Thursday 22 December 2016

ALHERI DANKO NE 1-50

mmi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣ 

Na UMMI A'ISHA

     JAN KUNNE- duk wanda ya canza min wannan labarin ko ya canja sunan taurarin ciki, ko yayi min editing ALLAH YA ISA BAN YAFE BA.

      Tafe yake yana cire  safar hannun dake hannunsa yana cillar da ita akan tile din dake malale aharabar runfar asibitin, leburorin wurinne suke biyeda shi suna tsince duk abinda ya yar awurin shikuwa sai faman yatsina fuska yake yi sai kace yaune ranar farko wadda yafara karbar haihuwa kokuma yafara operation,ahankali yake tafiya sai kace marar jini ajiki yana sanye da light blue colour din t shirt mai dogon hannu da black din jeans idonsa sanye cikin farin gilashi amma da alama gilashin nasa na gayune bana kara karfin ido bane, duk inda ya ratsa babu abinda kakeji sai weldon sir! Shi kuwa gogan baya magana sai daga hannu domin magana tana mutukar bashi wahala saboda yangarsa da jan ajinsa gashi da iyayi kamar mace amma hakan yana mutukar kara masa kyau kuma da alama iyayi nature dinshine, ayanda na hango fuskarsa zan iya kiyasta shekarunsa bazasu haura 27 ba aduniya,fari ne dogo siriri lange lange kana ganinsa zaka gane baya aikin wahala kuma hutu ya zauna ajikinsa, cikeda yanga ya karasa office dinsa wanda yake jere a rukunin ofisoshin manya likitoci ( consultants) wani office yabude yashiga wanda asaman kofar aka manna wani dan katako aka rubuta DR TAFIDA ajiki da manyan harrufa, ahankali yashiga cikin office din wanda yayi tsananin tsaruwa kamar ofishin shugaban kasa, kan wata doguwar kujera baka yaje yakwanta yamike yatasa kansa da hannun kujerar yafara cire (neck tied) din wuyan rigarsa yacire gilashin fuskar sa yalumshe manyan idanuwansa wanda suke zagaye da bakaken gashi masu mutukar baki sai da yadan huta sannan ya mike a hankali tamkar mace ya isa kan teburinsa yadanna wata kararrawa aguje wasu fadawa guda uku sanye cikin jajayen kaya suka shigo, suna shigowa suka fara zabga kirari, Allah ya taimaki mai girma tafida, dan sarki jikan sarki kuma sarkin gobe da yardar Allah, Allah yakara maka nisan kwana!
[6:56PM, 11/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣

Na UMMI A'ISHA

   Hannu yadaga musu take sukayi shiru saboda sun gane nufinsa kuma dama can shi baya son yawan magana duk maganarshi atakaice yake yinta itama sai takama mutuka amma in bakamawa tayi ba sai dai yayi umarni da hannunsa, kallonsu yayi yanuna musu kan table dinsa tuni suka zabura suka fara harhada takardun dake kan table dinsa gamida dibar wasu files manya, laptop dinsa da brief case dinsa suna gama harhadawa sukayi waje yayinda shi kuma dr tafida ya sake mikewa a kujerar da yake kai sai da ya shafe sama da minti 20 ahaka sannan yatashi yahau kan kujerarsa ta aiki yajawo drawer dinsa yaciro tabar wiwi (ganye) yadauki ashana ya kyasta yafara busa hayaki, wani dan madaidaicin glass cup ya ajiye musamman akan table dinsa inda yake tara tokar tabar da yakesha kuma da alama yana sha akai akai domin har kofin yakusa cika da tokar tabar, zukar tabar wiwin yaci gaba dayi har ta kare sannan ya kishingida ajikin kujerarsa nanma yashafe fiyeda minti goma sannan yatashi ya dauki phones dinshi da gilashinsa yafita daga office din yana fita fadawansa suka zabura suka nufi motarsa dasauri suka bude masa gidan baya yashiga yazauna suka rufe kofar motar suka runtuma tasu yayinda daya daga cikinsu yashiga mazaunin direba ya zauna yatashi motar ya harba suka bar harabar cikin asibitin.
[7:33PM, 11/11/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣

Na UMMI A'ISHA

         Fita sukayi daga harabar asibitin mutane sai kallon motocin nasu sukeyi gamida daga musu hannu amma dan mulkin yana daga kishingide acikin kujerar baya hannunsa rikeda jaridar daily trust yana karantawa da haka har suka isa kofar fada inda anan gidansu dr tafida yake, wani makeken gida nagani gaba dashi kuma filine babba tuni digarawan dake zaune abakin kofar gidan suka mimmike tsaye saboda ganin motar tafida,kan motocin suka kutsa cikin babban gidan wanda yasha zane iri iri da adon kala kala irin na sarakai nidai ummi Aisha tun daga nan nagane cewar gidan sarki nashigo domin gaba daya tsarin gidan namasu sarauta ne, cikeda iyayi da takama hadida kasaita dr tafida yafito daga cikin motar yatasamma cikin gidan wanda akalla sai da aka wuce zauruka sunfi 5 sannan yakarasa wani babban fili mai dauke da part part akalla zasu kai guda 5 kansa tsaye yawuce wani sashe mai mutukar kyau wanda yasha ado da kwalliya, budewa kofar falon yayi yashiga nan nahango wani dattijon mutum wanda akalla shekarunsa zasu kai 65 yana kishingide akan kilisan dake malale acikin falon wanda yawansu zai iya kaiwa guda biyar kala kala gashi jikin bangon dakin yasha zane na sarauta, gefensa tumtum ne wanda yajingina ajiki ga kayan marmari nan agefe dangin itatuwa kamar su inibi, tufa, ayaba, kankana, gwanda, zaitun, ruman, da sauran kayan itatuwa cike cikin wani dan madaidaicin kwando wanda aka tanada musamman dan adana kayan marmari, cikeda alamun gajiya yayi sallama ahankali yashiga wannan al'adarsa ce duk lokacin daya dawo daga office sai yaje ya gaida mahaifinsa da mahaifiyarsa,washe fuska dattijon yayi ya amsa sallamar da Wa'alaikas salam wa rahmatullahi wabrakatu, barka da zuwa ibrahim cikin jin dadi yakarasa inda mahaifin nasa yake yazube akasa yafara kwasar gaisuwa,barka da hutawa mai martaba dafatan mun sameku lfy, ya akaji da jama'a? Cikin jin dadi yace alhamdulillah ibrahim dafatan ka dawo lfy? Lfy lau  yafada yana murmushi gamida mikewa yana fadin nabarka lfy ranka yadade, Allah yakara nisan kwana, Allah yaja zamani.


4⃣

      Yana fitowa ya gangara izuwa wani sashen nagaba wanda tun daga nesa nafara hango bayi da kuyangu sai faman kaiwa da komowa suke, wasu suna aikace aikacen gida wasu kuma suna ta faman shige da fice tunda tafida yadoso su suka fara zubewa suna dibar gaisuwa barka da dawowa mai girma tafida, takawa lfy dan sarki jikan sarki, tafiya sannu sannu kwana nesa sarkin gobe, hannunsa kawai yake cira musu amma ko kala yakasa furtawa sai dai da alama sun san halin tafidan domin hakan bai hanasu cigaba da gaishe shi ba, ko kallo basu isheshi ba balle ya amsa gaisuwarsu wannan dalilin ne yasa mutane da dama suke kiransa da mai girman kai wasu kuma suce yanada iyayi da wulakanci to koma dai menene da alama iyayin nature dinsa ne
[8:36PM, 11/11/2015] Ummi A'isha: Tamkar wani mai ciwon kafa yaci gaba da tafiya har ya cimma sashen mahaifiyarsa hajiya  Kilishi wadda yake tangamemen gaske yana shiga kasaitaccen falon nata wanda yasha adon kayan alatu yafara cin karo da bayinta wasu sunata aikin gyaran falon wasu sunata wawwatsa wani abu mai mutukar kamshi kamar turaren wuta suna ganinsa suka durkusa barka da shigowa mai girma tafida! Kai kawai ya gyada yawuce cikin dakin inno kamar yadda yake kiran mahaifiyar tashi, akan wata katuwar darduma ya hangota tana zaune ta jingina bayanta da babban filo kafafuwanta kuma ta dorasu kan tumtum wata baiwa sai aikin mammatsa mata kafafun take, da sallamarsa yashiga yana shiga wannan baiwar ta zabura barka da zuwa yallabai, bai bata amsaba tatashi tafice, agefen gadon mahaifiyar tashi ya zauna wani irin gadone nakarfe mai runfa fentinsa kalar ruwan hoda yasha lallausar katifa da shinfidu na alfarma ga kamshi mai dadi dayake tashi daga cikin dakin, barka da hutawa inno yafada yana wani lallausan murmushi, yawwa barka da zuwa tafida tafada tana murmushin itama, kallo daya zakayi mata kagane cewa mahaifiyarshi ce domin babu ta inda ya barta akama, kamarsu daya dashi kuma da alama tana jidashi sosai, macece mai fara'ar gaske kuma bata tsufa ba dan shekarunta bazasu wuce 45 amma bazaka taba gane hakan ba saboda jikinta bai nuna ba ko kusa, cikeda kulawa tace zakaci abinci ne yanzu? Kai ya girgiza tamkar wani karamin yaro yace a'a inno sai anjima yanzu bacci nakeji, to atashi lfy tafada tana murmushi,murmushi yakuma yi yakwanta akan gadon mahaifiyar tashi yaja filo yatasa kansa dandanan bacci yayi gaba dashi, tashi inno tayi takoma falo tazauna gudun kada azo adameshi yana bacci.


5⃣

     Karfe 3:40 yatashi daga baccin da yakeyi yafito idonsa duk yayi kalar masu bacci afalo ya taradda inno tana salla dan haka bai tsayaba yawuceta yafita daga lungunta yanufi nashi yana shiga yafada toilet ya hada ruwan zafi yayi wanka yafito yasaka farar t. Shirt mai gajeren hannu yasa wando jeans baki yafesa turaren FOGG yafito yanufi masallaci lokacin dayaje har anshiga salla, yana idarwa ya fito ya wuce ma 'ajiyar dawakai yasamu an shirya masa dokinsa anyi masa shimfida an gyarashi domin fita kilisa bai bata lokaci ba yahau suma fadawansa wanda suka hada da sarkin fada, sarkin mota, da maja sirdi suka hahhau nasu suka fito daga gidan ahankali suke tafiya tacikin garin har suka fita suka shiga dokar daji, dama idan da sabo sun saba dan kusan kullum sai tafida yafita kilisa, kilisa tana daya daga cikin abubuwan da suke burgeshi a harkar sarauta, tafiya kawai suke suna shakar iskar dake ratsa dajin sannan suka billa tawata hanyar domin komawa gida alokacin mangariba takusa yi har ta kawo jiki, suna zuwa gida ana kiran salla, akasalance tafida yasauka daga kan kosasshen dokinsa yayi alwala yashiga masallaci ana idar da salla yafito adaidai lokacin wata hadaddiyar mota tashigo baka kirar croutoure mai tsananin kyau ajiki an rubuta TAFIDA 1 kallon motar yayi yai tsaki yawuce gaba, agabansa aka yi packing din motar aka fito wani saurayine wanda zai kaishi atsaye kuma ashekaruma bazai fishiba yafito daga cikin motar yana dariya Allah yaja zamanin tafida, batare da tafidan yayi masa magana ba yawuce yafara tafiya shikuma yabishi abaya har suka karasa sashen tafidan suka shiga, afalo suka zauna cikin muryar iyayi tafida yace wai kai faisal meyasa bakada mutunci ne? Motar tawa kadauka katafi yawon iskanci? Dariya yayi wanda aka kira da suna faisal yace haba abokina kaima iskancin nan kana dan tafabawa, fuska tafida ya yamutsa, ni bana wani iskanci kaine dan iska, ok naji ni dan iskane saboda ina neman mata kai kuma dan ganye? Filon kusa dashi tafida yadauka yajefeshi kai dan iska ne idan ni dan ganye ne ai dasauki tunda har yanzu ni saurayine cikakken saurayi kuma, dariya abokin nasa yayi dakyau virgin boy, amma dai abi ahankali banda ganganci,shiru tafida yayi bai kara magana ba domin shi baya doguwar magana idan kajishi yayi magana mai tsawo to da mahaifinsa ne ko mahaifiyarshi ko kuma abokinsa faisal.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [7:23PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE !

6⃣

Na UMMI A'ISHA

      Tashi tafida yayi ya shiga daki yahaye gado yakwanta minti kadan faisal yabiyoshi cikin dakin abokina ya zaka kwanta bayan ba mugama magana ba? Kai malam bana son surutu, eh nasani ai shiyasa nake son na sanar dakai cewa na dauki wadannan kudin naka nayi sadaka dasu, tsaki tafida yayi mtwww to ina fata ba iskanci kaje kayi da kudina ba? Murmushi faisal yasake yi wai kai finka laifi nayi? Kaima fa mai laifi ne, kana shan ganye over ni kuma ina neman mata jifa jifa ba koda yaushe ba, murmushi tafida yayi yatashi zaune, to ai ni matan ne ma tsoronsu nake, gaba daya ban san ta inda zanbi ba yanzu haka idan ka ajiye min mace wlh ban san yadda zanyi da itaba, wata irin dariya faisal yayi hahahaha! Ammafa kacika dan rainin wayo, ta ina kake karbar haihuwa? Kaida ka karanci mata kasan yadda suke, karfa ka manta kai likitan matane su kake gani kake dubawa akoda yaushe, dan malalacin murmushi tafida yasaki to sai aka fada maka kuma nasan hanyar? Karya kake kasani mana, dariya tafida yayi kai dan iska ne, wlh duk ranar da mai martaba yasan kana neman mata sai ya tube rawanin da ya daura maka,cikin dariya shima faisal din yace kamar yadda kaima mai martaba zai tube rawanin daya daura maka ba duk ranar da yagane kai mugun dan ganye ne, murmushi tafida yayi ra'ayina shine nasamu cikakkiyar budurwa kamar yadda nake cikakken saurayi, taba baki faisal yayi eh munji kai saurayine amma ai dan ganyene, dariya tafida yayi duk da haka dai nafika,ni yanzu ma ka kyaleni wlh yunwa nakeji sai da inno tace naci abinci dazu nace bacci zanyi amma bari nayi mata waya akawo mana, wayarshi ya dauka kirar yota phone yakira inno yace akawo masa abinci shida faisal ba awani jimaba sai ga kuyangi guda 2 sun shigo hannuwansu dauke da tirarrika na silba manya manya anan suka ajiye suka fita, suna fita faisal ya fara bubbude kwanukan abincin, abinci ne kala kala na gargajiya saukowa tafida yayi suna ci suna hira har suka gama, suna gamawa suka tafi masallaci sukayi salla suka shigo gida afalo faisal yazauna yafara waya da yanmatansa shi kuma tafida yawuce daki yafada kan gado yajanyo tabar wiwi yafara zuka.


7⃣

      Washe gari dasafe dr tafida yashirya tsaf cikin shirinsa nafita office bakin wando yasa da bakar t.shirt mai dogon hannu yadora jar jacket asama yasa bakin takalmi cover shoe
[7:38PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: Yafesa turaren fogg yafito lokacin faisal yanata bacci kasancewar shi a ministry for local government yake aiki baya fita dawuri shikuwa tafida 7:30 yasaba fita office, yana fitowa sarkin fada da sarkin mota sukazo suka zube suka fara zabga kirari barka da fitowa mazajen fama hadiri sa gabanka inda kakeso, murucin kan dutsi baka fitoba sai da ka shirya, atafe dakyau, atsaye dakyau amma azaune kafi dadin kallo dan ahmadu jikan sani gyara kintsi giwa kinfi karfin waiwaye, kura ko kin mutu kinfi karfin kare, wani kaya sai amale wane jaki, cikeda takama yace barkanku da safiya yawuce cikin gida yanufi dakin inno mahaifiyarshi alokacin har ta harhada masa kayan karyawarshi tsaf ta zuba acikin akushi mai kyau tana jiran shigowarsa, yana shiga yazube agabanta tana kushingide hannunta rikeda carbi tana ja sukuma bayinta har sun fara aikace aikacen da suka saba yi, barka da asuba inno yafada idonsa akasa, barka da tashi tafida, kafito lfy? Lfy lau inno, to Allah yabada sa'a, Allah ya tsareka, Allah yadawo dakai lfy, amin inno nabarki lfy, tashi yayi yafita yanufi sashen mai martaba lokacin shima yana zaune afalonsa yana karatun alqur'ani mai girma, cikin girmamawa tafida yadurkusa barka da asuba ranka yadade, cikin murmushi yace yawwa ibrahim har anfito? To Allah yatsare Allah yabada sa'a, amin mai martaba yafada yatashi yafita inda aka adana motarsa yanufa aka bude masa gidan baya yashiga yazauna cikeda nuna isa yake daddana wayar hannunsa fadawa sai kawo gaisuwa suke yi amma yakasa amsawa,asibitin Rasheed shekoni specialist hospital suka dosa inda tafida yake aiki.
[7:48PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

8⃣

      Na UMMI A'ISHA

Suna zuwa kamar kullum yafito yashiga office dinsa wanda yake jere ajerin gwanon ofisoshin kwararru na asibitin, yana zama wata nurse tashigo tana sanye da fararen kaya,morning sir! Morning ya amsa mata idonsa yana kan laptop dinshi yana daddannawa, sir akwai patient wanda jiya kayiwa operation tofa har yanzu bata farfado ba, cikeda damuwa ya tashi domin shi yana tausayin mata duk lokacin dayaga mace acikin halin rashin lafiya sai yaji kamar zaiyi kuka, maternity yanufa wannan nurse din tana biye dashi abaya ita dai wannan likitan yana burgeta domin yasan aikinsa matsalarsa kawai yanada girman kai ga nuna isa kamar shine sarkin ko dan sarauta ne? Yahadu sosai ga kudi da sarauta ga ilmi ga uwa uba kyau, yana shiga maternity yafara bin patient din daya bayan daya yana dubasu har yagama yakoma office dinsa alokacin yafara ganin marassa lfy wadanda suka zo ganin likita kuma gaba dayansu matane domin shi mata kawai yake dubawa baya duba maza sai wurin 11 yagama ganin marassa lfy yayi breakfast yatashi yashiga round.
[8:16PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

9⃣

    Na UMMI A'ISHA

Yana dawowa daga round yanemi wuri a office dinsa yazauna lokaci lokaci fadawansa suna lekowa domin ganin lafiyarsa, sai misalin karfe 5 yatashi lokacin yafito daga theatre cikin gari suka shiga akan hanyarsu ta tafiyane suka ratsa tawani dan kauye anan yaga wata makekiyar gona wadda akalla zata kai kilo mita 5 anyi shukar shinkafa aciki, shukar tayi kyau sosai sarkin mota ya yiwa magana cewa ya tsaya cikin sauri ya taka birki yaja ya tsaya yabude kofa yafito suma fadawan firfitowa sukayi suka tsattsaya, gonar ya zubawa ido ta kayatar dashi hakika wannan zatayi daidai da wurin da yake nema domin gina business suit dinshi hadida gidan shakatawarsa motar ya koma yashiga ya zauna, fadawansa suka shisshiga suka nufi gida tun da suka shiga yasan cewa mai martaba yau yana fada dan hakan fadan yashiga wacce ta kayatu sosai, mai martaba yana zaune akan wata karagar mulkinsa ta alfarma wadda tasha ado da zinare, gefe daga hannunsa nadama wazirine da galadima ga chiroma, kusa dashi kuma hakimin cikin garine, daga hannun hagu kuma wani dan dattijone zaune wanda shekarunsa zasu kai na mai martaba kusa dashi kuma san turakine wato faisal aminin tafida, cikin sallama tafida yazauna yayi gaisuwa yatashi yashige cikin gida yawuce dakin inno yau bai wani jimaba yafito yashiga dakinsa yayi wanka yafito cikin bakar riga da bakin wando, yanufi lambu wanda yake girke acikin gidan, wurin yasha shukoki na kayan marmari ga wata korama daga tsakiya tana gudana can gefe wasu kujerune hadaddu aka ajiye saboda hutawa kan kujerar yaje yazauna amma ko minti 5 bai yiba yatashi yafita yanufi dakinsa yashiga yakunna tv yakamo tashar kwallo yafara ganin wasan arsenal da man u, wasan yafara kayatar dashi faisal yashigo remote ya dauka yakashe tv din domin yasan yanzu zasuyi fada saboda faisal dan arsenal ne shi kuma tafida dan man u ne gashi ancisu har 2-0 yasan idan faisal yagani yau zai sha tsiya, kusa dashi faisal yazauna.
[8:32PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣0⃣

    Na UMMI A'ISHA


Kusa dashi faisal ya zauna yafara dariya ko kallonsa tafida bai yiba yadauke kansa shikuwa faisal sai dariya yakeyi, haushi tafida yafara ji yace ya isheka haka,dariya faisal yayitayi sai da yayi mai isar shi sannan yace kasan me nake yiwa dariya? Jiya jiyan nan kagama yimun bayanin kaifa bakasan hanyar da zakabi ba awurin mace idanma aka ajiye maka mace bakasan yadda zaka bida itaba to sai gashi yanzu za abaka mace nan da sati 2,kaga ashe kenan ka kusa kasamo hanyar ko? Wani kallo tafida ya watsa masa ni zanyi aure amma ba yanzu ba sai nan da 3years dariya faisal yakumayi kasan Allah? Kai angone kakusa ganin hanya, wai kai waya fada maka aure zanyi ne? Uhm abokina bazaka yarda da abinda nake fada maka ba sai kaji kira daga wurin mai martaba sannan zaka gasgata ni, tsaki tafida yayi insha Allahu kai zai yiwa aure amma baniba,ni daba dan iska ba wa zaiyi min aure yanzu? Kai da kasan mata kake nemansu ai kai yadace ayiwa aure, dariya faisal yayi kasan Allah? Wlh kakusa zama ango kai barima kaji dazu daka zo kasamemu da mai martaba wlh maganar aurenka akeyi kuma nan da sati biyu za ayi, cikeda mamaki tafida ya kalleshi wai dagaske kake yi? Wlh Allah dagaske nake tafida wlh aure mai martaba zaiyi maka dazu akanka mukayi meeting da yamman nan kuma wani abin burgewar ma zaka samu virgin girl kamar yadda kake virgin boy, zumbur tafida yamike ni za ayiwa aure yanzu? Wanne laifin nayiwa mai martaba da zai hukantani ta wannan hanyar? Wa zai aura min? Yaya kamanninta suke? Girgiza kai faisal yayi wlh ban saniba abokina, to nima dai  ummi Aisha ban saniba sai muci gaba da bibiyar tafida, masu karatu muje zuwa kubiyo Aisha.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [8:53PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣1⃣

Na UMMI A'ISHA

Kallon faisal tafida yayi ai kuwa wlh bazai taba yiyuwa ba nikadai ne da agidan? Akan me za ayi min wani aure yanzu kai ba gaka nan ba haba da Allah wlh bana so babu wanda zai rabani da gidan nan yanzu, kuma wlh duk yarinyar da tayi kuskure ta aureni sai ta raina kanta, dariya faisal yayi wadda takara kular da tafida kaga bani zaka fadawa ba kamata yayi kaje gurin mai martaba kayi masa wannan bayanin amma nidai ina tayaka murna sai dai shawarata agareka itace kasan mai martaba baya yin magana 2 daga yayi magana to yagamata so be careful kar kaje kajawa kanka, kaga mitumin nan nadazu daka samemu afada dashi? Shine mahaifin yarinyar wlh kayi dacen suruki cikeda bakin ciki tafida yace malam banfa tambayeka ba dan haka kayi min shiru banza kawai dariya faisal yaci gaba dayi ganin haka yasa tafida ficewa daga dakin yatasamma lungun inno wadda yake da dan tazara daga sashensa, yana shiga yatarar da bata cikin dakin sai kuyanginta suna gyara dakin kusan ko wanne lokaci dakin nata cikin gyaransa ake, shiyasa koda yaushe yake cikin tsafta tamkar dakin sabuwar amarya, suna ganinsa sukayi waje suka bar aikin da sukeyi, gadon inno ya dale yakwanta idan dasabo kowa agidan yasaba ganinsa akan gadon inno koda wanne lokaci yagadama zai zo yahaye yasha baccinsa akai kamar wani yaron goye.
[9:36PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣2⃣

Na UMMI A'ISHA

Rufe idanuwansa yayi amma yasan ba bacci zai iya yi ba maganganun faisal ne kawai suke dawo masa jiya jiyan nan kagama fadamin idan an baka mace baka san yadda zakayi da itaba sai gashi nan da sati 2 zaka zama ango an baka mata, zunbur ya tashi zaune jin abin yake kamar a mafarki aurefa? Daidai lokacin inno tashigo taganshi zaune akan gadonta, tafida ashe kana nan? Nima daga wurin mai martaba nake yakira ni yabani wani sako wurinka ras! Gabansa yafadi wato maganar faisal ta tabbata kenan ai kuwa tunda yake da mai martaba bai taba yimasa musu ba amma awannan karon dai zai yi, domin bai kamata ayi masa haka ba, abinda yafi cancanta shine abarshi ya zabi matarsa da kansa tunda sauran yayyensa ba haka akayi musu ba, maganar inno ce ta dawo dashi cikin hankalinsa mahaifinka yace nasanar dakai zai daura maka aure nan da sati 2 da wata yarinya yar gidan abokinsa amma ayadda naji yafada yarinyar ma ba lafiyayyiya bace, cikeda damuwa yace inno kuma ni za aurawa marar lfy? Haba inno yanzu mace ma an daina yimata auren dole balle namiji kuma naga sauran duk ba haka aka yimusu ba agaskiya nidai afasa maganar auren nan idan bahaka ba wlh za aji kunya, cikeda tashin hankali inno tace haba tafida mai martaba kake fadawa haka? Mahaifin naka zaka kunyata a idon duniya? To bari kaji wannan sakon naka yafi karfina sai dai yanzu katashi da kanka kaje ka sanar dashi bazakabi zabin da yayi maka ba, amma kasani mahaifinka ba yayin magana 2 magana daya yakeyi kuma aduk inda yasaka doka a garin nan ana bi balle agidansa dan haka ina baka shawara da kayiwa mahaifinka biyayya kar kajawo abinda zaiyi fushi dakai, shiru tafida yayi ransa duk yagama jagulewa wannan wanne irin abu ne? Shidai wlh wannan auren bada shiba, kallon inno yayi to inno abawa faisal mana amma sai ace ni za abawa? Wlh bana so ni babu auren da zanyi ban shirya yin aure yanzu ba kafin inno tayi magana jakadiya tashigo gafara dai ranki yadade barka da hutawa ayi min izini nashigo, kya iya shigowa jakadiya inno tafada tana kokarin kishingida.
[10:49PM, 11/12/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣3⃣

Na UMMI A'ISHA

Shigowar jakadiya ne yasa tafida dago dara daran idanuwansa yafara kallon jakadiya cikin girmamawa jakadiya ta durkusa ranki yadade barka da hutawa, Allah ya kareki uwar dakina sarki ya aikoni, kallonta ta maida kan tafida mai girma tafida sako daga mai martaba sarkin adalci sarki nakwarai yace kaje yana son ganinka cikeda damuwa batare da tafida yabata amsa ba yatashi yafita izuwa lungun sarki gaba daya jinsa yake kamar a mafarki, yana isa dakin sarki yaja yatsaya abakin kofa sakamakon ganin maga kofa dayayi toge akofar, cikin girmamawa maga kofa yafada dakin sarki yayiwa sarki bayanin zuwan tafida, yashigo sarki yafada atakaice, dasauri maga kofa yadawo yayiwa tafida iso suka karasa dakin sarki sannan maga kofa yafita yabasu wuri sunkuyar dakai tafida yayi Allah yaja zamaninka yanzu na samu kiranka daga wurin jakadiya,eh nine naturata takira min kai, ranka yadade na amsa kira, ibrahim! Mahaifin nasa yakira sunansa na'am, Allah yaja zamaninka, Allah yasa kafi haka tafida yafada kansa yana duke akasa, dalilin kiran da nayi maka shine kayi hakuri da abinda zakaji daga gareni, wato ibrahim aure zanyi maka nan damako biyu, ina fata zakayi dukkan wasu shirye shiryen dasuka dace nan da sati biyun, sannan ina so kayi hakuri da ita matar da zan aura maka domin ba lafiyayya bace kuma ga hotonta idan kana da bukatar gani, kansa akasa yace ya mai martaba ayi min adalci kuma asausauta min dan Allah afasa auren nan domin banida shirin tunkarar aure ahalin yanzu, kai! Wata tsawa mai martaba yadaka masa wadda ni kaina ummi Aisha sai da narazana, bafa shawararka nake nema ba umarnine nake baka, yanzu kai ibrahim har kayi girman da zan fada maka magana kayi min musu? Tuba nake ranka yadade, natuba mai zamani, ayi min afuwa hakika nayi kuskure amma ayafe min, cikin fada sarki yace to aure babu fashi zan daura shi inyaso aranar dana daura kana iya warwareshi ta hanyar sakin matar, ai kuwa zan sakenta tafida yafada acikin ransa.
[8:17AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣4⃣

Na UMMI A'ISHA

      Tabbas ko wacece sai narabu da ita danme za ayi min auren dole bayan ga faisal nan shi ba ayi masa ba, kuma naga komai mai martaba zai yi tare yake yi mana nida faisal sai a wannan ne za a banbanta mu? Fadan mai martaba ne ya dawo da shi cikin hayyacinsa, sanin kankane ni ba karamin mutum bane bare jama'ata su rainani, bana alqawari in saba sannan bana yin magana biyu dan haka dolenka ka amincewa umarnina domin ba kaine ka haifeni ba nine na haifeka idan hukuncin dana yanke maka yayi maka tsauri to ka mutu kabar duniyar inyaso sai ka huta da auren da zanyi maka, tuba nake ranka yadade, ayi min aikin gafara, tashi kabani wuri mutumin banza mutumin wofi, Allah ya huci zuciyarka ya mai martaba cikin hanzari tafida yatashi yafita gaba daya idanuwansa sun kada sunyi jajawur kamar gauta, ransa in yayi dubu yagama baci, dakin inno ya koma acan yaci karo da momcy bai iya yi mata magana ba yashiga dakin inno yazauna akusa da kafafunta, inno wai dan Allah laifin me nayi muku ne haka kuka tsaneni? Murmushi tayi irin nasu na manya haba tafida na, da daya tamkar da dubu, wlh tafida idan na rantse maka cewa dani da mai martaba munfi sonka fiyeda kowa acikin yayanmu ba zanyi kaffara ba, ni da mahaifinka duk cikin yayanmu munfi nuna maka so da kauna ba wai dan kasancewar ka dan auta ba a'a soyayyar daga Allah take haka nan Allah ya sanya mana sonka fiyeda sauran yan uwanka sannan nasan mahaifinka bazai taba cutar dakai ba, saboda idan kashiga damuwa sai yafika damuwar, dan Allah tafida ka kwantar da hankalinka kayiwa mahaifinka biyayya kaji? Shi wannan mutumin da zai baka yar tasa mutumin sarki ne tun suna yara, yayiwa sarki alherai da dayawa wadanda bazasu lissafu ba to kaga kuwa shi ALHERI DANKO NE! Baya faduwa kasa banza sannan kuma dadi musanye ne, abinda nakeso dakai kawai shine kayi biyayya, cikin kunar rai tafida yace amma inno ga ba faisal nan ba why not shi baza abashi ba? Sai ni za abawa danni aka tsana? Kai rufe min baki marar kunya inno tafada cikin fada dan kaga inata shawo kanka ina lallaminka da kalamai masu dadi shiyasa zaka fada min maganar banza? Anki abawa faisal din kai aka yi niyyar bawa in yaso aranar da aka daura auren ka saketa ko kuma idan ankaita gidan naka ka kasheta kaji? Fitsararren kawai in banda tsabar rashin kunya har sarki yabada umarni katsaya kana ja in ja da umarninsa? To sai gareka karka fasa, tashi maza kafice min daga daki kuma kar nasake ganin kafarka acikin dakina, da sauri tafida yatashi yafita bayi da kuyangu sai mamaki suke domin inno bata taba yiwa tafida irin wannan fadan ba kowa agidan yasan tafida shine dan lelen inno da mai martaba.
[8:41AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣5⃣

Na A'ISHA (UMMI)

  Tafiya yake ahankali duk da cewa dama haka yasaba tafiya amma tafiyar yau tasha banbam data kullum lungun momcy mahaifiyar abokinsa faisal kuma dan uwansa najini yanufa yana shiga jakadiya tayi masa iso yakarasa dakin momcy tana zaune akan gado wata baiwa tana yimata firfita da muhucin kaba gefenta kuma wata baiwar ce take yi mata labarun ban dariya ko sallama bai iyayiba yashiga take bayin suka bar abinda sukeyi suka tashi suka fita, akan daddumar dake malale acikin dakin ya zauna yadukar da kai barka da hutawa ranki yadade, barka kadai tafida,cikin damuwa yace momcy ko kin samu labarin abinda zai faru dani? Cikin bacin rai tace nasamu tafida dazun nan jakadiya tazo min da labarin kuma inaji banyi kasa agwiwa ba natashi natafi wurin mai martaba domin jin sahihancin labarin anan ya tabbatar min da gaskiyar lamarin sai dai nayi takaici da ba abar min kai kazabi matarka da kanka ba kamar yadda aka yiwa sauran yan uwanka sai amma kirana gareka shine kar kayi jayayya da umarnin sarki domin hakan zai iya janyo maka fushin mai martaba akanka sanin kanka ne kuma fushin Allah yana daga cikin fushi na iyaye wannan hadisine ingantacce saga bakin annabinmu annabin rahma, kayi hakuri kayi biyayya idanuwansa jawur ya dago yadubi momcy dama momcy duk wanda kaji anbawa hakuri ai cutarsa akayi cikin damuwa tace babu komai tafida ni kaina narasa dalilin sarki nayimaka wannan irin aure acikin gaggawa amma babu komai kayi biyayya kawai ni naso ace ma wannan shashan dan uwan naka faisal za ayiwa auren, babu komai momcy nagode, tashi yayi yafita yanufi sashensu shida faisal yana shiga yasamu faisal kwance afalo cikin kujera cikeda damuwa yanemi wuri ya zauna faisal yana kallon fuskarsa yasan ya amsa kiran mai martaba tashi zaune yayi yadafa kafadar tafida abokina ya akayi? Kamar tafida zai yi kuka yace faisal wlh bana son auren nan bana so bana so, cikin damuwa faisal yace wlh tafida dazun nan lokacin da akeyin maganar tun alokacin nafara rokon sarki akan yayi hakuri nasan bazaka so auren nan ba amma yaya chiroma da baba galadima suka hayayyako min da fada wai nida kai mun raina kowa afada bama bin umarnin mai martaba saboda mu yan gata ne nida kai ne kawai sarki zai bawa umarni mu tsaya muna jayayya dashi ganin sun dauki zafi yasa nataso nabaro wurin amma dan Allah kar kadamu kanka, lallashin tafida faisal yayi tayi da kalamai masu sanyaya zuciya tareda nuna masa illar rashin bin umarnin iyaye.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:21AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣6⃣

Na UMMI A'ISHA

   Shidai tafida yau rauni yafi gaban ciwo kallon faisal yayi kasan Allah? Ana daura auren nan sai nasaketa kowacece cikin sauri faisal yakatse shi kar kasoma yin haka abokina domin zaka aikata babban kuskure kar kazo kayi abinda mai martaba zaiyi fushi dakai, tashi tafida yayi yashige daki yabar faisal afalo cikeda damuwa domin damuwar tafida ta faisal ce.

***********************
Alhaji Ahmad Muhammad sani shine sarki na uku ajerin sarakunan garin misau ta jihar bauchi, garin misau babban gari ne sannan kuma babbar masarauta ce mai girman gaske, sarkin misau nayanzu shine sarki na uku yagaji sarautar ne ahannun mahaifinsa alh Muhammad sani nabiyu, alh Ahmad sani sarkin misau nayanzu yana da matan aure 2 hajiya kilishi (inno) da hajiya mabruka (momcy),hajiya Kilishi wadda akafi sani da inno itace uwar gida sunyi auren saurayi da budurwa ita da mai martaba lokacin baifi dan shekara 23 ba alokacin aka nadashi sarkin garin misau, Allah ya albarkacesu da yara guda 5 duka maza babban dan sarki shine chiroman misau alh Muhammad sani sai mai bimasa marafan misau alh adamu Ahmad sani sai turakin misau alh jamil ahmad sani sai barwan misau alh Mahmud ahmad sani sai kai gaman misau alh mannir ahmad sani daga nan sai dan autansu tafidan misau sannan hakimin disina alh ibrahim ahmad sani, amaryar mai martaba hajiya mabruka (momcy) yara biyu suka haifa da mai martaba babbar yarsu itace hajiya maryam (hajiya daso) sai kaninta alh faisal ahmad sani san turakin misau hakimin dambam, faisal da tafida tare suka taso adaki daya kasancewar babu yan ubanci agidan kowa yana kaunar dan uwansu bazaka taba iya banbance tsakanin dan hajiya inno da dan hajiya momcy ba saboda tsabar hadin kai, gaba daya yaran inno adakin momcy suke tasowa yayinda itama momcy ita ta aurar da hajiya daso kasancewar bata da ya mace, shi kuwa faisal da tafida kusan lokaci daya aka haifesu tsiransu kwana 5 ne atsakani shiyasa suka taso kamar wasu yan biyu sannan suka zama abokan juna dukkaninsu basuda wani aboki sai junansu tun suna yara haka suke kiran junansu kuma wani abin sha'awar shine bazaka taba jinsu sunyi fada ba kullum cikin zolayar junansu suke, gashi suna yar kama duk kuwa da cewar tafida yafi faisal kyau domin shi mahaifiyarsa ya dauko ita kuma bafulatana ce.
[10:03AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣7⃣

Na UMMI A'ISHA

Tunda suka taso basa rabuwa tare suke yin komai har suka zama samari shekarunsu daya tsayinsu daya kuma ko amakaranta ajinsu daya, tun lokacin da suka gama primary school suka tafi america acan sukayi karatunsu gaba daya suna gama degree suka jona masters dinsu, zaman da sukayi akasar waje anan tafida ya koyi shan ganye shikuma faisal yakoyi neman mata amma daga nan baya wata dabi'a shima tafida daga shan ganye baya komai mace kuwa babu abinda yake hadashi da ita sai asibiti idan bata da lafiya, tun akasar turai yan mata suke nuna masa maitarsu afili daga turawan har bakar fatar amma bai taba yadda ya kusanci kowacce mace ba neman mata sai dan uwansa faisal, suna kammala karatunsu suka dawo Nigeria kowannensu yakama aiki shi tafida kwararren likitane a fannin mata shikuma faisal auditor ne a ministry for local government, basu jima da fara aikiba akayi musu sarauta shi faisal sarautar sa san turakin misau hakimin dambam shikuma tafida sarautarsa tafidan misau hakimin disina,tun asali shi tafaida bamai yawan magana bane bashida surutu magana bata dameshi ba wannan dalilin ne yasa ake yimasa kallon mai girman kai yanmata dayawa kuma suke masa kollon mai takama dakyau basusan shi haka yakeba naturally.

***********************
Tafida yana shiga daki yakifa akan gado zuciyarsa sai tukuki take tamkar zata fasa kirjinsa tafito waje cikin damuwa faisal ya tashi yabishi cikin dakin yaci gaba da bashi baki amma tafida Ji yake kamar ya rushe da kuka, tashi yayi ysdauko ganye yafara busawa shikuma faisal ganin haka yasashi fara tsaki dalla malam kafita waje kagama busa hayakinka acan hararsa tafida yayi kana iya fita kai tunda ba daureka nayi ba dan iska kawai, dariya faisal yayi kaima ka kusa zama dan iskan ai tunda kakusa sanin hanyar da baka sani ba, tsaki tafida yayi yasake xukar tabar ya busar da hayakin ai wannan hanyar ko zan santa ba yanzu ba, kai dan iska ne sau nawa zaka santa? Inji faisal murmushi tafida yayi kaine dan iska amma ni banida hadi da kowacce mace,yanzu ai zakayi hadin da ita faisal yafada yana dariya, hira suka cigaba dayi har karfe dayan dare sannan suka kwanta bacci amma shi tafida bacci gagarar idonsa yayi shima faisal din baiyi dayawa ba yatashi. Kamar yadda yasaba fita yauma haka ya shirya ya dakin inno ya gaisheta dakyar ta amsa fuskarta babu walwala, fitowa yayi ya shiga dakin mai martaba shima hakan take, dakin momcy ya shiga itace ta karbeshi da fara'a ga kayan karyawa ta shirya masa sai data kara yi masa nasiha sannan yatashi yatafi. Yana zuwa asibitin su ya zauna jugum yana nazari wai shi mai martaba zai yiwa auren dole, bayan auren dolen ma marar lafiyace yarinyar, kai ai auren nan bazai dadeba yafada yana bude laptop dinsa.
[10:30AM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣8⃣

Na UMMI A'ISHA

Laptop dinsa yabude yashiga email dinsa anan yaci karo da wani sako daga kungiyar litocin mata ta duniya  ta shirya musu wani course har na tsawon wata 5 kuma har dashi aciki zasu gudanar da course din ababban birnin kasar India wato Mumbai dadi yadanji domin dama garin yayi masa zafi da azamarsa yatashi yanufi maternity domin duba halin da suke ciki. Tunda yadawo daga office yakule adaki shi kadai yafara cike ciken takardun tafiya course dinshi anan faisal yazo yasameshi abokina dama kana ciki, eh gani kaganni kuwa, akusa dashi faisal yazauna me kakeyi? Wlh wani course zan tafi na 5 months, kai dazakayi aure wanne course kuma zakatafi bayan ga babban course zaka samu duka tafida yakaiwa faisal yace zan yimaka rashin mutunci wlh, dariya faisal yayi duk tsiyarka dai ana daura maka aure kazama bazawari,waya fada maka? Wlh karya kake kaine bazawari amma ni virgin ne dariya faisal yayi ai mun kusa muga karshen virgin domin virgin zai koma disvirgin dariya tafida yayi yace ka karaci iskancinka kagama akwai ranar ramuko. Tuni aka fara shirye shirye agidan mai martaba har an hada kayan aure irin na al'ada dana zamani ankai gidansu amarya kullum bushe bushe da raye raye akeyi agarin mai girma tafida zai angwance,ni ummi Aisha hannuna asama nace Allah yaja zamanin mai girma tafida, tunda aka fara shirin biki tafida baya shiga sabgar kowa agidan tsakaninsa da kowa gaisuwa ce daga angaisa shikenan dama can shi ba mai magana ba da faisal kawai yanzu yake magana mai tsawo shima faisal din dan bazai iya fushi dashi bane saboda sun shaku sosai, amma ko inno da mai martaba tsakaninsu gaisuwa ce yadda suke fushi dashi shima haka yake fushi dasu, ana igobe za afara gudanar da biki yafara shirye shiryen tafiyarsa India domin nan da sati 2 zasu fara gudanar da course din mai taken yaki da cutar sankarar mama (cancer),shi dai faisal shine yazama tamkar angon domin komai wanda ango yakeyi shine yayi, shikuma tafida hakan ko ajikinsa tashi yayi yaje wurin mai martaba yayi masa maganar tafiyarsa India maimartaba bai damuba yace babu matsala dama itama amaryar taka karatu takeyi koda tana nanma nace babu maganar tarewarta yanzu tunda bakaso duk lokacin dakaso ta tare nan gaba, dukar da kai tafida yayi yace godiya nake mai martaba Allah yakara nisan kwana yatashi yafita.
[8:41PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

1⃣9⃣

Na UMMI A'ISHA

     Yana fita yayi kicibus da faisal kallon faisal yayi yadauke kai domin yafuskanci faisal ya zake akan auran nan, cikeda dariya faisal yaja hannunsa mutumina ya akayi? Shiru yayi kamar baijishi ba cikin zolaya faisal yace wai kai duk dokin zaka samu hanyar ne ya hanaka magana? Sai alokacin tafida yayi murmushi wlh kai wannan yadama ni yanzu ba wannan ne agabana ba, dariya faisal yayi zo muje abokina kaji hannunsa yakama suka nufi cikin gida har dakinsu suka zazzauna faisal ya dubeshi yace dan Allah tafida ka tsaya ka nutsu ka rungumi matarka shifa aure mukaddari ne, cikin jin haushi tafida yace me zai hana kai ka rungumi kaddarar ka aureta? Dariya faisal yayi ai ni ba abani bane amma kai kaga da yake dan gatane aure za ayi maka kasha sha'aninka tsaki tafida yayi yajawo earphone dinsa yajona ajikin wayarsa yafara shan sauti dariya faisal yayi yace kadai kusa ka zama bazawari, jin shiru tafida bai amsa ba yasashi gane cewa bai ji abinda yace ba domin dayaji da sai ya bashi kyakkyawar amsa domin babu abinda yatsana irin yaji yakirashi da bazawari tashi faisal yayi yafita yana dariya. Shirye shiryen biki ya kankama yayinda shi kuma tafida yaketa shirye shiryen barin kasar, ranar alhamis aka sanya amarya a lalle faisal shine yake tsaye akan komai kullum baya samun lokacin kansa daga nan zai yi nan gidan mai martaba kuwa ya cika yayi dam da al'umma garin in banda kade kade da raye raye babu abinda akeyi domin sarki zai aurar da dan autansa kuma dan gaban goshinsa amma shi tafida in banda fushi babu abinda yakeyi gaba daya yadaina walwala yazama marar fara'a gashi kullum sai sunyi fada da faisal, ranar juma'a aka fara niyyar daura auren tafida amma kememe yaki kirshayawa.
[9:05PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣0⃣

Na A'ISHA (UMMI)

Babu yadda faisal bai yi da tafida ba kan ya shirya su fita domin da misalin karfe 1:30 za adaura auren amma yaki yarda yatashi ya shirya tun faisal yana yimasa cikin lallami har yafara fada shiru tafida yayi masa bai tanka masa ba, ganin haka yasa faisal yakara tunzura ya hasala yafita daga dakin, lokacin har su mai martaba sun tafi inda za adaura suren, faisal shi kadai yatafi yasha fararen kaya masu tsada yana zuwa lokacin wurin yacika makil amma haka yasamu ya kutsa ya isa wurin mai martaba sarki yana ganinsa yafara tambayarsa ina tafida cikeda damuwa yace ranka yadade bashida lafiya ne bazai iya zuwa ba, cikin fushi mai martaba yace yayi daidai kuma rashin zuwansa bashine zai sani nafasa yimasa wannan auren da nayi niyya ba, hakuri faisal yafara bawa sarki tuba muke ya mai martaba ayi mana uzuri,galadima ne ya matso yace ranka yadade ni ina ganin afasa daura auren nan da tafida abawa faisal, girgiza kai sarki yayi a'a galadima banki ta takaba amma nidai da tafida zan daura auren nan, nan aka fara daurin aure waliyyan amarya sunzo aka daura auren tafida da amaryarsa akan sadaki naira dubu dari, ana gama daurin aure sarki yakira uban amarya gefe yafara yimasa bayani kan cewar amarya ba yanzu za akawota ba sai lokacin da yayi magana gyada kai mahaifin amaryar yayi tareda yiwa mai martaba godiya, ana kammalawa faisal ya koma gida afalo ya taradda tafida kwance yana danna wayarsa dariya faisal yafara yi yamikawa tafida hannu assalamu alaikum mr ango harara tafida ya cilla masa yayi tsaki wata dariya faisal yayi mr ango asamo hanya lafiya amma banda rashin imani dan wlh idan kayi mata takarfi zaka iya kasheta, tashi zaune tafida yayi wlh faisal kar ka kaini bango, ya isheka, murmushi tafida yayi daga fadar gaskiya? Allah yabaka hakuri gyara kayanka baya zama sauke mu raba, murmushi tafida yayi yau kam yazama amma kabari duk lokacin dana nemi hanyar narasa zan nemi taimakonka, zama faisal yayi bawani nan dama can kasan inda take, wai kai sau nawa zan fada maka ne? Wlh Allah ni ban san ta inda take ba kai nifa ko haihuwa idan zan karba bana tsayawa naduba kawai aikina nakeyi dariya Faisal yayi to congratulations yanzu zaka gane ta inda take sallamar jakadiya ce ta katse musu hirar tasu.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:27PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣1⃣

Na UMMI A'ISHA

Har cikin falon jakadiya tashigo tarussuna barkanku da hutawa samarin kwarai tafida ta kalla ranka yadade mai martaba yana kira tana gama fadin haka tajuya tana cewa afito lafiya, tashi tafida yayi yafita shikuma faisal bai bishi ba domin yasan fada zaisha awurin mai martaba yana tsoron kar yaje ahada dashi, tafida yana isa dakin mai martaba yasameshi shida inno da momcy zazzaune gabansa wuri yasamu yazauna gabansa yanata harbawa, cikin fada mai martaba yafara magana ibrahim ka raina kowa agidan nanko? Kanuna mana mu bamu isa dakai ba kenan tunda har za muyi maka umarni amma kasa kafa ka shure, saboda baka daukemu da daraja ba shine zaka ki halattar daurin aurenka ko? To ka kyauta kuma duk abinda kayi daidai ne domin ahalin yanzu sai dai kanemi wani uban amma baniba aure kuma nayi maka shi sai dai zaka iya nunawa duniya rashin matsayina ta hanyar sakin matar, nanfa inno itama tadauka ya saketa mana shiyasani kuma mutumin banza kawai kai in banda tsabar raini har ayi maka umarni ka ki bi? Yaran yanzu bakuda kunya kota sisin kobo muda aurenma basai an tare zakaga matar ba,waye zai tsaya jin ra'ayin mutum, hakuri momcy tafara basu hajiya inno ayi hakuri dai, mai martaba dana yayi kuskure amma ayi hakuri ayi masa gafara ayafe masa kar yashiga cikin wani hali dan Allah aduba kokena, tashi inno tayi tafita tanata fada shima mai martaba tashi yayi yafice yatafi fada, kallonsa momcy tayi tafida baka kyauta ba meyasa zakaki zuwa wurin daurin auren? Cikin kasala yace momcy ni auren ne bana so, 27 years nayi aure? Is too early wlh,murmushi momcy tayi babu komai yanzu abinda nakeso dakai anjima da daddare kuzo kaida faisal kubawa sarki hakuri kaji? Naji momcy, yawwa Allah yayi maka albarka, tashi yayi shima yafita.
[9:47PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣2⃣

Na UMMI A'ISHA

Da daddare faisal yasaka tafida agaba sukaje wurin sarki suka bashi hakuri amma sai dakyar suka samu ya sauko sa'arsu daya su yan lelensa ne domin badan hakaba da zai dade yana fushin bai huceba, daga nan sashen inno suka shiga itama suka bata hakuri tsakanin da da uwa sai Allah nan itama ta huce tace tahakura suna dawowa dakinsu faisal yafara bawa tafida shawara, abokina kafin katafi India yakamata kaje kaga amaryarka kayi mata sallama, tsaki tafida yayi naji zanje, yawwa mutumina yakamata kaje. Abangaren gidansu amarya kuwa koda mahaifinta yaje musu da batun rashin tariya dawuri nan dangi suka fara kace nace wasu kuma mamakine ya kamasu wannan wanne irin aure ne kodan anga basuda kudi shiyasa za araina musu wayo? Shidai uban amarya baice komai ba kuma zancen da nake yimuku har yau nidai ummi Aisha banga kalar amaryar tafida ba balle na zayyano muku yanda take, kasancewar sarki mutum ne mai adalci yasa ya aikawa da gidansu amarya kayan abinci kala kala yace arinka ciyar da amarya kuma duk lokacin da yakare zai aiko wani sannan duk wata bukata tata arinka sanar dashi hakan da yayi ba Karamin dadi gidansu amaryar sukaji ba. Tafida shirin tafiya yagamu domin yau saura kwana 2 yabar kasar, wanka yayi ya shirya yadau kwalliya cikin bakin danyen boyel yasa bakar hula takalmin kafarsa ma baki yaafito sai zuba kamshin turare yake take fadawansa suka bude masa motarsa yashiga suka rufa masa baya driver yaja sai disina, suna zuwa suka zarce wani dan madaidaicin gida daga ganin gidan gidan talakawa ne masu rufin asiri, cikeda yatsina fuska tafida yafito daga motarsa yanufi cikin gidan fadawansa suna take masa baya, babu ko sallama yakutsa kai cikin gidan yana rayawa aransa wai dan abin kunya nanne gidan sirikansa kai Allah ya kiyaye, atsakar gida yahango mahaifin matarsa da mahaifiyarta tana hura wuta, kafarsa yasa yayi bol da wata buta ta farin karfe atsakar gidan da alama butar mai gidan ce, dayake gwanine wurin kwallo take butar tawuce tasaman kan mai gidan taje tadaki bango tadawo baya tafadi atsakar gidan ta tankwashe yanda bazata moruba har abada.
[10:07PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣3⃣

Na UMMI A'ISHA

Cikin tashin hankali mahaifiyar matarsa tafara magana suwaye ku? Me kukazo yi anan gidan? Cikin yayyatsina fuska tafida yadubi wannan mitumin yace bawan Allah yadda kasa aka daura min aure da yarka to tun wuri kaje kasa awarwareshi domin bazan zauna da itaba kuma bazan taba sonta ba, banda tsabar son zuciya tayaya zaka dauki yarka ka kaiwa mai martaba rallarta har alika min ita, to bana sonta kuma sai nasaketa sai asannan suka gane ashe shine mijin yarsu sirikinsu duk cikinsu babu wadda yayi masa magana kawai tsayawa sukayi suna kallonsa fadawansa kuwa sai fadi suke hutawarka lafiya tafida wannan sako naka ya je inda kakeso yaje, abi tafida a zauna lafiya tafida buhun karangiya ko an zazzage dole sai ya makale, gaba salamun baya salamun dan sarki jikan sarki, gunbar dotse, icen kan kabari titi kafi karfin a tsallakaka dole sai an waiga, takawarka lafiya toron giwa dawisu da ado aka sanka, ragayar dutse namijin fama, juyawa tafida yayi yafita daga cikin gidan fadawansa suka rufa masa baya kai tsaye fadarsa yawuce inda wakilinsa yake, anan ya tambayi wakilin nasa wacce gonace tafi kowacce girma agarin? Cikin washewar baki wakili yace ranka yadade gonar sirikinka malam faduluddeen gonarsa tafi takowa girma cikin rashin damuwa tafida yace ok to inaso nan da sati mai zuwa agyara min domin zan turo masu aiki zasuyi min ginin gidan shakatawata awurin, cikin mamaki wakili yace yallabai sirikinka fa, ka iya bakinka wakili fadawa suka fada lokaci daya, shiru wakili yayi yace tuba nake yallabai tashi tafida yayi yana bawa sarkin fada sallahun ginin da za azo ayi masa, cikeda farin ciki yakoma gida domin yasan abinda yayiwa mahaifan matarsa dole zasuji haushi kuma kila zasu samu sarki suce yasashi yasakar musu yarsu amma abin mamaki shiru yaji ba wani batu alokacin har ansoma fara yimasa ginin gidan da yabada umarni acikin yanayin yashirya yanufi kasar india yana cikeda haushin auren da yake kansa.
[10:45PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣4⃣

Na UMMI A'ISHA


Lokacin da tafida ya tafi india ya samu damar mantawa da auren dayake lankaye akansa sai dai kusan kullum idan sunyi waya da faisal yana yawan yimasa maganar amaryarsa dariya kawai tafida yakeyi domin yanzu ya daina damuwa idan faisal yana yimasa tsiya, cikin ikon Allah yasamu yagudanar da course dinsa cikin kwanciyar hankali da nasara wata 5 daidai yayi yafara shiri ysdawo Nigeria. Ranar da yadawo ranar fada ta cika makil da yan sannu da zuwa faisal kuwa sai zolayarsa yakeyi amma yashareshi har sai da suka koma daki sannan yakalli faisal yace mekake cewa dazu? Dariya faisal yayi abokina kayifa kyau sosai kayi fresh kodai kabi hanyar ne? Tsaki tafida yayi kai wai baka da wata magana sai kwaya daya? Ai ni nafada maka ko zanbi hanyar da kake fada to ba yanzu zan bitaba, dariya faisal yayi to malam yakamata fa kasan inda dare yayi maka dan wlh nakusa korarka daga dakin nan? Wazaka kora? Kai zan kora tunda yanzu Kai magidancine so sai kakoma wurin iyalinka, kamanta zurriyya ba iyaliba tafida yafada tareda mikewa yafara cire rigar jikinsa domin shiga wanka. Washe garin ranar da tafida yadawo yakwanta yayi baccinsa ranar bai je office ba sai wurin 11 sannan yashirya cikin suit milk colour yasa milk colour din takalmi yasha turare yafito dan zuwa asibitinsu yana so yaje yakai report, agidan baya yazauna acikin motarsa fadawansa suna tareda shi har asibitin yana fitowa daga mota wasu yanmata wanda zasu kai kimanin su 20 suna sanye da unifoam suka fara kallonsa da alama yan practical ne aka turosu asibitin duk cikinsu babu wadda tafida bai tafi da imaninta ba nanfa suka fara tattauna maganar a tsakaninsu. Sai da tafida yayi hutun sati 2 sannan yafara zuwa office aranar dayaje yana tsaye acikin office dinsa yana daddanna wayarsa wata nurse tashigo masa office akidime pls sir ka taimaka mana munada patient wadda take neman taimakon gaggawa kamar baijiba yayi har saida ta sake maimaitawa sannan yace yaji yabi bayanta har zuwa female ward can gadon karshe takaishi tace gata sir wannan ce, gaban gadon yakarasa wata yar budurwa yagani wanda shekarunta zasu kai 23 aduniya tana sanye da farar riga da bakin dark blue din wando daga gani yar practical ce domin yaganta da unifoam din yan lab science.
[11:12PM, 11/13/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣5⃣

Na UMMI A'ISHA

Kallon fuskar ta yayi kyakkyawa ce ta daukar hankali shidai yana ganin mata masu kyau amma baiga wadda ta kai wannan kyau ba duk kuwa da cewa baka ce amma bakinta mai kyau ne har wani shining take kallon nurse din yayi me yasameta? Cikin inda inda tace let me go and call her friend she's d one dat brought her here, dasauri tafita Jim kadan sai gata dawata budurwa itama tana sanye da uniform irin na wadda take kwancen kallonta tafida yayi meya sameta? Dr wlh kawai muna zaune mukaga tafadi, sai alokacin yasa hannunsa yatabata amma da bai taba koda hannunta ba ya salam! Yafada saboda jin laushin fatar jikinta, nan yafara jin wani yanayi ajikinsa daurewa yayi yafara checking dinta anan yasamu yagano matsalar tata yayi mata allurai har guda hudu alokaci guda, kallo yabita dashi dama wannan ai dole tasamu matsala saboda tahadu sosai shiyasa takamu da ciwon mara mai tsanani wanda bazata taba warkewa ba har sai tasadu da namiji, fita yayi yakoma office dinsa sai 3 yashiga round yana shiga yan practical suka fara gulmarsa wannan likitan duk asibitin nan yafi kowa kyau, ai duk misau ma babu mai kyanshi inji wata aciki, yana tafiya yana duba patient har yazo gadon karshe inda yanmatan nan suke, waje yace sufita yafara duba patient dinshi wadda har ta wartsake kallonta yayi doguwa ce baka tanada manyan idanuwa da dogon hanci gata da dan tsukakken karamin baki, gashin girarta mai yawane batada kiba dayawa amma tana hips da cikar kirji sosai, yanmata kin tashi? Ya tambayeta, biron hannunsa ta karba da takarda tayi masa rubutu kamar haka, bana jin abinda kafada ni bebiyace kuma kurma ce, mika masa tayi yakarba ya karanta cikeda mamaki ya rubuta mata, ayya sannu, amma ko kin san ke kyakkyawa ce? Mika mata yayi takarba tagani takaranta tayi masa reply nagode amma Kayi hakuri ni matar wanice, karba yayi yai murmushi nima mijin watane, murmushi tayi wlh inada aure, bai gasgata ta ba saboda yaga tana fama da matsalar ciwon mara sperm yataru dayawa a mararta gashi har ya haifar mata da ciwo shi kuma yasan da ace tanada aure da hakan bazata faruba kallonta yasakeyi waye zai mallaki wannan a matsayin mata yatsaya yazuba mata ido yana kallonta? Kai karyane gaskiya budurwa ce cikakkiya kuma.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣6⃣

Na UMMI A'ISHA

Wani tsadadden murmushi tafida yayi mata yace ok koma dai menene bari na rubuta miki maganin dazai taimaka miki, wata yar takarda yadauka ya fara rubutu yana gamawa ya mika mata gashi Allah yabaki lfy, duk wadannan maganganun da yakeyi bata jinshi murmushi yayi mata kinyi min kinyi daidai da tsarina hannunta tadaga tayi mai nuni ma'ana me yake nufi, murmushi ya sakeyi wanda har sai da fararen hakoransa suka bayyana kumatunsa na dama ya lotsa kusan ko magana yakeyi sai yadan lotsa kallonsa tayi taji gabanta yafadi wannan likitan yanada kyau tafada acikin zuciyarta astagfurullah tayi saurin tuba saboda tunowa datayi itafa matar aure ce, fuskarsa ta kalla lokacin da yake yin rubutu ajikin takarda yadan dunkuyar da kansa yanayi yana lasar lebenshi nakasa wanda suke jaja jaja duhu duhu domin tabar wiwin da yakesha tahadu da jan lebensa sai tabada wata irin kala mai kyau kamar yana shafa jan baki gashi farinsa irin mai dan jan nanne kura masa ido tayi kai wannan saurayin yana yimata kama da Seth rollins dan wrestling domin har tsayinsu ma zai zo daya gashi manyan idanuwansa ma irin nasane sak, dagowa yayi yana murmushi yamiko mata takardar yayi mata wani kasalallen murmushi yajuya yafara tafiya ita dai nurse tana tsaye tana kallon ikon Allah domin tunda take acikin asibitin nan bata taba ganin dr tafida yayi irin haka da wata patient ba babu ruwansa da kowa tsakaninsa da kowa gaisuwa ce amma sai gashi yau har dasu bude hakora taf lallai wannan tacika mai nasara.
[12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣7⃣

Na UMMI A'ISHA

Yana juyawa marar lafiyar tafara kallonsa yahadu sosai ta kissima aranta sai da yafita tabude takardar da yabata tafara karantawa kamar haka Yake kyakkyawa agaskiya yau idona ya yi duban da be taba yiba hakika banyi kuskure ba idan nakiraki da suna tauraruwa kigodewa mahaliccinki domin ya tsara halittarki irin tsarin da har yau banga wadda takaiki ba, ina sonki zuciyata takamu da kaunarki alokaci guda,ina taredake aduk inda kike luv u! I. T. Tana gama karanta wasikar kawayenta suka shigo dukkaninsu kowacce tana sanye cikin unifoam nanfa wata daga ciki tafara yimata tambaya da hannu alamar meya ce mata murmushi kawai tayi bata fargaba taji sun fizge takardar hannunta karantawa sukayi take kuma bakin ciki ya mamaye zuciyoyinsu domin agaskiya wannan likitan bai dace da ita ba dasu yadace mutum dayace bataji haushin hakanba asalima murna tayi sukuwa sauran ji sukeyi kamar su shaketa dan haushi. Dr tafida yana fita daga female ward yanufi office dinsa zuciyarsa cikeda tunanin yarinyar da yagani sai dai yana jin tausayinta har cikin ransa domin abin atausaya matane gata budurwa har budurwa kyau iya kyau amma dayake Allah alhakimu ne sai ya iyota kurma kuma bebiya, duk da haka zuciyata tana sonki yanmata ni babu ruwana da jinki ko maganarki ke kawai naji ina so, zama yayi yafara kiran fadawansa minti kadan sai gasu kayansa yace su hada masa zai tafi gida babu bata lokaci suka harhada duk wasu abubuwa nasa suka fita,tashi yayi yacire bakar coat din jikinsa yabar iya tacikin wadda take light green mai dogon hannu da neck tie baki da green, ahannunsa yariko rigar idonsa yana sanye cikin farin glass yana tafe yana daddanna wayarsa.
[12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣8⃣

Na UMMI A'ISHA

Fadawansa na hango shi suka zabura suka zo suka fara take masa baya suna tafe suna zabga kirari, takawarka lafiya, alafiya dai tafidan alheri, gaba salamun baya salamun namijin fama, babban goro sai magogin karfe, karo da karo sai rago, wani Kaya sai amale wane jaki, buhun kaya kake mai daukarka sai wanda ya shirya, kogi ba ayi maka katanga, kaga katangar sukari kowa ya jingina sai ya lasa, sauka lafiya dan ahamadu jikan sani, farin wata sha kallo, lafiya dai mai dogon zamani, gaba salamun baya salamun,shi dai tafida tafiya kawai yakeyi yana yin waya da faisal amininsa kuma dan uwansa har ya isa gun motarsa suka bude masa ya shiga ya zauna, daliban nan duk akan idonsu hakan tafaru har motar tafida tafita daga cikin asibitin, daya daga cikinsu mai suna sakina itace ta tabe baki wai kuga haduwar wannan gayen amma yarasa wacce zai so sai waccan kurmar,bebiya dukansu baki suka tabe wayaga abinda rai keso inbanda haka me zaiyi da ita kuma kunji ma dan gidan sarki ne ashe, daya daga cikinsu ce ta katsesu haba sakina meye amfanin haka? Ina ruwanku dasu, wannan abun da kukeyi babu kyau hassada ce ita kuma hassada Annabi yayi hani da ita domin akwai wani ingantaccen hadisi da manzon Allah s.a.w yake cewa iyyakum wal hasadu, fa innal hasadu ta akulul hasanati kama ya akulul narul hadabe, ma'ana nahaneku da hassada domin ita hassada lallai tana cinye kyawawan ayyuka kamar yadda wuta take cinye itatuwa ko kuma karare, dan haka wannan abin da kukeyi wlh bashida amfani ko kadan,soyayya ta Allah ce idan kukayi hakuri kuma zaku samu rabonku, tana gama fadin haka tabar wurin takoma cikin female ward, tsaki sakina taja wannan damuwarki ce amma wlh bazai yiyu ace mu masu baki da kunne yakimu yaso kurma ba. Tafida jinsa yake kamar bashiba har yaje gida,shidai bai taba soyayyaba asalima ko budurwa bai taba yiba saboda shi miskili ne nagaske kai kallon mata ma bai dameshi ba, baya hulda da mata ko kadan amma yau yayi gamo, gamo wanda za a iya cewa kyakkyawan gamo.
[12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

2⃣9⃣

Na UMMI A'ISHA

Cikeda farin ciki ya isa gida sai wata walwala yakeyi marar kan gado domin babu wadda ya saba ganinshi cikin wannan yanayin su kansu fadawansa mamaki sukeyi yadda yau yake cikin nishadi da walwala, suna isa tangamemen gidansu yafito daga cikin mota fadawan dasuke tsaron kofar suka mimmike tsaye suka fara gyara kintsi gaba salamun baya salamun barka da shigowa tafidan zamani tafida ba akawo maka wargi, takawarka lafiya dan toron giwa, dan zaki kafi karfin rainon kura, ko kura ta mutu tafi karfin kare yaja gawarta, namijin dawa kake mai kayan alfarma, barka da shigowa zaki dangin sikari, tsawo dangin rama, takawarka lafiya gaba salamun baya salamun, cikeda jin dadi tafida yadaga musu hannu kamar yadda yasaba yanufi zauren dazai sadashi da lungun mai martaba yana zuwa kansa tsaye yawuce cikin dakin mai martaba yasameshi zaune yana kallon labarai atashar CNN zubewa yayi yafara diban gaisuwa, sannan yatashi yafita yanufi wurin inno itama a falonta ya taradda ita tana kishingide jikin tumtum ga bayi zagaye da ita sunayi mata firfita ka kayan motsa baki a gabanta shiga yayi yazauna a kan kujera bayinta suka tashi suka fiffita anan ya zamo kasa ya gaida ta yatashi yafita yau gaba daya jinsa yake kamar wani sabon mutum dan tsabar nishadi, yana isa dakinsu yashiga toilet yayi wanka yafito yasaka kayan yan kwallo jar riga mai number 1 ajikin rigar da wando dogo,adaki yayi salla yana idarwa yafito yanufi wurin dawakansa yasamu har an daura masa sirdi domin fita kilisa shi kadai kawai ake jira baiyi wata wata ba ya haye dokin shima sarkin fada yahau nasa da alama yau su biyu zasu fita kilisar, tafe suke ahankali kowannensu rikeda linzamin dokinsa har suka isa wasu manyan gonaki, tafida ne yayi yar magana ahankali kamar yadda yasaba, sarkin fada wannan gonar idan baka mantaba nataba fada muku zatayi daidai da tsarin danakeso wurin gina business suit dina, Allah ya taimakeka tafida sarkin fada ya fada,amma yallabai wani hanzari ba gudu ba wannan gonar itama ta sirikinka kace idan ban mantaba, yatsina fuska tafida yayi koma tawaye a cikin satin nan za afara yimin aiki, Allah yaja kwana,Allah yasa kafi haka, sarkin fada yafada amma acikin zuciyarsa cewa yake wannan wanne irin mutum ne ace duk gonakin sirikinka sai bi kakeyi kana karbewa kana gini marassa dalili.
[12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣0⃣

Na UMMI A'ISHA

Haka suka karaci shawaginsu suka koma gida lokacin magriba tana daf da kawo jiki, suna isa gida tafida yasauka daga dokinsa a gajiye ya shige gida afalonsu ya zube akan carpet ya kwanta gaba daya ya gama gajiya, jinsa yake kamar yayi wani gagarumin aiki, fuskar wannan yarinyar ya hango take yayi wani murmushi insha Allahu sai na auri wannan yarinyar yafada azuciyarsa domin kyakkyawa ce ajin karshe, amma mamakinsa shine yadda take karatun science alhalin kuma bata ji kuma bata magana hakika ta cika yar baiwa gashi komai nata mai kyaune tamkar ita tayi kanta saboda yadda halittar ta tatsaru sosai, lumshe manyan idanuwansa yayi oh ko meye sunanta? Tsabar yarude yamanta bai tambayi sunanta ba shigowar faisal cikin falon ne yasashi dago kansa yakalleshi abokina daga ina? Zama faisal yayi daga dambam nake kasan garin nawa kullum basa rabo da rikicin manoma da makiyaya, murmushi tafida yayi uhm dakyau hakimi, dariya faisal yayi kaima dai dadinta hakimin ne, murmushi tafida yayi masa wadda har saida faisal yayi masa magana yau naga kana ta fara'a kodai? Murmushi tafida yayi babu abinda yafaru amma nazo maka da albishir nasamo matar aure dariya faisal yafara yi bakada seti tafida yaushe kayi aure da har zaka fara neman wani? Tsaki tafida yayi kaga babu ruwanka malam ni namanta ma wlh da wani auren da mai martaba yayi min, kallonsa faisal yayi to wlh kafadawa yarinya gaskiya tunda wuri ka sanar da ita gaskiyar lamari kai bazawari ne ba saurayi ba dan kanada mata yakarasa maganar cikeda dariyar mugunta,shiru tafida yayi masa bai bashi amsaba amma yatsani faisal[truncated by WhatsApp]
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣1⃣

Kallon faisal yayi malam banida lokacinka yanzu yana gama fadin haka ya mike yanufi lungun inno zuciyarsa fes domin yana cikeda farin ciki a wannan rana. Daren ranar bacci kadan yayi domin alla alla yake gari ya waye yaje yaga wannan yarinyar, asuba tana yi yatashi yafita masallaci yayi salla yana dawowa ya dauko alqur'aninsa ya buda yafara karantawa har karfe 6 tayi sannan yaje yayi wanka yafito ya shirya cikin suit ash colour hatta takalmin kafarsa ash colour ne yadaura agogon Gucci na azurfa duk wannan budurin da yakeyi faisal yana kwance yana kallonsa sai da yagama shiryawa tsaf faisal yace gaskiya kayi kyau mitumina wlh babu wanda zai ganka yace kai ba saurayi bane kamar ba kayi aure ba, tsaki tafida yayi Allah yasa kaima asatin nan dai ayi maka auren inyaso muga ta tsiya, dariya faisal yayi gaskiya kam gara mai martaba ya taimaka min yayi min aure tunda gashi har Kanina zaiyi mata 2 ina zaune niko daya banyi ba dariya tafida yayi yajuya yafita bai ce komai ba yana fita yashiga gurin inno ya gaidata yafito yaje wurin mai martaba shima ya gaidashi sannan yayi haramar tafiya office lolacin karfe 8 saura minti 20. Yana zuwa office yazauna akan table dinsa yadauki yar farar takarda yayi rubutu yasa agaban rigarsa yafito yanufi female ward, yana shiga nurses suka fara gaisheshi morning sir! Morning kawai yake cewa yawuce, da haka har yaje last bed inda budurwar nan take, kallon kyakkyawar fuskarta yayi yai mata murmushi ita dinma shi take kalllo wata farar takarda ya miko mata takarba yana bata yajuya yafita dama abinda yakawo shi kenan, theatre ya hara dan yanada aiki acan, yana fita ta bude takardar tafara karantawa rubutunsa kyau kadai kamar wadda aka buga ajikin computer, sakon nasa takaranta kamar haka "some people hv a nice smile, some hv a nice eyes,and some hv a nice faces, you u hv all of them & nice heart Good morning & hv a nice day! I. T, tana gama karantawa sai kuma tasoma hawaye wanda nikaina ummi Aisha ban san ko na menene ba.
[12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣2⃣

Na UMMI A'ISHA

Kuka take sosai wannan wanne irin abune da aurenta ta rinka son wani mutum nadaban, istigfari tafara yi ba kakkautawa acikin yanayin kawarta zara'u sulaiman tazo ta sameta zama tayi gefen gadon tafara tambayarta da hannu meyafaru?  Dakyar tadauki biro zara'u yau zan bar asibitin nan dama kin san acikin satin nan zan gama practical dina gida zan koma idan kingama naki ma hadu a sch dariya zara'u tayi to kijirani zanje nadawo tana gama rubuta mata ta tashi tafita, hawayenta tagoge tadauki takardar taboyeta acikin rigarta, tana nan zaune aka kawo wata mata marar lafiya agadon kusa da ita aka kwantar ta Jim kadan sai ga likitanta yazo wato dr tafida idonsa akanta yaje yagama duba matar nan yabata dukkan taimakon daya kamata sannan yadawo inda take, da ido yayi mata alama wai meya sameta idonta yayi ja, murmushi tayi takada hannu alamar babu komai takarda yadauka yarubuta mata meye sunanki? Da babban baki tabashi amsa sunana HANFA yana karantawa yayi murmushi meye ma'anar hanfa? Dan ni ban taba jin wannan sunan ba, murmushi tayi yakamata ka rinka bibiyar tarihi amma nabaka assignment go and find out d meaning of hanfa murmushi yayi yace zan kuwa baki mamaki domin zan samo miki ayau basai gobe ba yana gama rubutawa yabata yafita daga masu jinyar har nurses din kallonsu suke tayi to kodai sun san juna wannan abin mamaki ya isa domin ada ibrahim tafida (I.t) baya tsayawa yayi magana da patient amma gashi yau yatsaya yanata rubuce rubuce da kurma gulma nurses din suka fara yi agefe daya duk dai sun san ita wannan marar lafiyar yar practical ta hadu ta cancanci hakan.
[12:16PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣3⃣

Na UMMI A'ISHA

Agurguje yagama abinda yakeyi ya koma gida abinda bai saba yiba tashi karfe biyu amma yau yayi saboda yana so yasamu damar binciko ma'anar sunan hanfa, yana zuwa gida yasamu sirikinsa yana fitowa daga fada ko kallonsa bayi ba balle yasa ran zai gaisheshi tafiyarsa yayi cikeda takama fadawa suna biye dashi suna takawarka lafiya dan toron giwa gaba salamun baya salamun dahaka yashige gida dakinsu yaje yabaje ya jawo laptop dinsa yafara searching din hanfa sai da yadade yana nema sannan ya samo cikeda farin ciki yatashi yaje dakin inno bata cikin dakin dan haka kan gadonta ya haye yayi dai dai yana tunanin hanfa ba shakka sunanta ya dace da ita kuma ya cancanceta ganin inno bata shigoba yasashi mikewa zai fita daga dakin sai gata kuma ta shigo,a'a tafida dama kana nanne? Kai yadaga mata ina nan inno ai tun dazu nadawo amma sake fita zanyi, to amma dai sai kaci abinci ko? Murmushi yadanyi to inno abani kadan naci dakanta tafita ta hado masa abinci takawo masa harda kayan marmari agefe zama yayi yadanci abincin kadan yatashi yafita yakoma dakinsu yayi wanka yafito yashirya tsaf cikin blue colour din jeans da riga dark brown mai gajeren hannu yana fitowa yahadu da faisal ya yau da wuri zaka fita kilisar ne abokina? Faisal ya tambaye shi, no zanje asibiti ne amma bazan wani jimaba zan dawo, ok sai kadawo faisal yafada yawuce ciki shi kuma tafida ya fita, yana zuwa su sarkin fada suka bude masa kofar mota ya shiga ya zauna sai asibitin kwararru na rasheed shekoni wanda yake da xango acikin garin misau.
[4:08PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣4⃣

Na UMMI A'ISHA

Suna isa asibitin ya nufi female ward yashiga nurses din dake ciki sai fadi suke welcome sir! Last bed ya hanga amma babu kowa cikin rudewa ya tambayi daya daga cikin nurses din ina patient din dake last bed? Ahankali tace dr dazu tatafi, ahargitse ya kalleta are you mad? Danme zaku barta tatafi ban sallameta ba, meye amfaninku agurin? Wannan ya nuna min cewar baku san aikinku ba, sai kun karbi query saboda sam bakuda hankali hakuri suka soma bashi we are sorry sir! Ko kulasu bai yiba yafice daga cikin ward din, to shi yanzu ina yanufa? Tunda bai san inda yarinyar nan takeba sa'arsa daya yasan sunanta, fita yayi yashiga motarsa fadawansa suka rufa masa baya, ransa abace yake yau sanadiyar rashin ganin hanfa da wannan bacin rai suka karasa gida yana zuwa dakinsu ya fada akan gado ji yake kawai kamar ya fashe da kuka, tabar wiwi ya janyo ya kunna ya fara zuka nan fa ya turnuke dakin da hayaki kamar salansar babur, faisal dake kwance kusa dashi yana bacci ya bude ido yafara kallonsa dan ganye ka fara zuke zuken naka ne? Shiru tafida yayi masa domin bacin ran dayake ciki baxai barshi ya iya yin magana ba tabarsa yaci gaba da busawa batare da yace komai ba tuni idonsa ya kada yayi jajawur kamar jini ganin abin bana kare bane yasa faisal kwace sauran wiwin ya boye yana cewa kai meyasa wani lokacin baka da saiti ne? Sai kaje kajawa kanka wata cutar, kana likita amma baka san abinda zai illataka ba, dakyar tafida ya iya bude baki yace faisal ban ganta ba, wacece? Faisal ya tambayeshi yarinyar da nace maka nahadu da ita a asibiti, to kuma shine zakazo kayita shan wiwi? Ai kamata yayi katsaya ka nutsu ka binciko inda take amma baka zauna kayita bunkawa cikinka hayaki ba lumshe idanuwansa tafida yayi yace nagode abokina insha Allah zan kokarta kwanciya yayi yafara hango kyakkyawar fuskar hanfa, Allah sarki kowa da yadda Allah yake jarrabarsa ita kuma haka Allah ya halittota kurma sannan kuma bebiya amma ya tsara halittarta yadda bazai kwatantu ba, dan tsaki yaja ni ba muryarta nakeso ba kuma ba jin maganarta nakeso ba ita kanta nake so kuma insha Allahu sai na mallaketa.
[5:09PM, 11/16/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣5⃣

Na UMMI A'ISHA

Zama jugum tafida yayi yana ta sake sake acikin ransa gamida tunanin yadda zai nemo sahibarsa hanfa daren ranar bashida wata walwala har gari ya waye, shiryawa yayi yadda yasaba cikin suit bakake yasa bakin takalmi yasa glass dinsa fari dan siriri yafito agurguje ya leka wurin mai martaba yafito yashiga wurin inno yana fitowa yanufi asibiti koda yaje tuni har ma'aikata sun firfito manyansu da kananansu, gakuma yan attachment suma duk sun fito, yana zuwa yawuce office dinsa yafito yashiga maternity jim kadan yafito yashiga female ward nanma bai fi minti biyar ba yafito yana fitowa yashiga antenatal,yana fitowa yadaga yan yatsunsa guda biyu yashiga office take dogarawansa suka furtsa aguje suka nufi office dinsa nanfa yan practical suka fara kace nace wato wannan daga yatsun dayayi ashe fadawansa yayiwa magana lalle sarauta sai me ita,basu farga ba sai ga wani bafade guda daya yazo inda suke yayi musu sallama yace wacece zara'u acikinku? Gani zara'u ta amsa, to kizo mai girma tafida yana son ganinki, hanzarta yanmata, tafida ikon Allah tafida mai jan doki, dasauri zara'u ta tashi tanufi office din dr tafida yayinda dogari yake biye da ita yana fadin takawarki lafiya yanmata, gyara kintsi bakuwar tafida alafiya dai gaba salamun baya salamun, ita dai zara'u gaba daya atsorace take domin bata san me zai biyo baya ba, yayinda kawayensu suna can suna ta gulmarta ita da hanfa to ko yanzu zara'u zai ce yana so? Inji wata acikinsu kudai jira muga dawowarta tukunna sakina tafada, zara'u suna zuwa office din tafida bafade yabude mata tashiga abinka ga jinin sarauta akishingide ta sameshi yana jiran zuwanta tana shiga yayi gyaran murya take fadawan sukayi waje suka ja musu kofa.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [6:39PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣6⃣

Na UMMI A'ISHA

Fadawansa na fita ya kalli zara'u yana daga kishingide yace hv a seat zarah, babu musu ta zauna akan kujerar dake nesa dashi, kallonta yayi ina hanfa take? Hanfa tatafi gida, a ina gidan yake? Ya tambayeta, acan disina gidansu yake, dagaske ne ita kurma ce? Daga Kai zara'u tayi tace dagaske kurma ce sannan kuma bebiyace, murmushi yayi wanda yasake bayyanar da zahirin kyansa afili to yanzu ki taimaka min kibani address dinta zanje gidansu na sameta amma kuma naji tace min wai ita matar aurece hakane? Girgiza kai Zara'u tayi wlh bani da masaniyar hakan amma nima tabbas ta taba fada min cewar ita matar aurece amma ban yarda ba gaskiya, murmushi yayi hakane metake karanta a makarantar? Lab science take karanta, a school of nursing & midwifery dake cikin garin nan amma asalinsu yan garin disina ne, ok to ke tun wanne lokaci kika santa? Sanina da ita baifi shekara daya ba lokacin da muka shiga makarantar nanne kuma tunda muka fara kawance da ita har yau babu abinda ta taba yi min na bacin rai har gidansu naje itama taxo namu gidan, ok good yanzu ki rubuto min address din ki kawo min nagode amma zan kara nemanki idan bukatar hakan ta taso,daga kai zara'u tayi babu komai tashi tayi zata tafi murmushi tafida yayi nagode zarah amma agaskiya ina son kawarki sosai kuma zan aureta, murmushi zara'u tayi tace Allah ya tabbatar da alheri amin tafada tareda ficewa daga office din.
[6:56PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣7⃣

Na UMMI A'ISHA

Zara'u tana fita tafida yayi kishingide yazama tilas agareshi gobe yaje disina yabinciko gidansu hanfa, tashi yayi yafito daga office dinsa yanufi motarsa nan da nan su sarkin fada suka tattaso suka fara bin bayansu daidai lokacin zara'u tazo tamikawa tafida address din gidansu hanfa ko dubawa bai yiba yasaka takardar acikin aljihunsa ya wuce yana cewa thank u, ita kuwa zara'u tana komawa wurinsu sakina sakina tayi farat tace wai zarah me wannan gayen yake so awurinki ne? Dariya zara'u tayi address din budurwarsa ya nema kuma nabishi, dakyau sakina tafada cikeda bacin rai. Tafida yana zuwa gida yayi dukkan abubuwan da yasaba yi yafita kilisa yau kilisar tasu daga shi sai faisal, suna tafe ahankali akan dawakansu tafida yace abokina gobe zanje disina, me zakayi a disina? Akwai abinda zai kaini, ok to ko gidansu matar taka zakaje? Eh can zanje tafida yafada ahasale, dariya faisal yayi Allah yabaka hakuri abokina abin bana fada bane daga tambaya? Eh daga tambayar tafida yafada yana harararsa kasan Allah tafida? Ka nemi matarka ku sasanta tun wuri, tsaki tafida yayi haba faisal wayace adaura min auren da banine na bukata ba, wlh babu wani sasanci da za ayi ni yanzu ma aure zanyi wanda duniya zata san nayi aure amma wanccan auren ai na mai martaba ne murmushi faisal yayi to kuwa sai Allah ya tambayeka domin nauyin yarinya yana kanka tun daga ciyarwarta da shayarwata ga uwa uba hakkinta na aure tunda ita macece mace kuwa kasan tanada rauni, kuma duk duniyar nan kai kadaine zaka iya yi mata wannan domin babu wanda zai bata sai kai, uwar me zan bata? Tafida ya tambayeshi kafini sanin abinda zaka bata to ai kuwa sai dai ta mutu wlh dan banida lokacinta, dariya faisal yayi yace Allah ya shiryeka abokina, da haka suka juya suka koma gida.
[7:18PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣8⃣

Na UMMI A'ISHA

Suna komawa gida tafida yashiga dakinsu ya zauna yafara bincike acikin laptop dinsa wanda ni kaina ummi A'isha ban san me yake nema ba sai da ya dauki tsawon lokaci sannan yarufe laptop din nasa yanufi masallaci yana dawowa yadora daga inda ya tsaya yaci gaba da bincikensa har faisal yazo ya sameshi yafara yimasa hira amma shi tafida sama sama yake jinsa duk hankalinsa ya tattara akan binciken da yakeyi. Washe gari da misalin karfe 11 nasafe tafida yayi shirinsa tsaf cikin wani tsadadden boyel fari yasa hula yasha turaren fogg ya daura agogon azurfa kirar kamfanin omega yasa farin takalmi cover shoe yafito yayiwa mai martaba da inno sallama cewar yatafi disina duk babu wanda yasan abinda yatafi yi sai faisal amma su mai martaba basu tambayeshi me yatafi yiba kasancewar sun san garinsa ne shine yake mulkar garin, wata jibgegiyar jeep yashiga wadda akalla zata iya daukar mutum goma ita yashiga yazauna agidan baya sarkin fada yashiga gaba yazauna yayinda sarkin mota shikuma yazauna a mazaunin driver yaja suka tafi, tafiya sukayi ba mai nisa dayawa ba suka karasa garin disina, address din da zarah ta basu sarkin fada yarinka bi har suka isa wata unguwa mai suna gangare, anan sarkin fada ya tambayi wani yaro ko inane gidan su hanfa? Wancan mai koren fentin ne yaron ya nuna musu shidai tafida yana zaune abaya kishingide ajikin kujera yana latsa wayar hannunsa, adaidai kofar gidan sarkin mota yayi packing din motar yafito shima sarkin fada fitowar yayi ya isa bakin kofar gidan yafara kwada sallama sai da yayi sau wurin biyar sannan wani yaro yafito, yana amsa sallamar, yaro nanne gidansu hanfa? Eh nanne,tana ciki? Eh tana nan to kaje kace ana sallama da ita, to yaron yafada tareda juyawa cikin gidan da gudu, Jim kadan kuma sai gashi yadawo wai ance inji wa? Kace inji tafida, dagudu yaron ya sake komawa can sai ga wani mutum yafito daga cikin gidan waye yake nemanta? Mutumin yafada cikin fada, daidai lokacin tafida yafito daga cikin mota wazai gani? Sirikinsa yagani mahaifin matar da mai martaba ya aura masa.
[7:50PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

3⃣9⃣

Na UMMI A'ISHA

Bata fuska tafida yayi yasauko dakyau ya tsaya yana kallonsa dama shima sirikin nasa kallonsa yake, cikin murtukewar fuska mutumin yace, lfy kuka zo min gida? Cikeda isa tafida ya kalleshi amma baiyi magana ba sarkin mota ne yace barka da safiya dama yallabai ne yazo gurin yarinyar gurinka hanfa, wata harara mutumin yayi musu sai yanzu yasan da ita? Da lokacin da aka daura auren ya nemi inda take balle ace ya ganta, tunda aka daura auren nan bai san cinta ba bai san Shanta ba bai san sutturarta ba uwa uba bai san lafiyarta ya takeba dan haka nidai nayi dana sanin aura maka yata kuma nayi bakin cikin auran yata da kayi domin kai ba mutumin arziki bane bakada wata kama ta mutanen kirki,dan haka ina mai shawartarka da kadauki sahunka a likkafa tun dare baiyi maka ba kabar kofar gidana sannan kuma yazama tilas, dole ka saki yata domin bazan hada zuri'a da mutumin banza ba irinka dama na aura maka yatane dan mutuncin mahaifinka to yanzu nafasa, yana gama fadin haka yakoma cikin gida tareda doko kofar gidan da karfi, sai asannan tafida ya iya motsawa daga mutuwar tsayen da yayi dama hanfa itace matar da mai martaba ya aura masa? Wata zuface ta fara karyo masa kamar an kwara masa ruwa ga kafarsa tayi wani irin nauyi marar misaltuwa, ahankali ya zare gilashin dake idonsa yafara tafiya ahankali tamkar kazar da kwai yafashewa aciki, batare da tsoro ba yatura kyauren kofar ya shiga gidane na talakawa babu yabo babu fallasa komai na cikin gidan irin na talakawa ne,yana shiga ya fara sallama tamkar mai yin rada, zuruf masu gidan suka fito daga daki baban matarsa ne yataso cikin fada, waye yayi maka izinin shigowa cikin gidana? Kai kafita daga idona yanuna shi da yatsa nadade da sanin kai marar kunya ne kuma bakasan mutuncin nagaba da kai ba, kafitar min daga cikin gida tun kafin nayi maka kamun kazar kuku, cikin rawar murya tafida yace baba zan fita amma sai ka bani matata, kar ka kuskura kasake kirana da baba domin baka daukeni uba ba kuma nima duk cikin yayana babu mai wulakanta mutane wanda bai san darajar mutane ba, kayi hakuri baba amma dan Allah kabani matata tafida yafada tamkar zai fashe da kuka, wai wacce matar yake fada? Wata mata ta tambaya cikin fada, wannan akwai marar kirkin yaro, sai yanzu kasan da matar taka, yau auren naka yafi wata 6 ko sau daya baka zo kaganta ba saboda kana gadarar kuna da sarauta? Kai gaka dan gata to mu bamu da sarauta amma Allah shine gatanmu, nuna masa hanya baban hanfa yayi fice min daga cikin gida marar kunyar banza marar kunyar wofi, cikeda rashin karfin jiki tafida yajuya yafita yayinda mahaifin hanfa yabiyoshi yayi masa korar kare, dakyar tafida yashiga mota yacewa su sarkin fada sushiga su koma misau take suka bi umarninsa.
[8:28PM, 11/17/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

4⃣0⃣

Na UMMI A'ISHA


Gudu sosai sarkin mota yayi amma tafida gani yake kamar ba tafiya sukeyi ba alla alla yake yaga sun isa garin misau, wani jiri yaji yana daukarsa wannan abin al'ajabi da yawa yake, tun farko dayasan wannan kurmar ce matarsa ai da ya amince, to ai sai da mai martaba yabaka hotonta amma kaki gani, shiyasa aka ce komai idan aka bishi a sannu yafi armashi zuciyarsa tafada masa, gefen kansa yaji ya sara kamar wanda zai tsage gida biyu, da sauri yasa hannunsa ya rike, sai yanzu yasan wulakanci bashida rana gashi yanzu yanaji yana gani yataho yabar hanfa batare da yaganta ba, amma da ace alheri yayiwa mahaifinta tun farko da bazai yi masa wannan cin mutuncin ba domin shi ALHERI DANKO NE! Baya faduwa akasa banza ko baka samu alokacin ba to agaba zaka dauki abinka watikil ma harda riba, wayarshi yadauka yafara kiran number faisal bugu biyu faisal yadaga abokina ya? Kana ina faisal? Ni gani a office kaifa kadawo daga disinan ne? A'a nakusa zuwa dai yanzu gamu acikin azare dan Allah kadawo gida nafi son da nazo nataradda kai agida pls abokina, ok dama nima nagama aikin da nakeyi yanzu zan koma gida, Allah yadawo daku lfy amin faisal, tafida yafada yakashe wayar, kansa yadafe yana ji kamar zai bar jikin wuyansa dakyar ya iya mikewa ya kwanta akan kujerar da yake, gudu sarkin mota yakara dan danan sai gasu acikin disina, suna isa gida tafida yatashi yafito anan yabar gilashinsa da wayoyinsa, sai sarkin fada ne ya dauko masa, yana shiga dakinsu yasamu faisal zaune yana waya kusa dashi yazauna faisal yagama wayar ya jiyo gareshi yace abokina kadawo? Kai tafida yadaga yace nadawo sai dai yau nayi dana sanin aikata kuskure da sharri arayuwata faisal hakika nayi kuskuren aikata sharri hakika faisal sharri jakada ne maishi yake dawowa yayinda shikuma ALHERI DANKO NE bazai taba faduwa abanza ba, kallonsa faisal yayi wai meya farune? Cikin damuwa tafida yace faisal yarinyar da nake baka labari ashe itace matar da mai martaba ya aura min sai yanzu da naje gidansu na tabbatar da hakan, dariya faisal yafara har da saukowa kasa daga kan kujera nan ran tafida yakara baci sai hawaye sharr! Cikin sauri faisal ya daina dariyar yace haba abokina be a man mana, ya zaka rinka kuka kamar mace, faisal ina sonta nd i can't do with out her! Hannunsa faisal yarike yace maza tashi muje wurin mai martaba mu rokeshi yabaka matarka, tashi tafida yayi yabi bayan faisal har suka isa fada kuma fadar acike take makil da alama sarki yana ganawa da yayun su tafidan ne, turakin soro shine yayi musu iso wurin mai martaba, a kasalance suka isa cikin fadar nan suka matsa gaban mai martaba suka yi gaisuwa caraf fadawa suka cafke,sarki ya gaisheku samarin alheri, sarki ya amsa gaisuwarku mazajen fama, tafiya dai sannu sannu kwana nesa.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [9:52AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!


4⃣1⃣

Na UMMI A'ISHA

Cikin fargaba faisal yace ranka yadade akwai abinda yake tafe damu, gyaran murya mai martaba yayi nan da nan fadawansa suka fice daga cikin fadar sai iya su chiroma da galadima da sa'i kawai aka bari awurin,cike da jin nauyi faisal yace ranka ya dade dama tafida ne yace yatuba yanzu yagane abinda yayi bai kyauta ba shine muka zo mu nemi afuwarka ayi hakuri abashi matarsa, cikin fada sarki yace kai! Idan ku shashasu ne to ni ba shasha bane, dama wannan ce maganar da ta kawo ku? Maza kutashi kubar wurin nan tun kafin raina ya baci, hakuri faisal yafara bayarwa yayinda shikuma faisal yakasa furta koda kalma daya in banda fararen idanuwansa da suka rine sukayi jajawur, cikeda fushi galadima yace kai! Akace kutashi ku bawa mutane wuri marassa kunyar banza, tashi faisal yayi yaja hannun tafida suka fice daga cikin fada, suka tafi wurin inno, afalo suka tarar da ita tana zaune kuyanginta zagaye da ita, rai abace tafida ya zauna kallonsu tayi ya akayi naganku duk kunyi wani iri, inno bukata ce take tafe damu inji faisal, kuyangunta ne suka tashi suka fita,meya faru? Inno ta tambaye su, inno daga wurin mai martaba muke dan Allah kisa baki adawowa da tafida matarsa ai abinda ya wuce ya riga ya wuce, au dama wannan ce ta kawoku? To maza ku tashi kubar min dakina kuma kar ku kara tunkarata da wannan maganar kunji dai na fada muku marassa kunya kawai, tana gama fadin haka ta mike tashige dakinta nanfa tafida yaji kansa ya sara, jan hannunsa faisal yayi taso muje wurin momcy bai yi musu ba yabi bayansa har fannin momcy, suna shiga lokacin tana kokarin fitowa ganinsu yasa takoma ciki suka bi bayanta, tafida me yafaru? Ta tambayesu faisal ne ya iya yi mata bayanin abinda ya faru nan tafara kwantarwa da tafida hankali, kar kadamu tafida insha Allahu komai zai zo da sauki kaji, kayi hakuri zanje nasamu mai martaba saboda dama yanzun nan wurinsa zanje jakadiya tace min yafito daga fada, kujirani naje nadawo yanzu, tashi tayi tafita zuwa sashen mai martaba.
[9:53AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!


4⃣2⃣

Na UMMI A'ISHA


Koda momcy taje wurin mai martaba hakuri tafara bashi akan maganar tafida ai kuwa nan mai martaba ya rufeta da fada baji ba gani, cikin fuskar alhini momcy tace to ranka yadade ni kayi min izini gobe sai naje disinan da kaina nataho masa da matarsa, hajiya mabruka muddin kikaje to wlh bada yawuna ba kuma babu hannuna aciki,aure dai ai nine nayi masa ko? To babu ruwanku aciki ku zuba min ido kawai, tashi momcy tayi tana fadin Allah yahuci zuciyar ka ranka yadade amma mai martaba sai fada yake ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba, tashi momcy tayi ta koma sashenta tana shiga tasamu su faisal suna zaman jiranta, cikin damuwa tafara magana, nayi duk iya kokarina amma mai martaba bai saurareni ba asalima cewa yayi idan naje disina to bada yawunsa ba, amma abinda nake so dakai tafida shine kayi hakuri mujira muga nan da gobe ko Allah zai sa ya sauko, kai kawai tafida ya iya dagawa yamike faisal yabishi suka fita, suna zuwa dakinsu tafida ya zube akan gadonsu yafara fitar da numfashi mai zafin gaske shikuma faisal ya zauna yafara bashi baki, wunin ranar nan tafida yayi shine kawai amma acikin bacin rai yake shi kansa a matsayinshi na likita yasan bp dinsa yahau sosai ba kadan ba dan yaji alamun hakan ajikinsa, gashi ko ruwa bai sha ba bare yaci abinci har dare yayi. Wurin misalin karfe 10 nadare tafida ya kalli faisal yace abokina dan Allah kayi min wani taimako, ina jinka fadi injishi, so nake gobe katafi disina gidansu hanfa kasamu mahaifinta kuyi magana ta fahinta kaji ko ahaka aka haifeta da lalurar kurmanci da bebanci, idan ba haka aka haifeta ka dauketa ka kaita asibitin tafawa balewa teaching hospital akwai likitan kurame acan kuma insha Allahu akwai taimakon da zai bata, cikeda tausayawa faisal yace dama kurma ce? Kai yadaga wlh faisal kurma ce kuma bebiya bataji kuma bata magana amma tahadu fiyeda yadda baka zato gata da hazaka domin ahakan take karantar nursing, girgiza kai faisal yayi Allah sarki Allah yabata lfy ya daidaita tsakaninku, amin faisal sa'ar danayi ma da ban saketa ba tun da farko da matsalar da zan shiga sai tafi haka, kayi hakuri dai tafida ka kwantar da hankalinka tunda kasan illar saka damuwa acikin zuciya daga kai tafida yayi yashiga duniyar tunani har faisal yayi bacci amma shi faisal yadda yaga rana haka yaga dare ga wani azababben ciwo da kansa yake yi masa dakyar yatashi ya dauko brief case dinsa ya bude yadauki abin auna jini yafara auna jininsa nan yaga yahau fiyeda zatonsa ahankali ya mayar yakoma ya kwanta, alla alla yake gari ya waye dan faisal ya tafi disina.
[9:54AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!


4⃣3⃣

Na UMMI A'ISHA

Wayewar garin ranar faisal yashirya ya tafi disina alokacin tafida ko tashi zaune baya iya yi, lokacin da faisal yaje gidansu hanfa tarbar arziki mahaifanta sukayi masa, bayan sun gaisa yace baba dama zuwa nayi naji ko dama hanfa haka aka  haifeta da wannan lalurar? Cikeda alhini mahaifinta yace wlh faisal da bakinta da kunnenta muka haifeta har ta girma ta xama budurwa, haduwarta da lalurar shekaru uku baya ne da suka wuce tayi wata rashin lafiya mai tsanani tun daga lokacin tadaina magana tadaina ji, amma da lafiyarta lau yakarashe maganar yana kwalla, ayya Allah ya rufa asiri faisal yafada yanzu tana ina? Tana ciki, dama ina sone zan kaita asibiti likita zai dubata, cikeda farin ciki mahaifinta yace Allah saka da alkhair madallah madalla nagode, tashi yayi ya shiga ciki bai jima ba sai gasu sun fito tare da ita kallonta faisal yayi agaskiya kyakkyawa ce sosai shiyasa tafida ya rikice da hannu suka gaisa ya bude mata mota tashiga yayiwa mahaifinta sallama suka tafi, suna zuwa asibitin faisal yafita yaje yabude mata polder aka nuna masa inda zai ga likita sannan yakoma yataho da hanfa suna zuwa tabi layi tazauna wurin ganin likita basu fi su biyar ba, tana nan zaune har layi yazo kanta suka shiga tare faisal, likitan da zai dubata bature ne nan yafara bincikarta yana wasu yan rubuce rubuce, tare da dauko wani zungureren almakashi yadauki audugu yatura a kunnen yafito dashi nan yacewa faisal gado zasu bata, za ayi mata aiki zasu biya kudi dubu dari bakwai da hamsin tashi faisal yayi yafita yaje banki ya ciro kudin yazo ya biya jifa jifa tafida yana kiranshi awaya yana tambayarshi halin da ake ciki, bayan ya gama biyan kudin ne yatafi gidansu hanfa ya sanar musu abinda zai gudana nan da nan mahaifiyarta tahada kaya suka nufi asibiti sai da faisal yagama yi musu komai sannan yayi sallama dasu yakoma misau sai yamma lis ya isa gida yana zuwa yasamu tafida kwance adakinsu ga ledar ruwa nan ana kara masa ashe duk wannan wayar da yake yimasa karfin hali kawai yakeyi shima yana kwance, sannu tafida yau likita ne dakansa ake kara masa ruwa? Murmushi tafida yayi faisal ya kukayi da hanfa? Cikin fara'a faisal yace an bata gado aiki zasuyi mata nan da kwana 3 fatan dai Allah yasa adace amin faisal nagode Allah yabar zumunci, haba tafida duk abinda nayi maka ai kaina nayiwa Allah yabaku lafiya, tashi yayi yafita saboda tsabar tausayin dan uwansa da ya shigeshi.
[9:54AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!


4⃣4⃣

Na UMMI A'ISHA


Acikin kwanakin kullum sai faisal yaje garin disina yayinda shikuma tafida yana nan akwance yana jinya jininsa ne yahau over gashi tunda yake bai taba yin hawan jini ba sai a wannan lokacin, ranar da za ayiwa hanfa aikin aranar faisal yatafi da sassafe dama duk abinda suke bukata shi yake kai musu, yana zuwa asibitin ya samu za ashiga da ita dakin da za ayi mata aikin ga iyayenta agefe ko wannensu zuciyoyinsu babu dadi haka shima faisal yatsaya suna nan tsaye har tsawon awa 2 sannan aka fito da ita kai daga ganinta kasan tawahala mutuka wani daki aka zarce da ita amma da alama ba ayi nasara ba, sai bakar wuya da tasha domin sai da aka fara yimata fanfo sannan aka yimata wankin kunne kai wuya dai kala kala tashata amma bata samu lafiya ba domin sauki daga Allah yake nan mamanta tafashe da kuka shi kansa faisal ji yake kamar yayi kukan domin bai san halinda tafida zai shiga ba idan yaji cewa bata warke ba, tashi yayi yashiga office din likitan dan neman karin bayani anan likitan yake sanar dashi cewa sunyi iya bakin kokarinsu amma ba adace ba kuma amma kunnenta lafiya lau yake dan haka agobe ma zasu iya tafiya gida godiya faisal yayi masa yafito yazo yasamu iyayenta yayi musu bayanin abinda likita yace, babu komai Allah yasa haka shine yafi alheri mahaifin hanfa yafada alokacin faisal yayi musu sallama yakama hanyar misau yana zuwa ya tarar da tafida yana jiransa nan ya zauna yafada masa dukkan abinda ya wakana, cikin damuwa tafida yace babu komai ni dama ita nakeso ba wani abu nata ba amma yanzu abinda nakeso dakai faisal dan Allah kaciri kudi gobe kaje kasiya musu gida mai kyau ka zuba musu furnitures kasiya musu kayan abinci domin babu amfanin ni ina zaune awuri mai kyau ina cin mai kyau amma matata tana cikin kuncin rayuwa kai faisal yadaga hakane Allah yakaimu goben. Acikin kankanin lokaci faisal yaje garin disina yasiyawa su hanfa hadadden gida mai kyau wanda yadace da zamani yazuba musu furnitures dama unguwar ba unguwace mai hayaniya ba babu bata lokaci suka koma gidan nan iyayenta da ita kanta suka shiga yiwa faisal addu'a domin duk atunanisu shine yake yi musu wannan hidimar, lokacin da faisal yadawo gida ya sanar da tafida ba karamin dadi yajiba anan yake sanar da faisal cewa an hadashi da wani malamin addini wanda yake taimakawa mutane dan haka zaije ya duba hanfa ko Allah zai sa adace, hakan kuwa akayi faisal yaje yadauki malami suka tafi gidansu hanfa, suna zuwa malamin yace taje tadauro alwala sannan ya bukaci da abashi ruwan zamzam original ba jabun ba nan faisal yatashi yaje wani Islamic chemist anan cikin garin ya siyo yakawo, ruwan zamzam din malamin yajuye acikin wani koko yafara addu'a yana watsawa akan fuskar hanfa take tafadi akasa, cigaba da watsawar yayi yanayi yana addu'a har aka kwashe tsawon lokuta alokacin yafara yiwa su faisal bayanin cewa hakika hanfa tana fama da matsala ta jinnu kuma kurame ne gashi sunfi wahalar sha'ani amma aci gaba da addu'a, nan faisal ya zauna agarin bai tafi misau ba sai dai suna yin waya da tafida. Kwana uku malamin nan yayi yana yiwa hanfa magani amma shiru sai akwana na hudune Allah yabada nasara jinnun sukayi magana amma da hannu suke nuni da haka malamin yace sufita daga jikinta amma da yake masu taurin kaine sai da suka sha wahala sannan suka fita.
[9:56AM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!

4⃣5⃣

Na UMMI A'ISHA

Sai da malamin yaja musu kunnen cewa su sakar mata kunnenta da bakinta kafin su fita, suna fita tayi wata irin atishawa mai karfin gaske, Allahu akhbar hakika sauki da rashinsa daga Allah suke tuni tafara wani bacci mai nauyi, malamin ne yajiyo gasu faisal yace wato abinda yafaru shine ruwan zafi ita wannan baiwar Allah ta zuba musu to shine suka shiga jikinta amma insha Allahu yanzu tasamu waraka farin cikine ya mamaye zukatansu asannan mamanta tayi magana tace dama lokacin taliya tadafa tana tacewa tashekar da ruwan shikenan tun daga lokacin tafara jinya, girgiza kai malamin yayi shiyasa ba aso azubar da ruwan zafi akasa dan haka sai akiyaye nan suka zazzauna suna jiran farkawarta sai da ta dade tana bacci sannan ta farka bakinta dauke da addu'a nan fa ta kalli mamanta tace mama! Wato masu karatu ni ummi Aisha sauran kadan nasaki wayata tafadi taci screen saboda tsananin zakin muryar hanfa danaji wata irin zazzakar murya ce da ita shi kansa faisal ji yayi kamar wata balarabiya balarabiya tazama maida kallonta tayi ga faisal tace nagode Allah yasaka da alheri tana gama fadin haka tatashi hawaye suna bin kumatunta tashiga daki tayi alwala tafara salla domin nuna godiyar ta ga Allah yayinda shi kuma faisal yadauki malam suka koma misau suna zuwa yafara yiwa tafida albishir ai tafida bai san lokacin da yadiro daga kan gado ba yazo ya rungume faisal tuni yaji jikinshi yaware nan yafara tambayar faisal nawa za abawa malam? Yace duk abinda yasamu domin shi bai yanke ba, ok to zan bashi dubu dari biyar da mota daya da gida guda daya take shima tafida yafada bathroom yadauro alwala yazo yafara nuna godiyarsa ga Allah. Bayan hanfa ta warware ne tafara shirin komawa makaranta nanfa tafida yayi siyayya mai tarin yawa yabawa faisal ya kaimata duk abinda yasan zata bukata sai da yasai mata kayan kwalliya da kayan abinci da drinks kala kala hatta pad sai da ya siya mata ga turarruka masu tsada nan iyayenta da ita suka shiga godiya bayan tafiyar faisal mahaifinta yake ta yabon faisal sannan yabata labarin cin mutuncin da dan uwan faisal din yayi masa wato mijinta tafida tun daga nan taji ta tsani tafidan tun kafin ta ganshi. Ranar Monday ta shirya tadawo makaranta nanfa yan makaranta suka shiga mamaki jin hanfa bebiya tawarke yayinda wasu kuma suke cewa ai babu mamaki da sha'anin Allah, ranar data dawo makaranta ranar tafida yafara zuwa office bai dawo ba sai 5 tunda yadawo yaci abinci yayi wanka yafita shida babban zaginsa da sarkin mota yana daga baya azaune yace musu school of nursing zasuje haka kuwa minti kadan sai gasu acikin makarantar suna shiga suka fara tafiya ahankali har sukaje gaban wani hall inda dalibai ke tsattsaye group group da alama daga lecture suka fito nanfa daliban suka fara bin motar tafida da kallo wata babbar jeep ce kirar kamfanin crotoure baka mai bakin gilasai an rubuta tafida 4 ajiki, ba aganin wanda yake ciki, ido tafida yafara budewa yana kallon daliban can ya hangota da uniform ajikinta da dan karamin hijabi iya kafadarta tayi wani kyau sosai tana tsaye cikin maza sunfi biyar da modern biology a hannunta da alama bayani take musu nanfa yaji ransa ya sosu, babban zaginsa ya cewa yaje yakira masa ita koda yaje hanfa bata kulashiba sai ma gurmuda baki da tayi duk abinda tayi akan idon tafida yana kallonta ta glass din motar dan haka koda babban zagi yadawo bai jira bayaninsa ba yabude motar yafita nanfa kallo yakoma kansa yatsuke cikin bakar riga mai gajeren hannu ajikin rigar an rubuta big guy da jan fenti yasa jan trouser da jan takalmi irin nasu na sarauta hatta belt din da yadaura ja ce yadora bakar jacket asama ahankali yafara tafiya yana zuwa yajiyo da ita yaja hannunta nanfa tafara turjewa ganin haka yasa tafida fizgota jikinsa ya rungumeta nan fa su babban zagi da sarkin mota suka fito da gudu suka zo inda suke suka baza babbar rigarsu sukayi musu runfa suka lullubesu ahankali tafida yadago kanta yasa bakinsa akan nata yafara zagaye lips dinta da harshensa,tofa muje zuwa dai masu karatu.
[1/20, 11:29 AM] Ummi A'isha: [5:39PM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!


4⃣6⃣

Na UMMI A'ISHA

       Cikin sauri hanfa ta bude idanuwanta ta fara kallon fuskarsa bakinsa kan nata gashi ya wani kankameta duk kamshin turarensa na fogg ya cika hancinta ras! Taji gabanta ya fadi, jan hannunta yayi yakaita cikin mota yabude gidan baya yasata shima yashiga sukuma su babban zagi suka zauna daga waje, yayinda dalibai suka yi cirko cirko suna tattauna wannan lamari da ya afku wasu kuma ba karamin burgesu tafida yayi ba, suna shiga cikin mota hanfa tafara matsawa yana binta, tana matsawa yana matsowa har taje jikin kofa daidai lokacin ya karasa matsowa kusa da ita kallon fuskarsa tayi yawani rankwafo jikinta, jikinsa yana gogar nata hatta numfashinsa akan fuskarta yake sauka, tunani tafara yi, yana yi mata kama da faisal sosai sai dai yafi faisal kyau, komai nashi ya tsaru sai kace shi yayi kansa dan kyau, to kodai shine tafidan? Duk yadda akayi wannan shine tafida mijina sannan kuma still dr din da ya dubani a asibiti tafada acikin ranta, hakika taji dadin kasancewarsa a matsajin mijinta amma kuma sai ta wanashi ta nuna masa kuskurensa na ciwa mahaifinta mutunci da yayi domin tana son ta nuna masa cewa iyayenta suna da martaba da kima a idonta, iska ya hura mata akan fuskarta take tajiyo wani kamshin strawberry me hade da splash ya fito daga bakinsa, ahankali kamar meyin rada yace kin gama gudun? Kallonsa tayi tadauke kanta tafara kiciniyar bude kofar motar amma bataga wurin budewar ba saboda tsananin tsaruwar da motar tayi, hannunsa mai mutukar laushi yasa yajiyo da fuskarta madam! Kijiyo kiji abinda zan fada miki, ko bakya ji? Well dama ni basai naji muryarki ba tunda nasan kina jina shikenan, nayi mutukar farin cikin kasancewarki mata ta hakanne ma yasa nayi alqawarin kyautata miki domin na nuna godiyata ga mahaifinki akan aura min ke da yayi, wannan dalilin ne yasa nima na himmantu har sai da kika samu lafiya tareda taimakon dan uwana, abokina, aminina faisal, wanda banida kamarsa aduniya, dam taji dama shine yasa faisal ya yimata dukkan abinda yayi mata? Shiru tayi tana sauraren taushashshiyar muryarsa tun da take bata taba jin muryar namiji mai dadi kamar tasa ba.


ALHERI DANKO NE!

4⃣7⃣

Na UMMI A'ISHA


    Mahaifinki yayi min alheri mai yawan gaske shiyasa nima na daura aniyar yi masa alheri ta hanyar sama miki lafiya domin shi ALHERI DANKO NE sai alokacin ta kalli fuskarsa idonsa tarr akan fuskarta, yatsina fuska tayi takawar da kanta, meyasa kika shiga cikin maza kika tsaya? Ko baki san ina kishinki ba? Shiru tayi bata bashi amsaba amma tajiyo takalleshi daidai lokacin da yake lasar lebenshi wanda ya kasance ja kamar ya shafa jan baki mai duhu, juya kanta tayi ta kalli window ahankali taji yakama hannunta yatsun hannunta ya zubawa ido fatarta bakace amma ga gashi nan kwance sai kace jikin namiji, kallon hannun nata yayi yai murmushi ai bakar mace tayi arayuwa dama shi can bakar mace yakeda ra'ayin aura, dayan hannun nasa yasa yafara shafa gashin hannunta, wani irin shock tafara ji amma sai ta maze, ahankali yace haka kike da gashin nan duk jikinki ko iya hannun ne? Sai alokacin tayi masa magana dubawa zakayi sai kaga, wani darr yaji acikin kunnensa saboda jin sautin muryarta.
[6:13PM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!


4⃣8⃣

Na UMMI A'ISHA


      Kamar wani sakali haka tafida ya zuba mata ido yana kallonta ashe tasan muryar ta tahadu shiyasa tatsaya ja masa aji sai da tagama yangarta sannan tayi masa magana, wani sanyin dadi yaji acikin ransa hakika hanfa tana daya daga cikin matan da Allah ya horewa baiwar murya zazzaka, kallonta yayi ya lumshe manyan  idonsa ya budesu akan fuskarta, kafar wandonta yakama yadago kafarta yadan janye shi sama nan yaga gashi kwance mamakine yakama hanfa shi wannan be san gatse ba, dan tace yaduba yagani shine zai duba din, hannunsa yasa yashafa kwaurinta nanma akwai gashin har cinyarki? Shiru tayi hannunsa yadauke daga kwaurinta ya ajiye kafar tata akasa yafara kokarin saka hannunsa acikin rigarta nanfa tayi caraf tarike hannunsa me zakayi? Cikinki zan duba naga ko nanma akwai gashin, to babu tafada tana buntsira baki, ni kika buntsirawa baki? Kefa kika ce dubawa zanyi sai nagani kuma ya zan duba zaki hanani? Bata bashi amsaba, kin san me nakeso dake daga yau kar nasake ganinki acikin maza kin gane? Buntsira baki tasake yi, yana ganin haka yakai bakinsa kan nata yahada yatsoti lebenta.


ALHERI DANKO NE!


4⃣9⃣


Na UMMI A'ISHA


    Bakinta ta kwace ta tofar da yawu tasaka bayan hannunta tafara goge bakinta wannan wanne irin kazanta ne haka? Tafada tana hararsa aranta kuma tana cewa wato kai ga mai mata ko shine harda wani biyoni school, kallonta ya danyi kyankyami na kike yi? Wannan abin ne kazanta? Zakiga kazanta kuwa wannan ba kazanta kika gani ba, yana gama fadin haka yajanyota jikinsa ya fara kokarin saka bakinsa cikin nata amma taki ta damke bakinta yanda bakinsa bazai shiga nataba, murmushi yayi wlhi ko ki bude bakinki ko kuma nayi maganinki yanzu, hannunshi yazira cikin rigarta ta baya bashiri ta yi magana, meye haka? Dan mitsitsin bakinta yakalla ga fararen hakoranta siri siri ajere gata da yar wishirya nan da nan yaji yawunsa ya tsinke, bakinsa yahada da nata yakama harshenta yarike yafara dura mata yawun bakinsa mutsu mutsu tafarayi tana tuttureshi amma yaki cikata, haka tarinka shanye yawunsa yana dura mata wani sannan yafara lasar harshen bakinta yana tandar lips dinta sai da yashafe samada minti 20 sannan yasaki bakinta, hannunta tasa akan bakinta tana tofar da yawu tuf tuf, dariya tafida yayi wadda har saida beautiful point dinsa yafito fararen hakoransa suka bayyana, yarinya zancen yaushe kuma ai kin riga da kinsha yawu na sai dai kiyi hakuri ki kiyayi gaba amma yanzu kan kin ga kazanta iya kazanta ko? Harararsa tayi mugu kawai, ni kike cewa mugu? Zakiga muganta yarinya.
[8:30PM, 11/19/2015] Ummi A'isha: ALHERI DANKO NE!


5⃣0⃣

Na A'ISHA (ummi)


Baki hanfa ta murguda kawai saboda tsabar kazanta zaka wani bani yawunka nasha, wannan ai kazanta ne, wani malalacin murmushi tafida yayi mata ai dan kinsha yawuna ba wani abu bane tunda zan zuba miki abinda yafishi ajikinki, wa? Allah ya kiyaye tafada tana harararsa tareda fara idonta wai nanfa ta kara saka tafida a wani yanayi, hannunta ya kama shidai hannunta yana burgeshi gashi da tsananin taushi kamar auduga ga laushi da tsantsi, farcenta yafara murzawa sannan yakai hannun bakinshi yayi kissing dinsa yasa dan yatsanta abakinshi ya fara lasar farcenta yana tsotsar dan yatsan, cike da mamaki ta kalleshi hannun hagun ne fa, to meye? Kece kike kyankyamina ni bana kyankya minki kanta takawar daka kallonsa, sai alokacin idonsa yakai kan agogon hannunsa dake daure akan tsintsiyar hannunsa karfe 6:20 har anfara kiraye kirayen sallar magrib sannan yawancin daliban dake harabar area classes din sun tattafi hostel sai daidaiku, dan yatsanta yadan ciza duk da taji zafi amma bata nuna masa ba, cire yatsan nata yayi daga bakinsa yace kije kitafi hostel amma ga zarah can nahango ta ki turo min ita, shiru tayi aranta tana cewa gaskiya kam kai dan sarauta ne ace magana tarinka yiwa mutum wahala kanata yimin magana kamar me yin rada kana magana dakyar,ni ummi A'isha nace dan hanfa bata san tafida bane amma ahakanma ita dakarfi yake yi mata magana, wani abu ya taba take kofar motar tabude, hannunta ya saki ba dan yasoba yace kitafi sai dasafe amma gobema zan dawo, bata bashi amsa ba tafice tanufi inda su zahara'u sulaiman suke tsattsaye tana zuwa tace zarah kije yana kiranki, dasauri xarah tatafi inda yake, tana zuwa yasauke glass din motar tafara gaisheshi, cikin sakin fuska ya amsa yace zarah ga amanata nan nabaki ki kular min da ita fiyeda yadda zaki kula dakanki, compliment card dinsa yamika mata ga wannan akwai phone number dina ajiki idan da wani abu sai ki kirani domin ita bazan bata phone yanzu ba.

1 comment: