Friday 14 April 2017

RAMUWAR GAYYA.. 47

*RAMUWAR GAYYA......💘*

_Love story 50,50_

*Fertymerh Xarah*

         &

*Ummy Aysher*


47

  Alhaji mukhtar yayi Saurin tsaidashi,

'karkaje ka raba wannan auren Abinda Allah ya rubuta ba Wanda ya isa ya hanashi, ko ba komai yarannan suna son junansu,

'idan mutum yayi ma ba dai dai ba, ka haqura kabarshi, ai *Alheri danqo* ne saka mashi da alherin kai kuma sai kaga kyakkyawar sakayya, kayi haquri kabarshi kabar komai ba komai ba abinda ya riga ya wuce ya tafi sai kubawa xuciyarku haquri amma Sam *Ramuwar gayya* bata dace da ku ba,

'kayi haquri yaya idan har nabar masu yarinyar sunci Lagona kenan, an karbemin budurwa an karbemin yarinya,

'Tun asali can ba matar ka bace, ai matar mutum kabarinsa, ya dubi yayan Ransa a bace,

*'Matar waye*? Sun dai ci amanata ne, kuma bawai ina son ta bane har ynxu kawai Ina so na rama abinda suka min ga yaron sune,

'Sam bai dace ba, Kada ka kuskura karaba wannan auren na khairi domin yaran suna son junansu, Kada ka shiga haqqinsu akan abinda basuda laifi akai, tunda baka jin magana kaje can kacigaba da gabar da kake da mahaifansa,

Abba ya sa Kai ya fice yana gunguni shi baiga abinda xai hanasa karbo yarinyarsa ba sai ya saketa,

Yana fita gidan motarsa ya shiga Ransa a bace kai tsaye Kano ya nufa, baisha wahalar neman gidan su mahaifin sawwam ba kasancewar yana da address ďin gidan.

Dad da Mami na xaune a falonsu lokacin suna tattauna Mgnr su Kan sawwam ne, yaga yaron ya daina xaman gida ina yake xuwa tunda ya bincika gurin aikinsa an tabbatar masa da lallai yana xuwa,

'Tace duk inda yake xuwa baxai wuce gurin abokansa ba kuma hakan yafi saboda xai rage damuwa sosai da kaďaici shi kaďai a ďaki,

'hakane ba laifi tunda yana xuwa gun aikinsa, sai a fara nema masa auren Rukayya kada abarshi haka ba mata,

Gaban mami ya faďi tun bata kai ga magana ba sai ga mai gadi ya shigo, ya gaidasu cikin girmamawa,

'Alhaji kana da baqo a waje, Dad ya dubesa,

'Waye shi,
'bai gayamin ba amma dattijo ne kamar irin mu,

'kaishi falon baqi... kodai shigo da shi nan ďin,

Maigadi ya fita da sauri bai jima ba sai gasu tare,

Suna haďa ido dad ya tashi da mamaki yana kallonsa, mami Kuwa kusan ruďewa tayi,

'me Kuma kaxo yi gidana?
'in banda ya'ta har akwai abinda xnxo yi a Wannan gidan naka,

Dad ya juya yana kallon mami data daburce kafin ya maida kallonsa garesa,

'wace ya'kuma, ko kayi batan kaine,
'wannan tambayar yaron ka ya dace kayiwa, ya'ta naxo abani a yau ďinnan, yaje ya sami guri ya xauna, jikin dad na soma rawa Ransa ya baci Kada xarginsa ya xama gsky sawwam yana tare da khairi ne,

A dai dai wannan lokacin khairi na kwance a jikin sawwam tayi matashi da cinyarsa,

'tashi mugani cikinnan ya qara girma, ta qara narkewa,

'wai kai kullum aka cema yake qara girma ne, kullum sai kace xaka duba kagani idan ya qara girma,

'tor shikenan gyara xn duba lafiyar cikin,

'yaushe Kuma ka xama likita bn sani ba,

'ni likitanki ne ai, barama kigani.... kafin tayi mgn ya kware rigar ya kara kunnensa a cikin yana saurare, kallonsa take cikin so da qauna kome yayi yana burgeta, sai ya dubeta da murmushi,

'kinji me yace....

Tayi far da ido cikin tsananin mamaki kafin tayi murmushi tana shafar fuskarsa,

'banda qarya sahibina, wata uku ne fa ko mutum bai xama ba,

Ya bata fuska alamar yayi fushi,

Tayi murmushi haďe da sumbatarsa a gefen kumatunsa,

'yi haquri gayamin inji, yaja hancinta yana kallonta da murmushi,

'baby abinci yake so abashi dan haka muje ďaki, ya soma qoqarin ďaukarta, taqi bari suna haka wayarsa ta soma ringing, yana ganin mamice ya sauke numfashi haďe da Kara wayar a kunnensa,

'kana ina ne?
'gida,
'kaxo ynxu tare da khairi,

Kafin yayi mgn ta tsinke Wayar, ya dubi khairi yana gayamata abinda mami tace,

'ko xa'a rabamu ne,
'bana tsammanin haka qila tayiwa dad bayanin komai kuma xai fahimce mu ne, tashi ki shirya,

Ta tashi a sanyaye ta nufi dakinta, duk shirinta ba kuxari a jikinta, hijab ta sanya fuskarta ba kwalliya ta fito, ya dubeta dai dai ya fito cikin nasa shirin,

'chab ina xaki bini a haka, sai kace wacce ke xaune cikin takura, yaja hannunta suka koma shi da kanshi yayi mata kwalliya harda Jan baki Kuma tayi kyau sosai, da kanta ta ďaura kallabi, yabata gyale yana kallonta tayi kyau sosai,

'Haba ko Kefa, xamu gaida surukai xakije da wannan shigar,

Ta rungumeshi tana murmushi kafin ta kai masa kiss yayi Saurin riqeta yana kissing ďinta sosai, sai da ya gaji dan kansa kana ya saketa,

Ga mamakinsa sai yaga ta turo bakinta a shagwabe,
'bai isheki bane? Ta make kafada tana nuna masa Jan baki akan mirrow,

Tayi murmushi haďe da shafa kansa,

'sorry dear, yaje ya ďauko ya qara sa mata kana suka fita daga gidan.

Tun a bakin gate gabanta yayi mummunan faďuwa ganin motar Abba, ta dubi sawwam dai dai lokacin da yake parking motarsa, ya kalleta yana faďin,

'menene naga duk kin tada hankalinki,
'motar Abba yaxo ya tafi dani ne, shima gabansa ya faďi,
'impossible, fito muje ba abinda xai faru, baxasu rabamu ba ina sonki,

Ta fito jikinta a sanyaye suka shiga gidan, nan Iyayen maxa suka hau faďa sosai kowa nayi kan yaronsa da faďa Kamar xasu dake so, kowane ransa a bace sai kumfar baki suke cikin tsananin fushi,

Khairi ce kawai ke kuka gurin, mami da sawwam kuwa bacin raine kwance a fuskarsu,

'ki tafi muje, kin gama xama dashi sai inga ynda xaixo ya qara ďaukarki,

Ga mamakinsu sai sukaga khairi taje gaban dad ta riqe qafafuwansa tana kuka,

'karka bari ya tafi dani, ina son sawwam dan Allah kada ku rabamu kabawa Abbana haquri,

A lokacin sai jikin dad yayi sanyi, tausayin yaran yakeji har cikin ransa, yayi shiru bai yi mgn ba,

Mami tace ba ynda xa'a raba aurensu, sawwam baxai saki khairi sai dai kaje da Ita tayi ta xama a gabanka, idan ta haihu ka maida mana yaron mu ka riqe yar'ka,

Sai sukaji mgnr wata iri banbarakwai  daga Abba har dad, khairi nada ciki kenan,

Abba yaxo a fusace ya fisgota, tana kuka take kallon dad aganinta shi kaďai xai iya cetonta,

'please dad.......

Abba sai janta yake, tayi saurin riqa hannu sawwam shima a ynxu hawaye yake, Abba ya juyo yana kallonsa,

'kai sake min yarinya bana son shashanci, ba musu sawwam ya saketa,

Tanaji tana gani Abba ya rabata da sawwam, ya sanyata a mota ya fice da sauri,

Sawwam ma ďakin sa ya nufa ransa a bace, ya bugo qofar ďakin ji kake gam kamar xai ballata....

'Dad yace duqawa wada baxai hana ya tashi ba, ni nayi masa laifi saboda ke, xnje na bashi haquri saboda yaran, suna matuqar son junansu,

'Mami tace sai muje tare a gobe kaga yarinyar nada ciki kar yaje ya salwantar dashi, munason cikin da farincikin sawwam,

'Nima haka nake tunani cewar dad.

Khairi Kuwa kuka take sosai acikin motar bai kulata ba har suka xo gidan, idanunta sunyi jawur luhu luhu da su,

Da gudu ta shiga cikin gida tana kuka, kukanta ya fito da mama daga kitchen anan ta sameta tsugunne riqe da cikinta sai amai take kwararawa kamar xata amayarda hanjin cikinta,

Mama sai sannu take mata cikin tausayawa yarinyar, taje ta kawo mata ruwa,

'sai dai ki mutu amma kin gama xama da wannan yaron cewar Abba yasa kai ya fice da sauri,

Khairi ta riqa ta tana kuka,
'mama ki taimakeni, mama kibashi haquri ya maidani inda sawwam,

Mama ta riqata suka shiga ďaki, yinin ranar komai bata ci ba har dare duk ynda mama tayi da Ita taqi taci komai, yayyunta maxa ma sai tausayamata suke suna rarrashinta taci taqi kasancewar ita kaďai ce Mace a gidan duk maxa ne shiyasa suke sonta,

Har goma na dare taqi taci komai, mama ta damu sosai sai taje ta gayawa Abba,

'ai ba'a fushi da abinci kibarta xata nemeshi dan Karan kanta ko dan cikin dake jikinta,

'cikine da Ita Alhaji? ta tambaya cike da mamaki,

'cikine da Ita wai injisu  Iyayen yaron, koma dai menene tagama aurensa, idan ta haihu xn kai masu abinda ta haifa shikenan,

Mama ta girgixa kanta kawai cike da takaici tabar ďakinsa wannan rayuwa dame tayi kama,

'ummu.. Ummu.. ta soma kiranta, can qasan maqoshinta taji ta amsa,

'tashi kici abinci ba dan niba sai dan abinda ke jikinki, bakisan xaman ki da yunwa xai iya janyo masa matsala ba, idan ya xube mijinki baxai ji daďi ba,

Khairi ta ďan dubeta tana share hawayen fuskarta,
'mama ni sawwam nake so,

'kici abinci tukunna xamuyi Mgnr,

'bana iya cin komai ynxu sai tea,
'shikenan bara na haďa maki,

Tea mai kauri ta haďa ta kawo mata ta bata,
'inbaki bread, ta girgixa kanta, biscuits fa, nan ma a'a, cake fa, ta yatsina fuska kafin ta girgixa kanta,

'haka xakisha ruwan tea bada komai ba ai baxai riqa cikin ki ba ummu,

'mama ya isa, tasa kai ta shanye tas, sai ga xufa na karyo mata sai wani ajiyar xuciya take, ta cire rigar jikinta,

'mama tace ko xakiyi wanka ne? Ta gyada Kai tana kallonta, mama da kanta ta haďa mata ruwan wanka taje tayi ta fito tana kallon maman dake xaman jiranta,

'mama bakuda ďan wake a gidannan?
'ďan wake ynxu ummu, Ina xn samu,

Khairi ta xauna tana yatsina fuska,
'mama kimin kona garin rogo ne kona flour,

Mama ta tashi tana faďin inaji kamar da akwai flour gidan bara na duba ingani, ni xama bai sameni ba tunda an haďa ni da lalurar Mai ciki ta fice....

Tana fita khairi ta dauki wayarta ta Kira Alhaji mukhtar cikin kuka take sanardashi duk abinda ya faru,

'kiyi shiru ki kwantar da hankalinki bai isa ya rabaki wannan auren ba, tunda ni har nayi masa mgn bai jiba Gobe xnxo da aminin babanmu nasan shi dole ya isa da shi,

Tayi godiya sosai xuciyarta fal da farinciki, ta kira wayar sawwam bata shiga sai ta ajiye wayar.

*

Washe garin ranar da sassafe Alhaji mukhtar yaxo gidan tare da wani dattijo aminin babansu suna kiransa da baffa,

Faďa sosai yayiwa Abba har sai da yayi danasanin abinda ya aikata,

Ana haka sai ga dad mami da sawwam,

Nan aka taru aka sasanta Iyayen bayan faďa da nasihohin da baffa yayi masu,

'a koda yaushe ka xama mai yafiya domin kaima a gurin Allah mai laifine,

Suka yafe juna tare da miqawa juna hannu suka gaisa haďe da rungume junansu cikin farin ciki, shekaru da yawa rabonsu da hakan,

Basu ankara da sawwam da khairi basa gidan ba sai da suka soma nemansu, tuni sun kama hanyar Kano sun bar Iyayen.......

*Pherty xarah*

        &

*Ummi shatu🏼*



My wattpad Phertymerh1

No comments:

Post a Comment