Saturday 4 March 2017

RAMUWAR GAYYA.. 9

*RAMUWAR GAYYA..*💘

_Love story 50,50_

   *_UMMI A'ISHA_*

          _With_

_*PHERTYMERH XARAH*_

  *_9_*

*D*riving yaci gaba dayi zuciyarshi tana hasko masa hoton ummulkhair lokacin da ta mareshi,

"Lallai yarinyar nan.." Yafadi hakan acikin zuciyarsa,

"Wai yanzu ni ta mara? Idan na kyaleta shikenan ta mari banza kenan...? Kai impossible wallahi,dole sai na rama wannan rashin mutumcin da tayi min.." Yafadi yana shafa sumar kanshi,

Da tunaninta ya samu ya isa gida, koda yaje gidan kin shiga wurin Mami yayi yawuce dakinshi saboda baya son taga shatin yan yatsun ummulkhair dake zane akan kuncinsa,

Wuni yayi acikin daki har sai da yamma tayi sannan yafito lokacin shatin dake fuskarsa ya dan goge.

  Ummulkhair hostel ta wuce kai tsaye taje ta bude dakinta ta shiga ta kwanta nan ta fara kuka sosai, ta rasa meyasa sam bata da juriya akan wulakancin sawwam, gashi dai ita kanta fadan nasu ya soma isarta amma bata son ta kyaleshi yayi nasara akanta, tafi son suyi tayi har shi da kansa ya gaji ya sallama mata,

K'arar da wayarta keyi ne ya katse mata kukan nata, babu shiri ta tashi ta dauki wayar bayan ta hadiye kukan da take yi saboda ganin mahaifinta ne me kiran,

Sakin fuskarta tayi suka gaisa tamkar babu abinda ke damuta, sai da ya jaddada mata cewar ta dage tayi abinda ya turota sannan ya hadata da mamanta suka gaisa, kasancewar yayunta duk suna gida lokacin suma sai da suka gaggaisa sannan suka yi sallama,

Hakuri tayi ta daina kukan taci gaba da abinda ke gabanta,koda suka hadu da alawiyya ma bata yarda ta sanar da ita fadansu da sawwam na jiya ba,sannan tun daga lokacin bata sake sakashi acikin idonta ba har tsawon kwana biyu, gashi kullum hijabi take sawa har kasa da nikab ta rufe fuskarta,

Sai dai shi sawwam duk inda ya hangota yana ganeta haka kawai ya rasa dalilin da yasa daga ya ganta zai san itace.

Tafe yake shida abokansa sun nufi filin kwallo wanda ke cikin makarantar, yasha jar riga mai gajeren hannu da wando jeans blue, kasancewar yammaci ne yasa ko ina ka hanga dalibai kake gani kowa yana sha'anin gabanshi, wasu na hira wasu na karatu,

Zaune ya hangota a kan wata kujerar karfe dake girke a kasan wata bishiya, tana sanye da blue din hijabi har kasa da nikab a fuskarta hannunta rikeda lecture note da alama karatu take yi, tabbas ya gane itace sai dai ita Sam bata zaci cewar ya ganeta ba,

"Hello guys, ku bani 2 minutes kuyi gaba zan taho, bari naje neman fad'a..."

Bai jira amsarsu ba juya ya nufi wurinta,kanta yana sunkuye tana duba lecture note dinta ya karasa wurin,

"Mtswwwwww" yaja dogon tsaki yana kallon kafarta,ba karamin kyau kafar tata tayi mishi ba domin faratanta gaba daya sunsha jan kunshi,

Bata ko daga kanta ta kalleshi ba taci gaba da karatunta,

"Ke...! Zuwa nayi na sanar dake kan ki shirya karbar rashin mutuncina ako wanne lokaci domin wallahi kinyi kadan ki mareni na rabu dake, tunda nazo duniya babu wanda ya taba marina sai ke..., to wallahi sai na shuka miki gonar rashin mutunci so get ready" yana kaiwa nan ya juya ya wuce yana fito da bakinshi,

Bayanshi tabi da kallo tayi murmushi, "ko me kake ji dashi to a shirye nake domin nima ina ji dashi" ta fada ahankali.

  Kwana uku da faruwar wannan al'amari ummulkhair suka nufi wurin yin photocopy itada alawiyya, sawwam yana kallonsu kuma duk da cewar ta lullube fuskarta to ya ganeta,

Gaba daya hankalinsu ya tattara kan lissafin adadin lecture notes din da za ayi musu gefe kuma wasu yanmata ne wurin su biyar suma suna jira ayi musu, daya daga cikin yanmatan ne wayarta ta fadi ba tare data sani ba kuma akayi Sa,a babu wanda ya gani, sunkuyawa sawwam yayi ya dauki wayar ya wuce, a kusa da ummulkhair ya tsaya yana yiwa mai shagon magana, sam bata luraba ya jefa mata wannan wayar acikin jakarta,

Juyawa yayi ya koma gefe can nesa ya jingina ya tsaya yana kallonsu, yana kallo wannan budurwar ta fara neman wayarta amma bata samu ba nan aka soma dube dube, wata wayar ta karba ta kira layinta take wayar ta dau kara daga cikin jakar ummulkhair wacce sam ita bata ma san abinda yake faruwa ba,

Kanta yanmatan suka iyo, "sannu barauniya daga zuwa shine zaki dauke mana waya? To Allah ya toni asirinki..."

Wata daga cikin yanmatan tafada, cikin rashin fahimta ummulkhair ta jiyo tana kallonta,

"Meya faru?" Alawiyya ta tambaya,

"Wayarmu ta sace gata nan tana kara acikin jakarta..." Kafin alawiyya ta sake magana har sun fusge jakar sun ciro wayar, daga alawiyya har ummulkhair kasa magana suka yi nan yanmatan suka hau zagin ummulkhair suka yi mata tatas mutane na tsaye suna kallonsu,

Jakarta ta dauka tana hawaye ta nufi hanyar barin wurin,

"Hy barauniya, ashe dama ke barauniya ce?? Even though kin saba satar kayan mutane...."

Taji magana daga bayanta tana juyawa taga sawwam ne yana yi mata murmushi...

Ummi Shatu
Pherty..

No comments:

Post a Comment