Ummi A'isha: ®OHW


SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

5⃣6⃣


  Sauka ummi tayi suka fara cin abincin, oh namanta ban tambayi junior ba ko yaci abinci ko kuma haka ya tafi gidan mom din, sannu matar junior, yawwa sannunki ummi, wlhi ummi aure da dadi dan wlhi ba zaki fahinci maganata ba har sai kin shiga daga ciki,

kuma duk sanyin nan da ake zafgawa to idan kina da miji ba zaki jishi ba ke bama zaki San anayi ba wlhi, Allah yar gidana? Wlhi Allah musamman ki samu mijin da ya amsa sunansa namiji sai kinji shi acikin gajimare kina yawo,

Allah ya shirye ki hawwa na gane yanzu ke bakida kunya,a kece ai kike son jin labari shiyasa zan baki, to barshi haka naji,

wai yaushe zaki fara zuwa sch? Wlh next week nake son komawa amma har yanzu ban ma fadawa junior ba sai dai yau idan ya dawo na fada masa, eh ki fada masa kam kuna yan shafe shafenku kina fada masa,

waya fada miki a wannan lokacin ake irin wannan maganar? Ke fa yar duniya ce hawwa kema haka ummi, tashi kuluwa tayi ta fita takoma kitchen, girkin rana ta dora musu ta dawo dakin.

Wuni guda ummi tayi mata sai da yamma sannan ta tafi, tana tafiya junior ya shigo, dakin kuluwa ya leka tana gyaran dakin,sannu da aiki, yawwa sannu da zuwa, binsa tayi zuwa falon na kawo maka abinci? A'a naci agidan mom ina ummin har ta tafi? Eh, amma bata jima da tafiya ba,

dama ina son fada maka next week zan koma sch, to ai nima next week din zan koma Ghana, dam! Gaban kuluwa ya fadi idan junior ya tafi ya barta acikin sanyin nan ai ta shiga uku, tv ya kunna ya kamo kwallo ya fara kallo,

zama kuluwa tayi suka dan fara hira sama sama saboda shi junior ba mai yawan magana bane, har karfe 9 tayi suna falon sai wurin 10 kuluwa ta tashi ta shiga dakinta, wanka tayi da gaske ta bi kowanne lungu da sako da turaren ambar shaikha, rigar baccin yau ja ce yar karama da dan karamin wandonta iya gwiwa, tana nan kwance tana ta makyarkyata, tana tunanin junior ne yasa mata wannan jin sanyin tunda ada ita bata wani rawar dari komai yawan sanyi amma yanzu gashi har wani karkarwa take
[2/4, 5:58 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

5⃣7⃣


   Makure jikinta tayi wuri daya, Allah Allah take taji shigowar junior, kamar daga sama taji shigowar sa, kanta ya fado ya rufeta yaja blanket ya rufe su,

harshensa ya sa ajikinta ya fara lasar wuyanta, yau abun na junior babba ne domin tun yana lasar iya wuyanta har ya gangaro kirjinta, lukus kuluwa tayi da jikinta ajikin junior,

rungumar da yayi mata bata wasa bace domin ko mai na jikinta manne yake ajikin junior, hannunsa yasa ya fara shafa cinyarta, shock kawai jikinta yake saboda jin hannuwan junior suna yawo a jikinta, sai da ya shafata son ranshi sannan ya barta ya sake matseta ajikinsa ya tsotsi bakinta yaja bargon ya rufesu sosai.

   Kuluwa dai jine nata bata iya mayar da martani asalima idan taji shigowar junior sai tayi lamo ko motsin kirki bata iyayi, da haka har baccin ya daukeshi,

sai da ta tabbatar da cewar yayi bacci sannan ta fara kissing din kumatunsa, wuyansa, goshinsa daga karshe ta yada zango akan bakinshi, kama lips dinshi tayi ta fara tsotsarsu a hankali tareda kankame shi sosai ajikinta, itama yau ta dan samu damar yin baccin saboda yanzu jikinta ya fara sabawa dana junior. Kullum haka suke kasancewa har tsawon sati daya a lokacin ne kuluwa tayi wankan tsarki ta fara salla.

   A ranar junior bayan yayi wanka ya shirya yasha turare, riga yasa t shirt dark green yar karama wadda ta kamashi sannan yasa jeans baki,

gaban mirror ya koma yasake kara turare ajikinsa,kwalbar turaren ya ajiye ya juya zai fita, fadowa kwalbar tayi tosh ta fashe, dawowa yayi ya fara tsine kwalbar data fashe,

bayan ya kwashe ya juya ya nufi abin zuba sharar dake cikin dakin ashe akwai wadda bai kula da ita ba kuma tana da dan girma, takata yayi ba tareda ya sani ba, nan ta nutse masa acikin kafarsa ta hagu, dakyar ya karasa ya zuba kwalbar a shara lokacin jini har ya fara bulbula daga kafarsa, fitowa yayi falo kuluwa na zaune tana duba lecture note dinta ta english,

ganinsa tayi ya fito kafarsa duk jini, junior menene? Jidda kwalba na taka a kafata, da sauri ta tashi taje ta kama kafar tasa tana dubuwa yau ta ma manta da batun kunya saboda ganin irin jinin da yake fita daga kafar tasa.

   Ganin jinin yana ta fita da yawa yasa kuluwa cire dan kwalin kanta ta nade kafar tasa da dankwalin, jidda bani wayata gata can tana charge da sauri kuluwa ta nufi wayar, dakinta ya shiga ya kwanta akan gadonta, wayar ta kawo masa dakin ta bashi,

kafar tasa ta kama lokacin dan kwalin data saka masa har ya jike da jinin saboda jinin da yawa yake fita, sannu junior ta fada duk ta gama rudewa ga tausayinsa da ya ke hudata yana shigarta domin ji take tamkar ciwon acikin jikinta yake, hannu ya mika ya jawota jikinsa,

kwantar da ita yayi ya haye samanta ya kankame ta, kunya ce ta rufe kuluwa domin wannan shine karo nafarko da ya yi mata irin haka da rana,

dakyar ya fara kiran wayar mom, tana dagawa yace mom turo min doctor zai dubani, junior me ya faru? Baka da lafiya? Me ya sameka? Mom ta fara tambayarsa a rude.
[2/4, 6:10 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

5⃣8⃣


Mom ba wata matsala bace kawai ki turo min shi, to junior bari na kirashi, ajiye wayar yayi yasake matsar kuluwa, bata ankara ba kawai sai jin hannunsa tayi ta cikin rigarta ya cafko na shanunta daya ya rike, nan yafara wasa dashi dan mutsul mutsul ta fara amma bai saki ba, yana kwance lamo ajikinta. Kiran doctor din mom ta fara yi amma baya kusa ya shiga theatre dan haka sai nurse dinsa ta samu, turata gidan junior mom tayi dan ta duba shi.

Yana nan kwance jikin kuluwa ya matseta sosai kamar zai tsaga cikinta ya shiga hannunsa daya kuwa rikeda breast dinta daya, nurse dince ta shigo cikin gidan, wayar junior ta kira,

hello gani nazo, ki shigo bedroom din dake kallon kofar falon, ok, dakin nurse din ta shigo, sannu meya faru? Kwalba na taka wlh kuma ta shige cikin kafata sosai, ayya sorry, bari acireta yanzu, dan wani box nurse din ta bude ta zaro kan allura ta kwance dan kwalin dake kafarsa wanda ya yi jagab da jini,

kafar ta kamo ta nutsa allurar aciki ta fara kokarin sakato kwalbar, washhhhh! Junior ya fada tareda cusa kansa acikin wuyan kuluwa gamida sake damkar na shanunta, bude ido kuluwa tayi ta fara kallon nurse din wacce ta dage sai caka allura take a wurin da kwalbar take, dan Allah kiyi masa a hankali kuluwa ta fada idonta duk ya cicciko da kwalla, ganin kwalbar bata fita ba sai faman caka allura nurse din take yi yasa kuluwa fara zubar da hawaye, shi kuma junior da yake shagwababbe ne sai wani washhh, washh, washhh yake tayi tare da sake kankame kuluwa ajikinsa, hawaye kuluwa take zubarwa sosai saboda ganin irin wahalar da junior yake sha, idonta ta runtse lokacin da taga nurse din ta fara zaro kwalbar.

  Dakyar kwalbar nan ta fita akayi treating din wurin, anan ma junior babu irin rakin da bai nuna ba domin lokacin da yaji za asaka masa hydrogyen wata kwakuma ya kaiwa kuluwa tareda danna kansa cikin kirjinta, rungume shi tayi ta fara sinsinar sumar kansa wadda in banda kamshi babu abinda take yi,lokaci kankani bacci ya dauke junior,

sallama nurse din tayiwa kuluwa tana tsokanarta mijinki ya fiya raki da lalaci very lazy, gashi kema kinada saurin kuka, menene wannan awurin maza? Dan an sa allura ajikinsa shine zai yi kamar zaiyi kuka, ina jin ma yayi kukan nice ban gani ba, wlhi bai yi kuka ba, kuluwa ta fada da sauri,

dariya nurse din tayi junior ragon maza, ba rago bane shi wlh, fita nurse din tayi kedai kawai kin kare mijinki amma nasan junior har kuka yayiwa kwalbar nan, tana fita kuluwa ta kalli junior wanda ke kwance ajikinta sai kamshinsa take shaka,

sumar kansa ta fara shafawa saboda tasan bacci yake tareda shafa lips dinsa a hankali wadanda suka kasance jajaye jur, kankame shi itama tayi tana mai jin tausayinsa har cikin ranta,Allah sarki mijina Allah ya baka lafiya ta fada acikin zuciyarta.

A can Gida kuwa mom hankalinta ya kasa kwanciya dole sai da tasa driver ya kawota gidan junior, wannan shine karo na farko data zo gidan kuluwa, tana shiga falo babu kowa, wayar junior ta kira,

karar wayar mom dinne ta tadashi dauka yayi hello mom, junior kana ina? Mom ina dakin jidda, ok to kafito na ganka, mom shigo mana, to bari na shigo, ai kuluwa najin cewa mom zata shigo ta ture hannunsa daga kirjinta, sake mayarwa yayi, ta ture, ya mayar, ta sake turewa ya sake mayarwa,

kyaleshi tayi jin mom zata shigo amma ta rufe idonta ruf kamar me bacci, shigowa mom tayi ta ganshi kwance jikin kuluwa da yake wayayyiyar mace ce sai taji dadin ganinsu a haka saboda wannan ya nuna mata cewar kuluwa tana kulawa da junior sosai, sannu junior wai ya akayi haka ta faru? Mom wlh kwalbar turare na ajiye akan mirror ashe bata zauna ba shine ta fado ta fashe,

bayan na kwashe ashe kuma nabar wata abayana ban ganiba ina juyowa na takata shine ta shige cikin kafata, kafar tasa mom taje ta duba sannu junior, bari nakoma gida ka gaishe da hawwan,zataji mom, kin ganta nan bacci take,

yafada yana kallon mom duk kuwa da cewar yasan idonta biyu tana jinsu kawai kunyar mom take ji dan ta gansu ahaka, to shikenan junior Allah ya kiyaye gaba amin mom, dad bai dawo ba ko? Anjima shima zai dawo,

to nima zan zo gidan anjiman kila, to sai kazo, ni natafi, bye bye mom ya fada yana dariya, yawwa junior mom ta fada tareda ficewa daga cikin dakin.
[2/4, 6:19 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

  Na
UMMI A'ISHA

5⃣9⃣

Mom na fita kuluwa ta bude idonta amma wlh junior baka jin kunyar mom, meye abin jin kunya? Dan na rungume ki agabanta? Ai ba iya shi Kadai kayi ba, to me da me nayi?

Ka dauke hannunka pls, tashi ma zanyi naje salla ya fada a hankali, tashi yayi ya dingisa ya fita, itama tashin tayi ta shiga toilet, har tayi alwala ta koma kai ba alwala ce ta dace dani ba wanka ne ya dace dan junior ya sa na zubar da wani abu,

wanka tayi ta fito tayi salla tana idarwa ta shiga kitchen lokacin kukun su har ya gama shirya table, tana cikin zuba abincin junior ya shigo, afalo ya zauna ya kwanta kan doguwar kujera, kusa dashi taje ta zauna agefensa, j

unior tashi kaci abinci, me kake son ci? Wannan menene? Kuskus ne da miya, to bani kadan naci, zaune ya tashi, tunowa da tayi lokacin da suka je gidansu a baki taga mom tana bashi yasa itama ta fara bashi a baki, yau babu laifi ya dan ci abincin da yawa itama da kanta tayi mamakin haka, debowa a cokali tayi ta mika masa, kawar da kansa yayi, ka koshi? Eh nakoshi yanzu koko kawai nake son sha,

to yanzu a ina zan samo maka kokon junior? In fada miki a inda zaki samo? Eh ta fada tana kallonsa saboda ita bata gane abinda yake nufi da koko ba, ki dauko min peak guda daya ki faso min ita, tashi tayi ta dauki filet din ta fita, kitchen taje ta ajiye sannan ta dauko masa peak din guda daya kamar yadda yace.

    A inda ta tafi ta barshi anan ta dawo ta sameshi ta mika masa, karbar gwangwanin milk din yayi ya dagata ya shanye nan take, hannun kuluwa ya kamo tareda janta cikin jikinsa,

zaki bani kokon nasha? Ai baka fada min a inda zan samo maka ba, yanzu ai zan fada miki inda za a samo, bakinta ya tsotsa ya fara shafar wuyanta zuwa bayanta, kafin wani lokaci har ya fitar da ita daga hayyacinta, rigar jikinta ya zare ya fara shafarta ta kowanne sashi, bakinta ya cafka ya fara tsotsar shi dagaske, kowanne bangare na jikinta sai da bakinsa ya taba, duk wani abun da yasan idan yayi mata zata rikice babu wanda bai yi mata ba, numfashi kawai suke fitarwa daga shi har ita, kokarin fara harka ya soma amma kuma sai yaji ya kasa, domin abunshi ya dawo tamkar lagwani, yayi yayi iya bakin kokarinsa amma ya kasa,

dole haka ya hakura gashi ya shiga yanayi iya yanayi ita kanta kuluwar yanzu a bukace take dashi saboda ya gama cazata kuma ta cazu, a jikinsa ya rukunkume ta yana mayar da numfashi to wannan menene? Meyasa ya kasa shigar kuluwa? Kodai da matsala ne? Ita dai kuluwa wannan abun yafi komai daure mata kai, to junior bai san yadda zaiyi bane ko kuma dai fasawa yayi? Shiru tayi ta kwanta lakwas ajikinsa suna nan kwance acikin doguwar kujerar falon sukaji alamun bude kofa, waye? Junior ya fada da karfi,

mai gadine, oga kayi bako abokinka yazo, kace mishi yatafi an jima mu hadu agidan mom, ok sir, jan kofar yayi ya koma, ita dai kuluwa ta shiga damuwa sosai sai dai damuwar ta ko rabin rabin wacce junior ya shiga bata kai ba, zaninta ya rufa mata ya tashi yasaka jeans dinsa ya dauketa ya kaita dakinta ya dorata akan gado,

toilet dinta ya shiga yayi wanka ya fito yaje dakinsa ya sake kaya ya fito ya fita daga gidan ya nufi gidan mom duk kansa a daure yake yana son Sanin me wannan abun ke nufi? Me yasa ya kasa shiga jikin jidda ko dai bata da lafiya ne? Domin shi yafi dora rashin lafiyar akanta ya manta shi ko addu'a ba yi yake ba idan zai yi bacci babu ruwanshi da addu'a idan ya tashi babu ruwanshi da addu'a, idan zaiyi wani abu ko bisimilla ba yayi, alhalin ita addu'a ibada ce inji annabinmu,

acikin wani hadisi annabi yace "lallai ita addu'a ibada ce",a wani hadisin kuma yace"addu'a takobin mumini ce" sannan babu abinda yakai addu'a tasiri domin karfin addu'a yana iya kawo sassauci akan mummunar kaddarar da zata afkawa mutum, dan haka ya kamata muyi riko da addu'a domin annabawa da sahabbai basu riki komai ba face addu'a kuma da ita sukayi galaba, muduba kissar annabi musa da fir'auna,

ai karfin addu'ar da annabi musa da dan uwansa haruna suka yiwa fir'auna ne yasa ya halaka kuma Allah ya amsa musu, sannan annabawa da yawa sun riki addu'a kuma Allah ya amsa musu, domin shine yace arokeshi shi kuma zai amsa mana, ya Allah ka amsa mana.
[2/4, 6:25 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

  Na
UMMI A'ISHA

6⃣0⃣

   Gidan mom yaje acan ya hadu da bobo yana jiransa, to kai haka ake yi sai kaje min gida ko waya bakai min ba? Sau nawa zanyi maka wayar dan rainin hankali? Naga nakiraka yafi sau 10 baka yi picking ba, sorry bana kusa da wayar ne, ko falon mom basu shiga ba suka zagaya filon kwallon junior sai dai shi junior yau babu damar buga kwallon sakamakon ciwon dake kafarsa.

  Bacci kuluwa keyi kamar me saboda sabin shigace a tsarin, sai da yamma tayi lis sannan ta tashi tayi wanka tayi salla, oh ni kuluwa yau wanka biyu nayi wankan salla tab lallai mata akwai rauni, falo ta fita duk amma acikin damuwa take na abunda ya faru dazu tsakaninta da junior, abinci ta dan zuba taci tasha lemo ta sake kwanciya.

Har magrib tayi tana kwance sai da lokacin salla yayi sannan ta tashi tayi salla tana idarwa ta shiga dakinta tafara hade haden kayan matanta ta tasha, wanka ta shiga ta sake yi ta fito ta zira rigarta bayan ta jike jikinta da turare, bata jima da kwanciya ba junior ya dawo gidan,

dakinsa ya wuce yaje yayi wanka ya shiryo cikin kayan baccinsa ya taho dakin kuluwa, wuta ya kashe ya murza key a jikin kofar dakin ya hau kan gadon nata,

jikinsa ya dauketa ya sata ya fara yamutsa ta kamar yadda yayi mata dazu sai dai yanzun ma babu maraba da dazun domin bai iya aikata komai ba,

cikin narkakkiya murya yace jidda meke faruwa ne? Wlh nima ban sani ba tafada cikin daskararriyar muryar ta, rungumeta yayi ajikinsa ya fara lasar albarkatun kirjinta, wasa yafara da dukiyar fulaninta har yaji ya dan samu dama dama sannan ya kyaleta kowannen su zuciyarsa cikeda damuwa fal haka suka yi baccin wannan ranar.

  Kullum abunda ke faruwa kenan, zasuyi duk wasannin da suke so amma da zarar junior yayi kokarin sakawa sai ya kasa saboda ji yake ta zama kamar lagwani abun tashi,

duk cikinsu babu wanda bai shiga damuwa ba, nikaina Ummi A'isha na shiga damuwa saboda i eager na rubuto muku first night din kuluwa da junior domin naga kamar kuluwa ta raina junior alhalin kuma cwt Kausar ta raina faruq acikin kausar yar autar mata daga karshe jikinta ya gaya mata, hanfa ta raina tafida acikin Alheri dankone itama at the end tafida yabata wahala, shiyasa nake jiyewa kuluwa wuyar da zata sha duk ranar da junior ya dawo normal.

   Haka zaman nasu yayi ta tafiya ba tare da sun sanar da kowa ba, sai dai ita kuluwa tunda hakan ta faru take jin kunyar junior ido wannan bata iya hadawa dashi,

acikin wannan yanayin ne ya shirya domin komawa Ghana inda zai je yayi final exams dinshi wannan semester itace semester dinshi ta karshe daga ita ya kammala degree dinshi,kayansa ya zauna ya shirya acikin jakarshi, yana gamawa ya nufi dakin kuluwa wacce ke kwance tamkar marar lafiya saboda jimamin tafiyar junior da take yi,

tana jajantawa kanta yanda zata zauna acikin gidan ita kadai idan junior ya koma Ghana kuma ba komai ne yafi daga mata hankali ba illa sanyin da yanzu ya karu ya nunka nada, saboda yanzu ko rana bata fitowa gaba daya garin lullube yake da hazo, ga sanyi kamar kankara ake zubarwa a garin.



Ummi A'isha[2/6, 5:55 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

   Na
UMMI A'ISHA

6⃣1⃣


    Yana shiga ya sameta idonta yayi ja da alama kuka tayi, "rungumeta yayi jidda bafa wani jimawa zanyi ba 3 weeks kawai zanyi kacal, da zarar na gama exam dawowa gida zanyi kuma daga nan bazan sake komawa na dade ba", hawayen da take kokarin boyewa ne suka gangaro kan kumatun ta, "a'a jidda meye na kuka? Yi shiru kinji", shima duk maganar a karfin hali yake yinta saboda hankalinsa a jagule yake, "dauko hijab dinki mu tafi gidan mom sai ki zauna acan da daddare sai driver ya dawo dake", hijab dinta ta dauka suka fita, jakarsa yaje ya dauko ya rufe dakinsa yazo dakinta ya ajiye key din acikin drewar gadonta, fita suka yi tare har inda motarsa take, daga nan gidan mom suka yiwa tsinke, acan dinma lallashinta yake tayi kan ta saki ranta kar tasa damuwa acikin zuciyar ta, "pls Jidda don't keep your self in worrying, ki daina damuwar nan, tafiya ai ba mutuwa bace", "uhm junior shikenan tunda baka son na damu na daina", "to jidda what's the point of this worry? Pls ki saki ranki nan da 3 weeks zaki ganni na dawo", "Allah ya kaimu", daidai lokacin bobo ya shigo falon "ya baabah zo mu tafi na kaika airport din kaga time yaja", tashi junior yayi "ok bari na kira mom", dakin mom ya nufa Jim kadan suka fito tare, daidai lokacin shima dad ya shigo, "junior tafiyar ce?"  "Eh" dad, sakin mom yayi yaje ya rungume dad dinsa "dad ayi min addu'a final exam zanyi",

'Allah yabaka sa'a junior we whish you gudluck in your exams", "much tnx dad", kallon kuluwa yayi wadda ta sunkuyar da kanta, bai karasa inda take ba yace "jidda natafi,Allah ya kiyaye hanya" inji kuluwa tafada muryar ta na rawa, fita suka yi dukansu domin raka junior mota, dawowa junior yayi "am hawwa i have forget to tell you something, dan Allah idan zakije sch ki rinka saka nikab kina rufe fuskarki kinji??"  "Naji" ta fada ba tare da ta kalleshi ba, juyawa yayi ya fita, yana fita ta fashe da kuka, a haka mom ta dawo ta sameta tanata kukan tafiyar junior, kamata mom tayi suka shiga bedroom dinta wanda haduwarsa tafi gaban kwatantawa, akan gadonta ta zaunar da ita,

"kiyi hakuri hawwa kinji, ai ba jimawa zai yi ba, kinga nima idan naga kina kukan nan hankalina tashi zai yi, dan Allah kiyi shiru kinji", kukan ta daina amma hawaye basu daina sintiri akan kumatunta ba.

Fita mom tayi ta tafi sashen dad tabar kuluwa kwance a dakinta, tajima tana kuka sannan tayi shiru ta tashi ta fito, falon gaba dayansa kafe yake da hotunan junior kala kala, wani ma tun lokacin yana karami, wani yana pri sch, wani da kayan kwallo wani da kananan kaya yasha dan kunne da sarka, kai gasu nan dai birjik, dakinsa na da ta leka, komai a shirye kamar yana ciki, gefe gadonsa ga wani frame nan mai hoton jar flower ajiki an rubuta I LOVE YOU JIDDA, frame din ta dauka tana mamaki, ita jiddan ko wata yake nufi saboda bakinta da nashi bai taba furta mata kalmar so ba sai dai dazu taji dadin kalamansa da yace ta rinka rufe fuskarta wannan ya nuna mata kenan yana kishin wasu mazan su kalle masa fuskarta, rungume frame din tayi ajikinta tareda "furta love you too junior!."



6⃣2⃣


   Haka ta karaci zagaye zagayen ta agidan tana kallon kayan kiriniyar junior wasu abubuwan ma tun yana dan karami yayi amfani dasu amma SANADIN GATA yasa an adana su suna nan har yanzu, kayan wasan Sa kuwa ba acewa komai, ga kekunansa da machine da motocinsa harda dokinsa a daure duk nasa ne, lallai sai yau kuluwa ta kara jinjina irin son da mom da dad suke yiwa junior.

Ranar sai dare driver ya kaita gida, tana shiga taji kunci ya rufeta, mai gadine ya biyota ciki "gashi dazu abokin yallabai ya kawo wai abaki inji oga", karba tayi ta nufi dakinta, wayar junior ce kirar smart phone baka, kunna wayar tayi i love you jidda shine welpaper din dake kan screen din wayar, ajiye wayar tayi ta shiga wanka ta fito ko rigar bacci bata saka ba ta zizzira rigunan sanyi har guda hudu, ta tukunkune acikin blanket, wasu hawaye ne suka zubo akan kumatunta, sai yanzu taji hankalinta ya sake tashi da rashin junior, "yau zanyi baccin maraici tunda junior baya nan", fuskarta ta cusa acikin pillow, tana ta son tayi bacci amma ta kasa har asuba tayi.

  Washe gari ta shirya ta tafi makaranta yanzu tana dan samun saukin damuwar rashin junior saboda in taje sch tun 9 bata dawowa gida sai 4 da ta dawo kuma zata fara ayyukan gida ko ta fara karanta lecture note dinta, sai dai har yanzu ba tayi waya da junior ba tun tafiyarsa, yau bayan ta dawo daga sch tanata aikinta a kitchen kasancewar gidan babu kowa daga ita sai yar shimi da dogon wando, wayar junior ce tafara tsuwwa da sauri ta daga "hello junior", "jidda yagida?"   "Lfy lau ya papers?"

"Alhamdulillah kinjini shiru ko? Wlh phone dina na manta a taxi din dana hau sai yau aka kawo min, ko mom ma ba muyi waya da ita ba", "ayya to yakake"
"lfy lau, naga girki kike ko? Me zaki dafa?"
"Ta ina ka ganni?"

" Ai video call ne duba ki gani", da sauri ta kalli screen din wayar sai ga junior da gajeren wando yana kwance akan katifa, "ashe kallona kake, gaskiya ni ban shirya waya dakai ba sai kasa riga", "ki bari anjima zan kiraki to", katse wayar tayi cikeda farin ciki yau taji muryar junior kuma harma ta ganshi, tun daga lokacin kusan kullum sai sunyi waya da junior sunyi hira amma har yau bai furta mata Kalmar so ba haka itama bata furta masa ba, ko meye dalili? Ummi A'isha bata da masaniya.
[2/6, 6:13 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

  Na
UMMI A'ISHA


6⃣3⃣


   Yanzu damuwar kuluwa kalilin ce shine na rashin jin dumin junior domin yau ya kai kimanin sati 2 da tafiya, bayan tafiyarsa taje sharada ta wuni sau daya a gidan anty Salma sannan taje gidan mom dinsa ma ta wuni.

   Yau tun acikin Hall cikinta yake ciwo dan haka lokacin data fito daga lecture masallacin mata ta wuce taje ta kwanta, tana nan kwance yanmata sai shigowa suke amma ita fuskarta da nikab, masallacin cike yake da mata sai kace kasuwa sai hayaniya ake, kowanne group da hirar da suke, "hello teemah? Eh, Allah? Innanlillah, Allah ya saka miki wlhi, ai dan iska ne zai iya, tab amma ya cuceki", wata budurwa ce take furta wannan maganar lokacin da take yin waya, tana kashe wayar ta fara masifa

"kuji wai junior yayi aure dan iska, waye junior?" Suka tambaya, "wannan dan kwallon mana, saurayin teemah nefa cousin dina gaba daya ta gama sakankancewa shi zata aura kunji yayi aure, bakuga yadda ya rinka daukarta ba lokacin da suna soyayya, gashi sch daya suke lokacin suna karatu a kasar Cyprus kullum suna tare da yake itama yar harka ce har dakinsa take zuwa ta kwana kafin a koreshi daga makarantar", "au korarsa ma akayi?", "eh iskanci aka kamashi sunayi shida wata malama a office dinta daga nan aka koresu gaba daya shinefa ya koma Ghana ya sake Neman admission a wata makarantar to har lokacin basu rabu da teemah ba daga Ghana yake hawa jirgi yatafi Cyprus weekend wurin ta,kawai kuma sai yanzu wai taji yayi aure, kunji dan iska", "wai da shi din waye ubansa?"

"Wannan dan siyasar ne mana na nan garin", "ance ma ai matar junior din a sch dinnan take", "yo kwana nawane ita dinma zai saketa ai da zarar ya gama da ita zai yi waje da ita wlh tunda ba isa auren yayi ba aka yi masa", "eh ai SANADIN GATA ne yasa iyayen nashi yi masa aure yanzu", "kuma kun san gayen akwai kudi da kyau tunda dan kwallo ne duk wata biliyoyin kudi government take tura mishi", "ni kuwa zan so naga matar nan ta junior", "to ai ance ba shi ya Aurota ba iyayen shine suka aura masa ita", "lallai ashe auren gata aka yi masa", jin maganganun sunyi yawa yasa kuluwa tashi ta fita lokacin da zata fita taji wata na cewa "ai ana zargin cewar ma junior din ba dan halak bane", kuna taji zuciyar ta nayi mata, "wlh junior dan halal ne" tafada acikin zuciyarta saboda duk wanda yaga junior yaga dad dinsa to zai san shine ya haife shi gashi dai ya dauko hasken mom dinshi amma duk da haka yana kama da dad dinsa ita kanta wani lokacin ma ganin kamar junior da mahaifinta take, "kai Allah ya kyauta meye amfanin haka yanzu?" Ita dai tasan junior gagararre ne amma bata tsammaci abin nasa yakai haka ba.

Waya tayiwa driver dinta yazo ya dauketa duk da cewar bata gama lecture dinta ba amma dai gara ta koma gida zai fi mata, yau taji duniyar tayi mata zafi sosai, tana zuwa gida ta kwanta a falo, haushin junior ta ji yana shigarta wato dama har korarsa a kayi a sch? Kalaman wata dataji tana fada ne ya fado mata,"ai insha Allah shima haka za ayiwa yayansa", "to kuma ai "yayan junior "yaya nane tunda nice mahaifiyar su, kai amma gaskiya junior ya bata wayonsa".



6⃣4⃣


    Haka ta zauna cikin damuwa amma ba tayi kuka ba sai dai idonta yayi tsananin ja, dakinta ta koma ta kwanta duk jinta take kamar bata da lafiya. Washe gari da safe ta dauki waya ta kira junior domin tana son zuwa asibiti ciwon ciki na damunta, tanata ringing ba a dauka ba, can taji mace ta dauka, da Sauri ta duba saboda video call suke yi da junior tana dubawa taga wata budurwa ce daga ita sai towel a dakin junior, da Sauri ta katse wayar ta samu wuri ta zauna ta ma rasa me zatayi, tana nan zaune junior ya fara kiranta, kin dauka tayi har tayi karar ta gama, text ya turo mata pls Jidda pick my call, banza tayi dashi, "kenan duk abinda taji an fada jiya akansa gaskiya ne?" Text ta tura masa cewar zata tafi tabar gidansa idan ya sallami karuwar tasa ya aiko mata da sakinta, tana gama tura text din ta kashe wayarta ta fara hada kayanta cikin babban akwati, lokacin da junior yaga sakonta ba karamin tashi hankalinsa yayi ba domin shi wlh bama ya gidan lokacin da ta iyo wayar, kuluwa na gama hada kayanta ta dauka ta fita ta sa driver ya kaita garinsu wato kauyen ciyako.

  Hankalin junior ba karamin tashi yayi ba gashi babu halin ya taho gida saboda ya fara exam, dole ya dan cire damuwar acikin ransa.

Ita kuwa kuluwa ko hawaye kasa zubarwa tayi kuma tayi alqawarin ba zata sanar da kowa wannan sirrin ba domin tsakaninsu ne ita da junior dan haka idan ta tona asirinsa tamkar ta tonawa kanta ne, shiyasa ma taga rashin dacewar taje gidan anty salma da sunan yaji ko kuma gidansu junior din domin dole sai an ji dalilin zuwanta ita kuma bata son kowa yaji.

   Karfe 1 na rana suka sauka a garin ciyako, nan driver ya shigar mata da kayanta, iyatu tana kwance ba ta da lafiya tun sati biyu da suka wuce ko tashi bata iya yi, babanta kuma yana zaune a tsakar gida, ganinta ya sashi fara fara'a "yau su hawwa'u ne agidan?", "eh nice baba", karasawa tayi ta durkusa agabansa, driver ne ya shigo da akwatinta bayan sun gaisa da babanta yace "hajiya da akwai wani abu ko na tafi?"

"A'a malam Isah kaje kawai Allah ya kiyaye hanya", "amin amin hajiya" ya fada tareda dan russunawa.
[2/6, 6:27 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

  Na
UMMI A'ISHA

6⃣5⃣

  Cike da annuri mahaifinta ya dubeta "kuluwa kinga abinda nake fada miki da jimawa ko? Dama nasan insha Allahu rayuwarki ba zata tozarta ba kuma naji dadin hakan, Allah ya barki da mijinki lfy", "amin baba" kuluwa ta fada tana sunkuyar da kai, "baba iyatu bata da lafiya ne?", "Eh tafi kwana 10 akwance da a asibiti ma take to jiya sai suka sallamomu suka ce mu dawo gida", "ayya Allah ya bata lafiya baba", "amin hawwa'u ina mijin naki?", "Baba yana can a Ghana sai ya dawo zai zo mu tafi tare", "to shikenan abu yayi kyau, Allah ya dawo dashi lafiya", "amin baba", kayanta ta kinkima takai dakin iyatu ta ajiye ta kwanta dan ta huta amma tunanin junior ya hanata, tabbas duk labaran da taji an bayar akan junior gaskiya ne sai dai ita kuma wannan ba zai zama dalilin da zai Sa ta rabu dashi ba, sai dai tayi alqawarin nuna masa bacin ranta,iyatu ce ta motsa ta kalleta baki a karkace, "kuluwa yaushe kika zo?", "Sannu iyatu, ya jikin naki?", "Da sauki", "dazu Nazo iyatu Ashe baki ji dadi ba?"

"Wlh", "to Allah yasa kaffara ne", "amin hawwa, dan Allah kiyi hakuri ki yafe min nasan duk hakkin ki ne yake bibiyata", "babu komai iyatu na yafe miki duniya da lahira", "nagode kuluwa Allah yayi miki albarka", "amin iyatu, Allah ya baki lafiya". Tunda kuluwa tazo gidan kullum itace ke jinyar iyatu har tayi sati daya da zuwa, duk ta shiga damuwa amma kuma babu halin ta fita tunda bata sanar da junior ba kuma tasan fita ba tareda izinin miji ba laifi ne babba, yaro ta samu ta aika shi gidan mairo tace "yace mata tazo gari", aranar da yamma sai ga mairo agidan da yaranta, dakin baban kuluwa suka shiga suka fara chafta, "kuluwa amarya ya mijin naki?", "lafiya yake Mairo, Ashe dai haka aure yake da dadi Mairo? Ai ban gane ba har sai da nayi", "kuluwa ai kedai ki bari amma gaskiya aure yayi, naga ma kamar ciki ne dake", "wlh Mairo ni banida wani ciki yanzu ma fashin salla nake yi", "ah to zan kawo miki kayan gyara kin San idan mace ta gama tana dan budewa, dan haka zan aiko miki da bagaruwa da ganyen magarya da zarar kin gama ki tafasa kiyi amfani dashi", "to Mairo na gode", kuluwa ta fada, "dama kina amfani da almiski ko?" "Eh tun kafin nayi aure ina using dashi", "yawwa to kici gaba zaki bani labari", dariya kuluwa tayi saboda ba zata iya fadawa Mairo Cewar har yau babu abinda ya gudana tsakaninta da junior ba, nan dai suka sha hirarsu Mairo ta tafi daf da magriba.

   Kwanan kuluwa 10 a ciyako junior ya sauka a Nigeria, yadda bata sanarwa da kowa ba haka shima bai sanar da mom cewar bata nan ba, aranar da yazo da yake zuwan safe yayi ya nufi gidan mom, rungume shi mom tayi, "barka da dawowa junior na, ina matar taka? Ta fara laulayi ko?" Murmushi junior yayi "mom ita ko ciki ma bata dashi", "me kace junior? Har yanzu?", "Wlh mom ni har yau babu abinda ya shiga tsakaninmu saboda da zarar naje da niyyar kusantar ta kasawa nakeyi", "amma junior me yasa tun lokacin baka sanar dani ba? Kai junior har yanzu na fahimci kuruciya na damunka, ba a boye irin wannan matsalar, ni ya kamata ka sanarwa tunda nice na haifeka amma insha Allahu za a samu waraka, zauna ina zuwa".



Ummi A'isha[2/8, 8:43 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

Na
UMMI A'ISHA

6⃣6⃣

  Tashi mom tayi ta nufi dakinta ta dauko gyalenta "maza tashi muje", tashi junior yayi yabi bayanta, "dauko mota kazo mu tafi", motarsa ya dauko mom ta shiga yaja suka fita daga gidan, unguwa uku suka je wurin wani malamin zaure, yana da almajirai fiyeda guda Dari sai karatu suke tayi a kofar gidan nassa, lokacin da suka shiga wurinshi mom da kanta tayi masa bayanin komai, girgiza kai yayi "tabbas ana samun irin wannan matsalar amma ba komai bane face sihiri dan haka sai a kula da yawaita addu'o'i da ambaton Allah a kowanne irin lokaci", tunani junior ya fara tabbas teemah ce tayi masa wannan aikin, rubutu malamin yayi a allo ya wankewa junior yasha "yace insha Allah za asamu waraka amma asa acikin rai sauki daga Allah yake domin shi keda ikon warkarwa ko kuma dorawa", "to Malam na gode yanzu menene abun sadaka?" "Hajiya ko naira Dari kika bayar ta isa", "a'a Malam ga wannan dai Allah ya saka da alkairi", tashi suka yi suka fito junior na gaba mom tana biye dashi, bayan sun koma gida ne yake sanar da mom cewa "zai tafi ciyako yanzu saboda kuluwa ma tana can ganin gida", adawo lafiya mom tayi masa ya tafi,gidansa ya koma yayi wanka ya dauki duk abinda zai bukata ya kama hanyar chiyako.

  Karfe 5 na yamma ya shiga cikin kauyen, sai da yayi tambaya kafin ya samo gidan su kuluwar, kansa tsaye ya shiga gidan bayan ya yi packing din motarsa a kofar gidan, lokacin da ya shiga kuluwa tana tsakar gida tana tafasa bagaruwa da ganyen magaryar da Mairo ta kawo mata, babanta kuma yana kishingide, sallama yayi cikin muryarsa mai sa kukuwa jin kasala, take ta gane shine, "sannu da zuwa", babanta ya fada bayan ya amsa sallamar tasa, "karaso karaso mutanen turai, ni ai rabon da na ganka tun baka fi shekara uku ba", kusa da baban junior yaje ya zauna ya fara gaisheshi ita dai kuluwa dan kar agane tsakaninta da junior akwai matsala ne ya sata yi masa sannu da zuwa gamida gaisheshi amma duk fuskarta babu walwala, daki ta koma ta dauro zani tazo ta juye kayan data dafa ta shiga wanka duk junior yana kallonta amma sai hirar su suke yi shida babanta. Har dare yayi junior suna tare da baban kuluwa hatta salla tare suka yi duk kuluwa tana jinsu lokacin da take yin abinci, sai da suka ta da sallar magrib sannan ta dan samu damar kallon junior tunda lokacin suna salla tasan ba ganinta zai yi ba, yana sanye da manyan kaya milk colour din yadi da hula yayi wani fresh dashi gashi fatarsa tayi haske, daki ta wuce wurin iyatu suka fara hira domin yanzu ta dan samu sauki sosai. Bayan ta gama girkin ne ta zuba musu shida baban ta kai musu ta koma daki bata san lokacin da suka gama hirar da babanta ba saboda ita tana yin sallar isha tayi bacci dama lokacin iyatu ta dade da bacci da yake lokacin sanyi ne.

  Cikin bacci taji anyi sama da ita kamar a mafarki, tsorata tayi sosai sai kuma taji kamshin turaren sa, da saura kadan ta kurma ihu, a dan dakin dake cikin soro ya shigar da ita dama anan yayi masauki, dakin duhu didim ga uban sanyi saboda ko kofa babu aciki, gashi iya tabarma kawai ce aciki sai dan abun rufar da bashida wani kauri, ko pillow babu,ga uban sauro, tausayin junior taji ya shigeta musamman ma da ta tino irin gatan da yake dashi, agida dakinsa ko na sarki iyakaci kenan amma yau gashi ya na kwance akan tabarma alhalin shi gadonsa ma ba a kasar nan aka sai masa ba, kwantar da ita yayi ajikinsa, yafara kissing din wuyanta da fuskarta "jidda meye haka?? Me yasa zaki yi min haka?", "Me nayi maka? Ai ni banyi maka komai ba saboda dama can nasan ba sona kake yi ba", "wa ya fada miki bana sonki?", "Ai da kana sona da zan sani, dama ko Kalmar so baka taba furta min ba", kansa ya dora a tsakiyar na shanunta ya shafo fuskarta "wlhi jidda ina sonki, ke kadai ce macen da gangar jikina da ruhina ke so, wlh ina sonki har acikin raina", "ai junior duk abinda zaka fada ni yanzu bazan yarda da kai ba saboda nasan duk ba gaskiya bane", hannunsa yasa ya damko na shanunta guda daya "wlh gaskiya nake fada miki ki yarda dani", "wlhi bazan yarda dakai ba junior saboda baka da gaskiya ko kadan, akwai wacce kake so na sani to nima ina da wanda nake so tun kafin na aure ka, dan haka ka sakeni nima na auri mai sona, ka sakeni, dama can ni shamsu nake so",wai ji yayi kamar ta zuba masa wuta hannunsa junior ya janye daga kan dukiyar fulaninta ya matsa daga jikinta "tashi ki fice min anan" ya fada cikin tsawa, "nace ki tashi ki fita, i said get out" ya sake fada cikin tsawa, tashi tayi ta fita jikinta har rawa yake yi saboda tsoron junior bata taba Sanin haka yake ba, dakin iyatu ta koma ta kwanta ta fara kukan zuci har tsawon wani lokaci, shima junior hakan take saboda kalaman kuluwa sunyi mutukar yi masa zafi, "shi zata kalla tace ya saketa saboda da taga ya kasa biya mata bukatar ta?" Hawaye ya fara zubarwa saboda bacin rai,wannan shine karo na farko da yayi kuka tun tasowar shi domin SANADIN GATA yasa iyayensa kauracewa duk wani abu wanda zai iya sashi kuka, daren ranar bai yi bacci ba.

  Washe gari da safe ya tashi idonsa jajur kamar gauta, bai ci abin karyawar da aka kawo masa ba, bayan sun gaisa da Baban kuluwa yace masa "yau zai koma kano", "ai sai ku tafi tare da hawwan tunda iyatun yanzu ta samu sauki", "to baba", duk wadannan maganganun a cikin kunnen kuluwa, daki ta shiga ta hada kayanta ta fito yanzu duk a tsorace take da junior saboda jin tsawar dayayi mata a daren jiya.
[2/8, 8:54 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

  Na
UMMI A'ISHA

6⃣7⃣


    Tana fitowa tsakar gida kawarta Mairo ta shigo, bayan sun gaggaisa da su baban ta ne suka kebe ita da mairon, "kuluwa ga wata bagaruwar na kawo miki kiyi ta amfani da ita kuma duk lokacin da kika gama period ki tafasa ganyen magarya kiyi amfani dashi in dai kin riki wannan wlh babu ruwanki da neman wasu kayan matsi", "to Mairo nagode kinga yanzu ma tafiya za muyi sai Allah ya kaimu wani lokacin idan na dawo", "Allah ya kaiku lafiya kuluwa amma wlh mijin naki kyakkyawa ne kamar ma yafi ki kyau, ke bama kama bace wlhi ya fiki kyau da aji", "to Mairo nagode da wannan cin fuskar", dariya Mairo tayi "ai kin san abinda na fada haka yake ba kage nayi ba", sallama suka yi da Mairo ta tafi ita kuma kuluwa ta je tayiwa iyatu sallama, har waje iyatu ta bisu tana sanyawa kuluwa albarka tareda zubar da hawayen nadamar abubuwan da tayi wa kuluwa a baya.


   Kuka kuluwa ta dan fara yi lokacin da ta shiga motar, har bakin motar babanta yazo ya na yiwa junior magana"Abdulrahman ayi ta hakuri kaji, kasan mata sai da hakuri, dan Allah ayi hakuri da juna", "ah baba babu komai kuma insha Allah babu wata matsala, to Allah yayi muku albarka" amin baba", motar ya tada ya fita daga kauyen ya dau hanyar birni.

Tsit cikin motar yayi saboda yau ko dan music din ma junior bai kunna ba sai fuskar shi da ya daure kamar wanda aka aikowa da mutuwa, wani irin kwarjini kuluwa taga yayi mata gashi dai ko a haife ba da wasu shekaru masu yawa ya fita ba saboda ita ahalin yanzu shekarunta 24 shi kuma tasan a yayi shekaru da yawa yayi 27 saboda junior yaro ne karami kawai SANADIN GATA ne yasa su mom yi masa aure a shekarun da yake yanzu, harare hararen da ta kula yana ta yine ya sata kifa kanta cikin cinyoyin ta ta yadda ma ba zata ci gaba da ganin muzaran da yake yi ba,kamar wadda aka tsikara sai ta fara kuka mai sauti, kyaleta yayi yana jinta tana kuka ita kuma bakin cikin yaki kulata ya sata sake daga murya, packing din motar yayi a gefen titi tare da daka mata tsawa " ke ya isheki haka, ko kiyi shiru ko kuma ki fice min acikin mota" jin tsawar da yayi mata ya sata yin shiru cikin mintocin da basu fi 2 ba, sai da yaga tayi shiru sannan yaci gaba da driving din.

Motar shiru haka suka ci gaba da tafiya har suka isa wudil sai a nanne taji ya dauki wayar sa ya kira bobo " hello bobo, na kusa shigowa fa, mu hadu kawai a gidan mom, nifa ban son kana zuwa min gidana gaskiya, yes mu hadu acan din, ok sai na shigo" ajiye wayar yayi tareda jan tsaki da karfi sannan ya daki sitiyarin motar.
[2/8, 9:05 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

  Na
UMMI A'ISHA


6⃣8⃣


   Da sauri ta dago kanta ta kalleshi ya ko juyo ya galla mata wata harara, take taji yan hanjinta sun juya, yau tsoron junior take ji sosai, "wayyo Allah na, yau ko zai bani dumin ma ko kuma shareni zai yi?" Ta fada acikin zuciyarta, "tab ai yau kema kin san ragargaza ki zai yi da gaske bada wasa ba, dan yau watakil sai ya rabaki da budurcinki,gashi kuma kuruciya na damunsa kila ta farat daya zai yi miki" wata zuciyar ta sake bata amsa, "hmmm" ta saki ajiyar zuciya mai karfi, har suka isa kano a tsorace take dashi ko kwakkwaran motsi ta kasa yi, sai dai duk inda suka dan tsaya ko a trapic jump haka sai taga anata kallon junior ko ana nuna shi ana cewa shine dan kwallon nan da haka har suka shiga unguwar su wato shagari quarters.

  Lokacin da suka shiga cikin gidan bayan yayi packing ya juyo ya kalleta, "ni kika cewa na sake ki ko? To bazan sake kin ba kiyi duk abinda za kiyi, inma zan sakeki sai bayan na gama koya miki hankali tukunna stupid kawai", take nadama ta shigi kuluwa jikinta yayi sanyi sai ta fara kuka kuma, kallonta yayi aransa yace "jita shagwababbiya kawai daga fadin haka har ta fara kuka, na rasa me yasa take da saurin kuka, daren yau akwai koke koke kenan, kiyi kukan ki ki gama kafin kiyi mai dalili da daddare dan yau duk kukanki sai nasha koko, nima jiya har kukan kika sani", duk acikin ransa yayi wadannan maganganun, bude kofar yayi ya fita "yace in kin gadama ki fito min daga cikin mota idan kuma baki gadama ba kina iya kwana aciki".

Juyawa yayi ya wuce ciki, cikin kuka kuluwa ta fito ta dauki jakar kayanta ta nufi cikin falon gidan, dakinta ta shiga ta kwanta bayan ta gama kukan da take yi. Tana nan kwance junior ya leko dakin nata, "kije ki gyara min dakina kafin na dawo", tashi tayi tabi bayansa da kallo ya sake kaya cikin brown din jeans da farar t shirt mai gajeren hannu ajiki an rubuta nectar,gashi yayi kyau sosai ya fito a junior dinsa na asali mai tashen kyau da kuruciya, kamshin da ya saba bar mata duk lokacin da ya shigo dakin yau ma shi yatafi ya bari sai kace aciki ya fesa turaren.

Tashi tayi ta nufi dakin nasa a karo na farko,budewa tayi ta shiga, dakin ya hadu sosai gashi yayi biyun nata a girma da fadi saboda an shirya shi ya shiryu, komai na dakin ja ne tun daga kan gadon ciki wanda yake katoton gaske har bedsheet din da blanket da labulayen duk red ne, gefe kuma an shirya wurin da yan kananan kujeru jajaye guda uku an shirya su kamar falo da wani dan center table a tsakiya, dakin ta gyare tsaf ta fesa air freshener da turaren tsinke, kallon gadon tayi, "oh akan gadon nan za ayi yakin rabani da budurci na, ko yau ko gobe,Allah yasa ba yau zai bani wannan wahalar ba".
[2/8, 9:42 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA

  Na
UMMI A'ISHA

6⃣9⃣-7⃣0⃣

  Bayan ta gama gyaran dakin ta wanke masa toilet dinsa wanda shima yake a tsare kamar a kasar turai, wani katon kwandon roba ta gani wanda yake tara kananan kayansa masu datti da kayan da yake ball dasu gasu nan sunfi akirga da alama duk wanda ya cire baya maimata su sai dai ya bude sabbi yasa.

Kayan ta kinkima ta shiga toilet din ta fara wanke masa su, tunda ta fara bata tashi ba sai da lokacin salla yayi, tana idarwa ta sake dawowa taci gaba da yin wankin, wuni tayi tana yi masa wankin kayansa har sai da ta wankesu kaf lokacin har yamma tayi lukwi. Agajiye taje kan dining ta zubo abunci ta zauna taci ta kwanta akan kujera a falo, yau jinta take agajiye lis tayi mugun gajiya.

Bayan sallar isha ta shiga dakinta ta kwanta bayan tayi wanka, yau ana surfa sanyi amma tasan junior ba lallai ne yazo dakinta ba tunda taga fushi yake yi da ita. Karfe 8 junior ya shigo gidan ganin irin aikin da kuluwa tasha ya sashi niyyar kyaleta yau saboda ta aikatu mutuka, "hmm yau zan barki ki huta saboda kin gaji dan haka zan barki  amma gobe sai kinyi bayani acikin dakin nan", haka junior ya fada acikin ransa, dakin kuluwa ya shiga tana kwance ta lulluba, "tashi kiyi alwala kizo muyi salla", bedsheet din taja ta rufe jikinta ta tashi saboda bata son ya ganta a haka domin rigarta bata da maraba da tsirara, fita yayi daga dakin ganin tanata kunbiya kunbiya, sai da ya daidaici ta gama sannan ya dawo dakin lokacin ta saka dogon hijabi ta shimfida abin salla.

Salla ya jasu suka yi raka'a 2 suka idar, kowannensu addu'a ya fara yi acikin zuciyarsa,addu'ar kuluwa ta kare ne akan Allah yasa junior ya zauna da ita har abada, shi ma junior addu'arsa ta tafi ne akan Allah yasa ta so ta kaunace shi kafin daga baya ya tashi ya koma dakinsa yaje ya kudunduna acikin bargo, sanyin yau jinsa yake yafi na ko wacce rana gashi baya son zuwa jikin kuluwa yau dan ya tabbatar ba zai iya yin hakuri ba muddin ya jita a kusa dashi, gashi tasha aiki ta gaji wannan ne ya sashi tausaya mata yaga gara ya kyaleta ta huta in yaso gobe sai ayita ta kare. Kasa bacci yayi saboda sanyin da yaji yana faman ratsashi, zaune ya tashi ya kudundune jikinsa wuri daya yana ta faman rawar dari, jikinsa sai karkarwa yake, shi dama ko agida in dai da sanyi ne to mom bata hutawa da hidimar sa duk abinda tasan zai bashi dumi to sai ta nemo masa.

Abangaren kuluwa kuwa yau ta gama tsurewa da lamarin junior saboda ko lokacin da ya shigo su kayi sallar nan jikinta ya gama bata cewar junior bazai rabuda ita a daren yau ba, labarin da Mairo ta bata lokacin da tana amarya ne ya fara dawowa cikin kwakwalwar ta,"wlh kuluwa idan mutum ya hadu da marar tausayi tsaf zai raunata ka domin sai yayi maka fata fata, wani ma saboda tsabar rashin tausayi yana ganin kana fitar da jinin wahala amma ba zai barka ba har sai ya gaji dan kansa sannan zai bari, ni kinga duk ihun da nayi mutumin nan bai barni ba har sai da ya cika burinsa" ajiyar zuciya kuluwa tayi "hmm to ni ko ya zamu kare da nawa gwanin? May be nima sai yayi min fata fatan". Tunanin abin tai tayi acikin ranta har bacci ya dauketa ga uban sanyin da take ji yana ratsata.

Washe gari da safe kuluwa ta tashi ta shirya breakfast tayi wanka ta danyi simple make up saboda yanzu tsoron junior take yi sosai gashi yaki sakar mata fuska sai daddaure fuska yake yi, tana zaune a falon tana shan madarar gwangwani ta ruwa ya fito daga dakin daga shi sai boxer babu riga ajikinsa yana tafe yana wakar fall in love, kitchen ya shiga bai jima ba sai gashi ya fito da maltina a hannunsa, kan dining ya hau domin karyawa, "ina kwana?" Kuluwa ta fada tana satar kallonsa, "lfy", ya amsa a takaice amma a ransa yana cewa "gara kam kisha madara ta ratsaki saboda yau a gidan nan bazan barki ba har sai na rabaki da abunda kika yi shekara da shekaru dashi a jikinki", ita kam kuluwa bata san shirin da junior yake yi mata ba dan haka sai kawai taci gaba da durar kayan matanta, kamar wadda aka saka haka ta wuni tana shan kayan mata, hatta bagaruwar da Mairo ta bata sai da ta tafasa tayi tsarki da ita,wunin ranar junior yana gida babu inda yaje sai da la'asar tayi sannan ya fita daga gidan ya tafi gidan mom.

  Tunda yaje gidan mom ke tambayar sa "ko yaji sauki ko kuma har yanzu akwai matsala?", "Mom babu matsalar komai duk dai da cewar har yanzu babu abinda ya faru amma nasan insha Allah naji sauki", "to Allah yasa junior","amin mom". Sai da yakai har dare agidan mom sannan yayi sallama ya dawo gida lokacin kuluwa har ta kule acikin dakinta bayan tayi shirin bacci.

  Sai da junior ya gama dukkan abunda zai yi, yayi wanka ya sha turare sannan ya nufi dakin kuluwa tana kudundune ya yaye bargon data rufa ya daukota cancak ya nufi dakinsa da ita, daga ita sai yar rigar bacci yar karama wacce tayi mata kyau domin kuluwa tanada kiba ba siririya bace wannan dalilin ne yasa ko ina najikinta a cike yake, musamman ma kirjinta, kan makeken gadonsa ya kwantar ta ya kashe light din dakin, acikin duhun ya lalubota ya janyo ta jikinsa, rungumeta yayi ya zira bakinsa cikin nata ya fara lasar lebenta na kasa, a hankali ya rabata da rigar dake jikinta ya fara wasanni da albarkatun kirjinta, abun yazo kenan "dama nasan akan gadon nan zai rabani da budurcina", ta fada acikin ranta, lasar jikinta ya fara tako ina kafin ya fara kokarin Isar mata da sakon shi, kuka kuluwa ta fara wurjanjan.

  "Wayyo nashiga uku", shine kawai abunda kuluwa ke furtawa lokacin da junior yake kokarin shigarta, "junior dan Allah kayi hakuri wlh bazata shiga ba in kace sai ta shiga kasheni zaka yi, wayyo mom kizo junior zai kashe ni, wayyo babana, dad, junior dan Allah kayi hakuri wlh zan mutu, Mairo kin cuceni, Allah ya isa tsakanina dake Mairo, wayyo, wayyo......!" Kara kuluwa ta kwalla da karfi sakamakon jin junior ya dage karfinsa akanta sosai, "wayyo Alla", kuka ta ci gaba da rerawa har junior ya cika burinsa ya zama cikakken ango bayan ta gama jigata, kukan ma dakyar take iya yinsa saboda tsabar ta wahala, muryarta ko fitowa ba tayi, sai da junior nutsuwar sa ta dawo sannan abinda kuluwa tayi ya fara dawowa masa, abun ma abun dariya, harda su yiwa Mairo Allah ya isa, "ko me tayi mata haka?" Shikam yau yasha duka da cizo har dasu yakushi, ga bakinta yanda ya rinka ambaton junior kilama har a makota an jiyota, janyota yayi ya kwantar da ita asaman jikinsa sai ajiyar zuciya take yi, hannunsa ya mika ya dauko phone dinshi ya kunna light ya haske fuskarta, duk tayi gaje gaje da hawaye harda majina gashi sai jan zuciya take wadda yaki karewa, sai dai ta inda yaji dadi ta wuri daya ne da bai ji mata ciwo ba domin wurin babu ko digon jini kuma dama yawancin doctors suna cewa dalilin fitar jinin nan shine idan anjiwa mace ciwo, kankame ta yayi tamkar zai mayar da ita cikin cikinsa ya fara lasar kumatunta, wani sobon sonta da kaunarta yaji yana shigarsa, ga wani tausayinta da yaji ya ratsashi, "Allah yayi miki albarka jidda, Allah ya albarkaci rayuwarki, Allah ya bamu yara masu albarka, Allah yayi miki albarka" haka yayi ta furtawa a zuci da fili, ita dai kuluwa bata san abinda yake yi ba domin tuni bacci ya dauketa.



   Ummi A'isha[2/12, 1:01 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA!

    Na
UMMI A'ISHA

7⃣1⃣


  Lumshe idanuwansa junior yayi tare da yin wani lafiyayyen murmushi shi kadai wanda bai san ko na menene ba, sake kankame kuluwa yayi gamida shafar kanta kamar wata jaririya, tunanin ragwantar ta kawai yake duk dai da cewar yasan tayi dauriya amma duk da haka surutan ta dariya suke bashi idan ya tuno su, hannuwansa biyu yasa yasake gyara mata kwanciyar ta ajikinsa, nan shima baccin ya daukeshi saboda dumin jikinta da yake shigarsa.

Sai da asuba tayi sannan junior ya tashi a hankali ya shiga toilet yayi duk abinda zai yi ya fito, yau kam ko masallaci bazai iya zuwa ba, agida ya zauna yayi sallarsa,bayan ya idar ya tashi ya koma inda kuluwa take, bacci take sosai kamar me baccin mutuwa, a hankali ya yaye bargon ya shiga jikinta, bakinsa yakai kan na shanunta ya kama, motsi ta fara yi amma kuma bacci yasha kanta, ci gaba da shafarta yayi har gari yayi haske karfe 6 tayi.

Tashi ya kuma yi ya saka kayan motsa jikinsa ya fita yau bashida niyyar zuwa gidan mom amma ya zabi yayi dan jugging daga gidansa zuwa bakin titi.

Kiss yayi mata a goshinta ya yiwa kumatunta sannan ya dan lashi lips dinta ya fita, duk sanyin nan haka yafita yana dan gudu gudu ahankali ya nufi titi straight wanda zai kaishi babban titin unguwar, dama shagari quarters unguwace da babu jama'a da yawa asalima gidajen tsilla tsilla suke, babu ruwan kowa da wani.

A bangaren kuluwa kuwa sai da tasha bacci ta more sannan ta iya tashi a hankali amma kuma sai taji ta kasa tashin, bude idonta tayi ta fara tunano abunda ya faru tsakaninta da junior ita da ta rainashi gani take kamar ba zai wani iya wahalar da ita ba ashe shima gwarzo ne, "tab! Wuya ba kyau" ta fada a hankali, kallon dakin ta fara yi shine ya fice ya barni acikin wannan halin saboda tsabar rashin tausayi? Dakyar ta iya saukowa daga kan gadon ta shiga toilet, bahon wanka ta cika da tafasasshen ruwan zafi sannan ta shiga amma taci azaba sai da ta daure, wanka tayi ta fito ta dawo dakin,can ta hango sleeping dress dinta a kasa, murmushi tayi "oh junior manya", jallabiyarsa ta dauka ta zira tayi salla bayan ta idar ta cire ta saka rigar baccinta ta jiya ta koma ta kwanta.
[2/12, 1:09 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA!

     Na
UMMI A'ISHA

7⃣2⃣

Tana kwanciya junior ya bude kofa ya shigo, hangota da yayi akan gadon ya sashi karasawa ya hau gadon ya dauketa a jikinsa, fuska ta bata tasha kunu

Kallon fuskarta junior yayi, "Jidda na!" Baki ta tabe "ka rabani da budurcina kaji dadi", wani dan murmushi junior yayi "ni ban rabaki dashi ba yana nan har yanzu ajikinki"

"Yawwa gara haka saboda shamsu kullum zancensa...." "Ke!" Ya fada cikin tsawa "ban hanaki ambaton sunan nan ba? Oh har yanzu baki hakura da shamsun ba kenan?

Nace har yanzu baki cire shi acikin ranki ba ko? Nasan maganinki, zanyi maganin ki yanzu yanzun nan", tashi yayi ya shige toilet, ita dai kuluwa tana kwance tana jiran hukunci, gabanta ne ya fadi "ko cewa zai yi ya sakeni?

Nasan junior da zuciya kila ya ce ya hakura dani, amma da na shiga uku in dai ya sakeni ina zan dosa? Gashi ko warkewa daga jinyar da ya dora min jiya banyi ba", acikin ranta take yin wadannan maganganun, fitowar junior ce ta katse mata tunaninta daga shi sai gajeren wando, kai tsaye kan gadon ya wuce, yana zuwa hayeta, tureshi ta fara kokarin yi, "ka bari in ba so kake ka lahanta ni yau ba,saboda har yanzu ma ban gama warkewa daga na jiya ba".

"Zaki fada musu ne, ba dai kince wani kike yiwa tanadin budurci ba? Shine dalilinki na jin haushina saboda na fara kokarin rabaki dashi? Ai na dade da fada miki kar na kara jin kin yi min zancen wannan yaron amma baki ji ba",mamaki ne ya kama kuluwa jin ya kira shamsu da yaro bayan ita kuma tasan shamsu ya girmeshi sosai ma, rigarta ya fara ja zai cire, ai tana ganin haka suka shiga kokawa, "zaki batawa kanki lokaci ne gwara ma ki kyaleni na biki a hankali, tunda dai akwai wanda kike so ai gwara nayi nayi na sallameki ki koma wurinsa", matseta yayi ta karfi ya cire rigar tata, ihu kuluwa ta fara zundumawa saboda jin za a maimaita irinta daren jiya, "wlh ko me zakiyi ba ihu ba kiyi amma bazan kyaleki ba tunda abun naki hakane", bakinsa yasa ya fara wasa da dukiyar fulaninta, take ya kashe mata jiki, ganin haka yasa shi fara kokarin aika mata da sako, sai dai yadda yaji jiya yau ma haka yaji, saboda ta koma ta mandake tamkar jiya bai shiga jikinta ba, wani wahalallen kuka kuluwa ta fara saboda wahalar da take ji,

Zafin yanzu bashida maraba da na jiya gashi junior bai sassauta mata ba, ko tausayinta bai ji ba ya dage karfinsa, "wayyo mom!" Haka kuluwa take fada ba tareda sani ba, dan lallabawar ma da yayi mata a daren jiya yanzu bai yi ba, tsabar wuyar da tasha har sai da ta fitar da jini amma junior bai saurara mata ba, numfashi ta fara yi sama sama, sai da ya tabbatar ya yi mata raga raga sannan ya kyaleta, toilet ya shiga yayi wanka ya fito, mai ya shafa, yafesa turaren malizia yasa yellow din riga da red din wando, a gaban mirror ya tsaya ya dauki cumb ya fara gyara sumarsa, kuluwa tana daga kwance tana kallonsa idanuwanta sun gama kumburewa saboda kukan da tasha, amma shigar da yayi tayi masa kyau sosai ta amshi jikinshi.
[2/12, 1:59 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA!

    Na
UMMI A'ISHA

7⃣3⃣

  Shiyasa take godewa Allah da samun junior a matsayin miji domin presentable ne ako ina zata iya nuna shi tace wannan ne mijinta ba tareda taji kunya ba, gashi ya iya daukar dressing kuma ya hadu 100%.

  Kallonsa taci gaba dayi lokacin da yake gyara sumar tasa ga wani mai da ya lakuta ya shafawa sumar tasa, take ta fara kyalli, tajewa yaci gaba dayi ita kuma kuluwa tana kallonsa har ya gama, jar belt ya dauko ya yadaura, ya juya zai fita,

"Ina zaka je??" Ta fada idonta cikeda hawaye, juyowa yayi ya kalleta, "gidan mom", "dan Allah junior kar ka tafi wlh bazan iya koda tashi ba, kar ka tafi dan Allah... ", Ta karasa maganar cikin kuka, tausayinta ne ya ratsa shi, hakika yasan yadda yayi matan nan dole ma sai taga doctor,

Dawowa yayi yahau kan gadon tareda rungumota jikinshi "washh!" Ta fada sakamakon jin ya kamo cinyoyinta, "kar ka hada mun su barsu ahaka", ta fada tana zubar da hawaye, "sorry Jidda na, to meye abun kuka kuma? Kiyi hakuri kinji, zakiyi wankan yanzu?" Kai ta daga alamun eh, "to ina zuwa", jeans din jikinshi ya cire da t shirt din ya shiga toilet ya hada mata ruwan zafi da gishiri da dettol ya dawo inda take,

Daukarta yayi ya kaita toilet din ya sata cikin baf din, ruwan na shigarta tafara kuka, "wayyo Allah, junior cireni daga ruwan nan wlh da zafi sosai, wayyo Allah", "sorry dan zauna kinji, saura kadan", "nidai wallahi da zafi, wayyo ka cireni" ta fada cikeda shagwaba ga kukan da take yi, "ai duk laifinki ne, kece kika sa nayi miki haka, banyi niyyar wahalar dake ba saboda nasan duk lukutancin nan naki k'ashinki bashi da wani karfi ashe kuwa hakan ne", fitowa tayi daga cikin bahon, tayi wanka, brush dinshi ta dauka ta wanke bakinta taja towel dinshi ta daura duk yana tsaye yana kallonta, juyawa yayi zai fita tayi saurin riko hannunshi, "ka tsaya mana mu tafi tare", hannunta ya rike "to muje".

Ahankali take daga kafarta tana takawa har suka shiga dakin amma fa kamar wata mai koyon tafiya haka ta zama, mansa ta shafa ta danyi kwalliya ba mai yawaba, tashi tayi "bari naje daki nasaka kaya", "ok ki shirya muje asibiti dan naga kamar kinji ciwo ko?" Fita tayi ba tareda ta bashi amsa ba sai da taje dakinta sannan ta fara kunkuni ita kadai, "ko ma meye ai kaine sanadi saboda tsabar kishi ka dage ka rinka nuna min rashin imani, tunda baka yi ahankali ba ai dole kajimin ciwo, shine kuma yanzu zaka wani ce naji ciwo, kaji min ciwo dai",

"Me kika ce? Dan sake fada naji", juyowa tayi ta ganshi tsaye a bayanta yana kallonta yadda yayi tsayuwar kamar wanda zai rungume ta, underwear kawai tasa ta zira skirt sannan tasa riga ba tareda ta tsaya saka bra ba domin ita kadai kawai tasan radadin da take ji,

Farin hijab tasa ta wuce gaba yana biyeda ita, takalmi flat tasa suka nufi motar junior, juyowa yayi ya kalleta lokacin da yake driving tayi wani langwai da ita kamar marar jini ajika,

Agefen titi yayi packing "ya naganki hakane? Menene?" Kallonsa tayi "babu komai", "no da komai" ya fada yana matsawa jikinta, "meye haka? Ina zaka?" Bakinsa yakai fuskarta, "babu inda zani, naga kamar kina cikin damuwa ne, ko duk bacin ran rabuwa da budurcin ne?"  "Eh shine" tafada tana kallon window, "ai kuwa kin yita bacin rai kenan dan ko yanzu idan doctor yace min da saura to sai na kuma yi, sai na tabbatar da na rabaki dashi", kyaleshi tayi bata kulashi ba ganin haka yasa shi daga hijabin ta "bari muga", nanma yi tayi kamar ba tasan yana yi ba, damka ya kaiwa na shanunta, "oh wadannan abubuwa kuna shan damka, kullum sai anyi muku kamar  za 'a... ", Jin bakinsa kan nata ya hanata karasa zancen zucin da ta fara.
[2/12, 2:06 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA!

  Na
UMMI A'ISHA

7⃣4⃣

Lips dinta ya fara tsotsa yana shafar na shanunta, dakyar ta kwace bakinta, "mun fasa zuwa asibitinne?" "Zamuje amma sai na dan sha koko kadan",

"A ina zaka sha kokon?" "Anan mana", "kaga idan ba zuwa za muyi ba ni kawai ka maida ni gida", "yi hakuri ai dole muje saboda daren yau ma ina son nasha koko".

Hannunshi ta cire daga cikin kirjinta, "kaga ni mu tafi kawai", jan motar yayi yana murmushi, "junior yasha kira a daren jiya da yau, fata daya nake miki Allah yasa masu gadi da sauran yan unguwa basu jiki b".,

Murmushi ta saki saboda ita kanta tasan jiya tayi ihu kamar makogaronta zai fita, ga Allah ya isa da ringa yiwa Mairo saboda itace ta bata bagaruwa gashi nan tasa junior zai kasheta.

Tunani junior ya fara yi shidai duk yanmatansa babu wacce ta taba yin kukan wuya dan ya jima ajikinta sai dai tayi kukan dadi, sannan kuma da zarar yazo kawai shiga yake ba tareda bata lokaci ba to amma ita Jidda gashi tun jiya yake abu daya amma budeta ya gagara, yau ma duk rashin tausayin da ya nuna mata bai sashi ya budeta gaba daya ba, lallai wannan shi ake kira da"virgin" ya fada acikin zuciyar sa, wani sonta ne yaji ya fara tasowa tun daga babban dan yatsan shi har tsakiyar kanshi,

Hannunsa yakai ya kamo nata ya dora akan cinyarshi ya dora hannunsa a saman nata yana shafawa a hankali da haka suka isa FMC dake gaba kadan da shagari quarters,

Bayan yayi packing din motar tasa ne ya jiyo ya kalleta fito muje to, fita tayi shima ya fito, ya kama hannunta suka fara tafiya a hankali saboda ita ba zata iya daga kafarta ba, clinic suka shiga inda ake karbar emergency, bayan yayi mata duk abunda ake yi kafin aga doctor ne layi yazo Kansu,

Tare suka shiga doctor din ya fara tambayar ta meyake damunta, kasa magana tayi sai shiru, "doctor amarya ce",inji junior, "to me ya faru da ita?" Doctor din ya sake tambaya, "Jidda fadi yanda kike ji kinji", kanta ta sunkuyar "cinyoyina ne ke ciwo da gabobin jikina sannan...,sannan....,sannan kuma", "barshi kawai", doctor din ya fada tareda fara yin rubutu jikin wani dan kati, "shiyasa a har kullum muke bawa mazaje shawara musamman ma wadanda basu taba aure ba, adaina garaje ana kokarin lallai sai an shiga a wannan lokacin arinka hakuri ana bin komai a hankali har wurin ya bude,

Sannan kuma ganin wannan jinin ba shine ke nuna cewar yarinya budurwa bace, dan haka akiyaye ko babu jini budurwa budurwa ce", shidai junior yana tsaye yana jin fadan da doctor ke yi masa saboda rashin tausayin da ya nunawa kuluwa.
[2/12, 2:29 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA!

   Na
UMMI A'ISHA

7⃣5⃣


Sai da doctor din ya gama yi musu bayanai masu amfani sannan ya basu katin magungunan da zasu siya tare da dauko allura zai yiwa kuluwa,

Kallon doctor din junior yayi tareda tambayar sa "doctor me za ayi kuma?" "Zanyi mata allura ne saboda wannan abun da kayi mata dole sai anyi allura", "a'a doctor" junior ya fada cikeda kishi karara akan fuskarsa "kabari idan munje chemist din da zamu siyi maganin ayi mata allurar acan", "ok babu damuwa inji likitan", hannun kuluwa junior ya kama ta tatashi suka yiwa doctor sallama suka fita.

A opposite din asibitin suka samu wani chemist wanda wata nurse ta bude,nan junior yakai kuluwa suka shiga domin ayi mata allurar, "wayyo junior kace kar ayi min pls", lumshe idonsa yayi saboda jin yadda tayi maganar cikeda shagwaba, "sorry Jidda na zo muje", dakyar ta yarda ta bishi suka fita suna shiga ta matsa jikin junior tareda kama hannunshi ta rike cikin nata, bayanin allurar da za ayiwa kuluwa junior ya fara yiwa nurse din, "ayya Allah ya bata lafiya" nurse din ta fada cikeda yanga,

"Sister dinka ce?" Murmushi junior yayi "kiyi mata allura kedai kawai", "ok ai naga kamar matsoraciya ce kanwar taka", "ko?" Junior ya fada yana kallon fuskar kuluwa wacce tasha kunu ta bata rai kamar zata sa kuka,

Sake shigewa jikin junior tayi lokacin da taga nurse din ta nufota, da sauri ta cusa kanta acikin kirjin junior, "sorry ki tsaya kar ayi miki a inda bai kamata ba", hijabin ta ya yaye yadan janye skirt din kadan yace "to yi mata da sauri", runtse ido kuluwa tayi har aka gama bata bude idonta ba, ita kuwa nurse din nan sai kallon junior take cikeda yabawa,

Ana gamawa yasa dan yatsansa ya fara mulmula mata wurin, "sannu Jidda", "wannan sister din taka tanada tsoro da yawa" nurse ta fada tana murmushin jan hankali, hararta kuluwa tayi ta dauke kanta,

"Meye sunanka kai?" Nurse ta fada tana kallon junior lokacin da take harhada musu magungunan, "ni?" Junior ya tambayeta, "eh ko sai kanwar taka ce zata fada min", "ni ba kanwarsa bace matarsa ce", kuluwa ta fada cikin daurewar fuska acikin ranta tana cewa "to duk iyayinki ba saurayi bane mijina ne kuma wlh yafi karfin ajinki".

"Wai dagaske matarka ce?" Ta tambayi junior, "to ke ya kika fahimta?" "Ni sai naga kamar kanwarka ce irin yar autar nan saboda ta fiya shagwaba da yawa", 1000 ya mika mata "dauki kudin maganin", "no ku barshi kawai Allah ya bata lafiya", "amin mun gode amma ai ba za ayi haka ba ki karba", "ai anyi ma angama, kuma ba rokata kukayi ba nice nagadama", "to mun gode", "karka damu saboda kai nayi".

Jan hannunsa kuluwa tayi "junior muje kwanciya nake son yi", "oh nice name", wani haushine ya kara kama kuluwa wannan shine kokari wai barawo da sallama tana tsaye ana neman yi mata kwacen miji,

Take kishi ya motsa taja hannun junior "dan Allah mu tafi", daukar maganin junior yayi yace "to mun gode fa", "yawwa bye bye", nurse ta fada tana wage hakora, suna zuwa mota kuluwa ta dalla masa harara, "kasan Allah? Ka mayar mata da maganinta danni bazan sha ba", "why jidda?" "Nadai fada maka, ai nasan ba don Allah ta bayar ba dan tana sonka ta bayar",

Niyyar zolayarta yayi yace "to meye? Kema ba kince kinada wanda kike so ba? To nima kinga yanzu gashi na samu wadda take sona nake sonta shikenan duk lokacin da kika tafi sai na kawota", da hanzari ta kalleshi, take wani dunkulen abu ya tokare kirjinta,

Kallon junior tayi da idanuwanta wadanda suka kada suka yi ja, "oh har ka kamu da sonta kenan?" "Eh mana dama shi so ai haka yake", hannunta ta dukule ta fara dukansa, "biyani budurcina, wlh sai ka biyani, ka biyani budurcina", hawaye ne suka fara bin kumatunta, "bayan ka rabani da budurcina kuma shine zaka rabani da kai, wlh bazan yarda ba",

Dakyar ya iya hada hannuwanta ya rike, "ya kike dukana haka", kuka ta fara yi mai sauti, "kiyi shiru Jidda yi hakuri dan Allah, ni da wasa fa nake yi miki kuma zolayarki nake yi", kujerar sa ya kwantar ya janyota jikinsa ya dorata akansa, fuskarta da tasa ya hada ya fara tsotsar bakinta.





Ummi A'isha[2/15, 2:38 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA!

    Na
UMMI A'ISHA

8⃣1⃣

Fita tayi daga cikin motar tana ce masa"dan Allah kar ka dawo",hijabinta ya riko,"tsoron me kikeyi?, ko kina jin kunyar nuna ni a matsayin mijinki ne?",da sauri ta kalleshi "ni ba haka bane","to menene?" Ya fada yana kallonta,"babu komai amma dai kar ka dawo","tom shikenan, ayi lectures lafiya" "yawwa" ta fada tare da tafiya bayan ta gyara nikab din fuskarta, tsayawa yayi yana kallonta har ta shige wani babban hall wanda suke lectures.

  Juyawa yayi ya fice daga makarantar ya nufi gidan mom, koda lokacin tashin kuluwa yayi driver ne yaje ya dauke ta ya kaita gida shikuma junior lokacin yana gidan mom, tana zuwa gidan wanka tayi ta shiga kitchen ta danyi musu girki dan kadan saboda dama junior ne ma zata yi girkin amma badon shi ba ita basai tayi ba tunda kuku yayi musu girki, tunanin babanta ta fara yi,sai da ta gama ayyukanta sannan ta fito ta shiga dakin junior, dakin ta gyara masa,"junior akwai son gayu da ado, lokacin da kayi yara kuma zanga yanda zaka yi" haka ta fada lokacin da take gyara masa kan mirror dinsa, ji tayi an rungumeta da sauri ta jiyo ta kalleshi,"har ka dawo?","matsoraciya, nadawo" murmushi tayi "yasu mom?" "Lfy lau suke, suna gaisheki","ina amsawa" cikinta ya shafo "kullum mom sai ta tambaya ko kin fara laulayi,tun kafin ma nayi take tambaya" murmushi kuluwa tayi itama kanta tana son yara tana son ta haihu da wuri basai ta dau lokaci mai tsawo ba,"Jidda kina son ki haifi yaro?" "Um ina so","indai kina so ki barni yau nayi tunda kinga jiya ban yiba","a'a gaskiya ba yanzu ba kabari sai na warke","to nabari maijidda" mirmushi tayi tareda kwace jikinta ta fita saboda tunda taji ya fara haka tasan dakyar idan zai barta.

Haka zamansu ya yita tafiya har tsawon sati biyu amma har lokacin bata bar junior yasake kusantar ta ba saboda ta tsorata dashi mutuka, yau ta kama alhamis tanada lecture 8:10 shiyasa ta tashi da wuri lokacin junior yana kwance asamanta yanata sharar bacci saboda tun lokacin da ya dawo daga sallar asuba ya fara wasanni da ita har bacci ya daukeshi, wanka ta shiga tayi ta fito ta shirya ta shiga kitchen ta dafa masa indomie da kwai, sai da ta ci nata abincin sannan ta koma dakinta inda junior yaketa bacci, akusa dashi ta zauna,"junior, junior, junior" motsi ba yi tareda rungumota jikinsa, kissing din ta ya fara yi,"junior zan makara fa, kaga yanzu 8 saura","yanzu jidda ba zaki bani kokon ba?" "Junior kayi hakuri idan nadawo sai....." Shiru tayi ta kasa karasa maganar "fadi naji, sai me?, zaki bani?" Kai ta daga a hankali,mikewa yayi daga shi sai shorts trouser black da yellow din body hug,"dauko min key din mota adakina" tashi tayi taje dakinsa ta dauko ta dawo ta dauki hijab dinta da jakarta ta fita inda junior yake jiranta, key din ta mika masa ya karba ya bude ya shiga, bayan sun fara tafiya ne ta kalleshi "junior na ajiye maka breakfast dinka", "ni ba wannan nake so ba koko nake so" kanta ta dauke ta kalli window, "idan kin dawo zaki bani ko?" "Ehh" tafada can cikin makogwaronta saboda yanzu itama tana muradinshi, jinta take tana son kebewa dashi, suna shiga sch din yafara kallonta, "kinji yadda kike kamshi kuwa?, ba na hanaki saka turare ba idan zaki fita?" ,"kayi hakuri dan Allah" kai ya gyada mata ba tareda yayi magana ba ganin haka ya sata fita daga motar ta nufi inda zasu yi lecture.

Karfe 2:30 tagama lectures dinta junior yazo ya dauketa suna fita yace mata,"bari mu biya ta wuni wuri ina son cin shawarma yau" "to" ta bashi amsa, a SHAWARMA & CO, yayi packing "fito muje kigani" fita tayi ta bishi suka tafi tare, kayan dadine kala kala a wurin ga kayan kwalama kamar me, shawarma da gasasshen kifi ya siya musu da ice cream lokacin da aka gama hada musu har sun jiyo zasu tafi sukaji ihu "heyy junior" da sauri suka juya gaba dayansu, teemah ce tazo batayi wata wata ba ta rungume junior, "junior kwana dayawa?" Hannunta ya rike "teemah dama ina nemanki amma Kafin nan meet my wife jidda" nuna mata jidda yayi da hannunsa, ita kam kuluwa juyawa tayi tai tafiyarta ba tare da tsaya sun gaisa da Teemah ba, kallon teemah yayi "teemah naga abunda kika yimin to amma ina mai sanar dake cewa asirin da kika yimin bai yi tasiri akaina ba kuma har yanzu ina tareda matata" "junior me kake son fada? Me nayi maka? Ni zakace nayi maka asiri? Look junior bai kamata kayi min sharri ba saboda kayi aure, tunda kace ba zaka aure niba to ka kyaleni da wannan radadin amma kar kayi min sharri","teemah ai ba sharri nayi miki ba dama kin fada min cewa zaki dauki fansa, to naga irin fansar da kika dauka" "junior wallahi kawai nafada maka hakane saboda kawai ina son na nuna maka ne banji dadin abunda kayi min ba amma wallahi bani da niyyar cutar da kai" "ok kina nufin kenan ke baki yi komai ba?" "Wallahi junior babu abinda nayi maka believe me","shikenan zamu yi magana a waya kinga yanzu wife dina tana jirana" "babu damuwa" juyawa yayi ya nufi wurinda kuluwa take tsaye ta cika tayi fam ji take kamar taje ta shake teemah dan haushi.
[2/15, 2:42 PM] Ummi A'isha: SANADIN GATA!

Na
UMMI A'ISHA

8⃣2⃣

  Ahankali ya karasa inda take "sorry jidda kinga na jima ko? Friend dina ce teemah" bata bashi amsa ba ta bude kofar motar ta shiga ta zauna, har suka fara tafiya bata kulashi ba da yake shima ba mai son surutu bane da yawa sai yayi shiru bai sake magana ba, zaman kurame suka yi har suka isa gida, suna zuwa itace tafara fitowa ta nufi ciki, shi junior yasan kila fushi tayi to sai dai bai san ta yadda zai tunkareta ba, ciki ya shiga lokacin har ta shige dakinta shima dakinsa ya shige koda yaje kwanciya yayi nan yayita bacci har 4 tayi sai a lokacin ya tashi  yayi wanka yayi salla ya nufi dakin kuluwa wacce take fushi dashi, daga ita sai best baka da jan tied iya gwiwarta, "jidda na, shine kika barni nayi bacci ko, alhalin kuma kinyi min alqawari" bata dago ta kalleshi ba tace "eh, ai ni bana salla yanzu" cikeda damuwa ya karaso kusa da ita "dagaske?" "Dagaske mana" "to bani abinci naci",tashi tayi ta fita ta je ta dauko masa kayan dazu da ya siyo ta kawo masa a tsakiyar gadonta ya zauna yaci abincin acikin ranta sai tsaki take tana cewa "me za ayi da auren dan gata? Komai nashi a sangarce yake" yana gama cin abuncin ya mike "ina zuwa bari naje gidan mom nadawo" "adawo lafiya" tafada ba tareda ta kalleshi ba yana fita ta zauna tayi tagumi,"yanzu ni haka zan zauna da miji mai yin kawaye da mata? Lallai akwai aiki a gabana, domin raba junior da mata sai an dage" tashi tayi ta fita falo,ita sam al'amuran junior basu fiya bata mata rai ba saboda tasan duk wadannan abubuwan da yake yi SANADIN GATA ne yasashi.

Tana nan zaune sai gashi ya shigo kallonta yayi "Jidda kinyi bakuwa, jawahir sister dina ce tazo tare muke da ita, yar sister din mom ce" "sannunta da zuwa" tafada tareda mikewa ta nufi dakinta domin dauko hijab dinta, tana fitowa tagansu tsaye jawahir tasha riga da wando na atamfa kamar zata rungume junior tana tsaye a gabansa, "sannu da zuwa" inji kuluwa lokacin da take karasowa cikin falon "yawwa sannu" jawahir ta fada tana kokarin kamo hannun junior, "ikon Allah" kuluwa ta fada acikin zuciyarta, hannun junior jawahir ta kama suka zauna akan kujera ta ciro wayarta kirar HTC ta fara nunawa junior picx, jikinsa ta shiga sosai suna kallon hotunan, kuluwa ji tayi kamar ta hadiyi zuciya ta mutu saboda bakin ciki, dakinta ta juya ta koma, abakin gado ta zauna, ita abun ma yanzu tsoro yake bata, tana nan zaune junior ya shigo "ya za kiyi bakuwa amma ki taho ki barta ko ruwa baki bata ba?" "To ai naga bakuwarka ce ba tawa ba so me zai hana kai ka bata ruwan?" Kallonta yayi " jidda kinada hankali kuwa? Yar uwata ce fa" " koma wacece kai ta shafa ba ni ba" "ni kike fadawa haka?" "Oho" tafada cikin masifa, juyawa yayi ya fice Jim kadan ta jiyo karar motarsa da alama sun tafi,"Allah kayi min maganin wannan masifar" haka ta fada acikin ranta.

Tunda ya tafi gidan mom can ya tare shida jawa sai wurin 10 sannan ya dawo gida lokacin kuluwa ta rufe dakinta ta kwanta duk da cewa ta kasa baccin amma haka ta zauna ita kadai, shi dinma dama bashida niyyar zuwa inda take, dakinsa ya wuce cikeda takaicin rainashin da kuluwa tayi saboda tsabar raini shine harda fada masa bakar magana dazu, wanka yayi yai kwanciyar sa ba tare da ya nemi dakin kuluwa ba.

Dukkaninsu daren ranar haka suka yishi babu wanda yayi bacci acikinsu, washe gari da safe kuluwa bata shirya masa breakfast ba tayi tafiyarta makaranta sai agidan mom yayi breakfast tun daga nan junior ya fita harkarta ko zaman gidan ma ba sosai yake yinsa ba yafi zama agidan mom, da haka har sukayi kwana 2 ahaka. Yau karfe 1 kuluwa ta dawo gida dan haka ta shiga kitchen daga ita sai farar shimi mai dan siririn hannu tanada santsi gata shara shara, dan babban dankwali ta daura asaman rigar, indomie ta dora zata dafa saboda ita take sha'awa kamar wata me ciki haka take sha'awar abubuwa amma tasan ba cikin gareta ba ita kuma yanzu babu ma abinda take so irin taganta da cikin junior ajikinta  tasan dansu zai sha gata wurin ta itada junior da kuma wurinsu mom, bata ankara ba ta datsa wuka a dan yatsanta saboda ta tafi duniyar tunani gashi tana yanka albasa ne lokacin, jini ne ya fara zuba gashi wukar ta yanketa sosai, juyawa tayi da niyyar fita a kofa suka yi karo da junior zai shigo ganin ta yanke yasashi saurin kamo hannunta " jidda me ya sameki?" Bata iya bashi amsa ba saboda zafin da take ji,ganin yankewar da tayi ya sashi karasawa ya kashe gas din da take girkin akai, binta dakinta yayi tana kwance tana kuka "sannu jidda na, hannun ya kama ya fara hura mata iska ga jini sai zuba yake, tissue ya yago da yawa yazo ya nade mata dan yatsan tareda jawota jikinsa "sannu kinji, bari muga" bakinsa yasa yafara hura mata wurin da ta yanke, bayanta ya fara shafawa a hankali, lumshe ido tayi acikin zuciyarta tana cewa "nayi missing dinka junior, bakinsa ya fara sawa yana kissing din fuskarta da haka yayi nasarar funcike yar guntuwar rigar dake jikinta,shafarta ya fara yi a hankali, tana jinsa sarai amma tayi lukus har ya gangaro ya fara kokarin aika mata da sakonni masu nauyi, runtse idonta tayi saboda tasan yauma junior bazai yi ta farat daya ba.





Ummi A'isha[2/17, 7:45 AM] Ummi A'isha: SANADIN GATA!

  Na
UMMI A'ISHA

8⃣3⃣

   Soyayya ya shiga nuna mata mai wuyar fassarawa, nan suka manta da duk wani bacin ran da suke ciki sai annashuwar da take shigarsu take suka samu kansu cikin farin ciki marar misaltuwa, kuka kuluwa ta fara yi sakamakon jin har yanzu bata zama daidai ba bata da maraba da amaryar daren jiya,ji tayi kamar yau ne ranar farko da junior ya fara kusantarta saboda wahalar da take ciki.

   Kukan da take bai hana junior aiwatar da abunda yaso ba har sai da ya samu nutsuwa sannan ya iya kyaleta ya fara lallashinta "am sorry my jidda, kiyi hakuri akan abunda ya faru kinji, kiyi hakuri wallahi jidda kece rayuwata you are the parts and parcels of my life, i can't survived with out you!, pls kiyi hakuri kinji",shiru kuluwa tayi ta kankameshi ta rungume ajikinta bata san lokacin da ta fara kissing din shi ba nan suka sake shagala sai lokaci mai tsawo sannan junior ya kinkimeta ya nufi toilet da ita, tare suka yi wanka suka fito, gajeren wando kawai yasa ya fita ya nufi kitchen, ita kuma wata riga ja tasa mai siririn hannu dogowa, binsa kitchen din tayi yana tsaye ya kunna gas yana kokarin dafa mata indomie din, ta bayanshi ta rungume shi to dora kanta akan kafadarsa tare da sakalo hannuwanta ta cikinsa tana shafa cibiyarsa "junior me zaka yi?" "Indomie din zan dafa miki",murmushi tayi " matsa nayi girkina kai wanne girki ka iya" matsawa yayi tazo gaban gas din ta tsaya dariya ta fara yi saboda ganin yanda ya cika tukunyar da ruwa, ruwan ta rage tabar daidai wanda zai isa,yana tsaye yana tayata yana shafarta yana yi mata kiss har ta gama suka koma falo ajikinsa ya dorata ya rinka bata indomie din abaki tana ci, shi kuwa dama abinci bai dameshi ba domin marar yawan cin abinci ne shi, sai da ta koshi sannan ya kyaleta, bakinta ya kama ya fara lasa tare da kokarin zame hannun rigarta sam bata hanashi ba kyaleshi tayi yayi wasanninshi son ransa da ita sannan ya dauketa zuwa saman kujera,"kitsona zanje na tsefe, ya tsufa" ta fada tana kallonshi "bari na tsefe miki" dakinta yaje ya dauko kibiya yazo ya zauna kusa da ita ta dora kanta akan cinyarsa yafara yi mata tsifar bada jimawa ba bacci ya dauketa har ya gama bata sani ba sai da ya tasheta.

    Tana bude ido ta shiga jikinsa "sannu nagode" murmushi ya cilla mata "anjima zan kaiki ki wanke kanki, sai ki shirya" kiss tayi masa akan cibiyarsa, kallonta junior yayi "jidda dama kin iya wadannan abubuwan shine bakya yimin? To daga yau ki fara" rufe fuskarta tayi da tafukan hannunta.

  Bayan sunyi wanka sun shirya junior ya dauketa zuwa wani shagon saloon, har ciki ya rakata "naje nadawo ko na jiraki?" "A'a jirani gaskiya" ta fada tareda riko hannunsa, kujera ya samu ya zauna yana ganin yadda ake yi mata gyaran gashin, duk yanzu tayi kyau tayi sumbul da ita gwanin ban sha'awa kamar mai juna biyu, addu'a ya fara yi aransa Allah yasa kuluwa cikine da ita saboda shi yana son yara ko lokacin da yake karami kusan kullum sai yayi wa mom korafi meyasa ba shida kani, sai mom ta shafa kansa tace "junior kai kadai Allah ya bamu bai baka kani ba kayi hakuri kaji, wannan tsari ne na Allah" murmushi yayi "Allah sarki mom kinyi hakuri dani mutuka" ganin kuluwa yayi kusa da shi,"tunanin me kake yi?" "Tunaninki keda babynmu nake" hannunsa kuluwa ta kama "to ai har yanzu baka bani babyn ba" "uhm zan baki ne yarinya kila ma a daren yau" "um,um nidai ban yarda ba" tafada cikin shagwaba jikinta ya shiga ya fara kokarin hada fuskarta da tashi ita kuma taki sai kakkawar da fuskarta take, ita dai mai shagon saloon ta tsaya tana kallon soyayyar da suke zubawa danma bata jin hausa balle tasan abunda suke fada.

Lokacin da aka gama mata basu koma gida ba cikin gari kawai suka wuce daga karshe yaje ya ajiyeta awani stadium din kallon kwallo, acikin mota yabarta ya rufeta shikuma ya shiga ciki, sai da yayi wurin minti 30 sannan ya dawo "harararsa tayi wallahi badan ka kulleni ba da biyoka ciki zanyi","eh ai saboda nasan zaki iya biyonin shiyasa na rufeki","to meyasa baka son nabika, saboda baka son aganka dani ko?" Murmushi yayi "wallahi zan nunawa kowa ke a matsayin matata kawai ina kishin wasu mazan su kalle min fuskarki ne" wani sanyin dadi taji acikin ranta domin kalamansa sunyi mata dadi, hannunta tasa ta rufe idanuwansa ta dora bakinta kan nasa ta fara tsotsa take ta fara kashe masa jiki dauke bakinta tayi daga kan nasa, "jidda dan Allah idan munje gida kimin" ya fada cikin shagwaba "junior me yasa kake da shawaba ne? Ko mace bata fika iya shagwaba ba wallahi" hannunta ya matse cikin nasa "me yasa kika ce haka? Ko dan kinga ina bacci da kirjinki a hannuna? To in dan hakane yau ki shirya abinda yafi haka zanyi", murmushi tayi tai kissing din hannunsa,fita sukayi daga harabar stadium din suka nufi Gida.

Zamansu haka ya kasance cikin so da kaunar juna kullum shi yake kaita sch har ta fara exam, kullum yanzu bata samun hutu ga karatu ga dawainiyar junior da ta zame mata dole, da haka har ta gama exam din ranar da ta gama yaje ya daukota ya kaita gidan mom acan suka wuni sai dare suka koma Gida, washe gari kuma ya kaita gidan anty Salma nanma ta wuni, a daki suka kule da ummi suna hirarsu,"kinga maijidda nima na samu wani sunansa suraj dan gayu ne sosai kamar junior" dariya kuluwa tayi "Allah yasa ayi da wuri kema ki shiga kiji, Ummi aure da dadi da wuya" "ke wanne junior ya baki? Dadi ko wuya?" "Hmm ni dadi junior ya bani amma matsalata yanzu guda daya ce har yau ban samu ciki ba Ummi, wallahi kullum fatana kenan amma kinji shiru" kallonta Ummi tayi "haba Jidda da yaushe ma kukayi auren? Wasu fa suna shekara biyar ma kafin su haihu balle ku yan shekara daya" "Ummi wallahi junior yana son yara kuma nima ina so, kinga acikin family dinmu daga ni sai ke sai junior, mu ukune kacal shiyasa nake son mu haihu da yawa saboda mu kara yawa, nasan indai ban haihu ba junior aure zai sake saboda mom dinshi kullum sai ta tambayeshi ko nafara laulayi" kwalla kuluwa ta fara zubarwa, dafata Ummi tayi "kinjiki ai, to ke ce miki akayi ba zaki haihu ba? Komai daren dadewa kema zaki haifi naki insha Allah kuma tunda shi junior din bai damu ba ai kema bai kamata ki damu ba, insha Allah zaku samu yara har sai kinji haihuwar ta isheki" murmushi kuluwa tayi "Allah ya amsa, amin".

Wuni cur tayi sai dare junior yazo ya dauketa suna falo a bararraje suna cin dan malelen da Ummi tayi musu ya shigo, kallonsa kuluwa ta fara yana sanye da t shirt dark blue da blue din wando,"Jidda wannan kwadayi haka?" Dariya Ummi tayi "may be babynka ne yasata kwadayin" dariya shima yayi "da alama kam ta harbu" "Allah yasa kuluwa ta fada tana murmushi" kusa da ita ya karasa ya tsugunna a gabanta ya zuba mata manyan idanuwansa, "jidda na sammin nima inci" "kaima kwadayin zaka yi kenan?" Ta fada kamar me yin rada, gira ya daga mata, a hannunta ta debo ta mika masa saitin bakinsa,hannunta ya kama yasa hannunta a bakinsa koda ya hadiye dan malelen bai saki hannunta ba sai da ya side yan yatsunta tas, cizon dan yatsanta yayi, "wash junior da zafi" ta fada cikeda shagwaba sakin hannun yayi yana dariya sai alokacin suka tuna da cewa ummi tana wurin amma Anty Salma bata nan, harhada shirginta tayi suka yi musu sallama suka tafi, ahanya ya kalleta "Jidda kodai ciki gareki kika boye min?" Hawaye ta fara saboda jin tambayarsa packing yayi yajiyo ya kamo hanunta a hankali ya fara mammatsa hannun nata "jidda menene abun kuka?" Kiyi shiru kinji,"junior ina jin bazan haihu ba fa, gashi har yau ban samu ciki ba" murmushi junior yayi tare da kissing din hannunta "kiji shirme, zaki haihu jidda kinji, ita haihuwa ai zuwa take, zaki haihu insha Allah, tunda dai inada wadataccen koko ai shikenan zan ta baki kina sha".
[2/17, 8:11 AM] Ummi A'isha: SANADIN GATA!

   Na
UMMI A'ISHA

8⃣4⃣

  Murmushin jin kunya tayi ahaka ta share zancen har suka karasa gida. Kwanansu 4 da yin hutu tace yabarta zataje chiyako kauyensu bai hanata ba yace ta shirya ya kaita haka kuwa ta shirya ranar laraba da safe ya kaita, karfe 11:40 suka isa, tunda sukaje take baza idanu tana kallon abun mamaki domin wani hamshakin gida ta gani wanda ko acikin birni ba kowa ne keda irinsa ba abun ba acewa komai, anan yayi packing, kallonsa tayi amma ba tace masa komai ba, fitowa tayi ta shiga cikin gidan wanda yasha blue din fenti, tabbas gidansu ne amma kuma ya akayi ya canja? Nidai Ummi A'isha banida amsa, tana shiga ta hango wasu matsakaitan mata guda biyu sunata aiki atsakar gidan, bayan tayi sallama suka nuna mata dakin iyatu, shiga tayi ta samu iyatu zaune a falo wanda ya kayatu ya tsaru ta jingina da pillow tana kallon katuwar plasma tv din dake manne ajikin bango, dago kai iyatu tayi tana ganin kuluwa ta mike da Sauri "sannu da zuwa maijidda,yanzu kuke tafe? Karaso, lale lale" shiga kuluwa tayi ta fara kallon yanda aka tsara falon hatta fentin abun kallone, junior ya shigo hannunsa rikeda akwatinta, "sannu da zuwa Abdulrahamanu, shigo" shiga shi dinma yayi suka gaisa, bayan an gaggaisa ne ya mike yace zai tafi, bin bayansa kuluwa tayi har zuwa soron gidan, jikinta ya matsa "baby yau zanyi missing dinki, kwana nawa zakiyi?" Ita dinma sai yanzu taji babu dadi ganin zai tafi ya barta "Sati biyu zanyi, dan Allah ka kula da kanka" "zan kula da kaina sosai, i promised you, sai dai zan kasance cikin kewar matata" idonta taji ya ciko da kwalla,"Allah ya kaika lafiya, sai munyi waya" hannunta ya kamo tareda janta jikinsa,"kar kiyi kuka tunda kece kikace min sai na kawoki, kiyi hakuri ki zauna sati mai zuwa zanzo mu tafi" kiss ya manna mata akan goshinta ya juya zai tafi, hannunsa ta riko ya dawo "rufe idonka" tafada ahankali, manyan idanuwansa ya lumshe ahankali ta dora bakinta kan nasa ta fara kissing din lips dinsa, ta dauki tsawon minti biyu ahaka sannan ta dauke bakinta daga kan nasa ta juya cikin gida da gudu, murmushi yayi ya juya ya fita.

Tana shiga cikin gida iyatu ta fara washe baki tana bata labarin abunda ya faru "ai wannan yaro akwai kirki da mutumci yanzu kiga yadda ya mayar mana da wannan gidan acikin kwanaki kadan, ga jari da ya bawa babanki, nikuma yanzu babu abinda nake yi kullum daga zama sai kwanciya kinga masu yimin aiki nan, yanzu duk garinnan babu matar da takejin dadin da nakeji, Allah dai yayi muku albarka, nidai babu abinda zance dake sai dai ki yafemin abubuwan da nayi miki abaya" kuka iyatu tafara,hakuri kuluwa ta bata tareda sanar da ita ta yafe mata tun jimawa, hira suka fara amma rabin hirar ta junior ce iyatu tanata bata labarin yadda yake hidima dasu dan ayanzu haka ma babanta yana can wurin kasuwancinsa a babbar kasuwa, wani son junior taji ya dada shigarta hakika junior alherine acikin rayuwarta sannan tayiwa Allah godiya domin ta sanadiyarta an samu canji agidansu lallai addu'ar da mahaifinta yayi mata bata fadi akasa ba.

Sai daf da magrib babanta ya dawo daga kasuwa, yana ganinta ya fara fara'a da sauri ta tareshi, ranar sai wurin 12 sannan ta kwanta, tana kwanciya kuma ta fara tunanin junior "da tuni yanzu ina jikin mijina Ina shan dumi ko juyi bazan yi ba sai dai idan ya fuskanci na gaji da barin da nake kwance ya juyani ya mai dani wani barin" runtse idonta tayi tareda shafa kirjinta "kuma yau nasan za kuyi missing din junior saboda kulum hannunsa yana makale daku", zaune ta tashi saboda tasan ba zata iya bacci ba, shiru tayi tanata tunaninsa har 2 tayi ganin haka yasata shiga toilet ta dauro alwala tazo tafara kai kukanta gurin ubangiji domin ya bata haihuwa, ta dade tana addu'o'i kafin ta shafa ta tashi, tana komawa kan gado wayarta ta fara kara tasan junior ne, "hello bakayi bacci ba?" Tafada a hankali, "naki wasane, taya zanyi bacci bayan bakya nan? Wallahi komai na gidan yau ya canja min, dan Allah ki fasa yin kwana bakwai dinnan, kiyi kwana uku sai nazo mu tafi" "indai hakan zai samar maka da farin ciki na yarda" murmushi yadan yi "wato shine dazu kika lasa min Zuma a baki kuma kika dauke ko? Meyasa kika gudu baki jira na bada tukwici ba? Alright tunda kin gudu amma duk ranar da kika dawo zan ramawa kura aniyarta" hira sukayi mai cikeda dunbin so da kauna har asuba tayi sannan suka hakura.

  Washe gari wurin karfe 11 tayi masa text cewar tana so zata fita, amsa ya dawo mata da ita cewar gidan Mairo kawai ya yarda taje saboda sunanta yaji tanata ambata a daren farkon su, murmushi tayi ta shirya ta fita. Koda taje gidan Mairo abun sha'awa Mairo tana dauke da tsohon ciki ji tayi aranta inama itace take dauke da cikin nan saboda a rayuwarta tana son taganta dauke da cikin junior ajikinta amma har yanzu babu alama, wuni tayiwa mairo Kafin nan ta koma gida.

  Haka kuluwa tayi hutunta na kwana 6 amma kullum ita da junior basa bacci saboda kwana suke suna yin waya kamar wasu saurayi da budurwa, ana gobe zata koma taje aka zano mata jan lallai wadda ya kama hannunta dau da kafarta, washe gari da yamma junior yazo daukarta, bayan sunyi sallama da kowa suka fita yasa mata jakarta a boot suka dauki hanyar birni, "wow!" Junior ya fada lokacin da yaga kunshin hannunta,"bani hannunki nagani" ya fada yana driving mika masa hannun tayi ya kama yasa cikin tafin hannunsa "yayi kyau zanen" ya fada tareda kissing din tafin hannunta murmushi tayi ta kalleshi yasha dark brown colour din shadda dinkin samfarin boda yayi masa kyau sosai, hannunsa daure da agogon Gucci na azurfa, hannunta ya makale cikin nasa, tareda yi mata albishir din zai tafi service bata rai tayi "kuma sai ka tafi ka barni?" " no ai a school dinku ma zanyi service din" "wooh amma dai ba a department dinmu zaka koyar ba?" "Idan anan ne menene?" Dariya tayi "dan Allah ka bari, kaje kowanne department amma banda namu" hannunta ya matsa da karfi " to shikenan tunda kina tsoron carryover nafasa koyarwa a department dinku" "haka yafi, gara mu hadu agida amma banda class" "to idan mun hadu a class meye? Iyakaci kawai kibi doka ko ki samu c.o","wallahi kuwa da sai na rama" kallonta yayi "tayaya?" "Kafi kowa Sanin ta hanyar da zan rama" hannunta yakai kan bakinsa ya dan ciza "i love you baby! Kika rama ta wannan hanyar ai kasheni zaki yi" murmushi kuluwa tayi "kajishi kamar gaske" "wallahi dagaske nake, kinji kuwa kwanakin nan da bakya nan kamar marar lafiya haka nadawo dan har mom sai da ta gane nayi missing dinki shine wai tace to idan wani abu nake bukata na sanar mata sai tasa masu aiki suyi min nikuma abunda nake bukata duk duniya ke kadai ce zaki iya bani shi, Allah dagaske nasha wahala da baki nan saboda kin sangartani da yawa komai kece kike yimin shiyasa nakasa sukuni", wani dadi taji ya shigeta saboda jin kalmominsa, kallonsa tayi "you lucky guy" "you too" yafada yana sinsinar tafin hannunta yana rike da yan yatsunta sai jujjuya su yake har suka shiga kano, dan murmushi kuluwa tayi saboda ganin yanda duk ya wani rikice ya rude kamar ta shekara bata nan,"yau zansha jagwalgwalo kenan dan nasan yau idan na shiga hannunka babu mai rabamu sai Allah" haka ta fada acikin ranta, lokacin da suka je gida kuwa dakinsa har dariya yabata saboda kaura yayi daga dakinsa zuwa nata lokacin da bata nan, duk kayansa da yasa ya ciccire gasu nan baje akan gadonta, koda ta leka kitchen ma abun ba acewa komai duk ya babbata mata kayan kitchen saboda kitchen din guda biyune daya wanda kukunsu yake amfani dashi daya kuma nata ne na musamman, kayan jikinta ta cire ta fito daga ita sai farar t shirt da farin wando irin na yan ball dan kayan kwallon junior ma tasa abayan rigar an rubuta junior, kitchen ta shiga ta fara gyara kayanta da yayi mata kaca kaca dasu tana ciki ya shigo ya sameta daga shi sai gajeren wando "dan Allah kizo kiji dani" kallonsa ta jiyo tayi, "haka ka bata min gida?" "Eh na danyi girke girke ne da bakya nan kuma wallahi duk ma food din bai ciyu ba saboda babu dadi irin naki" juyawa tayi zata fara wanke wanke  dagata yayi ya sabeta ya nufi dakinsa da ita dariya tafara "kabari nagama aikin mana" "ai baki isaba ko zakiyi aiki sai kin bani koko nasha" kan gadonsa ya kaita ya direta nan suka shiga nunawa junansu yanda suka yi rashin juna, kuluwa kam tasha jagwalgwalo a hannun junior, kiss kuwa kamar zai cinyeta haka ya rinka lasar ta.


      *****************

Zamansu haka yayi ta tafiya lokacin har junior ya fara service a b.u.k yana koyar da organizational behavior ga yan public administration department year 2/1, kullum tare suke fita da kuluwa ya sauketa shima ya wuce inda zai yi lecture damuwarta yanzu kwaya daya ce ta rashin haihuwa amma baya da wannan bata da damuwar komai domin tana jin dadin zama da junior mutuka.

  Yauma kamar kullum ta fito daga lecture ta hango junior tsaye shida wata daliba tasha wata doguwar riga da dan siririn mayafi, kyakkyawa ce sosai kuma daga gani mahaifinta wanine, daga nesa ta tsaya tana jiransa, kallonsa ta fara yi sosai yana sanye cikin yellow din t shirt mai dogon hannu da pink din wando sai yatsine yatsinen fuska yake, "junior kenan, Allah ya rabani da sharrin yanmatan jami'a" ta fada a hankali, yana hangota ya taho inda take,"muje gida ko jidda na" "eh" ta fada tare da yin gaba, motarsa suka dosa suka shiga yaja suka tafi kallonsa tayi "budurwa kayi ne?" Murmushi yayi mata tareda kashe mata ido "kin fara gajiya danine kike neman abokiyar zama?" "Junior Allah serious ya kamata kayi aure tunda har yanzu ni ban haihu ba kuma gashi su mom sun kagu suka yaranka" hawaye ta fara "kayi aure ni babu komai tunda nasan bana haihuwa ai banida ikon kishi idan zakayi aure" hannunta ya kamo ya sakale cikin nasa "jidda kin daina sona ko? Tunda kika ce haka nasan kin daina sona kuma bakya kishina, haihuwa ai ta Allah ce kuma da kiketa maganar su mom suna son ganin yara na to kuma idan nine bana haihuwar yaya zasu yi?" Da sauri takai hannunta ta rufe masa baki cikin kuka tace "insha Allahu ma kana haihuwa","kema kina haihuwa kawai Allah ne bai kawo rabon ba, kuma wannan yarinyar ni ba budurwa ta bace, saboda ko zan haihu to nafi son na haihu dake" "Allah yasa" ta fada a hankali,"amin" ya fada tareda tsotsar bakinta.




Ummi A'ishaSANADIN GATA!

  Na
UMMI A'ISHA

8⃣5⃣

  Duk da cewa junior yayi mata bayani amma bata cire damuwa aranta ba haka take ta fama da tunane tunane ganin haka yasa junior daukarta suka je asibiti domin ganin likita bayan likitan ya duba su ne ya sanar dasu dukkaninsu lafiyarsu lau kuma zasu iya haihuwa a kowanne lokaci sai a sannan hankalin kuluwa ya dan kwanta ta rage damuwa.

  Shirye shiryen bikin Ummi yar gidan Anty Salma aka fara wanda za a gudanar watanni biyu masu zuwa tun da bikin ya kusa kuluwa take rokon junior kan yabarta taje gidan anty Salma in yaso bayan biki sai ta dawo, kin yarda yayi ganin ya hanata harda su kuka tayi, ana saura kwana 5 bikin kungiyarsu ta kirashi kan yaje Ghana zasu buga wani match shirye shiryen tafiya ya fara wanda hakan ba karamin dadi yayiwa kuluwa ba har sai da ya gane tana murna zai tafi harararta yayi "wato murna kike yi zan tafi ko? "Ba murna fa nake yi ba" janta yayi jikinsa yahada bakinsa da nata ya fara tsotsa, kokarin rabata da kayan jikinta ya fara, kyaleshi tayi ya gama jagwalgawalata son ranshi kafin ya aika mata da sakonsa mai wuyar fada.

A ranar da ya tafi itama ta tafi gidan anty Salma nan suka hadu da Ummi aka fara tsare tsaren yadda bikin zai gudana, anko kala biyar anty salma ta dinka musu iri daya ita da Ummi, tare sukaje akayi masu kunshi da gyaran gashi har gyaran jiki duk tare aka yi musu nan kuluwa ta zanzare ta fito kamar itace amaryar dan alokacin babu wanda zai ganta ya zaci matar aure ce kuma da yake itace akan komai tafito a babbar kawar amarya sai su kansu abokan angon suka zaci budurwa ce, kullum suna yin waya da junior har lokacin da ya buga wasan yake sanar mata da cewa yayi targade "gaskiya junior ya kamata ka daina ball haka saboda kar wata rana ka karye kuma" dariya yayi "kiyi mun addu'a kedai kawai Allah ya dawo dani kisha koko" murmushi kawai tayi, hidimar bikinsu suka ci gaba dayi, kullum mom din junior itama tana zuwa kayan gyaran amaryar da Anty Salma ta hadowa Ummi kuwa da kuluwa suka shanye tare, ranar alhamis akayi kamu, kai ranar idan ba sani kayi ba kaga kuluwa cewa zakayi itace amaryar tasha wani material orange riga da skirt tayi dam acikin kayan tasa gwaggoro orange ta dan yafa dan siririn dan kwalin gwaggoron sai kaiwa da kawowa take tana karbar bakinsu kawayen Ummi, mom tana daga can tana hangota sai murmushi take yi tana cewa "wannan yarinya da kokari take, ga ciki ga kuma taki zama ta huta" saboda alokacin kuluwa tayi wani fresh ga cika da tayi tako ina.

Ranar ko waya ba suyi ba da junior saboda shagulgula sun hau kanta, sai dare sannan ta samu damar yin waya dashi. Washe gari akayi wuni aka daura aure, kuma a ranar za akai amarya kuma za ayi dinner dan haka daga wurin dinner din gidan amarya za a zarce, shirya amarya kuluwa tayi sannan itama ta shirya kanta cikin material red, gwaggoro red, takalmi red mai mutukar tsini tasha sarka fashion katuwa golden, kwalliya aka yiwa amarya itama aka yimata, ko dan abun yafawa bata dauka ba haka suka tarkata suka tafi wurin dinner din kuluwa ce a gaban motar da amarya da ango suke, suna zuwa ta fita tareda shiga cikin hall din taje ta gyara high table, nan ango da amarya suka shigo daga can ta hango mom amma bataje wurin ba, shagali aka fara gudanarwa nan kuluwa takasa zama tayi nan tayi nan gashi komai za ayi ita abokan ango suke zuwa su fadawa, khamis daya daga cikin abokan angon ne yazo kusa da ita "um jidda dan Allah ga wasu matan abokan mu can sunzo kije ku gaisa tunda ita amaryar babu halin zuwa" " OK ina zuwa" "harda kishiyarki aciki" wal tayi da ido "nifa matar aure ce, wallahi ina da aure" hannunta taji an kama tana juyowa taga junior janta yayi take ta bishi babu musu, suna fita ya fara balbala mata masifa "ke kin manta kinada aure ne? Oh saboda ana biki shine zaki ajiye auren ko? To wuce mu tafi gida" kuka tafara "dan Allah kayi hakuri ka barni nakai Ummi gidanta" "bazaki kaitan ba" jikinta ya matsa ya matseta a jikin kofa, hannunsa ya tura cikin rigarta ya chafko kayan wasansa ya fara matsarsu dama tasan yadda ya jima baya nan dinnan dole yau ta gane kurenta, yar kara ta saki saboda jin yadda ya matsa da karfi "dan Allah ka barni na koma ciki" shiru yayi mata babu amsa, mom ce tafito ashe tare sukazo da junior shine ma ya kaita saboda tun yamma ya dawo amma bai fadawa kuluwa ba, dakyar mom ta shawo kansa ya yarda ya barta saboda idan ta tafi babu wanda zai yi maraba da bakin Ummi, komawa ciki tayi shikuma ya koma cikin mota ya zauna.

Sai karfe 11 aka tashi daga dinner din aka nufi gidan amarya agurguje kuluwa tayiwa Ummi huduba ta fito saboda junior yana jiranta, tunda ta shiga motar yaji yawunsa ya tsinke, "wash nagaji" tafada tana mika "ai kuwa yau dolenki ki bani hakkina wallahi, babu ruwana da wata gajiyarki" zaro ido tayi amma batace komai ba har sukaje gida, suna zuwa ya dauketa cak yayi bedroom da ita, suna shiga ya fara cilli da gwaggoronta, da su sarkarta sai da duk ya ciresu sannan yafara nuna mata zallar so.

Washe gari kasa tashi tayi dan gajiya, sai junior ne yayi musu girki, sati biyu da gama bikin Ummi kuluwa ta fara laulayi sosai, nan suka fara murna ita da junior kafin wani lokaci har ya sanar dasu mom zancen cikin nan fa aka fara lissafin haihuwa gaba dayansu sun dauki burin duniya sun dorashi akan wannan cikin na kuluwa shi kuwa junior kullum bashida magana sai "me zaki ci? Me kike sha'awa?" Gashi yanzu mom ta hanata aiki babu wani abun da take yi in banda dawainiyar junior gashi kusan kullum sai sun fita yawon zaga gari ita dashi. Sannu ahankali cikinta ya girma cikin kulawa da koshin lafiya, alokacin taga gata wurin junior domin komai shine yake yi mata tundaga kan wanka, wanki, yanke farce, tsifa, shaving, gyaran daki, girki, komai shine yake yi mata domin yana mutukar tausaya mata, lokacin da cikinta ya shiga wata tara da kwana goma ta tashi da azababben ciwo, cikin rudewa junior ya dauketa ya kaita standard hospital suna zuwa akayi maternity da ita, gefe junior ya koma ya kasa zaune ya kasa tsaye gashi saboda tsabar rudewa da burkicewa ma ya manto phone dinsa agida balle ya kira mom, mintuna kadan nurse ta fito ta kirashi tare da yi masa albishir din kuluwa ta sauka lafiya ta haifi yaronta namiji, "zan iya ganinta?" "No kabari yanzu mun shigar da ita dakin hutu sai nan da 20 minutes zaka iya ganinta" da sauri ya juya ya nufi motarsa ya shiga dagudu ya figi motar ya nufi gidan mom yana zuwa ya sameta ta caba ado tana zaune tana waya "mom, mom where are you? Jikinta yaje ya fada yana dariya,"mom yarki ta haihu yanzu" cikeda murna mom ta tashi "dagaske junior? Me ta Haifa?" "Mom an samu little junior" da sauri mom ta nufi dakinta taje ta dauko mayafinta ta fito gashi lokacin dad baya nan ya tafi taron siyasa mintuna kadan suka isa asibitin lokacin har an fara shiga ganin masu haihuwa, suna shiga dakin da kuluwa take junior yaje ya rungumeta ko kunyar mom bai jiba "sannu jidda na nagode, nagode jidda" hannunta ya kama ya rike cikin nasa,"sannu hawwa, sannu kinji" mom tafada tare da karasawa inda jaririn yake ta daukoshi bashida maraba da junior lokacin data haifeshi,gefen gadon ta samu ta zauna tana murmushi "like a father like a son" hannun kuluwa ya saki duk idonsa ya ciko da kwallar farin ciki ashe dama zai ga danshi na kanshi? Karbar jaririn yayi daga hannun mom ya fara kallonsa. Ganin bata da matsalar komai yasa aka basu sallama, gidan mom suka wuce direct nanfa junior ya fara tambayar mom "mom to kuma nida wa za abarni agidan?" "Kai kasani mom ta fada tana dariya tana rike da jaririn "shikenan mom tunda yanzu kin daina sona" junior ya fada cike da shagwaba.

Suna zuwa gida suka wuce side din mom wani daki dake kusa da nata ta bude musu kayan jarirai ne aciki iri iri da kayan wasansu nan aka shiga nunawa kuluwa gata ita da jaririnta, kafin wani lokaci sai ga su Anty Salma da Ummi amarya, nan Ummi ta dauki yaron tana Santi, yamma tana yi sai ga iyatu tazo domin tace itace zata yiwa yarta wanka, tunda aka yi haihuwar junior yayi wahalar gani saboda dakin nata kullum acike yake da jama'a gata dai kuluwa ta Ganshi har sai da tayi kuka domin dad din junior gida ya bata sukutum da makudan kudi ita kuwa mom wata dankareriyar sarkar gold ta biliyoyin kudi ta siyo mata ga dinkunan da tasha fiyeda kala 50 yaronta kuwa abun ba acewa komai, kwananta biyar da haihuwa kawarta Mairo tazo gashi ta taho mata da kayan gyara nan suka hadu da Ummi da ita suka sha cafta, ranar suna yaro yaci suna Muhammad zasu kirashi da haisam, tunda akayi suna junior ke bin mom kan ta bashi matarsa su tafi amma mom taki tace sai sunyi 40 domin har yanzu iyatu na nan tana gyara kuluwa dama babanta yazo yaga jaririn ya koma. Ranar da yamma mom bata nan ya shiga gidan ganin mom bata nan ya sashi tayarwa da kuluwa daru, jikinta ya shiga ya fara kissing dinta tareda shasshafa ta dakyar ta samu ya iya hakura ya kyaleta.

   Kullum junior yana gidan mom manne da kuluwa da haisam har suka yi 40 alokacin ya tada rikici dole mom ta barsu suka tarkata suka tafi, suna zuwa gida ya dauki haisam "ke ko nemana ma ba kyayi ko?" "Waya fada maka wallahi nayi missing dinka mijina" "zaki fada musu ne bari muje ciki" suna shiga dakinsa yaje ya kwantar da haisam wanda yake ta sharar baccinsa ya nufi dakin kuluwa tana tsaye tana waya da Ummi lokacin da ya shiga dama gata katuwa yanzu da ta haihu sai ta kuma zama katuwa sosai,"malama kizo kiyi biyan bashi" ya fada a hankali, wayar ta kashe ta karasa jikinsa ta fara shafashi tana kissing dinsa shi dai junior kamar wani soko haka ya zama nan suka fara nunawa junansu yanda sukayi missing juna.

Rayuwar junior da kuluwa yanzu ta zama abun kwatance ga wasu domin suna zaune lafiya da juna yanzu haisam yana da watanni biyar bul bul dashi komai nasa irin na junior, tare dashi suke renon haisam kusan kowanne lokaci yana tare dashi ko ya kaishi gidan mom ko kuma yafita dashi ganin gari abun nasu gwanin dadi amma har yanzu junior bai daina buga kwallo ba, idan ka Ganshi tsaf dashi kamar wani saurayi,Sam bai yi kama da magidanta ba, kuluwa kuwa an zama manyan mata domin duk wanda ya ganta yasan tana hutawa kuma ta zamto shalele wurin mijinta. Sai da haisam ya shekara biyu sannan ta yayeshi nan kuma ta fara wani laulayin lokacin har ta gama degree dinta itama Ummi ta haifi yarta mace, ita dai kuluwa haihuwa ko yau ko gobe amma hakan bai hanata hidima da junior ba domin ko yanzu ma kwance yake jikinta yana lalubarta hannunsa ta rike "bazaka barni na huta ba?" "Sorry baby na kokon zaki sammin dan kadan" murmushi tayi tareda rungumeshi ajikinta.


ALHAMDULILLAH!
Anan nakawo karshen labarin SANADIN GATA duk wanda ya sarrafa min shi ta wata hanya ban yafe ba.

SANADIN GATA TUKWICI NE GAREKI
Uwar dakina

HAUWA M JABO ( kuluwan junior) Mrs... To be.

KUNA INA?
Kawayena na kaina

Khadija Sidi kawata
Teemah cool kawata
Ummu Samha kawata
Chucu masoyiyar asali
Nana Chocho kawata
Fido sodangi kawata
Mamie hamma kawata
Sady kawata
Hafsat Bunza kawata
Maman Kdj kawata
Hajara Gamji kawata

JINJINA AGAREKU
Baby pherty
Maman Shakur
Sallyn junior
Kdeeyn junior
Futhan junior
Lubieen junior
Mom Halamcy
Maman Ansar ( Yar garinmu)
Hafsat mai sheriff

FATAN ALKAIRI GAREKI
Cwt namcy A'isha Dansabo lemu

GAISUWA GA TAKWARORIN KULUWA

Hauwa (hawyn junior)
Hauwaty
Kulu hydar
Jiddah m husain

Kina Raina Babbar yaya, abar alfahari na
ADDA BENAXIR OMAR

Kawata kinfi ta kowa
KAUSAR LUV, u are always in my mind, Luv you kawata! Allah ya barmu tare eva,gaisuwarki ta musamman ce yan matan faruku!.

Gaisuwa mai tarin yawa ga masoyan junior, musamman wadanda suka kaunace shi da kuluwa, junior loves you too!

LITTATTAFAN MARUBUCIYAR
~Biyayyar Iyaye
~Sultan
~Bakin Alqalami
~Mace guda daya tilo
~Benaxir ko Kausar
~Kausar Yar autar mata
~Sai naga Benaxir Omar
~Kwarya tabi Kwarya
~Ruwan Dare
~Aure yakin mata
~Alheri Danko ne!
~Sanadin gata!


Masoyan UMMI A'ISHA nagode da soyayyar da kuka nunawa wannan littafin Allah ya barmu tare, ina son ku kamar yadda kuke sona, sunan ku bazai iya lissafuwa ba acikin wannan dan karamin littafin amma aduk inda kuke Ummi A'isha tana gaidaku, ban manta daku ba yan group dina ina godiya a gareku, luv you all! Taku ahar kullum UMMI A'ISHA

8 comments:

  1. Wow nyc story Allah ya Kara basira

    ReplyDelete
  2. This is a great temple of the Illuminati were you find, POWER, RICHES, FAMOUS, WEALTH, if you want to get rich quick and be famous"you need to cross your heart and do what is in your mind, are you a business man or woman,i want to share on how i belong to Illuminati member, a friend of mine that always give me money because he was very rich, one day he said he is not going to give me money,and how to fish that he is going to teach me how to fish, so i was very happy, i never new he was a member of Illuminati all my life will spend together! so i was initiated to the Illuminati world and few days i was awarded a contract worth of millions of Dollars, in my business i am doing very well right now,i am now the one that give money out before it was heard, if you want to belong to us email us on:famousilluminatitempel@gmail.com do you want all your dreams to come to pass? Are you an upcoming artist? dancer? businessman? etc the Great Illuminati Society offers you a life time opportunity of making your desires come to accomplishment. If you are interested in being a member please contact us online via email>:famousiiluminatitempel@gmail.com or call me on this Mobil number:+2349059980562

    ReplyDelete
  3. WELCOME TO THE GREAT BROTHERHOOD. be a member of Illuminati as a
    brotherhood that will make you rich and famous in the world and have power
    to control people in the high place in the worldwide .Are you a business
    man or woman,artist, political, musician, student, do you want to be rich,
    famous, powerful in life, join the Illuminati brotherhood cult today and
    get instant rich sum of. 2 million dollars in a week, and a free home.any
    where you choose to live in this world and also get 10,000,000 U.S dollars
    monthly as a salary BENEFITS GIVEN TO NEW MEMBERS WHO JOIN ILLUMINATI. 1. A
    Cash Reward of USD $500,000 USD 2. A New Sleek Dream CAR valued at USD
    $300,000 3. A Dream House bought in the country of your own choice 4. One
    Month holiday (fully paid) to your dream tourist destination. 5. One year
    Golf Membership package 6. A V.I.P treatment in all Airports in the World
    7. Access to Bohemian Grove IF YOU ARE INTERESTED IN JOINING US IN THE
    GREAT BROTHERHOOD GROUP OF ILLUMINATI SATANIC HAND CONTACT US WITH OUR
    EMAIL; mrwilliam666illuminati@gmail.com or whatsapp me+2348140425775

    ReplyDelete
  4. Asama mana bakuwar fuska Dan Allah

    ReplyDelete
  5. hello 4 letest hausa novels complete visite www.hausabook.com

    ReplyDelete
  6. WELCOME TO THE GREAT BROTHERHOOD.
    Do you want to be a member of Illuminati as a brotherhood that will make you rich and famous in the world and have power to control people in the high place in the worldwide .Are you a business man or woman,artist, political, musician, student, do you want to be rich, famous, powerful in life, join the Illuminati brotherhood cult today and get instant rich sum of. 2 million dollars in a week, and a free home. any where you choose to live in this world and also get 20,000,000 U.S dollars monthly as a salary %2026
    BENEFITS GIVEN TO NEW MEMBERS WHO JOIN ILLUMINATI.
    1. A Cash Reward of USD $800,000 USD
    2. A New Sleek Dream CAR valued at USD $500,000 USD
    3.A Dream House bought in the country of your own choice
    4. One Month holiday (fully paid) to your dream tourist destination.
    5.One year Golf Membership package
    6.A V.I.P treatment in all Airports in the World 7.A total Lifestyle change 8.Access to Bohemian Grove
    9.Monthly payment of $2500,000,000 USD into your bank account every month as a member
    10.One Month booked Appointment with Top 5 world Leaders and Top 5 Celebrities in the World.
    If you are interested of joining us in the great brotherhood illuminati satanic hand symbol contact us now with this number or whatsapp me (+2348083325148 }OR Email- Illuminatimoney66@gmail.com

    ReplyDelete
  7. WELCOME TO THE GREAT BROTHERHOOD.
    Do you want to be a member of Illuminati as a brotherhood that will make you rich and famous in the world and have power to control people in the high place in the worldwide .Are you a business man or woman,artist, political, musician, student, do you want to be rich, famous, powerful in life, join the Illuminati brotherhood cult today and get instant rich sum of. 2 million dollars in a week, and a free home. any where you choose to live in this world and also get 20,000,000 U.S dollars monthly as a salary %2026
    BENEFITS GIVEN TO NEW MEMBERS WHO JOIN ILLUMINATI.
    1. A Cash Reward of USD $800,000 USD
    2. A New Sleek Dream CAR valued at USD $500,000 USD
    3.A Dream House bought in the country of your own choice
    4. One Month holiday (fully paid) to your dream tourist destination.
    5.One year Golf Membership package
    6.A V.I.P treatment in all Airports in the World 7.A total Lifestyle change 8.Access to Bohemian Grove
    9.Monthly payment of $2500,000,000 USD into your bank account every month as a member
    10.One Month booked Appointment with Top 5 world Leaders and Top 5 Celebrities in the World.
    If you are interested of joining us in the great brotherhood illuminati satanic hand symbol contact us now with this number or whatsapp me (+2348083325148 }OR Email- Illuminatimoney66@gmail.com

    ReplyDelete
  8. WELCOME TO THE GREAT BROTHERHOOD.
    Do you want to be a member of Illuminati as a brotherhood that will make you rich and famous in the world and have power to control people in the high place in the worldwide .Are you a business man or woman,artist, political, musician, student, do you want to be rich, famous, powerful in life, join the Illuminati brotherhood cult today and get instant rich sum of. 2 million dollars in a week, and a free home. any where you choose to live in this world and also get 20,000,000 U.S dollars monthly as a salary %2026
    BENEFITS GIVEN TO NEW MEMBERS WHO JOIN ILLUMINATI.
    1. A Cash Reward of USD $800,000 USD
    2. A New Sleek Dream CAR valued at USD $500,000 USD
    3.A Dream House bought in the country of your own choice
    4. One Month holiday (fully paid) to your dream tourist destination.
    5.One year Golf Membership package
    6.A V.I.P treatment in all Airports in the World 7.A total Lifestyle change 8.Access to Bohemian Grove
    9.Monthly payment of $2500,000,000 USD into your bank account every month as a member
    10.One Month booked Appointment with Top 5 world Leaders and Top 5 Celebrities in the World.
    If you are interested of joining us in the great brotherhood illuminati satanic hand symbol contact us now with this number or whatsapp me (+2348083325148 }OR Email- Illuminatimoney66@gmail.com

    ReplyDelete