Thursday 30 March 2017

RAMUWAR GAYYA.. 43

*Ramuwar gayya...... 💘*

_Love story 50,50_

*Fertymerh Xarah*

          &

*Ummy Aysher*


43

Qarasowar su da mai napep yayi dai dai da qarasowar Abba,

Da sauri ta baiwa mai napep ďin kudinsa tayi cikin gida jikinta na rawa,

Tun a waje yake kwala mata Kira, tana jinsa bata amsa ba har ya qaraso, mama na jinsa ta fito,

'Uban Waye naga ya ajiyeki bakin titi,

'yayan maryam ne, xasuje kasuwa da budurwarsa shine ya ajiyeni acan na qaraso, dama Muna can tare a asibiti,

Ya sauke ajiyar xuciya kana ya juya da sauri, Numfashi taja haďe da lumshe idanuwanta,

'God save me....

'ya Mai jiki mama ta tambayeta,

'Mai jiki da sauqi, tayi cikin ďaki da sauri, kayanta ta soma cirewa kana ta shiga toilet domin watsa ruwa,

2 days~

Ranar da sawwam ya dawo sai da ya tsaya a inda suka saba haďuwa, ya kirata a waya,

Ta duba Abba yaje masallaci mama Kuwa ta shiga sallah, ta ďauki takalminta saďaf saďaf ta fice da sauri taji daďin da ko yayyunta bata gani a hanya ba,

Tana xuwa ta shiga motar tana sauke numfashi, ya kalleta,

'gudu kika yi hala?
Tayi far da ido tana kallonsa,

'wane irin gudu kuma sai kace yarinya,
'ai bakida Banbanci da yarinya naga sai maida Numfashi kike,

Ta janyo hannunsa ta ďora kan qirjinta,
'kaji ynda xuciyata ke bugawa, ina tsoron Abba ya ganni ne, ranar fa yaso ya gane sai da ya bini a baya,

Ya janye hannunsa yana kallonta,
'ni ai naganshi tare da wani tsaye, ban gayamiki ba Kada hankalinki ya tashi nasan ki da tsoro, da fatar bai taba min lfyr jikinki ba, ya faďa yana tattaba jikinta,

Ta girgixa kanta tana kallonsa,

' bana son abinda xai sami wannan jikin ki kula da shi sosai,

ta gyada kai tana kallonsa,
Yasa hannun ya mintsini bakinta,

'shi bakin baya mgn ne, sai dai kita gyada kai kamar kurma,

Ta tunxuro bakin cikin jin xafin mintsinar da yayi mata,

'oh sorry dear da xafi ko? nan ma gyada kai tayi,

Ya janyota sosai xuwa jikinsa, a hankali ya xira harshensa cikin bakinta, a Yanxu ta soma sabawa da wannan itama sai ta shiga maida masa martani, sun jima a hakan kafin ya saketa, ya gyara mata hijab ďinta ya qara haďa fuskarsa da tata,

'Ina son ki khairi, ta lumshe idanuwanta xuciyarta nayi mata sanyi, itama tana jinsa har cikin ranta,

'Yanxu idan ka tafi Kuma sai yaushe xaka dawo?
'I don't know too, duk ynda hali yayi,
tayi shiru tana kallonsa, yaja hancinta,
'kinaso na dawo da wuri ne? ta gyada Kai tana kallonsa,
'kimin Abinda xai sa nadawo gobe ma,
'Tace menene,
Ya matsa yayi mata raďa a kunne (na tabe bakina Ina kallon Ummi Aysha)

Rufe fuskarta tayi da tafin hannuwanta tana murmushi,

'kin amince? Ta girgixa kanta, shima murmushin kawai yayi,

Sun ďauki lokaci suna hira kafin yabarta ta tafi, sai da yaje gidansu maryam suna tare sai ga qaninta yaxo nemanta gidan ba shiri suka fito,

Sanda taga Abba a bakin qofar gida sai da gabanta ya faďi,

'kai Nafi'u Ina ka sameta?
'gidansu maryam na ganta,

Ga mamakinta baice komai ba ya juya cikin gida, ta sauke numfashi tabi bayansa.

Tana shiga mama ta soma mata faďa sosai akan yawan fitar da take a ynxu Wanda ada batayi,

Abba ma yasa bakinshi, tanajinsu bata tanka ba, batada matsala a ynxu tunda taga sahibinta koma menene suyi tayi,

Abinci taje ta diba kitchen tadawo tsakar gida tana ci, yanayinsu da sawwam take tunawa sai faman murmushi take ita kaďai a tsakar gida, tana haka wayarta ta soma ringing, tana ganin shine tayi Saurin karata a kunneta,

'badai ka isa ba,
'Nooooooo na tsaya hotel ne gobe xn qarasa, hope kina lfy,
'lfy kamar ynda kake,
'kinsan yanda nake kuwa, Ina matuqar buqatarki a kusa dani, ta juya tana waige waige bakowa,

'kayi haquri watarana muna tare har xaka gaji dani,
'baxan gaji da ke ba bakisan ynda nakejin ki a xuciyata bane,
'I feel what you feel, kayi haquri,
'haquri idan nagaji da yinsa xnxo na ďauke kine mu gudu,

Fitowar Abba yasanyata yin shiru jikinta na soma rawa,

'baxaki bini ba shiyasa kika min shiru, tayi Saurin cewa
'A'a qawata baxan xo ba ke kixo gobe sai ki tayani haďa kayana, ni hr ynxu bnsan matsayina ba mai aure ko marar aure,

Abba ya juyo yana kallonta har xaiyi mgn sai Kuma yasa kai ya fice,

Ta sauke ajiyar xuciya, taji sawwam na dariya
'dariya ma kake shikenan,
'ni xaki maida Mace saboda Abba ne ko mama,
'Abba ne,
'OK we talk later xn shiga wanka......

Bayan sati biyu basu qara haďuwa ba olways suna kan waya, tun lokacin bata qara fita ba ko qofar gida ma bata xuwa, sai Abba ya qara yarda da Ita yasan baxata iya cin amanarsa ba,

Ranar da sukayi waya ya gayamata xaixo, tayi shirinta ta feshe jikinta da turare Mai sanyin qamshi kana taje inda Abba,

'Abba xnje duba Farida ta haihu gobe suna baxan iya shiga taro ba saboda bakin mutane,

'yace hakane ummu, yasanya hannu a aljihunsa ya ciro kuďi yabata,

'Gashi sai kibawa Mai jego ko, ta karba tana godiya kana ta tashi ta fice da sauri,

Hotel ďin daya sauka nan suka nufa, sunyi planning yanda xasu gudu idan Iyayen sunqi saukowa, sun sha soyayya kamar kada su rabu,

Yaxo maidata sunyi Sallama kenan ta fita motar, yana kallonta ta baqin glass ďin motar tana tafiya, sai ya sauke glass ďin da sauri ya Kira sunanta, duk akan idon Abba yana hangosu daga inda yake xaune,

Tana juyowa ta saki murmushi, yayi mata kiss a tafin hannunsa ya hura ta iska xuwa gareta,
'I love you....
'Love you too muah ta tura masa itama,

Yayi murmushi ya maida glass ďin motar kana ya fice xuciyarsa cike da farinciki,

Hankalin Anna yayi matuqar tashi, yaushe khairi ta xama yar iska, bama Wannan ba yaushe ta fara masa qarya tun yaushe ma suke haďuwa da wannan yaron? ya tashi yabita da sauri,

Tana shiga gida gyalenta kawai ta ajiye, ba xato ba tsammani ta soma jin duka ta ko ina ajikinta,

Da waya yake dukanta sai ihu take, mama taxo da sauri ta kwace ta hannunsa,

'metayi kake dukanta haka, idan kajimata ciwo da wannan bulalar fa?

'gwanda na jimata ciwo da ta kunyatani idon jama'a, Ashe bata rabu da wannan yaron ba, tun yaushe kuke tare Ina kuke haďuwa ne,

Khairi ta boye bayan mama tana kuka tana duba jikinta, bulalar harta kwanta mata,

'Haba Alhaji ya kamata a sassautawa yarannan haka tunda suna son junansu, laifin iyaye bai kamata ya shafe su ba, badasu xakayi *Ramuwar gayya* ba tsakaninku Iyayen,

'ke kimin shiru kina Goyon bayanta ne tor wallahi daga yau karna qara ganin qafarta a waje, ba qawarkiba ko qanwar uwarki taxo nan kika rakata bakin gida sai ranki ya baci ballantana kije ganin mai jego, shashashar banxa kawai,

Mama tayi shiru amma kalamansa sun mata xafi, har xai fita ya juyo yana kallonta,

'bani wayarki nan, ba musu ta miqa masa jikinta na rawa, ya fice sai mamakin abinda idonsa ya gane masa yau yake, idan labari aka xo masa baxai yarda khairi xata iya haka ba, ya yarda namiji shike bata Mace, tunda gashi khairi bata masa biyayya ta koyi yimasa qarya hartana bijire masa duk saboda ďa namiji,

ďakinsa ya nufa ya sami takarda da Biro yayi rubutu akai kana ya fito yabawa ďaya daga cikin ya'yansa yaje ya kaiwa mahaifin sawwam,

Wasiqar bata samesa ba sai a Washe garin ranar ,

Yayi mamakin da jin wai sawwam bai saki khairi ba gashi har mahaifinta yana baraxanar maka su a kotu idan har bai sake ta ba,

Sosai Ransa ya baci wato sawwam ya raina masu hankali,

Koda mami taji batun batayi mamaki ba dan taga take takensa yayi yawa akan tafiye tafiye Kuma ta taba kamasa yana waya da khairi bata damu ba saboda farincikinsa shine nata, ita da xasu sasanta kansu subar yaran da tafi kowa farinciki,

Sawwam na xaune a ďakinsa da laptop a hannunsa dad ya shigo, ba xato ba tsammani yaji saukar Mari a kuncinsa,

Ya dafe kuncin yana kallonsa cikin tsananin mamaki,

'ni xaka rainawa wayo kace ka saki yarinya alhali baka sake taba, me kake nufine?

Sawwam ya ajiye laptop ďin gefe ya tashi yana kallon mahaifinsa,

'Dad let's bygone be bygones, abinda ya riga ya wuce ya xama past dad, abinda ke tsakaninku iya kune , mu miye laifin mu anan dan Allah dad kuyi haquri kubarmu mana,

'Baka isa ba sai ka saketa a yau ko ranka yayi matuqar baci.......



    *Pherty xarah*

           &

    *Ummi shatu*


My wattpad Phertymerh1

No comments:

Post a Comment