Saturday 7 January 2017

RUWAN KASHE GOBARA.. 2

*RUWAN KASHE GOBARA..!*🔥
_(labari mai tab'a zuciya)_


  *_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*


_Sadaukarwa ga kawata Khadija Sidi_


_2_



~~~ Batare da tsoron komai ba Lamido ya karasa wurinta, ahankali yakai hannunshi jikinta ya dago fuskarta, duk da dattin daudar dake dank'are ajikinta bai hana hasken fatarta fitowa ba,

K'ura mata ido yayi yana kallon kyakkyawar fuskarta wacce take bud'u bud'u da kura gamida dauda,

Bash yana daga cikin mota yana kallonsu ta glass, kamo hannunta Lamido yayi yana kokarin tayar da ita tsaye, nan suka fara kokawa wadda har shi kanshi lamidon sai da yayi mamakin karfinta amma kuma kasancewarta mai rangwamen hankali shiyasa take da wannan karfin,

Dakyar ya iya murde hannuwanta ya kinkimeta zuwa wani kango wanda yake a baya kadan da shagunan da take zaune, ihu take son yi amma ya toshe mata baki, duk tsananin daudar dake jikinta bata sanya Lamido jin kyamatarta ba gashi dan gayu mai mutukar class amma haka ya iya hada jiki da ita,

Kusan awa guda cif lamido yana manne da ita, wata irin runguma yayi mata yana kallonta duk jikinshi zugi yake masa saboda yakushin da ta yiyyi masa gashi faratanta zako zako suke,

Tashi yayi yana gyara belt din jikin jeans dinsa yana kallonta kwance shame shame ko motsi ba tayi, daga ganinta bazata haura shekara 25 ba sannan har acikin ranshi yasan ya sameta a matsayin cikakkiyar budurwa domin shine namiji na farko da yafara rabata da *MARTABAR TA*,

Kinkimarta yayi ajikinshi ya nufi inda ya daukota da farko, sam shi baiji wani warin dauda ko karnin dauda atare da ita ba amma kuma gata nan dak'a dak'a, shinfidar da ita yayi ya tsaya yanata kallonta wanda shi kanshi bai san dalili ba,

Yana nan tsaye yana kallonta bash ya cika masa kunne da horn dole ba dan yana soba ya juya da niyyar tafiya har yayi taku daya biyu ana uku ya tsaya ya jiyo da sauri yazo ya kama dan yatsanta ya cire wani zobe dake jiki na bakin karfe yayi jifa dashi ya zare wani a karamin dan yatsanshi na azurfa wanda aka rubuta L ajiki ya saka mata a babban dan yatsanta,

Tashi yayi da sauri ya karasa wurin bash ya shiga suka tafi, kwantar da kujera Lamido yayi yana fitar da numfashi ahankali yana kallon hadirin dake gudu a sama ta cikin glass din motar,

"Gaskiya Lamido sai yau na tabbatar da cewar kai marar imani ne, in banda rashin imani da rashin tausayi ta yaya mutum zai samu mahaukaciya wacce tunaninta ya gushe har ya tara da ita"

Ya jiyo muryar bash yana fada, jiyowa yayi ya kalli bash,

"Bash bazaka gane bane, wallahi ni kaina tabani tausayi kwarai saboda bakaga yadda ta rinka kokarin hanani abinda nayi niyya ba amma takasa, banyi haka da niyyar zalunci ba, kawai dan babu yadda na iya ne"

"Wai kai ko warin da jikinta yake yi bai hanaka sukuni ba?" Bash ya sake tambayarshi yana kallon titi,

Shiru yayiwa bash bai amsa mishi ba saboda shi kadai yasan irin abinda yakeji yana ratsashi domin bai taba jin irin wannan yanayin ba sai yau,

"Lamido ka dade kana bin yaran mutane kana lalatawa ashe abin naka bai tsaya a iya nan ba har mahaukaciya zaka bi"

"Bash shifa *RUWAN KASHE GOBARA* nafada maka basai mai kyau ba, rashin mafita ne yasani bin mahaukaciyar nan,sannan duk yan matan da nakebi ai da yardarsu ne ba fyade nake yi musu ba, wannan mai tabin hankalince kadai nasan na taba yiwa fyade tunda uwata ta haifeni"

Jinjina kai bash yayi yaci gaba da driving daf da zasu shiga kwanar gidansu Lamido ruwa ya kece kamar da bakin kwarya,

Hankalin Lamido ne yatashi sakamakon tunowa da yayi da wannan mahaukaciyar,

"Bash ka juya mu koma mu dauko yarinyar nan, wallahi nasan nayi mata illa, na illatata bash, nayi mata abinda ba zata iya kare kanta daga dukan ruwan nan ba, idan bamu koma mun taimaketa ba ruwan nan akanta zai kare gashi da alama yau sanyi za ayi"

Lamido yafada cikin tashin hankali gashi muryarsa har rawa take amma hakan bai hana kyawunsa sake bayyana ba,duk maganar da zaiyi sai kumatunsa ya lotsa,

"Gaskiya nifa kafara takura min, yanzu sai mun sake komawa?"

Jijjiga kai Lamido yayi,

"Idan ba zaka koma ba bani motar ni nakoma,bazan iya kyaleta acikin wannan yanayin ba, gashi wani irin zazzafan zazzabi nakeji yana neman saukar min ajikina"

Dole haka bash yayi ribos suka juya, kwanciya Lamido yayi akan kujerar yana dan karkarwar sanyi domin zazzabi yafara rufeshi, tunanin mahaukaciyar yarinyar nan kawai yake yi sai dai yabarwa zuciyarshi nishadin da yaji agame da ita,

Saboda gudun da bash ya sharara basu wani jima ba suka karasa wurin lokacin har ruwan yayi yawa,suna isa wurin suka ga wayam,

Zazzabin dake jikin lamidone yaji yasake tsananta, zuciyarsa ce tafara dukan uku uku saboda ganin yarinyar bata nan.






_*Ummi Shatu*_

No comments:

Post a Comment