Sunday 26 March 2017

RAMUWAR GAYYA.. 39

*RAMUWAR GAYYA...... 💘*

_Love story 50,50_

*Fertymerh Xarah*

          &

*Ummy Aysher*

39

    Da sauri ta turesa, ta matsa baya haďe da tunxuro bakinta yayi dariya yana kallonta qasa qasa,

A fakaice ta juya tana kallon Abdul sai taga kwata kwata hankalinsa baya gunsu, ta maida kallonta ga sawwam,

'tor sai anjima,
'korata ma kike yi, lallai ma yarinyar nan, to jibi sai kihanani abinda naso ko ki korani daga gidan,

Ta juya tana murmushi tayi hanyar gida shima murmushin yayi yana kallonta,
'bako sallama ,ta juyo tana kallonsa,
'gobe da wuri xaka shigo ko, banaso ka bata lokaci,
'baxan ma bata ba dear, Inaso dinner ta qayatar...
'Allah yasa,
'yace Amin, sukayi Sallama da juna.

Washe garin Ranar ta Kama dinner, 

Amarya khairi tayi matuqar kyau sai kyalli take tamkar wata sarauniya, kalar fatar jikinta Mai kyau da sheqi, tayi kyau sosai cikin wata gown doguwa pink, an yane kanta da wani qaramin net shima , komai in pink daga cikinta hr waje, tayi matuqar kyau sosai,

Yayin da ango ke sanye cikin wani lallausan yadi Mai shara shara fari sol, yayi matuqar kyau sosai

Kallo ďaya xakayi wa sawwam ka sake marmarin kallonsa saboda haske da kwarjininsa ya dushe hasken Duk wani matashi Mai ji da kansa dake harabar hotel ďin,

Su Abdul ma ba'a barsu baya ba, cikin nasu anko sai waige waige suke Acikin abokan amarya ko xa'a dace....

Dinner tayi kyau ta qayatu anci ansha anyi raye raye harda amarya da ango,

Sanda aka tashi dinner ango yaja amaryarsa motarsa da kansa ya kawota gida, yana xaune a motarsa har ta shige gida kana yabar gurin, yana son khairi sosai ya qagu safiya tayi ta xama mallakinsa.

Daren ranar sun jima a waya, sun sha soyayya sosai baxasu manta wannan ranar a tarihin rayuwarsu ba domin sun amayarda irin qaunar da suke wa junansu,

Washe gari ta kama asabar ranar ďaurin aure,

Acan gidan alhaji mukhtar xa'a ďaura auren, shiyasa suka dunguma acan,

Ango yasha manyan kaya cikin farar shadda harda babbar riga da hula, anko sukayi da Dad,

Mami ta dube su da murmushi,
'kunyi kyau, Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy, suka amsa da Amin, sawwam ya sumbaceta yana faďin,

'khairi will be part of us mami K......
'karka tsaya gurin surutu lokaci na tafiya ga dad ďin ka harya fice,ya fita da sauri yana dariya,

Sun iso gombe kai tsaye gidan baba mukhtar suka nufa, yayi ta kiran wayar khairi tana ringing bata ďauka ba, xai sanarda ita xuwansu ne, daga qarshe ma sai yaji wayar switch off,

Bai kawo komai a ransa ba yacigaba da amsar wayar friends ďinsa masu taya sa murna, yana tare da dad yan uwansa suka fara isowa,

Suma su Abdul tuni sun iso da tasu gayyar, yauma anko suka sha abokan 3 pointers,

Wuri ya taru, jama'a sai son barka, mutane kamar da bakin kwarya sun hallaro bikin sawwam da khairi, kowa na gurin bnda mahaifin amarya, sai suka tsaya jiran isowarsa,

Mutane sun soma damuwa ďaurin aure nason xama lalura Abinda ya kamata ayi tun ďaxu Gashi kusan awa ďaya da xuwa baa daura auren ba kuma har lokacin Abba bai xo ba,

Kowa gurin ya damu bama kamar sawwam, hankalinsa ya soma tashi Allah yasa lfy Gashi ya Kira Wayar har lokacin switch off.

*

Khairi xaune hannuwanta da suka sha qunshin baqin lalle da surkin ja akan fuskarta,

Kuka take sosai gwani tausayi, kuka take Kamar ranta xai fice daga jikinta, a halin da take ynxu gwanda mutuwarta  da rayuwarta dan baxata iya rayuwa batare da sawwam ba,

Mama ma cikin damuwa da halin da yar'ta take ciki ta dubi Abba,

'wannan hukunci Sam baiyi ba alhaji, bai kamata ka hukuntar da ummu ta wannan sigar ba, amma meyasa baxaka haqura kabarsu ba tunda suna son junansu,

'saboda *Ramuwar gayya* nayi wannan so bnga dalilin ki na sanyo bakinki acikiba, kinfi kowa sanin meke faruwa Kuma kinfi kowa sanin dalilina nayin haka,

'ummulkhairi baxata auri sawwam ba, faruq xata aura kuma dole xata min biyayya ynxu xnje can a gudanar da komai,

Jin kalaman sa ya Sanya khairi fashewa da wani irin kuka, idanunta sunyi jawur sosai ta dawo gabansa ta tsugunna haďe da riqe qafafuwansa,

'Dan girman Allah Abba kayi haquri ka tausayawa rayuwata, na kasance mai biyayya agareka Abba, na cika ma burinka nayima biyayya kabarni da Wanda nake so, shi kaďai nake so Abba baxan iya rayuwa da wani namiji idan ba sawwam ba, bana son faruq Abba ka tausayamin,

Ya janye qafarsa a hankali yana kallonta,

'Kinsan ina son ki ummulkhairi, kinsan baxanyi Abinda xai cutar dake a rayuwarki ba, kin kasance mai biyayya agareni shiyasa xn xaba maki miji dai dai rayuwarki, faruq shi kaďai xai iya riqeki amana yana son ki khairi kema ki koyi sonsa domin shine uban Ya'yan ki,

'Abba sawwam ma yana sona xai iya riqeni amana, wlhy baxai cutar dani ba, maminsa ma tana qaunata Abba, karka raba soyayyar mu Abba, ka cika min burina na kasancewa da sawwam kamar yanda na cika maka naka burin,

'idan na kasance mai laifi a gareki ummulkhairi to Kiyi haquri amma baxaki auri sawwam ba yasa kai ya fice da sauri, ta durqushe gurin tana kuka Kamar ranta, mama ma tausayinta take,

Mutane sun soma gajiya wasu har sun fara qorafi da yawa suna da abinyi gurin, wasu Kuma nesa suke, wasu Kuma suna da wani ďaurin auren shiyasa suka qagu, barin ma kamar dad daxai bar qasar gabaki ďaya ya dubi baba mukhtar,

'Alhaji ai gurinka Muka xo neman aure Kuma kai kabamu yarinya, kaine waliyinta kai Yakamata ka ďaura mata aure tunda mahaifinta baya kusa kowa nan gurin ya qagu wani ba'a San uxurinsa ba,

'hakane, tor bara a ďaura......

Nan take aka daura auren sawwam da khairi, dai dai lokacin Abba ya iso gurin, da sauri ya fito cikin motar ya soma kutsawa cikin dimbin mutanen dake gurin,

Suna haďa ido da alhaji mukhtar abinda ya tambaya,
'Kada dai an ďaura auren ne? Sawwam kaďai ya lura da xuwansa dad nacan na gaisawa da mutanen sai dai yanayin da ya ganshi ya tabbatar masa ba lfy,

'eh an ďaura yaya saboda mutane sun gaji da.... ya katsesa a fusace Wanda ya janyo hankalin jama'a harda dad xuwa garesa,

'amma meyasa xakamin haka, nikeda haqqin auradda ita, dole ya sakarmin yarinya ynxu,

Xuciyar sawwam ta buga ya xare ido yana kallonsa kome ya faru yayinda gurin yayi tsit,

'dad ya dubi sawwam,
'Kada dai wannan ne mahaifiyar yarinyar da kake aure sawwam? Jikin sawwam ya ďauki rawa yana kallonsa ya gyada kansa,

'baxai yiwu ba, ai tun farko danasan shine mahaifinta baxaka neme ta ba, wannan auren Kuwa xa'a warwareshi ynxu,

Sawwam ya tashi tsaye idanunsa sun sauya Kala,
'why dad? wai meke faruwa ne?
'you must divorce her sawwam,
'I can't dad, Ina sonta and you know it...... Bai qarasaba ya ďauke sa da Mari,

Mutane suka shiga ruďani abin ya ďaure masu kai, su Abdul suka matso jikinsu a sanyaye suka riqe sawwam dake dafe da kuncinsa yana kallon yanda faďa ya qaure tsakanin mahaifinsa da mahaifinta, miye tsakaninsu Ina suka San juna?

Sabon al'amari ne Wannan ga dimbin mutanen dana xo ďaurin aure gurin, musamman ganin mahaifin ango da mahaifin amarya suna faďa Kamar xasu cinye junansu,

Sawwam ya fita gefe ya Kira mami yana sanarda ita, kuka yake sosai yana roqonta ta taimaka masa baxai iya rabuwa da khairi ba.......

Sosai hankalinta ya tashi to meke faruwa meya janyo fitinar, ta tsinke Wayar da sauri dan baxata jure jin kukan sawwam ba, ta soma qoqarin nema layin dad da jin meke faruwa,

Yana ganin kiranta baxai iya ďaga wayar ba kasancewar hankalinsa baya jikinsa, kallo ďaya xaka yiwa Iyayen biyu ka gane suna cikin bacin rai sosai na tsawon wasu shekaru da suka shuďe a baya,

Manyansu tsofaffi suka sanya baki,

'yace lallai sai an sakar masa yarinya,

'dole ma xai sake ta saboda muma bamu buqata,

'ya saketa ynxu xa'a ďaura mata aure da Wanda ya dace faruq,

Dad ya dubi sawwam,
'ka saketa ynxu xn ďaura ma aure da wacce ta dace Rukayya,

Hankalin sawwam ya tashi Cak numfashinsa na ďauke ya xube gurin a sume....



*pherty xarah*

         &

*ummi shatu 🏼*



My wattpad Phertymerh1

No comments:

Post a Comment