Thursday 30 March 2017

RAMUWAR GAYYA.. 45

*RAMUWAR GAYYA...... 💘*

_Love story 50,50_

*Fertymerh Xarah*

         &

*Ummi Aysha*

45

      Tana fitowa ta soma waige waige ba Abba a waje, ta fice da sauri,

Inda ya saba ďaukarta anan suka haďu, ta shiga motar suna kallon juna sukayi murmushin farin ciki kafin suja motar,
Sai da suka biya yayi masu take away na abinci kana suka nufi masaukinsa,

Bayan sun gama cin abincin ya dubeta ,

'Dad ya gano bn sake ki ba, ya matsamin ko ya yafeni, miye mafita?

Tayi shiru tana kallonsa, shima ita yake kallo,

'ko xamu gudu ne?
Tayi Saurin girgixa kanta,
'a'a Abba xai iya yafeni,
'nida xnbar nawa mahaifin fa, ko kin fison kullum nayita xarra akan titi,
'nida ke jure duka saboda kai fa,
'wake dukan ki,
'Abba mana, ta nuna masa tabon bulala dake hannunta, ya dubeta,
'saboda me xai riqa dukanki, ni ba mijinki bane?

tayi shiru tana kallonsa,
'nifa nagaji da wannan takura xamu gudu,

Jikinta ya fara rawa tana tsoron ta gudu tabar iyayenta batasan halin da xasu shiga ba Kuma baxata iya bijirewa sawwam ba,

'kasan bnda waya ynxu, da kyar nasamu na fito ka maidani tun abba bai dawo ba,
Yayi mata kallo kasa kasa yana harararta,
'kin ma isa, tun yanxu, ok guduna ma kikeyi,

'kayi haquri,
'alqawarin mu mekikace xaki bani idan naxo,
'komai fa, kabari ka sake dawowa,
'saboda kin raina min da wayo ko? baki isa ba kafin tayi mgn ya janyota xuwa qirjinsa, jikinta ya ďauki rawa sai ta qanqame jikinta guri ďaya,

'wai me kikeyi haka ne khairi? am your husband ko xn cutar dake ne, beside ma kinsan baxaki bani ba meyasa kika kwadaitamin a waya?

'Dan Allah kayi haquri har na tare bana so a ynxu, don't mean to hurt you.... ga mamakinsa sai ya ganta tana hawaye,

Ko khairi bata lfy ne shi baiga matsala anan da xatace sai sun tare ba, yaushe tarewar ma, ko xai xuba ido yana ta kallontane, matsalar ďayace ace basuda aure amma kowa ya Shaida matarsace, ya tashi a harxuqe batare da ya kalletaba ya soma xira takalminsa yana faďin,

'tashi na maidaki gida,
taqi tashi sai ma kuka da take tana bashi haquri, tafiso harta tare xatafi mutunci a idanuwansa, ya daka mata tsawar dana firgitata ba shiri ta tashi da gyalenta a hannu,

Kafin ta fito tuni ya shiga motarsa, tun bata qarasa shiga motar ba yajata da qarfi, ta juyo tana kallonsa fuskarsa a murtuqe take sai taji tsoro,

'kayi haquri please,
'enough please bana son damuwa, daďin abin inada yan mata abinda kike taqama dashi kijiqa kisha,

Gabanta yayi mummunan faďuwa, hankalinta ya tashi,
'karkaje inda wata, zina ba kyau,

Wani mugun kallo yayi mata,
'tor waye sanadi.... xatayi mgn ya katseta a harxuqe,
Nace karki dameni please,

Tayi shiru xuciyarta kamar xata tsinke, sai hawaye take sharewa akai akai yana kallonta ta gefen idanuwansa bai damu ba,

Isowarsu Unguwar yayi dai dai da dawowar Abba daga asibiti yaje nemanta bai sameta ba, yana tsaye yaga motar sawwam murmushi kawai yayi yaran sun raina hankalinsu,

Ganin Abba hankalinta ya tashi ta juyo tana kallon sawwam shi baima ganshi ba, kuďi ya ďora mata akan cinyarta batare da ya Kalle taba,

'Dan Allah kayi haquri...
'please get out,
Jikinta a sanyaye ta ajiye masa kuďin gefen seat ta fito daga motar, yaja motar da qarfi yabar unguwar sai ta kasa karasawa gida ta tsaya suna kallon kallo da Abba,

tana tsaye taga Nafi'u ya fito da trolley ďinta ta kaya ya Sanya cikin motar Abba,

Da hannu yayi mata alamar taje ta shiga motar, ba gardama kai tsaye ta nufi motar xuciyarta na bugawa,

Abba da kanshi yaja motar suka bar unguwar batasan inda xasu je ba tana ganin sun ďauki hanyar gombe hankalinta ya tashi ta juyo tana kallonsa amma ba fuskar mgn, ta maida kanta jikin cinyoyinta tana kuka sosai Kamar ranta,

Shikenan an rabata da sawwam gashi yaje yana fushi da Ita, matsalarta ynxu sun kusa resuming Skul batasan isalin karatunta ba,

Sanda suka iso gombe Alhaji mukhtar baya gida sai yabar sallahu ga matarsa umma akan Kula da khairi, ba Ita ba waya Kuma Kada abari ta kuskura fita daga gidan ko lalurar mecece, batasan kowa a gombe ba batada qawayen da xataje garesu, yasa kai ya fice a harxuqe sai kuka take,

'umma tace wai har ynxu ba'a daidaita wannan auren ba?

'yaqi yarda umma, ina sonsa yana sona, mama ma ta amince dashi Shikadai ne bnsan ya xnyi ba,

'wannan auren ai baxaa rabashi ba, dole xa'a sasanta tsakanin Iyayen, fadansu ma shiryen banxane Abinda ya wuce ya riga ya wuce kawai a yafi juna duk da mahaifin sawwam ďinne yaci amana,

Bayan sati biyu khairi ta dawo wata iri gatanan dai ba fasali duk ta rame abinci ma bataci sai dole idan umma ta tursasata matsalarta sawwam har ynxu fushi yake da Ita yaqi ya saurareta idan ta sami waya ta kirashi dayaji muryarta xai tsinke,

Ynxuma tana kwancene tana kuka bayan umma ta gama yi mata Faďan damuwar da take sanyawa a xuciyarta,

Wayar umma ta ďauka ta kirashi, yana xaune yana ganin kiranta yaqi ďauka, duk da shima juriya kawai yake amma yana tsananin buqatar ta,

Karo na biyu da ta kira ya ďauka sai dai baiyi mgn ba, sai ta fashe masa da kuka, sosai yaji tausayinta musamman dayaji tana bashi haquri, sai yaji wani iri ba daďi,

'is ok na haqura shikenan,
'kaxo ka ďauke ni na yarda xn bika,
'da gaske?
'Ina gombe Abba ya kawoni tun ranar da kaxo, ko ina bana fita a takure nake kaxo kaje dani mu gudu,

'kibari xnyi wani plan ynda abin xaixo da sauqi, a gidan wake son xamana dake,

'Duk suna so, har Alhaji baya goyon bayan Abba amma umma tafiso,

Yace tor ki kaimata waya ynxu xamuyi mgn, ba musu taje ta kai mata,

Sun jima suna waya yanda xasu bullowa Al'amarin daga baya ya tsinke Wayar, umma ta kalleta,

'kishirya kayan ni banaso ana raba ma'aurata ballantana irinku, sawwam xai turo qawayensa gobe da motoci axo a daukeki xa'a gayawa Alhaji daga abbankine shiya turo, kinga kafin mgn ta fito qila komai ya daidaita,

Khairi ta soma murna sosai ta rungume umma tana godiya itama umma taji daďin yanda taga khairi a yau,

Sawwam Kuwa mami ya kira yayi mata bayanin komai kuma tabashi hadin kai 100% baxasu gayawa dad ba,

Dama gidan su a shirye yake olready tun kafin aurensu akayi mata jere, yaje yasa aka share gida tare da qara tsabtace shi,

Washe gari su Abdul sukaje gombe suka daukota Alhaji baisan komai ba sai yayi mata nasihohi sosai kana suka fice ko kaďan baiyi tunanin kiran Abba ba to sunce shiya aiko aje da ita,

Koda suka isa Kano ana magrib sukaje gidan suka ajiye ta suna mata tsiya,

Sawwam Kuwa wanka yayi ya ďauki Abinda yake buqata masu muhimmanci a gidan yaje ya kai a motarsa,

Mami tabashi abinci ya kaiwa khairi yaje ya Sanya a mota,

Sai wajajen 9 dad ya shigo gidan, sawwam na ganinsa ya tashi xai fita,

'Ina xakaje ynxu da dare, ya bata fuska batare da ya Kalle sa ba,
'xnje gidan abokaina, yasa kai ya fice, dad yabisa da kallo ya lura yaron na fushi da shine, mami na tsaye tana kallonsa,

Yana isowa gidan yayi horn Mai gadi ya buďe masa ya shiga, parking yayi ya fito da kayan ya nufi cikin gida,

Sai ynxu yake ganin gidan yayi masa kyau ba kamar kullum idan ya shigo ba, har wani qamshi falon yake yi masa, ya duba bata falon, sai ya ajiye abincin anan falon ya nufi ďakinsa da sauran kayansa, ya sauya kayansa xuwa na barci,

Yana fitowa yayi ďakin ta, tana xaune tana duba wata jarida da Suhaib ya bata wai xata ďebe mata kewa kafin yaxo, tana jin sallamarsa ta ajiyeta gefe, ta amsa sallamar tana kallonsa,

'oh ashe haka khairi sa ta koma, duk tayi rama, sai ya ware mata hannuwansa alamar taje ba musu taje a kunyace ta faďa qirjinsa ya rungumeta sosai tamkar xa'a kwace masa ita,

Sun jima ahakan kafin yajata xuwa toilet arwalla sukayi sukaxo sukayi sallah domin godewa Allah, sun jima suna adduo'i kafin ya dubeta,

'Abinci na falo kije kici inji mami,

Ta girgixa kanta tana kallonsa,

'na qoshi,
'me kika ci?
'Hafiz ya kawo min abinci daga gidansu,
'Kice abokaina sunyi hidima, Allah ya saka masu,
'Amin ta faďa a kunyace,

Lokaci ďaya suka tashi tayi falo yana bayanta, abincin ta ďauka taje ta sanya a fridge gudun kar ya lalace, ya riqa hannunta suka nufi ďakinsa bayan sun kashe komai,

Yau ma qanqame jikinta tayi a tsorace take dashi ynda taga jikinsa na rawa akanta ba kamar ynda suke haďuwa a hotel ba, sai taga yau yafi xumudin ta har wani rarrashinta yakeyi cikin muryarsa mai sanyi,

Tana jin lokacin da ya haďa bakinsa da nata haďe da xira hannayensa cikin rigarta, ta rumtse idanuwanta...........

Asuba ta gari🏻



*Pherty xarah*

       &

*Ummi shatu*



My wattpad Phertymerh1

4 comments: