Sunday 26 March 2017

RAMUWAR GAYYA.. 41

*RAMUWAR GAYYA...... 💘*

_Love story 50,50_

*Fertymerh Xarah*

          &

*Ummy Aysher*

41



Ya ďago yana kallon mahaifinsa, fuskarsa a kansa, Idanunsa taf da hawaye,

'please dad....
'don't pleased me sawwam...,
'Dad xn rubuta mata amma kabarni na kaimata da kaina,
'shikenan rubuta idan ka Kai da kanka xasu ga Baka damu ba, saki uku xaka mata dan baxaka qara aurenta ba,

Sawwam na hawaye ya duqufa yana rubutu, ido mami da dad suka sanya mashi cike da tausayinsa, ba ynda xasuyi dole raba auren shine mafita,

Yana gama rubutun ya dunqule takarda ya Sanya aljihunsa, ya ajiye biron qasa kana ya tashi yana share hawayen fuskarsa ya fice batare da ya qara waiwayensu ba,

Yana xuwa ďakin sa ya ciro wayarsa anan yaga missed calls na khairi, kamar baxai kirataba sai Kuma ya kirata lokacin tagama sallah tana Kan darduma, tana jin wayar ta fara qugi ta tashi da sauri saboda ringing tone ďin sa daban ne, toilet ta nufa kafin ta ďauki Wayar,

Lokaci ďaya suka saki ajiyar xuciya, ba Wanda yayi mgn acikinsu kowa najin xafin xuciyarsa,

Kusan minti biyar suna haka, batare da sun kashe Wayar ba kuďin na tfy a banxa sai tayi qarfin halin mgn,

'kayi shiru,
'kema kinyi shiru,
'da gaske xaka sakeni? sai ta fara hawaye sharrrrr hannunta har rawa yake gani take rabuwarta da sawwam tamkar rabuwa da rayuwartane,
'Ina hanya ynxu idan naxo xamuyi Mgnr, Kiyi haquri khairi I don't know what to do, tana jin haka ta fashe da kuka mai tsanani kenan ya sake ta,
'Ashe xaka iya rabuwa dani dan Allah ka maida auren baxan jure rashinka ba,
'ke kina tunani xn iya rayuwa ba kene, we have to br it, kidaina Wannan Kukan bana so,
'ai kasan baxaa barni tsayuwa dakai ba, Abba baxai Bari ba,
'kiyi dabarun nan naki na mata mana Kisan ynda xaki fito tunda da dare ne sai muje hotel ďin dana sauka muyi mgnr,
'hotel Kuma? Meyasa xamuje can,
'OK baxaki iya bina acan ba, ni ba mijinki bane ko kina tunanin xn cutar dake, jin ya ambaci miji xuciyarta nayi sanyi,
'tor kayi haquri sai kaxo,
'shikenan ki kula da kanki, kidaina kukan nothing can separate us,
'shikenan kaima ka Kula da kanka,
'to Kiyi murmushi naji mana, tayi murmushi kamar yana ganinta tana jin lokacin da ya sumbaci wayar kafin ya tsinke,

Yana gama wayar da Ita wanka ya shiga, a gurguje ya shirya ya ďauki Abinda xai ďauka ya fito, har lokacin suna xaune falo suna maimaita Mgnr,

'Ina xuwa haka cewar mami, ya dubesu fuskarsa a yatsine,
'xanje na basu takardar yar'su na haqura tunda bakwaso,

Dad ya taso cikin farinciki yaje ya rungumesa harda sumbatarsa,

'Allah shi maka albarka, sai kadawo Allah ya kiyaye I will surprise you sawwam,

Murmushi kawai sawwam yayi ya ďagawa mami hannu ya fice ita kanta tasan qarfin haline kawai yake bawai dan ya haqura ba,

Suna gama wayar ta fito ta nufi kitchen abinci ta diba taje falon Abba ta xauna tanaci,

Hakan da tayi Abba yaji daďi sosai a tunaninsa ta haqura da sawwam xata Karbi xabinsa,

Suna cikin haka ta fakaici idonsa ta dannan ringing tune na wayarta tana kuka ta ďauka bayan ta kashe kamar gaske,

'wow da gaske kikeyi, shikenan gani xuwa ynxu kice su siyama ma su jirani ynxu xnxo ta tsinke tana murmushi yaqe ta dubesa,

'Abba kabarni naje gidansu maryam yau xa'a kawo mata kayan aure Kuma qawayen mu na Skul sun xo mun dade bamu haďu ba tunda Muka gama secondary school,

'wace maryam kike mgn inaji an kawo mata kaya Tuntuni ai, sai da gabanta na faďi muryarta ta soma karkarwa,

'a'a Abba wannan kayan nagani ina so ne Wannan kuma kayan aure ne, lefe kenan, dan Allah Abba kabarni naje baxan jima ba,

Yayi shiru yana kallonta Kamar baxai amince ba sai Kuma ya gyada Kai alamar taje, Kada ya gane xumudin ta tunda sawwam bai isa isowa ba, sai ta xauna tana cin abincin tana Jan sa da hira kamar dama ba damuwa a tare da Ita,

Shi da kansa yaga batada alamar tashi yace wai baxakije bane,

'a'a xnje ina jiran mama ta shigo ne ingayamata karta nemeni bana nan,

'kije ki mata bayani daga can sai ki tafi,

Ta tashi ta fice.

sanda ta fito gida ana kiraye kirayen sallar magrib, ta shiga gidansu maryam ďin a gurguje tayi mata bayanin komai in case idan an aiko kiranta tasan yanda xata kareta,

Tana gama sallah kiransa ya shigo, ta ďauka yayi mata bayanin inda yake inda baxaa ganshi ba, ta fice da sauri,

Ta ďan yi tfy kafin ta isa inda yake, yana xaune sai kallonta yake ta hasken wata, wani qaton hijab ne ajikinta har qasa sai wani abu da take boyo ta cikin hijab Wanda baisan ko menene ba, ta buďe motar ta shiga, ba Wanda yayi mgn acikinsu ya tada motar ya fice,

Suna xuwa hotel yayi parking, Atare suka fito suka nufi ciki ďakin daya tara,

Xuciyarta har bugawa take dan dai bata iya yimasa gardama ne, Idanunsa akanta,

'meke cikin hijab ďin ki? ta yane hijab ďin kular abinci ce, ta dubesa,

'nasan baka ci abinci ba shiyasa na xoma da wannan kaci ko kaďan ne, yaja Numfashi da kyar kafin ya karbi abinci ya ajiye a qasa ya riqa hannunta suka shiga cikin ďakin bakin gado suka xauna yana faďin

'I need you not food, tayi rau rau da idanuwanta tana kallonsa sai taga ya ciro farar takarda a aljihunsa ya sanyamata a tafin hannayenta yana kallonta,

Lokaci ďaya xuciyarta na buga sai ga hawaye sharrrrr shikenan ya sake ta ,muryarta na rawa ta soma mgn,

'shikenan ka sake ni?
Ya girgixa kansa yana kallonta,
'idan kinje kibawa yaro ya kaiwa Abba inji sawwam amma Kada ki buďe,
'meyasa ta tambayeshi,
'ke meyasa kike tunanin xn iya rabuwa dake?
'saboda tursasawar iyayenmu,
'kenan bama son junan mune shiyasa har xamu yarda su rabamu, saboda naxo nagankine fa nayi wa dad dabarar xuwa garinnan amma ni bana son Wannan Kukan da kike, yasa yatsun hannuwansa yana goge hawayen fuskarta,

Bata ankaraba taji bakinsa Akan labbanta, ya soma kissing ďinta sosai, sai ta saduda duk da xuciyarta na tsananin bugawa amma batajin xata iya hanasa cos tana sonsa tanajin Abinda yake ji a xuciyarsa,

Hannuwanta tasa ta rungumeshi idanunta a lumshe, a hankali ya buďe nashi idanuwa yana kallonta yana jin sonta ta ko ina baya jin akwai abinda xai rabashi da Ita,

Sun ďauki kusan minti goma a hakan abin na neman canxa salo, hijab ďin jikinta ya cire sai tayi qoqarin sai ta hankalinta bata so wani abu ya faru tsakaninsu a ynxu, bata ankaraba sai ji tayi ya xuge zip ďin rigarta, ta soma kiciniyar kwace jikinta,

'please khairi, ta maida zip ďin rigar ta rufe, ta saqalo hannuwanta ta wuyansa, ta girgixa kanta,

'Kefa matatace you know it,
'kayi haquri har adaidaita, ya sauke numfashi haďe da janye hannunta akansa ya juya fuskarsa gefe alamar yayi fushi,

'am sorry please kaima kasan is not the right place Kuma ma.... sai Kuma tayi shiru,

'kayi haquri please,
'shikenan tashi na maidaki gida,
'abincin fa,
'baxan ci ba,
'Dan Allah kayi haquri, taje ta ďauko abincin ta dawo gabansa ta tsugunna, da rarrashi da komai tasamu yaci Kuma sosai rabonsa da abincin kirki tun jiya sai ga sawwam na xuba shagwaba Abinda ko mami baya yiwa lallai ya yarda mata ma rahama ne, yaji ya qara son ta ba abinda xai rabasu komai runtsi komai wahala,

Sun jima suna hira kamar basu da damuwa a ransu kafin ya ďauketa ya maidata gida, nan ma sai da yayi mata kiss,

'karki manta Mgnr mu gobe ki tambayi iyayenki su gayamaki dalilin dayasa suke son raba auren mu nima I will asked them tomorrow sai muji dalilinsu, tayi murmushi

'shikenan I will miss you,
'miss you more,

Kamar kada su rabu yaja motar ya koma hotel,

Koda taje gida ba'a gane ba, kuma tana yaro yakai takardar acewar inji wani bata buďa taga Komenene ba,

Ranar sunyi barcin daďi cike da kewar juna sai faman juye juye suke a gadonsu sun qagu safiya ta waye,

Washe gari sawwam yabar garin, yayi Sa'a koda yake gida ya sami dad na gidan,

Ya Shaida masu yabata takarda,

Dad ya soma sa masa albarka,

'amma dad meyasa kuka rabamu, meke tsakaninku?

'a'a ba ruwanka da wannan,
'mami tace ya kamata a gayamasa dalili tunda har an rabasu,

'dad yayi shiru kafin ya gyara xamansa yana kallonsa.

Khairi Kuwa Washe gari Faďan mahaifinta ya tada ta barci a tare suka fito da mahaifiyarta suka nufesa harda yayyunta ma,

'yaronnan ya rainamin hankali ya sakarmin ya shine xai rubutomin wannan abin,

Mama ta karba tana karantawa kafin ta miqawa khairi,

     _I can't divorce my wife, I truly loves her, Dan Allah Abba kayi haquri kabarni da matata fadanku karya xo kanmu._

'dole ya sakarmin yarinya kona kaishi ga hukuma,

'Tace Abba Dan Allah ka gayamin dalilin dayasa kakeson rabamu, Abba dan Allah ka gayamin abinda kuke boyewa,

'gsky ne Abba ya kamata musani ansanyamu a duhu cewar Mustapha yayan khairi,

Abba yayi shiru yana kallonsu kafin ya nemi guri ya xauna.



*pherty xarah*

       &

*ummi shatu*


My wattpad Phertymerh1

No comments:

Post a Comment